Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

sunce bayan sati biyu ya dawo a kara duba lafiyan shi da aikin jikin shi.
A zatona zasu wuce gida amma sai Baba yace ba zai bari su koma ba ya tsaya gari har sati biyun ya cika gidan gwagona aka gyara mashi nan suka zauna da mama tabawa.
Komai sadauki yana masu duk da baya gari amma bashar abokin shi yana zuwa kai da kai yana duba lafiyan su.
Hakan yaiwa Maji dadi sosai da yadawo ranan ina jin tana mashi godiya sai cewa yayi haba Maji ai taimako kamar yiwa kaine abinda ka taimaki wani dashi shine rabonka.
Ban mata da yadda yarinyar nan itama ta taimaka maki ba da kike asibiti wanan ne kawai zamuyi mata mu saka mata da abinda tai muna muma.
Allah yai maka albarka, sadauki halinka na alheri ya bika duk inda kake Allah ubangiji yasa kafi haka a rayuwan ka.
Yaji dadin wanan adduan sosai don ya kasa boye farinciki sai cewa yayi Maji ina jin dadin adduan ki akaina ko yaushe tace ba dole na ba baba na .
Kaine farin cikin rayuwan mu ni da yan uwanka dama,wasu al,umma dake ci daga gareka.
Yace mata zai fita akwai inda yake son zuwa don akwai wani da suke son hada business dashi na mai.
Tace to Allah yaba da sa,a har yakai kofa zai fita take ce mai ai na manta za,afa kawo kayan lefen Fatima nan da kwana uku insha Allahu.
Don haka nake son kudi don nai shirye shiryen taron su.
Yace maji wanan ai maganan ku ne, ni dai bana son ki zauna ba kudi a hannun ki bani jin dadin irin haka.
Idan na fita zan ciro maki kudi, sai na kawo maki idan bai isa ba sai akara maku.
Har ya juya sai yake cewa amma maji wai sauri may wanan yarinyar takeyi, hakane da take son aure.
Wani kallo ta,watso mashi, tace shi aure ga yarinyar da takai sha biyar zuwa sama har wani abu ne yanzu.
Fita yayi kawai bai tsaya ba don yasan fadan zai kawo kan shi idan har baiyi hankali ba.
Ina wanki duk ina jin hiran su nace tunda kowa irin kane da bai tsoron Allah zauna har mutuwa ta riske ka ahaka.
Kamar yadda Kabir yace ranan laraba za,a kawo kayan lefena a gurin mama hakan ne kuwa,don ranan mama da,su Amirah basu huta ba sai aikin abincin masu kawo kaya sukeyi.
Maji ta,gaiyaci abokan arzikin ta daga ko ina a cikin gari kamar yadda akeyi.
Karfe hudu na yamma gida ya cika da abokan arzikin mama masu zuwa mata karan karban kayan lefen diyar ta.
Nayi kwalliya cikin wani swiss lace kore anyi min dinkin riga da siket Amira ta daura min dan kwali gashina ya zubo daga baya.
Sai dai ban fito ba ina dakin mu zaune don kunya daga cikin kawayen mama wasu ke fadin basu gane ni ba nan mama ta,tura Maryam data kirani nazo na gaida mutanen ta.
Maryam ta shigo cikin dakin ta samayni zaune nayi shiru tace Amarsu ta ango may ye haka kuma ranan farinciki kin zauna kinyi wani tagumi dake.
Nace kai anty maryam ni wallahi ina tunanen wanan kokarin na mamana ne kawai .
Tace ke taso su hajiya Larai na son ganin ki wai sunce basu san ki ba shine maji tace na kiraki ku gaisa.
Nai wani iri nace walkahi Anty maryam kunya nakw ji tajawo min gyale na dake gefe na fari ta dora min akai amma can bayan tuntun kaina ya tsaya.
Tare muka fito fallon dasu duk a kunyace nake idona yana kasa sai da nakai kasa na tsugun na a tsakiyan falon nace masu mama ina wunin ku?
Tubarkallah masha Allahu suke fadi hajiya maijidda wanan yar taki haka kamar ita tai kan ta dayar matan tace may ma sunan ta maryam na dariya na yadda duk na tsorace tace masu Fatima Bintu.
