Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

muka samu suna jiran mu a airport din.
Yawancin masu taron mu yan zuwa taya shi murnan samun wanna babban nasara ne na shugabancin wanna babban kafanin da zai jagorantan a kasan mu Nigeria.
Mun sauko daga matakalan jirgin cikin shiga irin ta alfarma dana saba yi a yanzu don fitar kunya.
Idanuwan mutane Cass akan mu wanda nai mamakin ganin wanna taron da akai muna a gurin.
Yana sabe da dan shi a kafadan shi yayin da nake biye a bayan shi Ina saukowa a hankali daga matakalan jirgin.
Nan aka shiga watso muna wasu flowers masu kyau da kamshi ana ta muna sannu da zuwa.
Acikin taron nan haka Maryam ta kutso kai naji ta rungumay ni ta baya take muka rungumay junan mu a cikin murna da saukin ganin junan mu.
Dan wani lokaci kadan ta sake ni tare da dagowa ta Dan kalle ni tana cewa wai Fatima kece haka ko dai mafalki nakeyi.
Nace kai haba anty na bagani a gaban ki ba tace kin koga yadda gaba daya Kika koma kin zama wata irin big madam dake Fatima.
Murmushi nayi na Kara jawo ta nai hugging din ta tare da rada mata cewa aikin yayan ki ne haka yar uwa.
Muryan shine a cikin taro yana fadin ke uwar surutu agajiye take please ki barta ta huta tukun kin wani tsare ta da gulman ki.
Nace haba Yaya baka ko tausayin mu yaushe rabon mu da ganin junan mu ne wai?
Ya jawo hannuna tare da watsa mata harara yake cewa kwayi gulman a gida idan kin hadu a can.
Gaba daya da masu taron mu muka wuce zuwa gidan mu sai dai nai matukar mamaki da ganin an canza hanyan da na sani zuwa gidan namu.
Inda naga an shiga wani irin mamakeken gida mai wani irin katon get ginin gidan ba sai na tsaya fadin shi ba don har da bene a gidan.
Nan ma yan uwane Mata dam a gidan a hankali ya rada min cewa welcome to our new house queen.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , ,


IDAN KIN BIYA KADA KI TURAWA WANDA BAI BIYA BA IDAN KINYI HAKA MUN BARKI GA ALLAH.


Alheri sosai ya tanadarwa su Mama da Umma da mummy har motar shiga sai da ya canza masu tare da gyara masu dakunan su tsab.
Wanan ya zamo karo na farko da sukaji dadi a ransu abinda taya sadauki yake masu na alheri wanda hassada baya bari suga irin alherin da yake masu abaya.
Yanzun ko abu yakai babu gare su duk yadda mutum yai masu alheri komai kankantan shi suna godiya sosai.
Don yanzu wanda suke samu gurin shi watau baba shima ta kanshi yake yi baida komai duk diyan su sun wawashe mai shago baida wani abin hannun shi kuma inba gonan da sadauki ya saya mai ba farkon fitan shi wasan kwallo da yafara zuwa.
A takure suke komai da suka fi karfi a baya yana basu sha, awa yanzu shi yasa suke ganin wanan kyautan na baya yazo masu kamar kyauta na farko da ya taba masu.
Har daki mama Asiya ta samu mama tana mata godiya wanda mama ma a lokacin bata san da wanan alherin ba inba yanzu da mama Asiya tashigo mata da zancen ba.
Mama tace ikon Allah wallahi yaya banda labarin wanan zancen yanzun ma nake jin shi a gurin ki.
Godiya dai ta karayiwa maji tare da fatan alheri tana ta saka albarka wanda maji ke gani yau kamar a mafalki.
Mama Asiya ce sakawa dan ta albarka haka akan alherin da yai mata don jin dadin zuciyar ta.
Mama Asiya tana fita har tsakar gida tana godiya Nafisa ta gamu da ita dakin su tashiga gurin mahaifiyarta tana cewa kina nan zaune halan may ya faru naga mama tana ta godiya a waje tafito dakin maji.
