Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

falon suke wanan hira da dane kafin maji ta hore su da rashin kunya da,tabasu amsa daidai da maganan su.
Sai da ta,dawo daki take fadawa maji abinda taji suna fadi kan tafiyan na sadauki.
Maji tace Allah ya sauwaka ai Allah yafi su ni dai ban wa dan kowa mugun nufi akan shi.
Amira tace ai ba zasu so suga ya zama abin kwarai ba tunda ba haka suke son ganin shi ba dama.
Ke kubar wanan magana duk ma abinda su ke nufi ni dai ga Allah na dogora.
Sai lokacin Bintu da bata faye shiga maganan su ba ta sa baki tace ai in ba abin mutum ba ba mai son yaga nashi ya lalace su dai suyi mashi fatan alheri kawai.
Ke kika san wanan amma ai su basu sani ba sunfi son ko yaushe su ganshi a hakanan inji Amira.
Amma maji kafin ya tafi da ki sa ai masa saukan alkur,ani maigirma Allah ya kare shi a can inji Bintu .
Ina da niyar yin hakan sai dai ban san wanda zan sa yai min ba tunda ba, baga hajiyan masa ba maji Amira tace mata da sauri.
Lalaifa haka za,ayi zan mata magana da ta san yadda zata samu na Allah da zasuyi min.
Amira tace ashe su ma wai har sun farga da wanan yawan barcin da yaya yake yi kwanakin nan
Ba sa ido bane duk abinda mutum yakeyi idon su yana a kai kamar wasu mayyu can
Mutane suce basu son suga dan uwan su a farin ciki ko kadan sai dai kullun aga kana wahalan tsiya kawai
Ai yanzun haka duniya ya koma hassada da bakin ciki yai wa mutane yawa a rayuwan su inji maryam.
Allah ai yafisu don duk abinda zasuyi Allah ya dai yana ganin su.
Uwar dai tana zaune tana jin su kala bata kare ce masu ba ga hiran nasu.
Duk zuciyar ta a jagule yake akan tafiyan da dan nata zaiyi a cijin wanan halin da ake ciki dashi.

A kullun, zancen Maji kan sadauki shine ya taimaka idan ya tafi ya kama kan shi da rayuwan shi acan.
Don Allah Baba na kada ka bamu kunya ni da mahaifin ka, sadauki yakan yi mata murmshi ne kawai yace kada ki damu maji insha Allah zan tsare kaina danan dacan kamar kuna tare da nine ai.
Mai masa ta tafi kamar yadda Maji ta bukaci da ta taimaka mata akan ai mashi addua kafin yatafi inda tabada kudi cikin asiri ko yaran ta basu san da zancen ba.
Da dare sadauki ya shigo gida inda ya samu maryam kaunan shi a tsaye gaban tsohon TV dakin su tana kwalan shi don ya tashi yai aiki don saboda tsufa ya gaji ya na tsayawa don kan shi.
Sai yake cewa ke Maryam kina ta faman kwalan Tv haka idan ya fashe fa?
Yaya idan ba dukan shi mukayi ba baya tashi sabofa ya tsufa da yawa sosai shi yasa muke dukan shi gashi za,ai program da karfe tara muna son muyi kallo.
Wani irin ba dadi yaji a,ran shi inda ya kara jin tausayin uwar shi sosai a ran shi . sai ya tuna yadda yaga dakin hajiya Kubura a ranan,
Komai akwaishi na,zamani a dakin amma su ga dakin uwar su kamar zaure ba komai a cikin shi sai yan tsofafafin kujeru da wanan tshon TV da maryam take kwalla.
Wani dogon huci yaja a fili har yasa su dago kai su kalle shi kan shi ya mayar saman makarin kujera ta baya yana shafo fuskan shi kawai.
Bintu tafito cikin wani dogon rigan atamfa wanda akaiwa dinki budade daga kasan shi.
Maji tafara sallah ishai a lokacin don haka ta waiga inda yake kwance saman kujera taso share shi amma tsoron shi take matukar ji.
