Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

don Allah dai kiyi hakkuri maji ya fadi cikin kwantar da muryan shi.
Yanzu Baba na kana ga inin irin hanyan da ka daukar wa kanka shine daidai gareka gare mu ma.
Kaiwa kanka fada,wallahi ka dibs ka gani saboda kai aka zaunar da ni kowa na fada min irin abinda yaga dama a lokacin.
Inda ka gyara halinka duk gidan nan wa ya isa yai muna haka babu shi wallahi don ni ba ruwana da harkan kowan su.
Amma sanadiyar abinda ka aikata ji irin yadda kowa ya takamu son rashin ana fada muna abinda aka ga dama.
Maji kiyi hakkuri don Allah insha Allahu ba,zan sake ba da yardan Allah hakan ba,zai sake faruwa ba.
Nan dai taita mashi nasiha tana cewa yanzu ashe badama su Amira su yi laifi na kawo maka karan su a matsayin ka na babba a cikin su.
Ni hajiya kubura wallahi tai min komai don ta nuna min ita uwace a gareka kuma tasan ciwon kan ta ba kamar sauran iyayyen naka ba.
Don haka wallahi kaiwa kanka fada kaceci kanka kace ceni ni uwarka da yan uwanka kafitar damu daga zagi mutanen duniya.
Sun kai wani lokaci tace ya tasgi ya tafi take ce mai kuma daga yau ya tabbatar da ya dinga zuwa gida yana cin abinci bata son yana ci a waje inda batasan ko ina bane.
Yai mata godiya ya mike yabar gurin tare da kara bata hakkuri yabada baya take cewa jika don Allah kamar wani mutumin kirki can ashe mutimin kawai.
Murmushi yayi yace kiyi hakkuri maji don Allah bazan sake ba insha Allahu.
Yana fita ta sauke ajiyan zuciya tare da cewa a filo Allah ka,shiyar mun da wanan yaron dama sauran yara masu halin shi na,wanan lokacin,,,,


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYABA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,

A LOKACIN MU KE,,,


Murna sosai takeyi don ganin ta dauko sabon fridge dinta da ta dade tana gurin taga ta saye a rayuwan ta, don bunkasa sana,arta.
Ta bude fridge din yafi a kirga tana duba ciki da wajen shi don tabbatar da lafiyan shi.
Ba laifi don ta samu yadda take bukata saboda sanyi da kankara yake daga sama har kasan shi tsab.
Wanan abin yasa ta yini tana farin ciki da wanan karuwan da ta samu na ci gaban ta.
Ranan sai da ta aikawa makwabta da kankara tana fada masu idan suna son saye ta sai fridge mai kankara da ruwan sanyi, don haka su sa mata albarka a ciki.
Wasu sun yaba, wasu kuma sun kushe don haka duniya take dama wani baka hada komai dashi ba amma yana bakin ciki da karuwan ka a duniya.
Shima maigidan ta bawan Allah da ya dawo yai mata fatan alheri akan fridge din, tare da yar guntuwar nasiha akan sai tayi hakkuri da jama,a don mai saye da sayarwa sai hakkuri dama.
Sai dai kassh matsalan hauwa shine bata da hakkuri don ta sawa ranta masifan son kudi sosai.
Ta manta cewa zafin nema baya kawo samu sai in Allah yaso bawan shi da arziki yake arziki.
Ba dama mutum yazo sayen kankara ya mayar mata koda yace bai kankareba sai ta hau masifa da fada taki canzawa mutum abinda yake so.
Gashi duk samun da takeyi yanzu baisa mijin nata yakai idon shi ba ga kudin ta, don ko ba dadi sai yakawo masu dan abinda zasu dafa agidan suci.
Yana da matukar kokari gurin ganin ya kare hakkin iyalin shi sosai a rayuwan shi.
Amma daidai da rana daya idan dan wani abu ya kasa ga cefanen shi sai Hauwa tai mirsisi taki yi masu girki wai sai ya ciko ta girka masu.
