Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ko shi suke jira ya dawo.
Nan dai aka hada plain yadda za,a fitar dashi daga gidan muna zaune sai ga Umma da maji sun shigo dakin da yaya Sagir.
Can mukaji sun fito mani tace Amirah ke da Fatima ku sako hijjab kuzo ku fita da yayan ku can gaba da layin nan Sagir zaizo ya dauke shi sai ku dawo.
Haka akayi muka futa tare da munafuki, yana bin mu solai solai har muka wuce matasan nan sai hiran sukeyi suna cewa yau suna nan ba inda zasu sai yadawo don sun san idan dare yayi ai zai dawo gidan ne.
Bamu dade tsaye ba saiga yaya Sagir da mashin yazo ya dauke shi yaciro muna hijjab din maji muka dawo mata dashi.
Garin aka bari dashi zuwa wani kauye da yan uwan su suke can.
Muna shigowa still su Umma na dakin da mama da sauri suke tambayan mu sun tafi mukace eh ya dauke shi sun tafi,
Tace cikin ajiyan zuciya wai Alhamdullahi yanzu dai sai asan abinyi don Alhaji ya hau sosai wallahi.
Duk abinda ke nan abari da safe sai a san abida ya dace ayi.
Suka fita daga dakin tsomai tsomai dasu cikin tashin hankali nan akaje aka rufe gida.
Haka yasa mutanen dake dakon shi suka fara watsewa daya bayan daya daga zaman jiran shi da,sukeyi.
Washegari haka muka,wayi gari da yansanda sun dawo kara tambaya still sai da suka kars search din gidan ko yana ciki.
Ganin bsina suka wuce suna fadin da zaran angashi a hanzarta kai shi ga hukuma kafin su dauki mataki amma dole Alhaji ya tafi ya saka hannu a furin su.
Ranan kan anga tashin hankali don Baba ya ce sai Umma ta bar maigida ta nemo danta in ba haka ba zai dauki mataki a kanta.
Umma kuka ranan yaranta kuka cikin tashin hankali duk gida ya rude da kuka.
Sun matukar ba mutane tausayi sosai ga irin yadda Baba yai mata kaca kaca a tsakar gida.
Ganin haka yasa maji takira sadauki a waya yana dauka yake cewa maji yanzu nake batun kiran ki ai.
Na kira Baba wayan shi bata shiga lafiya dai yake ko don hankalina ya tashi sosai.
Babana kabar duk abinda kakeyi kazo gida akwai matsala babba ya taso a gida jiya.
Maji may yafaru da Baba ?
Tace ba Alhaji bane yayanka Imirana ne kaddara ta hau kan shi yaiwa wata yarinya karama fyade abin ba kyau wallahi.
Salati ya saka yace yanzu Imiranah yana ina maji?
Tace yana can anboye shi nan dai ta dan bashi bayani a takaice ta dora da fadin nasan Alhaji zai dauki mataki mai zafine akan shi yadda ya hasala din nan.
Yace to gani nan zuwa maji zan taso yau insha Allahu.
Sadauki bai shigo ba sai guraren shidda na yamma ya iso garin shida Bashar suka zo gida.
Ina daga ciki mukaji muryan shi ana gaidashi shine muma muka fito don gaidashi da dawowa.
Hankalinshi a tashe yake sai fada yake akan abinda Imirah yaja masu a gari.
Bashar yace yanzu mataki guda ne mu ganshi muje dashi gurin yan sanda asan abinda za,ai mai sai kuma muga iyayyen yarinyar mu basu hakkuri haka zai kawo dan sauki abin.
Yaya abinci fa inji maryam ?
Yace maryam bari kawai mu fita mu san yadda za,ayi wanan al,amarin.
Gurin Umma ya shiga yace ina Sagir tace yafita yace Imirah din yana ina ne yanzu?
Tace yana bodinga gidan yaya hassan tun shekaran jiya da dare.
Daga haka suka fita duk ta ramay tafada kamar tai ciwon shekara daya.
Basu tsaya ba sai gatin BODIGA can gidan yayan Umma sun samay shi ya ramay ya koma wani iri dashi.