Don haka takara waigawa still yana a yadda yake kamar mai barci, tace cikin daurewa yaya sadauki ina wuni.
Tankar a cikin mafarki ya tsinkayi zazzakan
muryan ta da take gaishe shi.
Batare da ya,sauke hannun shi daya kare fuskan shi dashi ba ya amsa mata da kyat da lafiya.
Tace akawo maka abincin ka ne yanzu kamar ba zai amsa mata ba sai can yace kawo min kawai.
Ta juya zuwa kitchen don ta dauko mata yai daidai da ya dago fuskan shi sai ganin bayan ta yayi tana tafiyan ta a cikin natsuwa.
Yace ke idan zaki fito ki zo min da ruwan sha daga nan, ta amsa mashi da tau kawai ta shige abinta.
Tana kitchen sai faman tunane take barkatai tana cewa, shi wanan haka Allah yayi shi da mudaden hali ne wai.
Girman kan shi da share mutane gami da nuna isa sunyi yawa don isa ma da izza wai ke yake ce mata.
Shigowan da Amira tayi kitchen din shi ya tsayar mata da tunanen zuccin da takeyi.
Amira tace abincin yaya sadauki ne zaki hada mai ta bata amsa a cikin ladabi da fadin eh nagan shi zaune nako san abinci ne ya kawo shi amma bai iya tambaya.
Amira tai dariya tace kin san shi magana ma matsalace a gurin shi kafin kiji yai magana aiki ne gare shi, dan dama idan da maji suke magana zai iya dan kai lokaci yanayi.
Tana hada abincin suke magana da Amira inda ta dauki abincin zuwa falon su inda yake zaune.
Wanan karon ta samay shi a,zaune ya dauki kafa daya ya dora ga dayan kafan shi yana kallon yadda maryam ke bugun TV nasu da karfi.
Daidai ta kusa karasowa inda yake taji yana cewa Please maryam kibar TV nan hakana idan ba zaiyi ba mana.
Bintu ta,kawo abincin a gaban shi ta dire mai zata juya yakw cewa ke mai aka dafa don banga cibi ba.
A tsorace tace mai tuwo ne shi yasa ban hado da cibi ba cikin jin tsoron shi take magana.
Da hanzari ta juya zata bar gurin yace ke dauko min cibi dan Allah ko tuwo ne ba,aci da cibine akace maki bakauyar banza kawai.
Simi simi Bintu ta juya zuwa kitchen din duk da zagin da yai mata yaci mata rai akan tai mashi abin arzikine kuma zakirata da bakauya.
Kai inji Maji da data idar da nafila take cewa kada na karajin kakirata da bakauyan nan don ba gurin ka tazo ba.
Ina laufin ta ta hado ma abinci don kai miskilancin ka bai bari ka tambayi mutane abincin ka.
Mikewa yayi tare da dauka abincin nashi yana kokarin barin falon don bazai yarda a raina shi ba akan bakuwar yarinyar Maji da bai san inda tafito ba.
A lokacin ita kuma Bintu tafito daga kitchen din dauke da cibin a hannun ta tana mika mai.
Yace ke barshi dan Allah ya fice daga falon Maji taja tsaki tace shiyasa ake ce ma mahaukaci yaji ta amma bai tsaya ba yafice kawai abin shi daga gidan zuwa part din su ranshi a bace.
Don shi bai son ai mashi fada a gaban yara kada su raina shi.
Sai bayan kwana biyu ya shigo gidan duk lokacin yana fushi wai maji ta kunyatashi a gaban kannen shi.
Jin gidan shiru sai maryam dake zaune falo tana karatu yace mata ina Maji tace mai tana ciki ta kwanta.
Yai kamar zai fita sai kuma ya tsaya ya mayar da hankali ga maryam yace ke,
Wai wanan bakuwar yarinyar da nake gani a nan daga ina tazo tace yaya sadauki kana nufin Bintu?
Yace ina ruwana da sunan ta nace dai ita din wacece ?
Tace diyar hajiyan masa ce makwaciyar mu Maji tace ta zauna nan don hajiyan yanzun bata zama tana jiyan yarta a kauye.