Sukace diyar ma,aikin Allah sai lokacin na daga kai na dan kalle su sake rudewa nayi da ganin su manyan mata ne hamshakai ban taba sanin mama tana da kawaye haka ba don banga tafaye fita,ba ita.
Naje gurin matar na zauna tace Allah yasa angon naki shima haka yake kamar ki zama nayi daidai kafar matan tace kaji arziki ba yarinyar da kunyanta yaushe za,a samu yara masu kunya haka wanan nan zamani aida yanzu muna nan dasu suna rawan kai.
Matar ta dan duko tana ce min kina karatu kuwa na ce eh tace a ina ?
Nace a hankali nan state university nake two hundred level.
Masha Allahu duk a kunyace nake zaune cikin su sai hiran duniya sukeyi.
Dayar matar take ce min jeki kin ji diyata don naga kinki sakin jikin ki namike cikin natsuwa nabar falon .
Ban karasa shiga ba naji wata na cewa kai amma hjy maijidda kin ban mamaki yaushe zaki bari wanan daman ya,wuce ki haka, aida kawai kin kamawa danki wanan zukekiyar yarinyar haka ga yarinya da kunya da sanin ya kamata.
Ban fi minti goma ba da shiga masu kawo kaya,suka iso da gudan su yan uwan shi ne mata su shidda suka shigo da,akwatina set biyu masu kyau da daukan ido.
Nan nake jin an shiga guda da yabon kaya basu dade ba suka ce zasu tafi aka bisu da kayan da aka hada masu drinks, kajin da aka soya, da su snacks.
Sai kudi tukwici dubu hamsin har mota aka kai masu nan aka dawo falo akabaje aka,shiga bude kayan ana yabawa.
Naji wata na fadin inji bata da ciwon kai dai ko da sauri maryam tace har biyu kuwa.
Kai tana da kishiya fa a,a,a yarinya kinko debo da zafi kamar wanan yar yarinyar ce za,ta shiga cikin mata biyu.
To Allah ya tsare ya kare ai sai ku tashi tsaye do dai kema gaki kina fama danaki a gida.
Zuwa yamma kowa ya watse gidan aka barmu iyamu hajiya kubura ce zance naji muryanta lokacin da aka kawo kayan har aka tafi tana falon tana yaba kyaun kayan .
Sai dare muka samu kan mu sai kuma a lokacin nafito ban kai minti biyar da zama ba yaya sadauki yashigo falon.
Ina cikin kwalliya na ban cire ba idon shi suka kai ga,akwatinan yazauna yana cewa har bakin naku zun tafi ke nan.
Amira tace su wuce sunzo wallahi kagama kayan da,suka kawo muna can.
Maryann tace kai yaya,wallahi kabir yai kokari sosai wallahi yana nuna yana matukar son Bintu ji wanan uban kaya haka haddadu dasu bari na,dauko maka kagani sai ta mike zuwa gurin kayan.
Yace ke ina wasa da kene ni mace ce da zan tsaya kallon wasu tarkacen banza can.
Da sauri nadago kai ina kallon shi don jin abinda yace, ya watso min harara tare da jan tsuki yace karamar yarinya sai shegen son aure haka.
Wanan tarkace kikewa rawan kan aure jekiyi ke kika sani indai wanan tsohon ne dana ga kina rawan kai akan shi.
Nace a hankali adaibar min abina ko yafi duniya tsufa ina son shi hakana .
Baki da kunya wallahi nike fadawa hakan na juya ina magana kasa kasa nikadai inda nake zaune.
Wai sadauki ban san wanan abinba yanzu shi Kabir din ne tsoho kuma koma dai may ye haka take son abinta sai kaje can kaji dashi.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,


IDAN KIN TURAWA WA WANDA BAI BIYA BA BA MU YAFE MAKI BA ALLAH YA ISAR MUNA AKAN KI,,,,,

Maji ne zaune falon Alhaji dake cin abincin da takawo mashi, abincin yai mashi dadi sosai kullun yana son cin girkin da maji da yaranta ke hada mashi idan itace da girki.