Don ita bazata yarda da akidar cikawa namiji kudun cefane ba saboda itama tana da nata bukatan ai da kudin ta don yanzu ta sa rai wai fili take son saye ta yarda kaddaran itama.
Baida fushi hakan bai damun shi, dole sai ya samo ya cika mata sai ta girka masu inba haka ba su kwana da yunwa har yaranta.
Wanan kuma ba komai bane sai zugin uwarta da kullun take mata hudubar shedan akanta.
Na karta yarda da namiji don tana ganin ta ita kadai bai hana wata rana sai tagama kashe maijiki ya ce zai jajibo mata kishiya.
Halin Rashi hakuri irin na hauwa yasa mutane suka dan rage shigowa sayen kayanta yanzu sosai sun kwammace suje wani guri su saye.
Haka yasa ake barinta da kimin kankara a fridge har su narke tayi hasaran kudin ta.

****** ******* ******
Cikin mota suke a kofan gidan su Raiha yana yadda ranshi yaso da ita, a cikin rashin damuwa Raiha ta barshi yana juyata yadda yake so.
Don son shi da kalaman shi ko yaushe suna kara tasiri ne a zuciyar ta don ta yarda dashi 100%.
Daga nesa matasan dake zaune suna hira hankalin su yana gare su tun shigar Raiha motar, daya daga cikin matasan yake cewa kai yanzu dai mutane basu da tsoron Allah wallahi.
Kadiba fa yarinyar can ina lura da ita tun dazun suke zaune a motar nan har takai motar tana motsi don kanta.
Ashe bani daya nake lura da hakan ba inji dayan matashin yaba dayan amsa.
Sai dayan da sai yanzu yai magana yake cewa ai wanan yarinyar batayi ba wallahi.
Gaba daya haliyar ta baida kyau bata dauki kanta diyan tallakawa ba ko kadan takai kanta inda Allah baikaita ba ko.
Ni yanzu Raiha tafita raina tunda abokina yake fada min cewa yagan ta uguwar su gurin sayen kayan maye.
Kaifa Nasir ?
Yace wallahi ranan daya ganta a uguwar nan yake ce min a uguwar nan take ne nace mashi eh.
Shine yake cewa babba yar hannu ce sosai tana zuwa uguwar su gurin wani deler ta sayo kayan aiki masu karfi a can.
Sai wanda yafara magana yake cewa kai amma ko udan gaskiya ne wallahi dole mu saka mata ido don kada ta kawo muna matsala ga sauran yan matan shiyan nan.
Yanzu kai ya kake ganin zamuyi yace kokari zamuyi mu kamata a hannu sai mu dauki mataki daga iyayyen ta mana ko yaya kuka gani.
Hakane sauran suka bashi amsa da,sauri suna cewa wallahi in har ba,a,dauki mataki ba zata iya gurbata wasu ba,a sani ba.
To yanzu ita ina ta koyo wanan bakar akidar naga dai a uguwar nan ta tashi a gaban mu ai.
Kai yanzu sai wani ya koya wa mutum hakane abin fa masifa ne kawai sa warai ne ai.
Ni wallahi mamaki take bani yadda idon ta ya bude baki daya a lokaci guda haka.
Kaidai bari ai yanzu haka kila a makaranta ko kuma wasu sabbin kawaye ne suka koya mata wanan harkan.
Tana shiga gidan mu gurin kanne na zan shiga nai masu fada wallahi su rabu da ita tun bata lalata min kanne ba.
Kaidai kawai Allah ya,sauwaka ita kuma Allah ya shirye ta don kaga ai mahaifinta mutumin kirki ne.
Uwarta kuma bata ko magana shiru shiru mutumiyar kirki ce sosai don bakajin ance ga abinda tayi a uguwar nan na assha.
Sai wani lokaci Raiha ta bude kofar mitar ta sako kafan ta guda daga waje, daga inda matasan suke zaune suna iya hango ta daga cikin motar tana gyara rigar ta da kuma saka hijjab din ta.