Ya koma tambayan ta a nan makwabtan mu suke ke nan shine maji tace ta dawo nan kuma,?
Tace eh daga kauye tazo karatu take kuma hajiyan masan bata zama yanzu.
Wani irin tsuki yaja yace kai Maji da kwashe kwashe take wallahi shine har zata disgani a kan ta?
Maryam duk ta kagu da tambayan da yake mata kada itama nata ya samay ta.
Idanuwan shi sun yi ja sun kada sai take tsoron ko ya shawo ne a lokacin.
Yana kokarin fita daga falon Maji tana fitowa tace ina jinka mara kunya dana kwaso ta akan ka nace ta zauna ko kuwa.
Tana kallon shi ido da ido taga idanuwan shi yadda sukai mai ja sun kade kamar an watsa mai barkono a cikin su.
Tace mashi kai mai kuma ka,shawo ne naga duk idon ka ya wani sauya haka.
Sai lokacin yace kai haba Maji shike nan ni banda aiki sai sha harda rana haka.
Kuna da lokacin shane tunda kun bushe filar ku baku jin kunyar kowa a wanan yanayin,
Kamar zaiyi magana sai kuma yace ni ban sha komai ba kaina ne dai tun safe yake min ciwo.
Ya juya yana fadin yanzun ma magani na sayo bari naje nasha na kwan ta, ya juta yafita daga dakin.
Yana tafiya Maji ke fadin in ma dai ka koma shane wanan kuma ruwanka.
Amma da yafita hankalin ta bai kwanta ba sai cewa take a ranta ko ya sha din ne ko kuma barin shan da yayi ne yake haifar mashi da ciwon kan oho.
Maryam ce ta katse da cewa nima wallahi yadda naga ya shigo ya tsare ni da tambaya tsoro ya bani .
Shiko yana fita sashen su na samari ya shiga kai tsaye ya nufi dakin su don da gaskiya kan shi din ke masa ciwo don rashin shan da baiyi ba kwana biyu.
Ya fada kan katifan shi batare da yasha maganin da yace ba din, kwance yake kamar mai barci yana tunanen kodai ya dan hada ne yasha ko zai samu relief.
Yana gurin a kwance sai faman sake sake yake a cikin ran shi kodai yashane ko ya bari.
Sai wata zuciya tace mai idan kasha shike nan zancen tafiyanka ya lalace.
Don ko kowa ya yarda Mani bazata yarda yatafi ko ina ba tunda ba bari yayi ba.
Amma wata zuciya kuma tana ce mashi yasha koda kadan ne don ya dan samu sauki a ran shi.
Mikewa yayi ya jawo ledan da yake aje kayan aikin shi a ciki yana kallon su sai faman sakan zuci yakeyi shi kadai a dakin.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYABA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,,,,


A LOKACI MU KE,,,,,,



Bintu bata da wani matsalar komai tsakanin ta da mummy da take zaune a shiyan ta.
Don mummy dai irin wayyayun matan nan ne masu faraf faraf da mutane ba,a gane gaskiyan cikin su.
Wata, yammaci da dare, Bintu tana kwance tana barci don yayi saurin kwanciya don ta gajiya sosai gashi bataci abinci ba da yunwa ta kwanta hakana.
Cikin dare yunwa ya damay ta don haka ta bude idon ta don ta sauko saman gadon da take kwance akai.
Tana son fitowa zuwa kitchen don dauko abincin ta da bata ci ba a daidai kofan dakin mummy take jin sautin muryan ta tana waya kamar haka.
Wallahi ina fada maki yau kwanan ta uku bata gidan tana can garin su ana mugun a bu,
Yanzun haka yarinyar da take gurin ta,da nake fada maki tana dakina ta barta ba,aje da ita ba.
Wai kin san may wallahi ni kin san ba yarda nayi da su ba matan gidan nan baki daya.
Kada taje can ta yi sa,a har ta samu galaba a kaina, don nasan kowan wansu ba wai ta zauna bane.