Umma tace nasan taje godiya ne godiya akan may kuma Umma ?
Tace yanzu Sagir ya samay mu da kyautan alherin da yayan ku dan kwallo ya aiko muna dashi mu uku motace ya sake muna da kujerun daki da gadaje sai kudi wai mu saka mai a mota da kayan abinci.
Nafisa tace tirkasa amma ko Allah ya saka mai da alheri wallahi to umma shine kike zaune ke baki zuwa kiy godiya?
Koda yake yadda naji kina magana kamar har yanzu kin saura hassadan abinda yafi karfin ki fada.
Dadai kin sakawa ranki ruwan sayi kibi kici arziki dayafi maki wanan hassadan da kukeyi shekara da shekaru yaki kare.
Ga yar uwar munafuncinki ta sulala taje tayi godiya tabarki nan kina hassada ga banza.
Kallon takaici taiwa yar tata da suke dauka a matsayin mara hankali ga maganan ta da dabiun ta amma kuma gaskiya ai Nafisa ta fada mata don tasan mama Asiya yanzu tana zare jikin ta tana hurda da al, amarin maji da yayanta.
Nafisa kan dakin ta tashige takwanta abinta yanzun ta daina sha sai dai bata bar harkan bazan ta ba da ta saba.
Sagir ya shigo ya samu umma zaune tayi tagumi ganin shi ya dan sata sake jikin ta tana mashi tayin abinci.
Yace Umma na fada maki yanzu a gidan yaya sadauki muke karyawa ni da Abdul komai dare sai Fatima ta kira mu muzo muci abincin mu yana aje haka ma dasafe.
Umma taji wani iri a ranta ba dadi tasan cewa ko ba komai anyi hadin zumunta a gurin kafin takai karshen tunanen ta taji muryan shi yana cewa.
Wai ko Umma kin san wani abu fatima fa tai muna kanfen gurin yaya ga sabon gurin aikin da za, a bude a abuja nasu.
Shi da kanshi yaya sadauki din ke fada muna cewa wai yar uwar mu ta nuna son kai ta matsa ita sai dai muma a nema muna babban gurbi a can mu kama aiki dasu ko kuma wanda ke nan sokoto.
Umma wallahi yadda suke gwada muna halarci irin haka ni abin ma har kunya yake bani yadda a baya mukai ta gwada masu kiyayya a filin Allah .
Amma sai gashi yanzu da ya samu mune na farko samun alherin shi harda mota fa yace zai saya muna wallahi.
Bamu kadai ba har dasu yaya Imiran naji ana magana a kansu suma za, a basu appointment a gurin.
Tace kai amma ko da ya kyauta muna wallahi don zaman banzan nan na Imiran ya fara ista wallahi.
Umma yanzun dai jekiyi naki godiyan kafin wani lokaci kuma kin san irin wanan alherin na bazata shi ake kira da kyautan dan aljanna.
Kyantan da zaizowa bawa a lokacin da bawa yake a bukace da wani abu a rayuwan shi dubi fa wa yan nan kujerun yadda suka koma kamar tsunma ni har kunyan nake jin azo agansu a dakin nan haka wallahi.
Bai bar dakin ba sai da yaga Umma ta mike yaga ta nufi dakin maji hankalin shi ya kwanta.
Don bai zai yuyuba ana masu alheri irin haka amma ace su har yanzu basu daina hassadan su ba da sukeyi.

****** ********* ******
Allah mai iko a yanzu ankai duk inda sadauki ya sa kafan shi yana tare da manyan body guard masu tsaron lafiyan shi dana iyalan shi wanda goverment da kansu suka bashi su don tsaron lafiyan shi.
Saboda gashi karamin matashi amma yana daya daga cikin manya masu shigo da manyan ababen amfani daga kasashen duniya.
Haka yasa ya zamo abin kula sosai a gurin manya na kasa da suke fada aji.
Saboda ya zamo daya daga cikin yan kasa masu kishin kasan su don sun cigaban matasa.
