Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

mika min cup din.
Yana fadin ki shaye shi don ki dan kara samun saukin jikin naki wayan shi ce tai kara ya dauka sai da suke magana na fahinci da mama suke magana .
Yadda suke magana na fahinci mama tana cikin matukar farin ciki da walwala a tare da ita tana cewa ka fara ganin al,amarin Allah ko.
Nikan raina kamar an fasa min guduma tsakiyan shi nake ji don nasan dada shike nan ni tawa ta kare ke nan.
Shiko sai wani lumshe idanuwan shi kawai yake abu ya taru yai mai yawa a zuciyar shi.
Na farko tunanen irin ni,iman da ya diba daga jikin yarinyar da yake ma kallon kitse saman ruwa don bai taba zaton haka zai samu ba daga gurin Fatiman daya raina da farko .
Suranta sai gizo yake mashi a idanuwan shi ya kasa mantawa da abubuwan da suka faru a tsakanin a daren jiya din.
Idon shi ya sauke ga dogayen yatsuna dake rike da kufin da nake kurban shayi a hankali bai san lokacin da ya sauke wani irin ajiyan zuciya ba wanda har yasa na dago kai ina duban shi.
Sai kuma nauyi da kunyan yadda ya kasa sarara min har takai yai min rauni a jiki ance dama dan hakin da ka raina shikw tsona maka ido.
Nauyi da kunyan maji sun rufe mai zucita don bai taba tsanmanin cewa akwai wani rana da zaiji nauyi da kunya maji ba sai ya din nan.
Kofin nake kokarin ajewa a gefe ya kura min ido cikin daure fuska yake cewa kin shanye ne.
Na dan marairaice ina cewa, nasha yaya hannu ya miko min yana karban cup din gani sauran tea a ciki yake cewa wanan fa ?
Na dan marairai ce nace na koshi yaya please tausayi na bashi ya dauki cup din ya fita dashi.
Ba,a dauki wani lokaci ba saiga sako daga mama ferfesu ne na kaji da kayan cikin rago sunji kayan kamshi na gargajiya, sai kuma gassan naman rago mai zafi .
Da kanta ta bugo min waya akan na tashi na ci abin da akakawo tare kuma da jaddawa yaya akan ya tsare ni naci sosai.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,


IDAN KIN BIYA KIN TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH,,,


A LOKACI MUKE


Washegari kamar yadda na saba tashi na kamala muna abin karyawa ina yi ina duban kofan dakin da Anty Amirah take ciki har na gama bata bude kofa ba.
Wanka nayi na gyara jikina duk da ba wani kwaliya nayi ba amma nayi kyau zani da riga ne na atamfan super the most classic one na daura.
Falo na fito na fara karyawa sai da na kusan gamawa ne, na ji ta bude kofan ta tafito daga dakin.
Cikin murmushi nake gaishe ta, inda ta amsa min cikin ko in kulla tare da zuwa tafara bude abinda na girka muna.
Sai can bayan ta zauna take cewa yanzun duk wanan abinda kika dafa haka wa zai ci su ne wai?
Nace dani dake ne fa anty sai masu gadi da zan dibanwa nakai masu.
Humm,ummm lalai dan tallaka bai iya samun guri ba wallahi, Bintu tun ba,a je ko ina ba kin fara wanan nan irin barna haka ?
Nace haba anty ina kuma barna haka ni dana tashi gurin mama ne kuma zan ce na yi barna.
Masu gadi fa har mutum uku ne gidan nan kuma shi da kanshi yace na dinga basu abinci suna ci.
Dakata Bintu may yakawo zancen yaya a nan magana ce iya ni dake mukeyin ta ko?
Kada ki soma kice zaki raba muna zumuncin mu da dan uwan mu don tare kika gan mu ke haye kawai kikai muna daga sama.
Kodan maji ta cuce shi ta mashi wanan cushe na auren ki har kike ganin kamar ke wata tsiyace yanzu.
