Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Ta dawo daidai irin yadda yake son macen auren shi ta kasan ce mai a rayuwan shi komai normal.
Yana zaune sai faman tunanen al,amarin Fatima ya keyi yaji anyi nocking din kofan shi kafin ya amsa sallaman shi yaji an turo kofan dakin don dama a bude take.
Linda ce tashigo dakin abinda yasa shi saurin tashi zaune ke nan a lokaci guda.
Da sauri ya mike zaune da kyau cikin dan kaduwa don baiyi expecting din zuwan ta saboda sun dade basu hadu ba da shi, tun lokacin da ya sasanta da Fatiman shi yaji gaba daya linda tafita mashi a rai.
Linda may yakawo ki gurina again bayan na fada maki abinda nake bukatan kiyi kince bazaki iya ba.
Ta watso mashi wani mugun kallo na see you tace to maye don anzo gurin ka saboda wanan karamar yarinyar daka aura ne da batafi sixth ba.
Yace don't dear insult my wife she is part of my life now.
Ganin da gaske yake nufin maganan shi har cikin ran shi irin yadda taga ya hade rai a lokaci guda haka don tasan halin shi sarai gurin rashin mutunci idan ya tashi yi.
Ta dan marairai ce tace haba my man kada ka mance da alkawrin dake tsakani na da kai mana please.
Yace kema kin manta da alkawarin da nayi cewa idan ba zaki musulunta ba ba zan iya auren ki a haka ba.
Rashin yardan ki yasa har iyayyena sukai min zabin mace da kan su wanda yakai yanzu na gane cewa gata sukai min da hakan.
Don haka tunda kin zabi son iyayyen ki a kaina nima yanzu na zabi zabin iyayyena akan ko wace mace.
Don haka ki tashi kifice min a gida i don't want to see you again, dont ever think about me again its over now.
Linda tace my man ni kake fadawa haka akan wanan little girl dinka wai wife kake nufin kayi komay.
Ka sanni ni na wuce ka wullakantani akan wanan yarinyar don kasan asalina ka kuma san waye ubana a kasan ghana.
Amma tunda kace haka jeka zaka gane kuren ka zaka gane ni Linda ba abin wullakantawa bace a take lafiya.
Ya ja dogon tsaki tare da nuna mata hanya yace babu abinda zangani sai alheri tunda bake ce Allah ba banza dake kawai.
Kije ki rike addinin ki da iyayyen ki nima na rike nawa koba shike nan ba.
Tsayawa tayi na dan lokaci tana kallon shi babu abinda zata iya don tasan ba saurarenta zai yi ba ma yadda yayi.
Ta juya kawai tafice kamar yadda ya umurce ta da yi ran ta a bace tabar dakin nashi.
Komawa yayi ya kwanta ranshi a bace da Linda duk da yasan tana matukar son shi amma ya zama dole yanzu ya kawo iyaka a tsakanin su kawai don Fatiman shi tariga da tai masu zara ko ta ko ina.
Ya sake wani dogon tsuki kawai tazo ta bata mashi jin dadin shi da yake ciki a lokaci guda na Fatiman shi.

****** ********* ******
Nai wankan tsarki a yau don haka na baro school da wuri don ina son a wanke min kaina a gayara min shi.
Shagon da muke zuwa da maryam gyaran kai na nufa daga gyaran kai har na jiki sai da matar tai min shi ban dawo gida ba sai yamma lis na shigo gidan.
Ina farka motana sai ga mai wankin mu Atiku yazo inda nake tsaye ina kokarin rufe motar ke nan yake cewa.
Hajiya barka da dawowa, sannu da zuwa dama tun dazun nake jiran dawowan ki.
Na juyo nace a,a baba baka tafi gida bane yau yace wallahi hjy ban tafi ba na dan tsaya don naga dawowanki ne don wallahi ina da bukatane.
Shine nace bari na kawo maki koke na ko zaki taimaka min ki bani koda dubu goma ne idan anyi biya saina mayar maki ko kuma a cire daga cikin albashi na wanda dai yafi sauki daga ciki.