Gashi akan kamfanin da suke son kafawa har guda biyu na mai dana manyan jiragen ruwa da zasu dinga shigo da kaya daga waje.
Ga manyan injima na haska wutan lantarki da za, a shigo dasu kasa don amfanin kamfanonin da za, a gina nan n
Nageria.
Ban fita sosai zuwa yanzu don cikina da yai matukar girma don ko a wanan ma likitoci sun kara bani bedrest sai dai ba kaman wancan na baya ba danayi na Amir din.
Ina kwance saman dogon kujera a falo na dan mike kafafuna na da sukai min nauyi.
Yashigo gidan a gajiye dashi su Sagir suna take mai baya shi da Abdul dauke da dan briefcase din takardun shi da laptop dinshi a cikin case din.
Ya zauna yana cewa kai nagaji da yawa wallahi nazaci a nan idan na dawo ko zan huta amma gashi duk ba wani hutu da mutum ya samu tare dashi.
Na dan lumshe idona tare da kokarin mikewa zaune don na karbi case din zuwa dakin shi.
Yace da sauri No No kwanta abinki ki huta barshi idan zan shiga zan shiga dashi ai.
Bayan ya karasa kaiwa zaune ne yake cewa duk rashin samun hutu ya saka har kirjina yana min ciwo wallahi.
Da sauri na dago ina kallon shi nace amma gaskiya tunda ka fara jin haka ya kamata ka samu hutu ka zauna a gida koda na kwana biyu da zaifi ma.
Yace na kwana daya dai Fatima kwana biyu yai min yawa ga mu da tulin aiki mai yawa a gaban mu.
Idan ba naga angama gina muna komai ba hankalina bazai taba kwanciya bane ai kinga dukiyar mutane ne nauyin shi ya hau kaina dole na kula masu da abinsu ko?
Nafisa ce tashigo gidan da alamun damuwa a fuskanta nan muka zauna da ita ana hira suko abinci suka wuce ci a dining.
Yana gamawa ya shiga ciki ya dan jima bai sauko ba yana sama koda zai fito ya sauya kaya jikin shi a lokacin.
Tun bai kai zaune ba ya soma magana yana cewa gaskya kauna ya kamata ace kifito da miji hakana kiyi aure na hada ku da Amira dama yan sa, a daya kuke kinga kowa sai ya huta abar Rukaiya har su karasa nasu karatun.
Cikin wani langabe kai tace ni yaya wama zai aure ni kawai ni na fitar ma da rai ga wani aure can
Da sauri nace haba anty ce astangafurullahi mana yaya zaki magana kamar ba musulma ba dake.
Tace to madam wakike gabin zai aureni a haka yadda nake duk masu zuwa gurina ba da sunan aure suke zuwa min ba sai dai da tasu bukata kawai.
Gaba dayan mu tausayi tabamu ga maganan ta don mun san cewa gaskiya ta fada maganan ta.
Amma kuma ai abin Allah ba a yanke kauna a gare shi nace anty gaskiya yaya ne ki natsu ki rage wasu halaiyar ki ko Allah zai tausaya maki.
Don kinga ai Allah miskaraziratin ne ba abinda ya gagari ubangiji sai kinyi mamakin irin mijin da Allah zai kawo maki idan kin natsu.
Kafin tabani amsa wayan ta yai kara jin sunan wace ta kira da Raye yasa na gane da Raiha take waya a lokacin.
Tambayan ta tayi tana ina tabata amsa da cewa gani nan gidan su madam ina shan sanyin A C.
Tabata amsa da gata nan tafe tana gamawa yake ce mata kinga ni maganan ki bawai ya karbu bane gareni fa kiyi tunane a kai ki gyara halaiyar ki Nafisa .
Mace fa dan guntun lokaci ke gareta tun anayi daku watarana masu neman naku gudu za, suyi su koma ga
wasu yan matasan
Ta amsa a marairaice da tau naji yaya insha Allahu zanyi kamar yadda kace amma zaka dinka min hijjabbai na fara sakawa ko?