Bari kiji koda ace auren so kukayi da yayana wallahi ke Bintu kinyi kadan ki rabani da dan uwana ana magana kin wani kawo zancen yaya kin saka a ciki mafari ki samu wani sheri ki kulla kice nace kada kiyi abinda yace kuma.
Kallon mamaki nake mata nace haba Anty may nai maki ne haka wai yanzu kike nuna min irin wanan rayuwan a tsakanin mu nifa kaunar kice anty.
Koshi yaya din bai gwada min irin wanan kiyayyan da kika dauko gwada min .
Yar uwar wa ai dake yar uwatace da killa zan dan raga maki ta wani guri amma ina hadin kifi da kaska kuma.
Sanan shi yaya ina yaga gurin nuna maki wani abu kisa uwarshi ta tsine mashi yana zaman zaman shi akan wata banza can.
Anty nice banza kuma yau ?
Kila da hafsatu nake magana .
Cewa mahaifiya ta data haife ni wai da ita take magana na dago cikin mama idanuwa sun kawo kwalla nace nagode Anty.
Kada ma ki gode din don wallahi ki sani Bintu nifa na tsane ki a rayuwana tunda kika sa maji taiwa yayana haka.
Murmushi nayi tare da mikewa ina kokarin daukan kulolin abinci na juye wa su maigadi nake cewa nagode babu komai.
Ina juyawa naji tana fadin mace a haka ba gaba ba wani fasali na mata kamar solama dake.
Mamaki nake ina tafiya yadda cikin dan lokaci ta sake akaina gaba daya duk ta manta da rayuwan mu a baya don kawai wanan auren na dan uwan ta da aka sakaniyi bada son raina ba.
Naji tana fadin wallahi duk wani muna funcin ki ke da gwagon ki tun farko na fahince ku kwadai ne kawai yakawo ku dama cikin rayuwan mu.
Allah ne shedan hakan kuma nace mata batare da na juyo ba tace ko kina so ko baki so sai wata tashigo gidan nan yar arziki taci arzikin yadda aka iya cin shi.
Haka zaman mu da ita ya kasance a gidan ba ruwan wani da wani har zuwa karfe hudu na yamma.
Sai iko da mulki take zuba min a cikin gidan har na kwammace dama ni kadai na zauna dayafi min.
Sallama yaya Bashar mukaji a falo ganin yadda muke a zaune yasa shi fara fahintar akwai matsala azaman mu da Amira a gidan.
Jin ayi wani sallama yasa na dago da sauri anty maryam ce sai kani na musa biye dasu da yar jakar kayan shi a hannun shi.
Na rasa wa zan tara a cikin su don murna na rugumay maryam ina murna tare da fadawa jikin ta.
Itama murna da ihun ganina takeyi sai wani uban tsoki da mukaji anty taja tare da mikewa tabar falon ta dan kalle tace taufa matsalan da kuma aka kawo maki kega a gida yar uwa.
Nai murmushi nace aikin san anty hukuma ce sai lalashi don ita halinta daban yake kin san.
Na juya gurin kanina ina mashi sannu da zuwa tare da tambayan shi mutanen gida na dago kai nace wa yaya Bashar nagode yaya yace ba ni bane mijin ki ne yace na dauko maki shi ai.
Yace madam ni zan tafi sai after eight zan dawo mu tafi lokacin kun gama gulman ku.
Mukai dariya na ce yayana ai bazata fara tai min gulman ka ba nakyale ta yace haka ne fa kuma Fatima shiyasa nake yin ki.
Yana fita na kawo masu abinci maryam ta harare ni tace ko kin man ta nima madam ce yanzu sai dana girka mukaci muka fito.
Nakai kani na dakin dake farkon shigowa falon wanda ina ganin dan baki aka gina shi.
Muka koma dakina muka baje dama ta matsu ta samu abar mu, mu biyu mu wala.
Dakin tabi da kallo tace dankari gaskiya Bintu yaya yayi kokari wanan irin daulan haka gaskiya ki godewa Allah da hakan.