Tv daga bangon falon da ka shigo dashi zakai arba ya na aiki yakai tashan CNN yana kallon news da akeyi.
Ahmad ne ya shigo falon da wani takarda a hannun shi, yana cewa uban ga takardun an karbo sai ka saka hannu a mayar masu gobe.
Imirana kun dawo yaya kasuwan amma kaman baiji gaisuwan da maji take mashi ba alokacin.
Saida ya gama bin takardan ya dago yana fadin, bakaji ana maka sannu ne ka kyale ta.
Ya dan juya inda maji ke zaune ya watsa mata wani kallo mai kama da harara.
Duk a idon mahaifin shi Alhaji yace yanzu kai da girman ka kana namiji kake shiga harka irin ta mata.
Imirah yace may kuma nayi baba gaisuwa ce taimin kuma na ansa a rai na ai.
Yace to lalai ashe da sauran ka kuma ka bani kunya kai da yau idan na kwanta dama, kaine zaka zama min jigo a gidana.
Ashe hasashen na ba haka bane yanzu nasan ko bani Umar zai iya hada ku ya rike min don shi banga ya banbanta wata daga cikin gidan nan ba.
Ni dama baba ai nasan baka daukan mu yanzu da wani matsayi tunda mu bamu ,,,,
Cikin tsawa Alhaji yace ashe rashin kunyan naka Imirah har yakai haka ban sani ba ?
Yau ni kake kallo ina fadu kana fadi haka kai tsaye babu jin kunya.
Imrah baiyi magana ba ya juya yafita daga dakin rai a bace sai dakin uwar shi.
Maji tace Alhaji da baka biye mashi ba ai, don ni wanan halin na riga na saba dashi ko a gidan nan .
Babu wani yaron gidan nan dake kallona da daraja a matsayin uwa sai diyan hjy Kubura kawai.
Tace don haka don Allah ka daina fadan abinda da duk kaga sunyi min a gaban ka.
Don bazasu daina ba saboda kullun huduban shedan ake masu a kaina.
To Allah ya,sawaka amma gaskiya ba zan lamunci irin haka ba a gidana.
Sai muryan Umma sukaji tana fadin anki agaishe ki din ke waye da sai angaisheki.
Shi da ya mayar dake wata tsiya sai ya zauna yai tayi amma babu mai tirsasawa diya na akan wata mace can marasa asali da ta cika muna gida da diyan tsiya diyan taulali da suka zama ma mutane alkakan kafa.
Maji dai ta fito daga dakin maigidan da kayan abincin da,ta kwaso daga gurin shi.
Muna fuka kawai tun shigowan ki gidan nan kan Alhaji ya burge saboda bakin kilibibin ki wai ke ga,saliha.
Maji tace yaya Allah ya baki hakkuri indai akan zancen nan kike magana ko ni ba da son raina yai mashi fada ba.
Rufe min baki bakar munafuka sai kinyi annamincin ki kizo kinawa mutane wani marairaicewa.
Kin iya kitihin da zaki raba miji da matan shi da yaran shi .
To wallahi hawau kiji na fada maki kinyi kadan a gidan nan muddi kikace zaki shiga tsakanin diyana da uban su.
Ke har ina diyan naki dayake kirarin zasu rike mai gida bayan ran shi?
Ba dai wanan bakin mashayin dan naki ba da duniya tasan da zaman shi yana yawo cikin gari a wukance yara na kallon shi.
Masu abin fadi har ba iyaka saura wa yan nan muna fukan masu kirarin su kamilai ne a gida a waje ko tantiran yan iska.
Kuma kin sa Alhaji yaci zarafin imiran a gaban ki, kinji dadi to ki sani indai ni na haifi Imirah har abada ba zai gaishe ki ba bashi ba duk diyana a gidan nan.
Tsiyan banza duk wani a halina ma bazai taba yin mu,amula da kuba idan kuma kin insa sai ki sa Alhaji ya sa wuka yai ta yankan su don basu gaidake ba.
Haka zai sa nasan yaji zafin, basu gaida ke ba tun da ke dashi kuka daukan min nauyin cikin su na haife su.