Wallahi matata ce amarya na ba lafiya don tana fama da laulayin ciki ina son ta tafi asibiti dana kuma Aliyu ya gama makaranta zai shiga secondry gashi har an fara karatu amma shi yana gida a zaune.
Tausayi mutumin yabani don gaskiya gaba dayan su yan aikin gidan suna da matukar mutunci sosai.
Nace mai ya bari na zo ita kuma mara lafiyan Allah ya bata lafiya mai karatu kuma Allah yabada sa,a sai na shiga.
Kudin da yaya yake bani ne bani kashewa na dauko dubu ashirin daga ciki nafito dashi.
Nabashi goma naba maigadin dare dana rana dubu biyar biyar su raba.
Atiku yace hjy nagode insha Allahu da anyi biya zan dawo maki da kudin ki da yardan Allah.
Nace haba Baba ka barshi na bakane kawai kaje kayi amfani dasu idan zai ishe ka.
Da sauri ya juyo yana cewa hjy kin bani wanan kudin haka dukka ?
Ikon Allah sai naga yakai tsugune tafara fadin Hjy nagode nagode yadda kika rufa min asiri Allah ya rufa maki duniya da lahira.
Allah yabaku zuria masu albarka a rayuwan ku, Allah ubangiji ya tare ku daga sherin makiya nagida dana waje.
Nace amin baba nagode da adduan ka baba sai ga sauran sun karaso suna min godiya da addua su ma.
Nagode masu na shige ciki don duk nagaji a lokacin wanka nake son yi nai sallah kawai sai na nemi abinda zanci a raina.
Ina shiga malam musa yace Atiku kaga ikon Allah ko yau inane baka shiga ba a garin nan dan neman rance amma baka samu ba.
Yanzu kaga ikon Allah ko yar arziki irin albarka nikan ai gobe gidana cefane lafiya na lau insha Allah.
Kai mutane mutane magindanta suna cikin wani hali yanzu na bukata saboda motsalolin rayuwa da yaiwa mutane yawa a wanan lokacin da muke ciki.
Duk yadda kake ganin kanka a cikin matsi wani nacan yafika don haka ko yayane ko ba yawa ka taimaka wa na kasa dakai don ita addua ba,a san inda take kamawa ga bawa ba.
Da wanan irin tunanen na shiga wanka nafito sai na jini wasa ina idar da,sallah naji abinci kawai nake bukatan ci a lokacin.
Don haka na fito na nufi kitchen don agazawa cikina dake dan kugin yunwa a lokacin gani ni kadai a cikin gida kamar mayya dani.
Hakan yafi min da zama cikin tashin hankali da anty Amira ke zuwa yi min wai da sunan zama.
Indomie na dafa na dan cika mai attardu nan da nan ya dafu na zauna naci nasha ruwa na kawar da kayan danaci abincin.
Kofa na rufe don karfe takwas na dare nasan babu wanda zai zo kuma gidan a lokacin.
Dakina na koma bayan na kashe duk wani kayan wutan dake falon, wanda shigana yai daidai da rurin da wayana ya soma a lokacin.

****** ********* ******
Yaya sadauki ne a layin da murmushi a fuskana na dauki wayan nace Assalamu Alaikum.
May ye hakane sai yace min babu ko dan irin honey, darling, sweet heart din nan sai ki wani ce min wai assalamu alaikum kawai ?
Nace haba yayana ni wani suna kuma kake so na canza ma,bayan wanda Allah ya dora maka a kaina na yayana.
Yace No ban yarda,ba gaskiya ni suna nake son kawai a canza min nagaji da yaya din nan kamar wani mai yaye miya yabar tuwo gaya can dani.
Ban san lokacin da maganan tashi tabani dariya ba nace kai haba yaya baka son girman ke nan kuma ko?
Yace kin daiji na fada maki ni dai ban son wanan sunan yayana din don haka yanzu basai gobe ba sai naji sunan da aka rada min din.
Shiru nayi ina tunanen ni yanzu wani suna kuma zan kirashi dashi indai ba son matsawa rai ba.