Duk yadda za,ayi gobe ki je min gurin nan ya kasance duk abinda ma taje garin su ta kullo a lalata min shi baki daya.
Bintu bata tsaya ta karasa jin komai ba ta juya a hankali ta koma dak8n da take ciki kwance,
Jin motsin mummy tayi don haka tamike zuwa dakin da Binta take kwance a ciki tagani in itace take sauraren hiran ta,
Jin motsin mummy tafito daga dakin ta yasa Bintu lafewa tankar mai barcin da yai nisa sosai.
Mummy ta,dan duba da kyautaga barci takeyi abinta hankali kwance,tai wani irin sauke ajiyan zuciya tare da dafe goshin ta tana fadi Allah ya soni yau da kashina ya bushe wallahi.
Komawa tayi taci gaba da wayan ta wanda babu wani abin arziki da take kullawa a cikin wayan sai kishi irin na kishiyoyin lokaci.
Imani da tsoro duk sun rufe Bintu a lokaci daya na irin maganan da,taji mummy tanayi a,waya akan uwar dakin ta, Maji ke nan.
Gaba daya kara tsanar gidan taji a ran ta kwata kwata babu mai imani da,tsoron Allah kowa kan sa yasani yanzu.
Idabn da a hira wani kefada mata abubuwan da taji Mummy tana fadi akan Maji da sai inda karfinta ya kare gurin karyata maishi.
Matar da duk gidan tafi nuna tausayin ta a kan Maj da yaranta yau kuma itace take wanan sake maganan a bayan idon mutane don tsaban iya kisisina na,zamani.
Washegari haka Bintu ta,tashi ta kasa sake jikin ta,ga yunwan da ta kwana dashi harsafe tare da,bacin rai na abinda taji mummy na fadi.
Ita ma dai yanzu gaba daya jin gidan takeyi duk yafita mata a,rai baki daya ba wanda ta yarda dashi dan dama maman ta watau maji ke nan.
Don in ba kazafi zatai mata,ba,zata iya cewa tunda ta,zo zama dasu bataga wani anin assha ba daga gurin maji har yaranta sai dai matsalan shaye shayen sadauki shine kawai abin da zata ce tagani na assha a gurin su.
Bintu tafito daga daki inda ta samu mummy zaune ta gaida ita acikin ladabi da biyayya.
Sai ta mike tana cewa cikin kwantar da murya zan tafi na gyarawa mama gurin ta don ina,ganin yau zasu dawo.
Kallon mamaki Mummy take mata tace Bintu yaki nan zo zauna muyi magana ta fahinta dake.
Komawa tayi ta zauna kamar yadda aka bukace ta da yi din.
Mummy sai da ta dan ja lokaci tace ba komai yasa na ce zanyi magana dake ba,Bintu sai ganin ki yarinya mai saurin fahinta,da sanin ya kamata.
Ina,fatan maganan da zan gaya maki zaki fahince ni ba,tare da,wani manufa ba a,ranki.
Murmushi Bintu tayiwa mummy kawai a lokacin sai da Mummy ta,dan yi shiru tace gaskiya Bintu a dan zaman da nayi dake na fahinci cewa ke yarinya ce mai mutumci da sanin yakamata.
Irin yarinyar da,na,dade ina gurin samu a,raina a gidan nan na rike ta.
Sai dai kuma,gashi kin zo min a ta,wani babban yanayi mai daure kai sosai, don zaman da hajiya maijidda zai ita kawo min akasi akan bukatana.
Don haka nake neman hadin kai a gurin ki idan ta,dawo don Allah ki jajirce kice a gurina na zaki ci gaba da zaman ki.
Kin daiga ni da ita,ba daya bane,don haka ki zabarwa kanki inda zaki zauna ki samu karuwa iyayyen ki, su ma su samu ta gareki,
Don kinga ni kudi zan dinga baki duk karshen wata sabanin yadda maijidda ta aje ki sai bauta mata kikeyi bata baki komai dake da gwagon ki.