Sunyi masu bayani kamar yadda suka tsara da farkon maganan duk da haushin dan uwan da yake ji amma ya matukar bashi tausayi sosai daya gan shi.
Gidan mahaifin yarinyar da abin ya sama suka fara zuwa tare da dattijan da suka dauko daga unguwan.
Nan dai aka,shawo kan mutumin sani Allah sani manzo har ya hakkura suka basu kudi har dubu dari uku wai aiwa yarinyar magani dashi tare da biyan kudin maganin da akai mata asibiti.
Nan kuma aka dunguma sai gurin yan sanda suma a kai rana dasu don sunce dole sai sun kuleshi har hukumar dake da Alhakin wanan shatian suzo.
Haka yasa aka nemo masu alhakin irin wanan matsalan suka zo suma saida aka shafa masu nasu rabon aka kashe case din sai dai anci kudi sosai wallahi.
Daga can suka kwaso zuwa gida gurin mahaifin su yana falon shi akace ana mashi sallama.
Yana fitowa yaga su sadauki da wasu dattijan shiyan ya juta zai koma aka dinga bashi hakkuri akan ya dauki al,amatin a matsayin kaddaran rayuwan yaron ne.
Yace aiba yaune yafara haka ba kungan shinan shedanin yaro ne don har wata yarinya ya taba yiwa ciki yanzun haka dan zaman shi yakeyi.
Yaro yace ya zauna bai mayar da zina bakin komai ba.
Yace yabasu su uku nan da wata uku ko mutum bai shirya ba sai yai mashi aure da kan shi.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,


IDAN KIN TURA WANDA BAI BIYA,BA BA MU YAFE MAKI BA ALLAH YA ISAN MUNA AKAN KI,,,,,,,


Sadauki bai koma ba sai dai yayi duk yadda malamin nan ya umurce shi da yi a baya.
Ya kama hanya yatafi an muna E,passport na batayi tare da duk wani clearing din da ya dace aiwa masu tafiya.
Na kira kabir nai mashi albishir kamar yadda ya dace nan fada mai don ya,sani .
Sai na fahinci bai yi farin ciki ba da hakan take naji raina ya naci nace, amma ka bani mamaki yayana da zakaji alheri haka ya samay ni ka kasa tayani farin ciki.
Yace umma gaskiya Fatima ban iya munafunci ba don haka idan nace maki nayi farin ciki to na munafunce ki giskiya.
Cikin mamaki nace Yaya Kabir lafiya kake kuwa ?
Yace lafiya ta kalau Fatima ,
Wanda dai ya kaiki saudiyane ban yi naam dashi ba gaskiya.
Kana nufin wai yaya sadauki ke nan?.
Yace shi nake nufi Fatima ya,fadi a takaice kawai ba shakkan komai
Yace ina matukar kishin zaman ki da yaron nan gida guda Fatima, a duk lokacin da na tuna cewa a guri daya kuke sai naji banjin dadi wallahi.
Don ni mutum ne mai matukar kishin iyalin shi sosai ina kokarin ganin matata bata mu,amula da wasu maza koda yan uwanta ne ko nawa.
Nace amma dai kasan ni ba,watsa,tsa bace haka shima wanda kace baka kauna din ba dan iska bane hakana.
No Fatima baki fahinci magana ta bane don haka mubar zancen haka nan Allah ya kaiku lafiya ya dawo daku lafiya ba shike nan ba.
Nai fushi na kashe wayan ba yadda na,saba yi mashi shagwaba ba idan zan kashe wayan.
Ni kadai maganan tai ta cina a,rai har na gaji na sake don kaina.
Nai fushi da yaya Kabir da kyat ya shawo kaina muka shirya dashi yana ta kamay kamay, wai shi ba wani abu yake nufi ba,
Hakalin shi, bai kwanta bane don kada yaya sadauki ya kwace mashi ni yahana ya aure ni ace yar gida gida za,ayi.
Jin maganan nayi cikin haushi da takaici, don may zai hada ni da yaya sadauki mutumin da yake a matsayin yayana yake a gareni.
Nan na nuna mashi ban ji dadin yadda yake min ba a matsayin yaya fa,sadauki yake gareni.