Ke fa nake saurare Fatima na nisa nace to yaya love yace daya nace my life ko?
Sai naji yai murmyshi yace to ke fa amna kamar wata tsohuwa can wai kullun yaya yadan make muryan shi yana,kwakwayona yadda nake kiran shi da sunan yaya.
Nace kai yaya nidai wallahi kana son ace min banda kuya daine wallahi amma idan akaji na canza maka suna ai za,a kalleni wata mara kunya can ne.
Yace da sauri mutane mutane su zasu hana ki dadada min zuciya ko kuwa ?
Shiru nayi yace abar wanan zancen yaya bakon ki yatafine ko yana nan ?
Da,mamaki na tambaye ina fadi bako kuma yaya ?
Waye yaya ko da wani kike magana,ne acan kusa dake ?
Nai sauri na tuna ina cewa wai yaya love wani bako kake magana ne wai ?
Wanda ya hanani farincikina da aka saba min mana, duk hakan bai sa na kawo tunane na akan period yake maganan shi.
Murmushi na dan yi a hankali nake cewa yananan har yanzu bai tafi ba da karfi yace what kina nufin har yanzun mesestration kikeyi nace eh yaya.
Shiru na dan tsawon lokaci baiyi magana ba sai can yace ok kina lafiya dai ko?
Nace mai Alhamdullahi dan hira,muka taba sama sama ya kashe wayan yana min sai da safe.
Har barci ya kwashe ni a gurin inda nake a kwance sai faman tunanen shi nakeyi ina matukar mamakin wanan sauyin nashi nace Allah ke nan mai iko yau wai ni Fatima ce yaya sadauki ke wa wanan kulawan haka yanzu.
Washe gari bayan nayi sallah na fara aikin gyaran gida da ta ko ina duk da gidan ba wani dauda ke gare shi ba sosai amma,sai kyalli gidan ke yi kawai.
Haka kawai nace bari nai girkin abinci rana mai kyau da haduwa ,sosai na zauna na girka ..
Sai da ga abincin na gama amma kuma na kasa cin komai daga ciki sai kallon shi nakeyi a gabana kawai.
Abin mamaki sai gani ina kewan ganin yaya sadauki don ina bukatan ace yanan yaci wanan girkin dana hada.
Ban kai ga karshen tunane na ba naji bell din gidan yana ringin a kasalance na mike zuwa duba wanda dake sallama a kofan gidan.
Yana tsaye rataye da coth din shi a kafadan shi sai yar jakar kayan shi dake sabale a hannun shi.
Na kasa boye farin ciki na dana gan shi a lokacin na ji kamar na fada mai a jikin shi na rungumay shi amma kuma bazan iya yin hakan ba.
Kamar wanda ya karanci zuciya ta a lokacin sai naga ya ware min hannayen shi da sauri ba bata lokaci na fada tsakiyan hannayen shi.
Ya mayar ya rufe ni dasu ina jin yadda yake sauke ajiyan zuciya a hankali kamar yadda nima ajiyan zuciyar na sauke ina cewa sannu da zuwa yayana.
Dago kai yayi tare da dan ture ni baya kadan nai mamakin hakan sai ji nayi yace niba tsoho bane da zaki dinga kirana wani yaya can na fada maki kuma sai kin biya bashin hakan da kika fasa min tunda na fada maki bana so.
Da sauri nace iam sorry my life ai min afuwan please bazan kara ba da yardan Allah.
Murmushi naji yayi tare da cewa yana tafiya ina tafe a bayan shi tare da jakar dana ansa a hannun shi.
Zubewa yayi saman kujera yana lumshe idanuwan shi a hankali dakin shi na wuce na kai jakar na dawo na dauko drink hade da cup na nufo shi.
Idanun shi suna a lumshe hannun shi na saman wuyan shi yana kokarin cire nicktie din da ya daura a wuyan shi.
Na tsiyaya mai ruwan lemo a cup tare da dago cup din ina cewa uhmm, yaya love ga ruwa kajika makoshin ka dashi ko.
Sai a lokacin ne ya dan bude daradaran idanuwan shi ya sauke idanuwan shi a kaina.