Banzan bazara dake mai gayyan tsiya gida masu abin fadi tab ga tsuliya kawai.
Allah ya sauwa inji maji ta nufi dakin ta da kayan dake dauke a hannun ta.
Sadauki tagani tsaye a kofan ta ya dafa, dan gishikin dakin da hannun shi daya.
Batai mashi magana ba ta shige dakin ta kawai,ran ta a bace tana mamakin irin wanan halin na uwargidan su.
Bai shiga ba juyawa yayi ya fita daga gidan ran shi a bace don wanan cin zarafi da akewa mahaifiyan su yana matukar damun shi a rayuwan shi.
Tun da safe yabar garin don bai iya tsayawa yana ganin irin wanan takaicin haka a rayuwan shi.

****** ********* ******
Zaman shi a turai yasa ya manta da bakin cikin da ya baro a gida.
Sai dai kusan kullun zai kira mahaifiyan shi su gaisa yakuma tambaye ta yaya suke da sauran kannen shi.
Yana kiran mahaifin shi shima suna gaisawa har su dan taba dan hira a tsakanin su.
Bangaren Bashar kuma komai yana tafiya masu daidai don yana da rikon Amana sosai .
Gashi kuma sadauki ya yarda da Bashar din don tun suna kana suke tare dashi, lokacin mahaifin Bashar na da rai yafi mahaifin su sadauki kudi sosai shine ke yi masu komai.
Koda sadauki ya fara shaye shaye bai hana bashar yai mu,amula dashi ba duk da hanashi da mahaifiyar shi tayi da farko.
Amma da taga alakarsu abin daga Allah ne sai takawo ido ta samasu kawai don tasan shakuwar su daga Allah ne.
Hankali shi sosai yake a kwance yana sha har yanzu sai dai ba irin na can farko ba irin shan kauyanci da kurciyan da yayi a baya.
Don yanzu ko mutum yafi aula dubara ba zai iya gane cewa ya sha wani abuba.
Haka yasa mutane ke ganin ya daina sha ne kwatakwata a rayuwan shi.
Wani yammaci ya bugowa mahaifin shi waya a yanayin da yaji muryan shi sai baji dadi ba.
Yake cewa Baba lafiya kake kuwa murmushin manya Alhaji yace lafiyata kalau sadauki sai dai dan zazzabin da ba,a rasa ba kawai.
Yace to Allah ya sawaka basuyi wani dogon hiraba yai mai sallama ya kashe wayan.
Washegari tun da safe sai yaji bari ya kira Baban yaji lafiyan shi saboda jiya, yana jin jiki.
Sai dai yana kira hjy Kubura ce ta dauki wayan suka gaisa take ce mai sadauki Alhaji ba lafiya amma gamu asibiti dashi don jiya anan muka kwana.
Hankalin shi ya tashi cikin rudewa yake tambayan ta komay ya sami mahaifin nasu.
Tace mai hawan jini ne akace kuma har ya fadi jiyan sai dai da sauki don yanzun ma ya bude idon shi amma dai har yanzu akwai jikin.
Hankalin shi yai matukar tashi yace mata don Allah ayi duk abinda ya dace dashi kafin ya iso garin.
Sukai sallama da ita hankalin shi a tashe tun a lokacin ne yafara shirin tafiya dawowa gida don ganin halin da mahaifin shi yake ciki.
Washegari Sai dare ya shigo garin don nisan inda yafito a lokacin.
Kai tsaye bai yo gida ba yace Bashar ya,wuce dashi asibiti nan ya samu yan gidan su gaba daya a gurin mahaifin shi.
Umma tana zaune a bakin gadon da Alhaji yake kwance ya shigo dakin daga cikin su wasu sunyi mashi sannu da zuwa.
Wasu ko sai harara shi kawai sukeyi yana saye cikin swoth na maza baki mai guntun hannu daga ciki yar rigace itama pink mai guntun hannu.
Sai dai bai sa aninin rigan saman ba haka yasa za,a hango tacikin sosai a fili.
Ganin Umma ta babake gaban gadon ba wanda ya isa ya matsa bakin gadon bai hana shi karasawa gaban mahaifin nashi ba.