Allah ya kyauta amma dole mu dauki mataki akan wanan fitsaran da ake muna da rana tsaka a uguwa.


****** ********* ******
Abin duniya ya ishi zuciyar Umar faruq ya rasa yadda zai shawo kan Maji ta yarda ta mara mai baya akan zancen tafiyan shi zuwa ghana kwallo kamar yadda yan club din su suke son yaje ya buga masu ball.
Haka yasa yafara dirkawa cikinshi kwaya kala kala har takai ya shiga hali na maye sosai.

Fatima don Allah zoki sayo min magani kafin duhu ya kara yi don yanzu dana aiki su Amira Alhaji yagan su fada zai min sosai.
Kiyai sauri ki dawo da wuri kinji Fatima kada ki dade kinji Fatima dare ya soma sosai.
Don takwas saura yanzu, ban son fitan dare ga diya mace haka koshi dole yasa zan aike ki don kaina ya matsa min da ciwo sosai wallahi.
Bintu ta dauko hijjab dinta ta,saka ta fito ta karbi kudin maji tafada mata kalar maganin da take son a,sayo mata.
Tana zuwa aka bata maganin ta juyo zuwa gida gap da zata shiga gidan ne taga mutum a kwance bakin get.
Sai faman nasari yake harta dan raba shi zata wuce don tagane wanene a kwance gurin.
Da,sauri ta dawo ta dan duka a kan shi a hankali tana fadin.
Yaya sadauki ka tashi ka,shiga daga ciki kada wani ya gan ka anan haka.
Da kyat ya bude idanuwan shi ya kalleta cikin maye ya nunata da hannu ya bude baki da kyat yana fadin, tare da nunata.
"Ke zan _ci uban,ki idan baki ban guri ba walla_hi sai ya mayar da kan shi kasa.
Innalillahi Bintu ta furta a fili ta mike tsaye kamar zata wuce sai kuma taji bazata iya ba don idan har wani ya gan shi a haka yashe a kasa cikin maye, yau bakwanciyan hankalin ga Maji dama gashi kanta tun safe take yana mata ciwo.
Komawa tayi iya karfin ta ta dago shi daga kwancen da yake ta na cewa tashi yaya ka koma dakinka don Allah.
Shegiya idan baki barni ba zan maki dukan tsiya wallahi, yafadi a cikin muryan dan maye.
Bintu bata bi ta nashi ba sai kokarin mikar dashi take shiko sai ashar yake jefa mata.
Cikin ikon Allah ta samu ta daga shi daga inda yake kwance ta kaishi daidai kafadan ta duk da yai mata nauyi amma haka ta daure ta ja shi zuwa dakin shi.
Da kyat ta lalabo key daga jikinbshi cikin wandon shi na baya ta bude dakin tana,shiga wani wari ya daki hancinta, haka ta daure ta kaishi bakin katifan shi.
Sai barci yake a kafadan ta cikin maye, tana son kifar dashi don duk tagaji saura kiris su zube tare sai ya kwararo mata amai da fitsari a lokaci guda duk ya bata mata jiki dashi.
Haka ta daure ga,warin amai yana damun ta ta kifar dashi akan katifan dakin.
Kallon hijjab din ta da ya lalace da amai da fitsari tayi tare da girgiza kanta tana Allah ya kyauta tajowo mai kofan dakin tare da dunkule hijjab dinta daya lalace da aman shi.
Gap da zata shiga gida taji karan motar Alhaji habu dake dawowa daga kasuwa, shi da sauran yaran shi dake bin shi shago.
Da,sauri ta karasa kada suga fitowan ta part din samarin gidan kuma dakin sadauki su fassara mata zance.
A can cikin gida kuma Maji hankalinta ya tashi sosai ganin Bintu ta dade sai gata saidai a hargitse take don hankalinta ya tashi.
Amira data kalleta yadda ta shigo gidan take cewa, ke lafiya kika dawo wata kala haka dake ji yadda jikin ki ya lalace.