Nace da mama kuma ko da tai sanadin kawoni ciki ko?
Nace, anty maryam nifa duk wanan bai a gabana kawai dai ni gurina mu samu zaman lafiya a tsakanin mu.
Ta dafani tace, haba Bintu ki kwantar da hankalin ki komai zai zamo daidai a tsakanin ku da yaya.
Tun da safe fa shi ya tayar damu daga barci akan aje yau azo maki da musa tunda kince kina son yazo,
Bai dade da kiran shiba kuma sai ga maji itama ta kiramu tana fadin aje a zo maki da dan uwan ki don ta san Amirah ba zata tsinana maki komai ba.
Nai murshi kawai tace kai Bintu aure fa rahama ne wallahi, sai yanzu na gane dalilun da yasa iyayye kan damu da yarsu tai aure ashe.
Kin koga yadda yayana ke wani haba haba dani ko kuda bai son ya tabani kuma da zaran ya ga na dan shiga damuwa ya shiga tambayana ke nan may ya samay ki may yafaru kuma.
Tace kai bari ke dai yanzu ga yaya ya bata ni idan ban ji shi a jikina ba wallahi har damuwa nake shiga wallahi.
Dariya sosai tabani nace kai anty maryam wallahi baki dai barin halin ki watau, tace bari mutumiyar wallahi duk na matsu na ganki na dan baki wasu hit,.
Nan dai tata min hiran irin rayuwan dadin da suke yi da yaya bashar sai nake ji ashe ni ba ma aure nayi ba.
Jin nayi shiru sai sauraren ta nakeyi, tace yaya kuma kin barni sai faman zuba nakeyi ni kadai na san dai yaya sadauki yafi yayana waye wa.
Murmushi nayi nace anty kufa auren soyayya kukayi da yayana bashar niko da akai mashi dole akaina ina zan samu wanan daulan haka.
Allah dai kawai ya kyauta ga sabon fitina anty Amira abinda take fada min ko wanda akaiwa dole a kaina bai gwada min hakan.
Tace dan Allah fita batun ta yar bakin cikine ita da fadin rai ta dauki duniya da girma ita.
Tace ni yanzun dai na fahinci tunda kika shigo baki samu kan yaya ba ke nan ko?
Nace kamar yaya anty ni har wani kan shi zan samu can mutumin da akai mashi dole a kaina.
Tace ji nan Bintu kefa mace ce kuma ki tuna aljannan ki ta na a,karkashin kafan shi ne don haka idan zaki kama jiki ki ma gurin gyara gidan ki.
Nace anty wani gyara kullun fa sau biyu nake gyara gidan nan a wuni may kuma ake bukata bayan hakan ?
Kai amma ke ma Bintu ashe da gaskiya ke yar kauye ce wallahi.
Dalla ni ba gyaran gida nake nufi ba kinji ki saurara ki ji ba wani boyo ko kunya a tsakani na dake don ke yar uwata ce Bintu.
Da farko zaki fara shiga ta daukan hankalin shi ta yadda don ubanshi sai ya gigice a kanki badon Allah ba shifa namijine.
Namiji kuma kamar kenwa yake gurin son jiki abinci mai jan hankali zaki dinga mashi.
Sai tai shiru can tana fadin ke Bintu ke ma yar iska ce wallahi don nasan yanzun haka yar tsama kuke a tsakanin ku kuna yabawa juna magana.
Nace idan ya fada min nima ai dole na mayar mashi tace kin fadi wallahi.
Kwaran ki yake don kece da zunubi duk abinda zai fada maki ke yazama wajibi dole ki kwanta don kece a kasa.
Ladabi ya zama dole yanzu akanki idan abinci zaici ki tabbatar kina zaune tare dashi, ruwan wankan shi da suturan da zai sa duk kece da Alhakin hakan don ki sani.
Tace gyaran dakin shi duk a kanki ya rataya idan ya dawo sannu da zuwa idan zai fita Allah ya tsare ya bada sa,a.