Murmushi yayi yace gatanan yana nufin ni zata dinka maki ko guda nawa kike so kaunata.
Nidai kawai ki natsu ki daina wanan halin please.
Shigowan Raiha ne yasa muka daina zancen suka gaisa da shi ya mike zuwa babban falon shi na waje da yake taron baki a cikin sa yabar mu nan zaune a na cikin gida da waya a hannun shi yanayi.
Nan muka fara hira dash nake tambayan Nuriya suke ce min wai tabi wani saurayinta dan Ibo sun tafi lagos tare.
Banji dadi ba na kasa boye bacin raina nake cewa haba dai haba ace kuma mutum yana hurda da harda wanda ba musulmi ba kuma ai abin yayi muni gaskiya.
Raiha tace madam kawai dai Allah ya gafarta muna zamuce don dai gaskiya nima yanzu da hankali yafara zo min na gane hakan ba daidai bane.
Ni yanzu fatana kawai Allah ya kawo min miji wanda zai soni tsakani da Allah wallahi ko yaya yake zan zauna dashi na natsu bakiga yadda al, amarina har yasakawa iyayyena cutan hawan jini ba.
Tace to mazan ne yanzun sai a hankali wallahi na rasa wanda zaizo ma da tsigar so na gaskiya bada bukata ba.
Nafisa tace maganan da muka gama ke nan da yayana kafin ki shigo abinda na fada mai ke nan kema yanzu sai gashi kinzo dashi.
Tace wallahi muna son auren bawai bamu so bane to amma wazaka aura shine matsalan.
Istigifar bai bar komai ba ku koma ga Allah kwana biyu kuga ikon Allah wallahi bana jin dadin irin wanan rayuwan da kukeyi yanzu ya kamata ace kunyi wa kan ku fadan hakan.
Shi yasa nake son ki madam wallahi kece kawai zan iya cewa a yanzu kina tsayawa ki nusar da mutum hanyan alheri bayan kowa ido yakawo ya saka muna.
Ana jiran da garin Allah ya waye kai wani abin asha asakaka ga faifai a tallata ka.
Yaya sadauki ne yashigo yana ce min sai ki shirya don muna da bakin da zasu duba gurin da za, a gina kamfanin shimkafa a garin nan
Gashi sunce min ba, a hotel zasu sauka ba anan gidan zasuyi masauki don haka sai ki samo wanda zasu yi aikin abinci idan kuma bayarwa zakiyi ai masu duka daya.
Kafin ma ya karasa zancen shi sai cewa Raiha tayi bagamu ba yaya aikin may mukeyi dabaza mu yi ba mu.
Baiyi magana ba don na lura hankalinshi bai kwanta da al, amarin Raiha din ba wanda shine bai fahince ta ba sauki kaine da ita sosai.
Amma shi yana ganin sune suke jefa yar uwarshi a cikin wanan mumunan harkan da sukeyi tare.
Bai san tafi su zama shedaniya ba don ita ta hure fitillar ta sosai ma fiye dasu.
Mun jima dasu muna tatauna abinda ya dace muyi da wanda zamu saya na bukatun mu.
Har sai bayan sallah magariba suka tafi mukai sallah suna cewa idan an shirya na kirasu.
Bayan yashigo gidane yake fada akan cewa may zaisa na yarje ma wa yan nan mashiririta suyi mai aikin abincin bakin shi yaushe ma suka zauna balle su san yadda ake girki su.
Nace haba yaya sai kace ba mata ba su gani kuma ga iyya a gurin ai zamu taimaka masu da wani abin.
Yace da sauri No no kada ki soma cewa zakiyi aikin komai kin dai san yadda condition din ki yake please kada ki fara ki taba komai idan ma bazasu iya ba sai a kira wasu suyi final nace ballema insha Allahu zasu iya duk abinda suka lissafo zasuyi din.
Bai kara magana ba haka muka bar zancen don yaga na aminta dasu sosai yasa ya kyale badon yaso ba.