Wani irin mumunan faduwan gaba ne ya daki zuciyar ta na wani dan lokaci inda tsoro da firgici suka ziyarce ta
Kanta ta,dukar kasa inda mummy take cewa ke nake saurate fa,
Murya kasa kasa take cewa mummy ai da nan da can duk dayane ni a gareni. Don duk mutunci ne ya hadani da kowan ku.
Ok tau yanzu zabi ya rage naki sai naji shawaran da kika yanke wa kan ki.
A cikin gatse tabata zuwa zabi don ta san bazata bar kudi ba da jin dadi ta koma inda uwa tsugunne diya a kwance ba dole zata dawo nan gurin ta inda ga dadi ga sutura masu kyau, ba second hand ba. Tasan dole ne ta dawo gare ta ma don ta kashe mata zuciya ko.
Haka ta mike ta nufi part din Maji tana tafe tana nazarin maganan mummy matar da a da take matukar ganin ta da daraja da sanin ya kamata tana tausayin uwar rikon ta maji fiye da ma mijin da ya hadasu zama tare a gidan.
Haka ta shiga gurin na maji tana aiki tana tunanen irin rayuwan wanan zamanin namu da muke cikin sa yanzu.
Har girki sai da taiwa maji tare da kamsashe masu ko ina na gidan.
Sai yamma Maji ta iso gidan da yaranta suna daukin ganin Bintu wace itama haka da murna suka tari junan su cikin jin dadi tsakanin su.
Tun fitan da Bintu tayi part din mummy zuwa,taron su Maji bata kara leko part din mummy din ba har zuwa dare takwas saura sosai.
Dan, ta mai bi ma na biyu ta tura wai a kira mata Bintu zata rufe part din ta.
Sai ga yaron ya shigo duk muka juya gurin shi inda ya nufo gurin da Bintu take zaune direct yana cewa,
Mummy tace nace ki zo zamu rufe kofan part din mu dare yayi wai.
Kafin Bintu tai magana Amira ta,watso ma yaron wani fitinaneniyar harara yaron ya,noke yana cewa mummy ce tace nazo na kirata ya juya yabar dakin zuwa,part din su.
Muryan Maji sukaji tana cewa,a,a Fatima tashi kije ku kwanta ko har kin gudo ne zaki mata halin yan duniya yau yau da dawowan mu.
Tashi ki dan tafi tunda ta aiko maki da sako bai kamata ace baki je ba kinji diyata ta fadi cikin dan kwantar da,muryan ta.
Shima yaron ai iyayi tsiyane dashi mai makon ya tsaya tun can yai sallama shine ya fado wa mutane daki haka.
Ai shi yaro dan auke ne baida laifi, an aiko shi kuma ya fada ya tafi a binshi yanzu shawara ya rage namu.
Maji takara yiwa Bintu magana da ta tashi taje ai yaune kawai gobe ta dawo dakin su.
A zuciyar ta take cewa Allah sarki Maji da kin san abinda ke nan da,baki barni na tafi ba ko yau din nan ma.
Ita ko mummy tana can dakin ta saikallon kofa take a kai akai tagani ko Bintu zata zo tabar Maji akan tayin da tai mata.
Zuwa can sai ga Bintu saye da,dan hijjabin ta tashigo gurin mummy a,bisa Umurnin Maji.
Sai dai ita kuma mummy tana ganin ai tayi nasara saye zuciyar Bintu da abin duniya shi yasa ta,dawo gareta.
Bintu na fita Amira tace maji da ma kin bar Bintu don naga bada son ranta ta tafi ba wallahi.
Allah ko ai ban san bata son zuwa ba da ban tura ta dole ba amma kuma,sai naga in munyi wa Kubura haka bamu kyauta,ba tunda har ta aikomata.
ko da,ta shigo falon Mummy tabita da kallo tare da,sauke ajiyan zuciya a fili, har ta karaso tsakiyan falon nasu.
Mummy ke cewa k8n wa kanki kiyamallaini yarinya don ba mai son wahala yanzu.
Bintu da bata ce uffan ba tashige dakin da take kwana abinta tabar mommy da yaranta suna kallo zaune a falo.