Duk kika tsare haka wallahi ko baiwa Allah nina fada maki dole ya sauko ku daidata a tsakanin ku.
Gama sauki yanzun yadda yai tafiyan nan waima kuwa kin kirashi kuwa?
Nace ni kan ko lanban shi ban dashi tace kin shigesu wallahi Bintu wai ke kina ganin yadda yaya yake kaman ba masu son shi ko?
Wallahi ki kama jiki Bintu, don na fada maki shine kawai bai damu da mata ba in ba don haka ba da sai kin raina kanki wallahi.
Ki dinga kiran shi kina mai sannu da sauran tare da tambayan lafiyan shi idan kuma zai dawo ki bashi mamaki hada mashi abincin da kika san yana so ki gyara gida da jikin ki tsab.
Kada ki tsaya wani jan aji can ki mai kyakyawan taro sai kiga yadda zaki juya abinki cikin ruwan sanyi wallahi.
Kai gaskiya nikan bazan iya ko daya ba mutumin da ke har hasashen wai ina son na kashe shi idan nai mai girki yace dole sai naci ya gani kada na kashe shi.
Dariya tayi tace ku takon kainan ku ai daban yake Bintu don baku bari agane har afahinci komai.
Muna ciki bamu san cewa har lokacin sallah magariba ya kawo jiki ba sai jin kiran sallah kawai mukayi a masallacin kofan gida.
Mun idar kuma tashiga kara min wasu haske sai mamaki nake wai ita a ina duk tasan wanan abin haka ne wai?
Takwas da yan mintina mijinta har ya iso daukan ta baiji kunyan idanuwan mu ba yake ta faman shige mata ajiki a gaban mu nikan sai faman kawar da kaina nake cikin jin kunyan abinda sukeyi.
Yaya bashar ne yace Fatima bari na baki layin mijin ki don ya sauka kasan waje ko tun da magariba ya bugo min waya.
Mukai sallama dasu sai lokacin da suka tafi na samu ganawa da musa nan mukai ta hira dashi har gurin karfe goma da wani abu na dare muka shige don Amira tun fitan su maryan da ta dan fito bata kara leko falon ba kuma har lokacin da muka shige muka kwanta.

****** ********* ******
Kwance yake saman gadon dakin da ya sauka waya yayi da wani abokin shi dan kasan saudiya da suka shaku dashi sosai.
Yana gama wayan ya fara juyawa a saman gadon gami da zubawa wayan dake hannun shi idanu .
Saboda wani mugun takaicin Fatima da yake ji a zuciyar shi yau kwanan uku ke nan baya gida amma wanan yar kauyen yarinyar mai fadin rai ta kasa daga waya takira shi.
Gashi yana son jin lafiyan su amma sai yake ganin kirata gare shi kamar kasawa ne hakan.
Itama da take mace mallakin shi zaman shi takeyi bata kirashi ba sai shine zai kirata akan may ma wai ?
Don yasan koda ya kiratan ba wani magana bane mai dadi zai samu a gareta banda bacin rai da zata saka mashi kawai.
Ya kifa kanshi a filo yana tuna maganan Maji dazun da suka gausa take tambayan shi kana ko waya da matar ka yaba amsa da eh maji muna gaisawa ai ina tambayan ta lafiyan ta?
To yanzun idan maji din ta bugawa Fatiman waya tace bai taba kiranta ba ko sau daya yaya zata dauke shi a makaryaci mayaudari mara rikon amana zuciyar shi ta bashi amsa da hakan.
Take yai matukar tausayawa kan shi do min kuwa yasan acikin garari rayuwan shi take zuciyar shi ta kara bashi shawara ka kira ta kawai don ka kirata shine wani abu.
A haka har barci ya dauke shi bai sani ba sai dare sosai ya falka tare da jin barci ya kauracewa idon shi alwala ya mike yayi ko zai samu relief a zuciyar shi idan yai sallah dare.