Izuwa yanzu alherin da sadauki yaiwa iyayyena bazan iya lisfoshi ba don muna waje sun tafi sun sauke farali ga gyaran gida da abin sana, a da ya sayawa kowan su a sanadiya na iyayyena da yan uwana sun fita a cikin talauci yanzu wanda hakkurina da biyayyana ne yajawo muna wanan alherin haka.
H
Yan uwa dama yan garin mu sukan zo neman alheri a gurina wanda nakan yi masu shi gwargwadon halina.
Lokacin zuwan bakin shi yayi bayan sati ya zagayo yabani kudi masu yawa akan abubuwan bukatan su.
Ban masu kyata ba na ba kudi fiye da wanda za, a kashe sosai suma su karu daga ciki suka shiga kasuwa saywn abubuwan bukata duk da wasu muna dasu a gida.
Ranan har anty maryam da Rukaiya sai da suka zo da mummy tare akai aikin komai dasu na fita kunyan baki yadda ya dace sai da aka hada abinci kusan kala goma sha biyu nau,i daban daban suka kara gyara katon falon muna na baki an saka kamshi da komai a falon yadda ya dace ayi.
Bakin basu shigo gida ba sai misalin karfe uku na rana dirin motocin da mukajine yasa muka gane cewa gidan mu ya dauki manyan baki yau don har dasu jiya da alaman akwa wasu manyan kusa a cikin su ke nan.
Nan aka shiga fito da kayan ci dasha bayan wanda aka kai masu da farko wa drivobin su.
Gida ya rude da hayaniya sai kai da komo su Anty Nafisa sukeyi a gurin ana yaba aikin da sukayi.
Allah da ikon shi a wanan sanadin Allah ya hada su da masu son su a gurin sukai wa yayan su magana kan ya basu kannen shi din nan yace yabasu.
Wasa wasa magana ya zama babba don ita Nafisa ta hadu da wani ustazune manager din wani babban company dake garin Abuja.
Ita ko Raiha wani sojane babba wanda gwaunati ta turo shi as a security guard na kasa ya kyasa mata.
Amira da mama tace tazo ta taya mu aiki tace ita ba yar aikin kowa bane ba inda zata tafi nan mama ta ganta ta kyaleta.
Amma daga baya da taji sun ba da tukwaicin dubu dari biyar wa masu aiki sai kuma ta shiga fada tana ganin laifina
Wai dama ni yar bakin cikine shiyasa na gaiyato yan iska su cika min gida shiyasa ita bata tafi ba.
Karshe kuma sai ga zancen auren Nafisa da Raiha da taji Allah ya hadasu da wasu manya sai dai ba yara bane su.
Nan kuma ta shiga zage zage kamar mahaukaciya wai ta yarda ni yar bakin cikine ta karshe sosai don ban son ta da arziki nafi bukatan komai sai a gani a gurina kawai.

****** ********* ******
Bukin anty Amira ya taso sosai ba kama hannun yaro don haka muke ta zirga zirga ba hutu don mu ke gudanar da komai akan bukin duk da gwatsale ni da takeyi tana nuna bata bukatan saka hannuna acikin al, amarinta sam.
Hakan bai sa na daina duk wani abinda nake da niyar yi ba don ba don itace nakeyi ba dama don Allah nakeyi da mijina da kuma mahaifan su.
Bata san ina da rana a gare ta ba sai da masu zuwa ganin dakin da za, a saka mata kaya sukaje suka dawo da labari mara dadi don ashe a family house za, a aje ta.
Kuma ga dakunan ba wasu dakuna bane maigirma a jere suke ita da uwargidan ta wace yar uwace ga mutumin da zata aura.
Da labarin yazo ba karamin tayar da hankalin ta tayi ba sosai nan ta tuburewa mutane akan Ibrahim ya cuce ta don cewa yayi gida zai kama mata haya don may yazu zaice a gidan su zai aje ta.
Sosai ta tayar da hankalinta akan bazatayi auren ba ta fasa hankalin mama yai matukar tashi gashi an gama komai akan shirin buki ga yan uwa na nesa har sun fara hallara a gurin bukin.