Amma shine zai ce, wai sadauki na iya kwaceni daga gareshi, ya aureni wanan maganan tai min zafi yadai bani hakkuri aka zauna lafiya.
Munsha magana gurin mutanen gidan mu da,ma,wasu yan sa ido akan zancen tafiyan mu,

****** ********* ******
Mun isa kasa mai tsarki, saukan asuba mukayi a garin kafin agama muna screening har anyi kiran sallah asuba ko.
Wasu motoci muka samu suna jiran mu su suka kwashe mu sai masaukin mu a cikin garin madina.
Bamu dauki tsawon lokaci ba muka fita zuwa masallaci don muyi sallah da ziyara kamar yadda yazo ga sunah.
Ibada muke sosai ba kama hannun yaro daga mu har uwar mu da yayan mu sai yaya,Bashar da muka zo dashi.
Aiki tukuru komai bamu da matsalan shi sai mura da ya kama mu kawai a garin don sanyin Ac da ruwan sanyi da yai muna yawa.
Yaya ke sayo muna duk wani abinda zamu bukata sai ya tambaye mu ko may zamuci daga haka har ya gane favorite abincin da kowan mu ke so.
Kwanan mu tara a na goma muka kama hanya sai garin makka nan ma mun samu anyi muna masauki inda zamu sauka .
Bamu kwana ba sai da muka je mukai dawafi a can muka kwana sai safe muka dawo masaukin mu.
Barcin gajiya mukayi bayan munyi wanka muka kwanta, mun tashi mun samu har mama ta farka tana zaune tana waya a gida.
Zaune muke a falon dagani sai ita su Amirah ana can an baje ana barci a cikin A,C.
Bashar da yaya sadaukine suka shigo dauke da abincin rana da zamuci.
Ganin da sukai min zaune a kasa gap da kafan mama nake zaune kamar wace zata koma ciki .
Fatima ke har k8n farka ke nab baki gajiya dai, mama ta karbe da cewa ai kai dai Bashar wanan yarinyar har mamaki takw bani karama da ita amma yawan ibadan ta kamar wata babban mace can wallahi.
Daga inda yake zama idon shi ya na a kaina yake cewa, addu,a takeyi wa mijinta kila ko kuma maman ta.
Ai na gode da Allah ya ban diya irin Fatima mai ibada ga sanin ya kama ta a tare da ita ko yaushe.
Kai maji kina da fasawa wanan yar kauyen yar taki kai koda yake yanzu naga,ta fara wayewa,ai don ina Allah Allah kada,tai muna,kauyancin ta, ta,bayar damu a cikin mutane muji kunya.
Nace cikin dan jin nauyi da kunya kai haba yaya wai kai kullun dai a bakauya nake a idon ka ne?
Kyaleshi Fatima ba abinda zai gwada maki yanzu na wayewa jirgine dai kin haushi don kin gama sanin komai.
Kai mama don Allah bari kada ta dauka ko jirgi shine karshen kauyanci a duniya.
Kada fa ka,zabo matar da tafi Fatima zama yar kauye muga tsiya wallahi don dai yanzu kasan Fatima ko kai sai kayi da gaske zaka gwada mata wayewa.
Aiko cikin auri yace don Allah MAN ka bari ka fa san a kasa mai tsarki muke kada yan amin su karba muna.
Nan suka dinga mashi sheri suna ta dariya yace aiko da na karkarya yar kauyen banza da duka.
Dariya nima na kama nace ni yanzu yaya idan ,al,amarinka ne bana jin haushi balle nayi kuka akan zancen ka.
Da can bayane da ban san halinka ba nake kuka yanzu ko kin waye ko?
Ya tambaya cikin son jin amsata daga bakina amma sai nai shiru don maji tace na kyale shi duk abinda zai fadi na dai fishi ne yasa yake jin haushi na kawai.
Bai da rowa ko kadan sai da,wanan tafiyan ya hada mu na tabbatar da hakan don duk abin da kannen shi sukace suna so shi zai masu ko nawane.
Munyi ibada munyi rokon Allah sosai ba dare ba rana muka kammala aikin mu muka fara shirin dawowa gida.