Hakan ne kuwa ya kasance dashi don sai yaji shi wani wasai dashi da rana ma bai sa wani abu a zuciyar shi ba.
Satin shi biyu cif da tafiya sai zaman doya da manja muke da anty Amira a gidan gashi ta hana min dan uwa shakat a gidan.
Da yai abu kadan yanzu zatayo cikin shi da masifa da zagi yadda ran ta yaso ita ko haka abokan ta zasu shigo suyi yadda ransu ke so agidan.
Ta mayar dani kamar wata kukun ta can tace Bintu zokiyi min kaza Bintu zoki dauke abu kaza haka nake takure da ita a gidan.
Lokacin komawan mu school yayi ranan da zan fara fita shiga nayi na mutunci irin ta matan auren da suka san kan su.
Ga socks da katon hijjab na saka a jikina fuskanane kawai mutum zai iya gani a lokacin.
Na samu anty zaune a falo na gaida ita nake fada mata zan shiga school ne.
Ko adawo lafiya ban samu ba har na fara tafiya na tuna da key din motan da ya bani na koma na dauko na kara fita.
Motar dake a rufe tasha wanki tun jiya yaya Bashar yasa aka wanke ta aka kuma cika ta da mai, fam.
Ina fita ashe sai Amira ta leka tana fadin yar iska ki taki sayyada ai a kafa don sai dai kije titi ki hai taxe .
Babu uban da zai kaiki da mota in kince kwadayi kuka iya ke da uwayen ki ai kunkai karshe gurin yaya sadauki.
Lekawan da zatayi ta hago har na zauna a mota ina service din ta wani irin ashar ra mulmulo daga bakin ta tana fadin kan uban can motar yaya sadauki fa.
Ashe akwai bura ubah a gidan nan kuwa ko ni ban shiga motan shi ba balle wanan bakar jakar kauyen ta ce shi zata shiga.
Nikan har maigadi ya bude min get nasa kai ina ganin fitowan ta cikin matsifa ban tsaya ta kanta ba nafice daga gidan.
A cikin masifa ta koma cikin gida tana masifa da zage zage wai sam bazata yarda ba da hakan.
Tayi kiran layin shi lokaci yana gurin wasa wayan shi yana kashe bai shiga ba.
Maji takira a cikin fada take fadin maji kinga abinda kika jawowa yaya ko kamar Bintu zatace ta shiga motan yaya ta fita da ita?
Amira kina da hankali kuwa mata da motar mijin ta har kike fadan wai ta shiga ke kije ki shiga ta mijin ki mana.
Kashe wayan tayi don har kukan takaici sai da tayi a lokacin gashi sai faman kiran wayan shi takeyi bai shiga a lokacin.
Ina isa makaranta idanuwan mutane yayo kaina caaa suna son ganin wake cikin wanan irin motan haka kamar yadda mutane ke saka ido ga abinda bai shafe su ba yanzu.
Sai da na gama na kulle ko ina na sako kafana dake cikin takalma mai hill wanda duk kwakwan mace da wuya ta samay shi a kasan nan.
Zan iya cewa a lokaci daya muka shigo da maryam don a lokacin itama ta fito har ta rufe motar ko.
Ina tsaye ina gyara tsayin hijjab dina da ya sauka har kasa naji tace madam you are welcome to new world.
Dariya nayi nace ,a,a anty kema shigowan ki ke nan dai yanzun ko ?
Tare muka jera da ita zuwa cikin makaratan sai kowa ya nufi department din shi.
Idanuwa akan mu don komai na jikin mu sai ya koma sabon yayi kasancewan mu amare sabbin fitowa.
Ban tsaya wani gaisawa da mutane ba don gujewa sabawa Allah don balain tsoro gareni.
Ban fito ba daga class sai da lokacin sallah yayi na tafi school mosque inda muke zuwa sallah.
Maryam ce ta kirani ga waya tana tambayan inda nake wai muci abinci.