Saida Binta ta kalli jikin ta take cewa cikin sauri faduwa nayi gurin kwata da,wata mota tabiyo gefena.
To amma ai ba kwata bane kamar amaine jikin ki tace gurin masu saida abincine gurin.
Ta mikawa Maji maganin ta,shige ciki don duk a tsawale take da aman dake jikin ta dama.
Saida tai wanka ta gyara jikinta tsab tafito falon inda suke ta zauna tana kallon shirin da ake a sokoto tv.
Maji dai bata ce masu kalla ba don kanta da yake damunta da ciwo a lokacin.
Sai da ta dauki lokaci bayan tasha magani sannan kan ya fara lafa mata don ranan bata ko fita zuwa yiwa maigidan su sannu da,dawowa ba.
Wai ko yau yayan ku yadawo kuwa don banga ya shigo ba daukan abincin shi.
Amira tace, waya sanan mashi kila yana can gurin yawon banzan shi sai baba yasan bai gidan yazo yaitawa mutane masifa akai.
Bintu tace da zan shigo nagan shi zai shigo da leda da,ya,sayo doya soyayya gurin mai sayar wa nagan shi da zan wuce yana saye.
Oho ashe shiyasa banga yashigo ba ya samu abinda zaici ke nan .
Ai da yana jin yuwa da yanzu yashigo ya cinyewa mutane abincin su ko inji maryam.
In baici abinci ba nan a ina kuke son yaje yaci ne maryam, ni dai idan zai shigo yaci a nan din ai zaifi min komai dadi.
Bintu taji tausayin Maji ya kamata a zuciyar ta take cewa kai uwa uwace dai.
Da yau maji zata san halin da dan ta yake ciki tasan da yanzu suna cikin tashin hankali da balai a rayuwan su a shiyar su.
Amma dai yau Allah ya rufa wanan asirin an wuce gurin in ba,wani ikon Allah ba kuma.
Tana jin su suna hiran su amma bata saka masu baki ba sai faman tunane take a ran ta.
Shigowan baba a part din ya katse mata tunanen ta suka fara gaida shi suna mashi sannu da,dawowa.
Bintu ce tafara mikewa tashige daga ciki sai Alhaji yabi su Amira da harara dole suka mike simi simi suka shige bayan Bintu.
Yace marasa kunya kawai wai har bakuwa tafisu hankalin sanin ya kamata.
Har yanzu gwagon yarinyar nan bata dawo bane ko kuwa dai?
Bata dawo ba Maji taba shi amsa a takaice, takara da cewa ni ban ma son rabuwa da yarinyan don halinta na kirki yai min.
Hmmm ki dai ji da na kanki kafinki kara jajibowa kanki sabon matsala ya bata amsa.
Ai Fatima ba matsala bace zan ma iya cewa zaman ta ya zama min alheri don kaga yaran nan suna samu karuwa sosai a gurin ta ga ta yar karama amma akwai addini sosai a kanta.
Ta godewa Allah da,ya bata wanan baiwan har takai ga samun yabo haka na alheri Allah muma ya shirya muna yaran mu.
Ban ganki ba ne yasa nabiyo nagani ko lafiya don nasan ba halinki bane rashin zuwa yi min sannu da kasuwa.
Maji ta dan ya mutsa fuskanta tana cewa wallahi tun safe nake fama da ciwon kai yanzun ma aka sayo min magani na,dan sha shine naji yadan fada min.
Naso naje gaishe ka amma sai nai tunanen ko ka shige ne ko ai.
Ki daina shan magani haka batare da likita ya baki umurni ba idan kinji kan ya matsa maki aida kin kirani nazo mun tafi asibiti ko .
Naga ciwon kaine kawai shiyasa ban dauke shi wani babban ciwo da zani asibiti ba.
Haka dai kikace a lokacin da ya karasa takon shi inda take zaune yana kai hannun shi akan wuyan ta don taba jikin ta yaji lafiyan ta.
Kai haba Alhaji ai na samu sauki dana sha maganin nan yanzu, ki dai bar wasa da ciwo don ciwon da ka raina shike zama babba yanzu.