Kuka wiwi takeyi akan ita kan wallahi ta fasa sai dai akai wata ba ita ba don bazata wanan gidan da ake bada labarin shi ba babu tsari.
Mama kuma da yan uwa sun kafe kan lalai sai anyi auren nan sai dai ta mutu idan an kaita don bazata basu kunya ba.
Ganin matsalan yai yawa ga tashin hankali ga fuskan kowa idan ka duba ya sa na tashi daga inda nake zaune lokacin cikina yai girma sosai wata bakwai saura kwana goma nake.
Dakin da take na shiga na samay ta ta kifa kai ga filo ita kadai a cikin dakin tayi buji buji da ita kanta duk a hargitse dashi.
Zama nayi bakin gadon don bazan iya tsayi tsaye ba a yadda nake lokacin don karfi hali kawai nakeyi da kaina.
Duk da taji anshigo dakin bai sa ta dago daga yadda take a kwance ba cikin yanayin tashin hankali.
Cikin yar siriryar murya nace Anty Amira ki tashi muyi magana musan mafita akan wanan al, amarin don kuka ba shine mafita yanzu tunda kinga mama ta kafe akan sai anyi auren nan ba fashi.
Jin muryana yasa ta dago kai a cikin fushi tace Bintu for god sake ki barni naji da abinda ya damay ni please ke har wani taimako zaki iya yi min ?
Wani matsayi ke gare ki da har zaki dauka zaki iya taimaka min dashi a matsayinki ko don kawai kinga kina auren dan uwana kina juya shi yadda kike so to ni ba shi bane ko maji ki sani.
Murmushi nayi kawai nasan ban taba fari a gurin ta amma ni don Allah kawai nai niyar taimaka mata.
Nace a fili ba matsala anty ni don Allah nazo gurin ki don mu san mafita kawai idan kina da lokaci ki tashi muyi magana dake mu san abinyi tun ba, a kai maki kayan ki ba a wancan gidan yawan.
Wani kallo ta watso min kafin tace ina sauraren ki nace nagode naci gaba da fadin nasan bawai baki son Ibrahim bane a yadda nasan kun dade tare dashi kuna soyayya.
Kawai dai wanan matsalace ta gurin zama yasaki bacin rai irin haka sai nake gani idan yace zai canza maki gurin zama duk wanan matsalan zai iya wuce a tsakanin ku tunda soyayya ce ta hada ku ba kiyayya ba.
May kike fadi mutumin da ya kafe akan shi baida kudin da zai karasa ginan shi kuma baida wanda zai iya kama min hayan irin gidan da nake so a yanzu.
Nace insha Allahu anty idan don gurin zamane na rokeki Allah ki kwantar da hankalinki ayi wanan bukin cikin farinciki.
Yadda kowa yazo lafiya don farin ciki ya koma gida da farinciki a ranshi anty baku gaji yin kunya ba a rayuwan ku balle kuji kunya don Allah ni dai yanzu abinda nake so shine ki kwantar da hankalinki ki koma kamar babu abinda ya faru a baya don marasa da suyi kunya don yanzu kinga ido aka sakawa mama aga yaya zata kaya ana farin ciki zaki shiga gida mai kuntatawa.
Wani kallone takara watso min tare da cewa wanan shine dama maganan da zaki fada min din.
Nace eh anty don Allah tunda kuna son juna da Ibrahim kiyi hakkuri ki daure ayi wanan abin cikin rufin asiri insha Allahu bazaki zauna a wanan gidan ba.
Tsuki taja tare da marya da kanta a saman filo tace na zaci wani shawaran arziki kikazo min dashi har na bata lokacina a kanki haka.
Na dade a zaune ba tare da tajuyo gare ni ba ga wayan ta dake ta verviration taki dagawa.
Wanda nasan ba kowane ke kiranta ba a lokacin sai angwan ta wanda yake a cikin tashin hankalin kan cewan da tayi bazatayi auren ba ta fasa.


Please Login or Register in order to submit comment