Nake bata amsa da ina mosque tace nasan dama baki wuce can ai gani kofa idan kin idar kifito ina jiran ki.
Nafito na samay take cewa ga abinci can da tazo muna dashi don tasan idan tanice bazanci komai har mu koma gida.
Nace a ina zamu zauna ya ustaziya dariya nayi nace nice kuma ustaziyan yau kuma anty ?
Nace sai dai mu shiga motar ki don gaskiya bazan zauna a fili ba can muka nufa muna ci muna hira akan matsalan anty Amira.
Sai after six na iso gida a gajiye dani nasamu musa a takure yana jirana don fitana da ya gaji da zama ga takuran anty Amira ya koma gurin su maigadi ya zauna.
Dakuma yagaji ya dan fita mike kafa yabi titi har saida ya gaji ya juyo ya dawo gida yana kofan gida zaune na shigo gidan ya taso da fara,an shi a tare muka shiga gidan .
Babu kowa a falon nan muka zauna muna dan hira dashi nace bari na dan shiga na dafa mashi abinci.
Dakina nashiga na kwabe na koma kitchen nafara dafa abinci mai saukin dafuwa don a gajiye nake a lokacin.
Ban san zuwan ta ba sai muryan ta danaji a bayana tana fadi ke mara kunya yanzu ashe harke kina ganin kin isa shine kika fita da motan yayana.
May kike nufi da hakan dakikayi don duniya tasan dake ko kuwa kinyi ne dan gadaran kan ki ?
Nace anty banda amsan baki ni amma kina iya tambayan dan uwan naki ai kiji daga bakin shi don shikeda amsan tambayan ki.
Wani tsuki taja ta jyya tana fadin zaki gane kuren ki wallahi na aikat hakan da kikayi.
Nace wai may ke damuwan anty Amira ne haka duk ta wani bi ta canza rayuwan ta lokaci guda.
Yaya sagir ne ya shigo gaida mu karan shi na biyu ke nan bayan tafiyan dan uwanshi yana zuwa duba mu a gidan.
Shima yaya Abdul yazo amma saudaya ya zo gidan ya dubamu yana min sheri wai yaga na canza may ye sirin ne dayake shi mutum ne mai son barkwanci da mutane duk inda ya ke sai anyi dariya.
Nafito muka gaisa yana tambaya na ba dai matsalan komai ko nace ba komai yaya lafiya kalau muke.
Bai wani dade ba mukai sallama ya tafi don irin sadauki ne shi miskiline bai magana sai wanda yaso yi dashi.

****** ********* ******
Duk muna falo a zaune musa da yashigo abinci yake ci yana kallo, sai wayana yai kara na duba nomba bata kasar nan bace ta kasar waje ne.
Nai matukar mamaki da tambayan kaina waye kuma ya kirani haka ne wai?
Har kiran ya katse ban daga ba naci gaba da abinda nakeyi tana zaune sai faman dakilan wayan ta takeyi.
Wayan ya kara kara sai naga ta kalleni cikin zargi yanzu tsoron ta nake ji don ta canza gaba daya.
Haka yasani daga wayan don gudun zargi kada ta kulla min sheri gashi yau nafita zuwa school.
Mai shi baiyi magana ba nake ta fadan Assalamu Alaikum amma shiru ba ai magana ba nace please don't called this nomba agai iam marriage woman.
Murmushi naji anyi yace wata irin matar aure ce da bata san hakkin mijin ta ba sai kuri fadi da baki.
Sai a lokacin nagane cewa shine online ashe cikin yar murya nai murmushi don kafe ni da idon da tayi tana son tasan dawa nake wayan.
Nace shine zaka kira mutum kaki magana ni wallahi har ka ban tsoro ma naga nomban kasar waje ban san mai ita ba kuma.
Mikewa nayi tsaye don barin gurin kada taji fitinan mu don nasan shi zamuyi tunda ya fara fadin haka ina fadin.
Yaya ina wuni?
Tabini da harara

Please Login or Register in order to submit comment