Tare da rage tsawon shi ya duka gap da kan mahaifin nashi ya dan rike hannun shi yana fadin Sannu baba ya jikin naka yanzu.
Alhaji Abubakar ya dan juyo tare da bude idon shi da suke mai a lumshe yace,
Alhamdullahi na samu sauki sadauki ya ya hanya har ka iso ne ?
Yace eh Baba,
Likita yace kada a damay shi da surutu abarshi ya huta kawai, Umma ce ke fadawa sadauki hakan.
Yasan nufin ta bai biye mata ba yace wa mahaifin nashi Baba amma ya kamata a fita dakai zuwa wani kasan a dubaka sosai zaifi zama haka anan.
Murmushi yayi tare da rike hannun yaron yace kada ka damu Faruku ai naji sauki sosai.
Kana dai jin abinda nake fadi likita yace kada asa shi yawan magana ko ?
A hankali ya dago kai ya dan kali inda take zaune tana shimfidawa sauran iyali ikon ta.
Daga bayan ta hjy Kubura tace haba ki barsu su gana mana yanzun fa ya iso shi.
Kada ki fada min magana Kubura don ke ba kunya ne dake ba yaya zan kyale shi yana sashi magana bayan likita yaba da doka.
Hannu Alhaji ya daga masu yace don Allah ya isa hakana please,
Idan shi zakuyi min ku koma gida gaba dayan ku,
Sadauki dai yana duke ya kurawa mahaifin nashi ido dake cikin wani hali gwanin ban tausayi.
Can ya mike ya juya gurin hajiya Kubura yana fadin wani likitane mai duba shi mummy ?
Tace tau kasan likitocin yawa gare su amma dai doctor Ango shine yake shigowa akai, akai gurin shi.
Man let's go yace wa Bashar dake tsaye daga can kofan shigowa dakin.
Ajima kadan sai gashi da likitan sun shigo dakin tare nan likita ya bukaci kowa ya fita daga dakin a lokacin.
Umma kaman zatai magana sai tai shiru tamike ranta a bace suka bar dakin yaran ta suka bi bayan ta.
Har an rufe kofan sai gashi an leko akace hjy kubura ta shigo.
Wanan abin yai matukar harzuka ran Umma sosai take ganin shi sadauki da hjy kubura sun fitane ga Alhajin da za,ace ita ta fita daga dakin.
Mikewa tayi ta nufi kofan ta tura da sauri likitan dake duke kan Alhaji ya dago kan shi hjy kubura tana kokari kamashi a daura mai abin gwaji.
Likita yace haba mama munce ku dan tsaya a waje har mu gama abinda zamuyi mashi ko.
Wani haushi ya kumay ta ta buga kofan ta wucd fuuu tana cewa yaranta su zo su tafi tunda basu da amfani a gurin.
Dan ta Sagir yace haba Umma yaya zamu wuce don kawai ana mashi gwaji ance mu fito.
Sagir kai dama nasan baka da zuciya wallahi, baka san ciwon kanka ba ko kadan a gidan nan.
Sagir yace ni dai ba zan tafi ba gaskiya tace zauna wanan mashayin ya gwada maku iko anan.
Mama ma mikewa tayi tabi bayan Umma suka bar asibitin cikin fushi suna sake bakar magana kai kishi ho.
Likita yace mai nan da kwana biyu idan ya kara jin sauki zasu iya fita dashi din don dai yanzu yana jin jiki tukun na.
Sai dare sosai Sadauki ya bar asibitin don yazo gida yacewa Sagir da Mustapha zai je ya gaida maji ya dawo idan basuyi barci ba.
Ya samu har mun rufe kofa don mama bata zuwa asibitin da dare don habaici da gori ne idan taje suna nan.
Wanka yayi yajuya sai asibitin a can ya kwana gurin mahaifin shi a zaune tare da kannen shi biyu.
Cikin dare Alhaji ya falka ya gan shi zaune saman kujera a gaban shi yana barci yake cewa a ranshi Allah sarki .
Ya Allah ka kara shirya min wanan bawa naka Allah ka shirya min duk zuria ta baki daya.