Naiwa iyayyena da yan uwana tsaraba haka naiwa Kabir shima nashi kalar tsaraban da ya dace da shi.
Munyi mamakin dawowan mu, gida muka samu an gyara ma mama part din ta gyara sosai na gaske akai mata na zamani mai kyau,.
Tafita daban daga sauran part din matan gidan an sauya mata komai nata ya koma side din ta daban yake a cikin sauran sai dai still a gida guda ake kuma farfajiya guda.
Mun shiga gida mun zama wasu abin sha,awa gurin mutanen gida sai sabon hassada ya kunno kai kuma.
Kishi kumallon mata nan zance yafara yaduwa cewa ba kudin halas bane shine muke tin kahon mun tafi saudiya wa mutane.
Wasu su, ce ai shi kan shi sadauki baya taimakon kowa,sai uwarshi da yan uwan shi ya sani kawai.
Sun manta duk irin taimakon da yake masu a cikin gida yanzu komai shine yake kawowa ayi amfani dashi a gidan don yanzu Baba yai sanyi sosai ga arzikin shi.
Ya rage saura wata biyu kacal buki na da Kabir, don haka bayan mun dawo su Baba sun shigo taron mu shida mama tabawa da wata kawar ta da tazo gulmq taga inda nake.
Nan Baba Alhaji yake bawa babana shawara kan kada ya tayar da hankalin shi akan zancen aurena.
Duk wani abinda za,ayi agurin bukin shi zai dauki nauyin yi da shi da matar shi Maji.
Baba na yace amma Alhaji auren ta na farko ke nan ya kamata ace a dan bari nima na taima a wani gurin inda ya dace dani na kauye.
Babu komai ai duk yiwa kaine don Fatima ta cancanci ai mata komai a rayuwa ai.
Sun dan yini muna sukai sallama na basu tsaraban su suka kama hanya sai gida suka koma, inda nace masu zan shigo karshen wata don nazo naga mahaifiyata .
A bangaren Kabir kuwa ji yake tankar ya lashe ni don irin so da kaunan da yake nuna min abi yai yawa sosai.
Duk da lokacin ya matso sosai amma shi gurin shi shine yadai ga an daura muna aure ace ni mallakinsa ce.
Sai kuma gashi ya dan bijiro da wani zance, wai yana son a dan kara matso da bukin don yana son zuwa wani course a lagos na wata daya.
Da zancen yazo wa Maji sai cewa tayi ace yayi hakkuri tunda an fadawa kowa sai wanan lokacin za,ayi bukin.
Da kyay dai na samu na shawo kan shi ya hakkura sai lokacin za,a daura aure daga baya sai na tare idan ya dawo.
Maryam itace ke shirya komai a kan sha anin bukin sai dariya mama da Amira suke muna.
Shiko yaya,sadauki yabi ya koma wani silent dashi koda yaushe fuskan shi a daure take bai wani walwala,
Shi kan shi din ma ba zai iya cewa ga matsalan shi kawai dai haka yake jin jikin shi ba dadi.
Haka ya daure yana yan al,amururinshi cikin rashin kuzari da walwala a tare dashi.
Kumshi da kitso da gyaran jiki duk su akai min zan fara zuwa na hadu da Kabir da,zai shigo inga mahaifiyana sai na,dawo sokoto sai gobe daurin auren mu zai dawo garin don suna,aiyuka yanzu sosai.
A gidan mahaifiya na ya iso da yamma na fito na sanay shi yana tsaye jikin motar shi nafito daga cikin gidan namu.
Murmushi a fuskan shi har na karaso gare shi yake cewa kai Fatima kinga yadda kika koma kuwa tun auren bai karaso ba kin koma haka?
May mamatake baki haka ne wai ?
Murmushi nayi kawai ,
Yace ban yarda ba don dai kawai baki son nima abani na koma hakane kamar yadda kika koma din.
Yace ya naga fusksn ki yau duk kwalliyan da kikayi amma babu walwala sosai.
Nace cikun dan yake wallahi kaina ne ke min ciwo sai faduwan gaba dake yawan damuna duk kwanakin nan.