Allah dai ya sauwaka inji maji tafada cikin dan sauke ajiyan zuciya.
Ki dai bar tunane akan wanan yaro ki kai kukan ki ga Allah shine zai bamu mafita akan shi,insha Allahu.
Allah yada inji Maji ta fadi voice din so soft don zancen Sadauki yana tayar mata da hankalinta sosai.
Daga haka yai mata saida safe yabar part din nata cikin tausaya mata halinda take ciki yanzu kan lalurar dan ta wanda duk ta tayar da hankalin ta.

Washegari sun tashi kowa na batun fita zuwa makaran ta sai Bintu ce a gida don ita yau basu zuwa makaranta suna hutu.
Part din nasu yai shiru bakajin motsin kowa duk lokacin kowa yafita zuwa nashi tsabgan gaban shi don ci gaban rayuwan su.
Wani irin yunwa ne ya farkan dashi daga nauyayen barcin da ya yi mai tsawo bai san inda yake ba.
A hankali ya bude idon shi inda ya kurawa silin din dakin nashi ido, can yakai kallon shi ga agogon dakin a hankali yaga har tara da rabi na,safe.
Da kyat ya iya mikewa zaune ya samu har yakai tsaye don yunwan da yake ji yai mai yawa sosai a lokacin.
Wanka yashiga yana wankan ne abinda yafaru jiya da dare ya dan fara dawo mashi a,rai.
Kai aiko na,shige su tunda wanan bakuwar yarinyar ta san da wanan zancen don yanzu nasan ta fadawa Maji halin da,ta ganni a ciki daren jiya.
Aiko idan har ta fadi sai yai mata dukan da sai an kwantar da ita asibiti sai da ya shirya tsab yafito tare da kulle dakin shi ya nufi cikin gida don ya gaida Maji ya kuma karya saidai gaban shi na faduwa badon yana son cin abinci ba da bai shiga gidan ba a lokacin.
Da sallama a bakin shi ya shiga part din nasu duk da ya hadu da mama a kofa amma bai mata magana ba ya shige abinshi tabishi da harara tana fadin mara kunyan yaro kawai tabbatacce.
Maji dake zaune saman salaya tana lazumi ta karba mai sallaman shi tana cewa sai yanzu katashine babana kowa a gidan manya da yara sun kama gaban su ko.
Yace cikin dan shafan kan shi wallahi Maji barci ne ya kara daukeni bayan mun dawo daga sallah.
Ai jiya da,dare muna ta jiran kazo kaci abinci baka shigo ba har ana batun rufe gida sai Fatima ce ke fada muna cewa.
Gaban shi yai wani faduwa ras ras kafin yaji ma yarinyar tafada wa maji din.
Maji tace take ce muna ta gan ka,,, lokacin Bintu tafito daga cikin daki tana cewa Mama a canza zanin gado ne.
Wani uwar harara ya,watsa mata saida ta kasa fadin maganan da zata kara fadi.
Maji tace ashe jiya doya kaci ka kwata gata itace ke ce muna tagan ka kana,sayen doya da kwai da dare dana aike ta.
Wani wawan numfashi ya sauke tare da dan sake fuskan shi yace eh wallahi maji shi nake son ci shiyasa na saya ai.
Fatima dauko wa yayan ku abinci shi ya karya yafita shima don ban son zaman gidan nan kamar mace.
Bintu ta juya inda yake tana cewa ina kwana yaya can kasan harshen shi ya amsa mata da lafiya kalau,
Ta juya zuwa cikin kitchen ta dauko mai abin karin shi takawo mai gaban shi ta duka don ta aje mai ya faki idon Maji yana cewa kin kuru baki fadiba dana karyaki yau wallahi.
Da sauri Bintu ta mike tabar falon don kada ya kara ce mata wani abin kuma don ko yanzu ta tsorace dashi don mashayi ba abinda bai iyayi shi.
Sunaci suna hira da mahaifiyar nashi tana dan mashi hira maikama da nasiha sai cin abincin shi yake hankali a kwance abin shi.