Sai ce min yayi bissimilah ko tare da gyara zaman shi yana nufin na bashi.
Gaban shi na dawo na tsugun na kadan tare da mika cup din a bakin shi a hankali yake kurbawa ina yi ina cire cup din daga bakin shi a hankali har ya sha fiye da rabin wanda na zuba mai a cup din ya daga min hannun shi yana cewa thanks.
Haka yasa nagane cewa ya koshi ke nan na aje cup din daga gefe dayan saman table din.
Nace mai abinci fa my love?
Zan so idan na samu amma bari na watsa ruwa na sauke gajiyana tukun .
Shigan da nayi yai matukar burge shi sosai don kayan sun min matukar kyau sosai english wear ne a jikina wando da riga yar rigan daga baya ne ya dan sauka min kadan amma daga gaba bude yake yana yauki sosai idan mutum ya motsa da jikin shi.
Yana matukar bukatan matar shi a lokacin amna sanin cewa tana cikin period yasa shi daurewa tare da jan guntun tsuki kawai yana kokarin mikewa tsaye.
Dakin shi muka nufa da taimakona ya shiga wanka ni kuma na kwashe kayan zuwa kaiwa mai wanki ya wanke su.
Tsab na shirya dining din na jera mai komai yadda ya dace na aje shi tare da komawa dakin nashi don nagani ko yafito daga wankan.
Na samay shi a tsaye gaban wardrobe din shi yana ciro kayan da zai saka a lokacin da sauri na kara tare da taimakon shi.
Na fitar mai da wasu masu saukin sakawa a jiki na mika mashi sai da ya shirya muka fito daga dakin a tare da shi.
Sosai yaji dadin girkin yafara ci cikin jin dadi da kwanciyan hankali sai dai yana mamakin yadda ya samu nai girki haka kaman nasan da zuwan shi garin ranan.
Sallama mukaji a tare muke kallon mai shigowa gidan yaya Bashar ne sai su maigadi dake shigo mai da katan shi har dining din yaya Bashar ya karaso yana fadin kai mutumina dama dai an san da zuwanka ke nan wanan girkin haka ?
Yai murmushi yace nima dai shine nake mamakin hakan kunyan maganan yaya bashar naji nai dan murmushi kawai.
Gyaran jikin da akaimin jiya yasa nai wani irin balain kyau sosai kurciyana ya kara fitowa fili sosai a lokacin.
Yaya bashar zama yayi sukaci abincin a tare suna hiran bayan robo a tsakanin su ganin lokacin sallah azahar yayi na sulale zuwa dakina nai sallah.
Ko da na fito na samu sun fita hakane yasani sanin sun fita zuwa sallah ne.
Bayan sun dawo a falo suka zube ranan a tare suka wuni a gidan can bashar yace kai bari na tafi gida nima gashi na hanaku walawa kaida yar kaunata.
Dan tsuki yaja yana fadin kai wani angwancewa tun tafiyana fa take zuban jini wai har yau bai tsaya ba wanan ai yazama matsala ke nan ko?
Haba wani matsala kuma kai mutumina badai har ka fara damuwa da rashin mace ba ke nan tare da kai.
Yace I dont know gaskiya amma kila hakan ne kasan ina under training din ka ne ai dole ne na ji hakan .
Kai ban son sheri kaji kai dai kawai kazo hannu ka shiga gari kawai amma ni yaushe na taba baka wani training can.
Wanda kulkun kana cikin jajayen mata da bakake kuna kallon ko wace kala har gida ake kawo maku tayi fa nasan a raha don fatin jinin ku kawai.
No no no kada kai min sheri wallahi bash ni idan ba a kan matana ba tunda nake ban taba aikata haka ba wallahi iyakata kiss kawai da mace ko shi ba wai wani can ba mai yawa.
To yanzun kan kaunata ta cira tutan ta akan haka ta kawar da wanan rantsuwan ai a zuciyar ka ko?
Ban sani ba yacd je gata can daki ka tambaye ta ina ganin zakafi samun amsanka a gurin ta.