Ya kara dan matsowa gap dani yace shine baki fada min ba ?
Kuma tun yaushe kike jin hakanne wai?
Na lumshe idanuwana nace tun kan nazo ne nake fama da hakan.
Yace da kinga likita tun acan Fatima, don asan abinda ke damun ki don kin ga nan kauye ne.
Wani irin kamshin turaren shi ne ya daki hanci na,wanda har na dan sauke ajiyan zuciyar da ya baiyyana a fili, saboda matsowan da yayi gap dani a lokacin.
Yace ko mu tafi ne ki ga likita sai mu dawo ?
Na bude fararen idanuwana ce na samu sauki ai ba matsala.
Yace da gaske kinji sauki kodai baki son zuwa ne likita ya duba min ke ?
Na girgiza masa kai nace ba hakana bane kawai dai ba,wai sai naga likita bane.
Yace toh bari na bude maki mota ki zauna a ciki don kada tsayin ya damay ki ko?
Ya bude motan na shiga dayan bangaren na zauna, sai ya rufo min kofan,
Shima yya zagaya ya shiga ya zauna daga dayan bangaren .
Wani irin sanyi ne da kamshin motan ya ziyarce hanci na dana zauna a motan
Take naji wani irin kasala ya dan fara rufeni a hankali, nan muka danyi hiran mu dashi a,tsatsaye don na matsu na koma gida na kwanta.
Waya ce aka bugo mai a yadda na fahinta daga ma,aikatan su ne suke magana dashi kan ana neman shi a gurin aiki.
Bayan ya gama wayan ya kashe ya ja tsuki yake cewa kai baz,a bar mutum ya huta ba da amaryan shi.
Yanzun kuma wai aiki zamu tafi a wani kasan shine ake neman mu.
Murmushi nayi nace ai neman halak ne don haka muna son aiki ko yaushe tafi zaman jiran tsanmani.
Yani sa yace wallahi haka kawai sai nake ji kamar nace na fasa don ban son rabuwa dake ko kadan Fatima.
Nace cijin yar murya har kwana nawa ya rage ka mallake ni a gidan ka idan kayi hakkuri.
Ya shafo fuskan shi yana cewa hakane kuma fa gaskiya dai sai naga ni lokacin ma yai min tsawo sosai.
Abinda bsi taba min ba shine yau yai min don kamo hannu na yayi ya hada da nashi ya matse guri guda ba,tare da ysi min magana ba na,wani dan lokaci mai tsawo.
Cikin yar siririyar murya nace mai sakeni yaya don har yanzu fa ka san,akwai sauran lokacin hakan gare mu.
Yace cikin murya mai kasala hakane Fatima yanzun dai ina son idan kin koma saiki fadawa maryam duk wani abinda ya dace ku shirya shi da,wuri don da an daura aure abuja zamu wuce acan zaki sha amarcinki.
Kunya maganan shi ta bani da sauri na bude kofan motan kafana daya a waje nace maganan ka tana sani jin nauyi da kunya wallahi.
Yace nima haka ya dan kwaikwaye ni.
Mukai sallama dashi tinda safe ya kama hanya sai Abuja don aikin su ba hutu.
Sai da na kara kwana biyu a gurin mamana nazo gurin Baba na nai kwana daya na dawo sokoto da zama.

****** ********* ******
Mamana ta sokoto cikin gyarana take sosai abubuwa take bani na kara lafiya da gyaran jikin na.
Nai kyau nasha gyara sosai na canza gaba daya duk wanda ya ganni sai yai maganan hakan.
Amma har lokacin banjin dadi a cikin raina nasan cewa jimamayn rabuwa da su mamane yake damuna a zuciyana.
Don in suna min sheri sai naji kamar nai kuka ban son zolayan da,suke min na amarya ta angi yar shagali yar biyan bukata yar garali.
Amirah tace makullin mota ke akaba, wani sauran canji ke akaba, nikanji wani iri a raina sosai.
Ko yaushe Kabir muna waya dashi yake ce min zasu tafi kasan Benin wani taro na kasa da kasa.
Cikin dare yaya,sadauki ya dira a sokoto sai ganin shi mukayi kwatsam.