Tun shigan ta bata fito ba sai washe gari ta farka kafin kowa ya,fito tai ma mummy duk aiki kamar yadda ta,saba yi a kullun tare da,dafa ma,yan makaranta abinci.
Bada,sanin kowa ba ta kwashe yan kayanta zuwa dakin maji tunda farar safiya.
Koda Mummy ta tashiga gurin ta ta samay ta zaune sai cewa tayi kinga Bintu nasan kina jin kunyar Maijidda ne ki barni da ita zan san yadda nayi da zancen ta.
Fitan mummy daga gidan Bintu ta kwashe sai part din Maji da farko taso ta boye damuwarta amma sai su Amira suka fahinci da damuwa a tare da ita.
Da suka tambaye ta sai take cewa babu komai kanta ne kawai ke mata ciwo.
Sai zuwa rana kowa na sha,anin gaban shi Kubura ta dan fakaici ifon su ta kwashe komai nata sai dan gidan gwagon ta ta bude ta shiga.
Shiga da fitan ta duk akan idon sadauki wanda yake zaune kofan dakin shi sai dai furannin gurin sun boye shi ba za,a iya ganin shi ba.
Sai bayan fitan ta ne daga gidan shikuma yamike yabi bayan sai yaga gidan su ta shiga.
Nan yakoma ya zauna a inda yake zaune cikin tunanen irin nasihan da yasha gurin kamilin kakan shi dan matashin dattijo mai dan farin gemu a fuskan shi.
Kubura ta gyara ko ina tsab tunda dakin kwanan su har tsakar gidan nasu ita kadai a gidan.
Sai da Maji taji shiru bata ga fitowan yar amanan ta ba ta ce Maryam ta diba mata ita taga may takeyi.
Da sauri Maryam ta,dawo tana fadin Maji Bintu fa bata gidan nan nake gani.
Da sauri Maji tace kodai tana bandakine ki koma ki duba min mugani.
Aikuwa har bandakin ta duba ta kuma duba gurin kayan ta babu komai nata a gidan.
Da sauri ta dawo gurin Maji tana fada mata Maji har kayan Bintu babu a gidan nan fa.
Hakali a tashe Maji ta mike zuwa dakin hajiya kubura sai dai a rufe dakin yake shima.
Ikon Allah ta dawo dakinta nan ta samu yaran ta duk a cikin damuwa Maji tacewa Amira jeki gidan mai masa ki duba min ita da sauri.
Shigowan sadauki yayi daidai da jan hijjab din Amira ganin yanayin su yasa shi kalkon su cikin mamaki yana tambayan su may ya faru ne wai.
Bintu ce bami gani ba shine zan tafi na duba gidan su.
Ke zauna naga fitan ts tana cikin gidan su don nan naga tashiga dazun da rana.
A jiyan zuciya Maji ta sauke tare da cewa akwai matsala ke nan tunda yarinyar nan tai muna haka.
Haba Maji wai may yasa kika damu da zancen wanan yarinyar ne haka bayan ita bata damu da ku haka ba.
Kai ban son rashin mutunci Fatima a dan zaman da tayi damu ni nasan irin karuwar da nasamu da zaman ta nan din.
To may akai mata da zata gudu bata fadawa mutane ba har zata kwashe tabar gida.
Nifa na ganta ban yarda da ita ba yasa na tashi na bi bayan ta amma sai naga ta shiga gidan su.
Yanzun haka ma da zan dawo naga gidan a bude da alaman tana ciki har yanzu.
Amira maza jeki ki jiyo min ko may ke faruwa da ita har ta guje muna hakan nan.
Amira da maryam suka fita zuwa gidan hajiyan masa lokacin Bintu ta idar da sallah tana zaune ita kadai ta hada kai da kujeran dakin gwagon ta inda tafi zama akoda yaushe indan tana gidan.
Da sallama suka tura kofan shiga gidan inda tun a tsakar gida suka hango ta a zaune.
Bintu na ganin

Please Login or Register in order to submit comment