Daidai Bintu na shigowa taji yana cewa ni dai Maji don girman Allah ki yardan min natafi wanan wasa kiyi hakkuri ki gwadani ki gani idan ban canza ba kada ki kara bari na tafi don Allah maji.
Daka ta sadauki na riga na fada maka cewa bazan yarda da zancen tafiyan ka ba,wani kasa can da babu kowa na gida a tare da kai, nan ma da kake a gaban mu yaya muka kwashe da kai?
Bintu batasan yadda akayi ba tace mama yace don girman Allah ki barshi yaje insha Allahu zakiga canji a gare shi da yardan Allah ke dai adduan ki yake nema da yardan ki.
Da har zai bude baki yace ke wayasa bakin ki zan balballaki yanzun nan, amma sai yaji maji tace .
Fatima bar shi kawai ni nasan halin abina ke yarinya ce baki gane may nake nufi da zance na yanzu amma ba zancen tafiya a guri .
Tafiyan ma fa wai na wasan kwallo haba sai kace uwar banza da batasan ciwon kan ta ba.
Maji komai zamuyi saida adduan ku don haka kamara yayi kisawa zancen albarka ki mara mashi baya yakai ga kudirin shi.
Don ba,a san mai gobe zai iya yi ba shiru maji tayi tace kai Bintu badai iya magana ba dai kam.
Shiko Umar shiru yayi yana mamakin wanan yarinyar yadda ta iya magana haka kamar wata tsohuwa can.
Fatima naji zancen ki sainai shawara ya dan dakance ni kawai nagama nazari nagani ,
Daga haka ya mike tare da cewa cikin murya ba dadi zan fita sai nadawo Allah ya tsare tace sai kadawo.
Haka fita jiki ba karfi yabar dakin sai dai yaji dadin yadda wanan yarinya ta saka baki har Maji ta dan yi taushi sosai yagani ai.
Tun lokacin da sukai wanan magana hankalin maji bai kwanta ba sai sakawa take ta walwalewa a ran ta daga karshe dai ta watsar da zancen ma kawai.
A na cikin haka gwagon Bintu ta dawo daga kawai ta zo gidan bayan ta huta don ganin Bintun ta.
Nan suka tare ta da murna sai bin Bintu take da kallon yadda gaba daya ta canza mata a fuskan ta ta kara haske da kiba, taiwani irin kyau da ita.
Nan ta shiga yi wa Maji godiya da karamcin da tai mata akan rike mata yarta yar dan uwan ta da take hannun ta.
Maji tace haba hajiyan masa ai Fatima mutun ce yarinya ce mai dadin zama da sanin ya kamata sosai.
Naji matukar dadin zama da ita a gidan nan don ta taimaka min da abubuwa da dama a gidan nan
Hakane ma yasa nace ko kin dawo bazan barta takoma gurin ki ba sai dai mu zauna nan da ita tunda danan da can guri ki ai duk dayane kuma a shiya daya muke dake.
In dai har hakan bawai zan takura maki bane gwago tai godiya da karamcin Maji tana cewa nagode Hajiya dama ba zama nadawo nayi ba don jinya nake a can na yayata da bata da lafiya.
Shine naga na barta a nan da suna sati biyu gashi har nai sati hudu a can baku da labarina, kada hankali ku ya tasbi na rashin jina da bakuyi ba na tsawon lokaci.
Ai babu komai nasan tunda najiki shiru lafiya ne ai tunda kin san inda aka barta ai.
Nan suka dan taba hira gwago tana bata labarin rashin lafiyar yar uwarta da take jinya a kauyen su.
Da zata wuce ne ta bukaci da Bintu ta rakata ta dan gyara gida don kuran da yayi na rashin mutum a cikin shi na wani dan lokaci.
Aiki sosai Bintu tayi a gidan harda girki saida tai masu don suci tanayi tana tambayan gwagon ta labarin mutanen gida.


Please Login or Register in order to submit comment