Murnan ganin shi kamar kullun yan uwan shi da mahaifiyan shi sukayi nima dai nai farin ciki da ganin shi don ban boye ba sai dana baiyyana a fili.
Ranan har ina mashi tayin abinci sai lokaci ya,dago yana kallona gaba daya sadauki yaga na sake mai .
Da sauri ya kawar da idanuwan shi daga kallona na kara tambaysn shi da cewa.
Yaya a kawo maka abinci ne kaci?
Yace au yau kuma duk murnan za,a gidan tsoho ne yasaka ake min tayin abinci haka?
Kasan fa amarya ce dole abita sannu yaya duk cikin murna ne hakan ai.
Na bata fuska na dan marairaice nace haba Anty Amirah sai ana maganan gaskiya kuma ki jefo wani zance can na fadi cikin shagwaba.
Yaushe rabo da kiba yayan mu abinci Bintu ?
Nace kai anty Amirah nifa yayanane yadda kike son shi haka nake son shi don haka kada ki bata ni gurin yayan mu ko yayana ?
See her bakiji kunya ba ni wai maji yar taki duk murnan auren ne yau take cewa nima yayan ta ne?
Yaya ni kima yar kaunar taka har zakai shakkan haka a gareni nifa yanzu banda kaman ka a duniya don ku ne uwata da ubana.
Murmushi yayi ciki ciki, yace to kawo min abincin na wuce ina yar dariyan jin dadin mun shirya da yayan mu yau.
Nakawo mai abinci na aje nace ko na karo ne yaya ?
Yace kai Maji wanan yarinyar taki fa ta rainani da yawa may kika mayar danine wai ?
Yaya nace a taikace.
Na dora da fadin wanda yafi min komai a duniya .
Yace har da dan tsohon mijin ki ke nan?
Nace ai shi mijine kai ko dan uwa rabin jiki.
Sosai yaji dadin zance na har cikin ranshi yake cewa a rayuwan shi ashe haka yarinyan nan take sauki kai ne da ita haka, ninr dai ban fahince ta ba ashe?
Waya da Kabir ya bugo min ne ya dakatar dani nabar gurin zan wuce niji yana fadin tsoho yai kira ke nan ?
Na dauki lokaci muna waya dashi sannan na fito falon na samu yana cin abinci suna fira da mahaifiyar shi.
Yana fada mata cewa maji mutumin nan fa abin tsoro ne wallahi sosai don yanzu.
Daniel bai yarda ko mu hada hanya dashi duk yadda muke da yawa a guri zakiga ya koma gefe daya.
Nace mugu ke nan dan ban Allah yafishi wallahi don ba abinda zasu iya dakai don kai daga Allah kake.
Dariya sukayi nace wallahi anty na rasa may yasa mutane suke yawan saka ma yaya wanan irin kiyayyan haka.
Maji tace hassadane kawai Fatima kin san in Allah ya haska mutum dole dama sai ya samu wanan kalubalin daga mahassada.
Mukan Allah ya kara tsare muna kai a duk inda kake yaya sai kuma addu,a don Allah akara zagewa don makamin mumunine.
Yau kan ni naga yar taki ta canza fa.
Dama haka take kaine dai baka gane ba kana ganin tana maka kokari kaiko kana ganin kamar sa idone.
Ya ce na sani maji.
Ta faye kauyancine shiyasa nake sake mata layi.
Bintu Kabir har yanzu bai dawo bane daga Benin din ?
Nace yace ysu da dare zasu sauka a lagos sai gobe zai karaso abuja zuwa jibi ya iso nan.
Ku dinga sa insha Allahu mana a zancen ku Fatima inji maji.
Nace insha Allahu mama,,
Kokefa to kuna magana kamar ba musulmai ba.
Ita fa maryam ta matsu Kabir yazo ta amshi dumus don zancen ta na kudine kawai.
Ya mike yana cewa zai shiga yai wanka yaje gun Bashar don yana son ganin shi.
Munyi hira sosai da daren kafin mu kwata bayan nai wanka nai shirin kwanciya

Please Login or Register in order to submit comment