Jin kaman motsin Alhaji yasa shi saurin bude idon shi ya mike yana cewa Baba yaya ne may ke damun ka ne?
Uban yai dan guntun murmushi yace Umar Faruk Allah yai maka albarka Allah ya kara shirya min kai.
Jinkin sadauki yai sanyi zuciyan shi ta fara bugawa don hankalin shi yai matukar tashi sosai a lokacin.
Nishi ya fara guda guda alaman yana jin jiki shi sosai a lokacin da sauri sadauki ya ke kiran Sagir yana cewa.
Yi sauri kira min nurse a waje sagir ya mike da sauri ya fita shiko yana tsaye sai sannu yake wa mahaifin cikin damuwa.
Nurse yashigo da sauri yana cewa bari akwai Alluran da dama za,ai mashi yanzu zai samu sauki insha Allahu.
Bayan anyi alluran da yan mintoci ne, sai ya samu barci sukan yaran basu barci ba suna tsaye a kan uban nasu har safe.
Jin kiran sallah yace su sagir su fara zuwa suyi sallah in sun dawo sai shi ya tafi.
Sagir yace yaya ku tafi kawai idan kun dawo ni sai na tafi haka sukayi suna dawowa sagir ya fita yai sallah.
Can Alhajin ya bude idon shi lokacin gari ya dan fara haske yace ba,ai sallah bane sukace mashi anyi Baba.
Yace ku taimaka min kuyi min alwala sai nayi sallah da taimakon diyan nashi su kai mai alwala yai sallah daga kwance inda yake.
Sai kuma ya koma barci suna gurin zazzaune ba wanda ya gusa daga cikin su har lokacin.

A gida kuma tun da asuba muka tashi muka hada abin breakfast don mune da girkin gidan.
Ni da anty maryam ne muka dauka zuwa asibiti don mukai wa wan yan da suka kwana dashi abin karyawa.
Muna shiga dakin da,sallama yana tsaye yaba da baya jin sallaman mu yasa shi juyowa.
Sai da gabana ya fadi danaga yadda ya sake min muka karasa muna masu ina kwana ya amsa da kyat cikin yanayin damuwa.
Yaya yaushe ka dawo yace mata jiya da dare daga inda nake tsaye ina kallon yadda Baba yake a kwance na dan dago kai nace mai,
Sannu da dawowa yaya sai lokacin ya dago kai ya dan kalle ni da sauri ya kawar da kanshi tare da cewa yauwa.
Yace ya maji suna lafiya jiya na shiga na samu kun rufe kofa ai.
Maryam tace yaya shine baka buga ba mun kai sha biyu bamuyi barci ba ni da Bintu ai.
Bai bata amsa ba yake cewa sagir su tashi su karya ga abin karyawa nan.
Sagir yace kaifa yaya naga alaman baka ci komai ba tunda kazo fa?
Yace No don't mind zan tafi gida yanzu na dawo sai karya a can idan na dawo sai ku tafi kuma kuyi wanka ku dan huta.
Bashar ya kira yace yazo ya kaishi gida yanzu, ba a dauki lokaci ba nacewa maryam mu tafi,
Tace zamu koma idan Baba ya tashi muna gaidashi don Allah.
Batare da ya juyo ba yake cewa, No ku tsaya Bashar yazo mu tafi tare ko kunzo da mota ne ?
Dariya tayi tace kai haba yaya wani mota kuma ina muka gan shi sai dai mu tare Napeo mu hau.
Dan dariya ciki ciki yai mata ba,adauki lokaci ba saiga bashar cikin jallabiya ya shigo suka gaisa yana tambayan jikin mahaifin nasu yace Not bad gaskiya.
Mukai masu sallama muka fara fita daga dakin kafin su fito mu tafi.
Muna fita maryam tace tau dada ga dodon maza ya dawo yanzu za,a fara ke nan ko ?
Nace ni gida zan tafi sai ya tafi na dawo ban iya zama mugun nan yana gari wallahi.
Ganin sun fito yasa nai shiru ba don na tashi ba yana cewa mutafin ku ko?
Nan muka bisu a baya suna

Please Login or Register in order to submit comment