Yace wani don Allah rufa min asiri kaji kada kasa ana daukana da daraja na koma shasha .
Sadauki yace dama may kake dan iska ita daine da bata san halinka ba take daukan ka wani kamili can.
Nafito daga daki na samay su sai kwasan dariya suke tayi sai dai wanan karon akwai hijjab a jikina kasan cewan yaya Bashar yana a gidan haka yasani rufe jikina don shi tunda ba muharamina bane shi.
Da hannu yaya sadauki ya yafuto ni lokacin zan shiga kitchen ke na hakan yasani na juyo garin su nuna Bashar yayi da hannun shi yace ga mai magana dake nan dama.
Kallon yaya bashar din nayi wanda kunya ya rufeshi sosai yace Fatima kyale shi kin ji sherin shi ne kawai na juya kawai da murmushi na bar gurin su.
Kayan tsaraba ne sosai yazo muna dasu na nan gida Nigeria daga doya manja mai kyai na kwarai irishi har buhu guda aka sayo.
Na juya naji muryan shi yake cewa cire mashi kayan su yatafi yabar mutum ya huta cikin iyalin shi.
Ni dai nabar gurin inda aka tara tsaraban na kalla gasu birjit dasu komai na girki an sayo bayan muna dashi.
Na debo wa yaya bashar da yawa nakai mashi na koma tare da hado wasu masu yawa zan fita dashi yake cewa nawaye wanan din kuma ?
Nace wai da su maigadi zanba don su suka shigo dashi gida yace yana da kyau hakan.
Murna sosai masu gadi sukayi suna ta zuka min albarka tare da godiya kamar nice na,sayo kayan.
Ban tsaya ba nafitar da namu dan kadan sauran na,shirya su na don za a kai can cikin gida gurin su mama.
Haka muka kwana bai tabani ba sai faman juyi da tsuki yakeyi shikadai a inda yake kwance.
Sai washe gari na barshi yana ta faman rankon barcin da bai samu ba daren jiya.
Haka muka wuni ya fita zuwa gida ya gaida su mama da sauran mutanen gida.
Bai dawo gidan ba sai da yamma lis bai bata lokaci ba yafita sallah
Na idar da sallah magariba ina addua ban san da shigowan shi dakin ba sai jin shi nayi yace uh,umm, haba Fatima kin fara sallah shine baki fada min ba ko yaune kika fara sallah dai.
Girgiza kai nayi yace what Fatima tun yaushe kikai wankan tsarki nace kwana biyu da ya wuce ke nan.
Wani irin kallon mamaki kaman take kuma fuskan shi ya sauya a lokaci guda sai naga ya juta ya bar dakin .


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,,


A LOKACIN MUKE,,,


Suna zaune tayi murtuk da fuskan ta yarasa mai zaiyi wanda zai iya jawo hankalin ta ta sake mai fuskan ta ko zai dan ji sanyi a ranshi.
Shi dai tun auren su shi dai ba zai ita cewa ga wani dadin wanan amaryan tashi ba da yaji a zaman su.
Kullun a cikin bashi commad take yau tace wanan take so gobe tace wancan take so.
Gashi iyanzun duk dan zarahin shi ya tafi baida wani kudi da zai juya a tare dashi.
Gashi kuma a bangaren ta idan ba kudi ne ya kashe mata babu zaman lafiya a tsakanin su ko kadan.
Shi da gidan shi amma har kofa sai Jamila ta rufe mashi don cin mutunci sai ya samo mata kudin nan da ta furta mashi tana so a gurin shi.
Jin sunan shi da ta ambata yasa shi saurin juyowa da sauri a dan firgice da tace Ahmed fa dakai nake magana ka zauna kana min wani tunanen can dakai.
Kaji na fada maka dubu dari shidda nake so ina son na kai babana asibiti saura kuma zanyi amfani dashi ne akwai bukin kawata da za,ayi ina son nasai mata abu mai munhinmanci don tasan inayin ta sosai.
Nisawa yayi tare da gyara zaman shi yace Jamila wallahi ban san inda zan samu kudin nan ba yanzu don wallahi dan abinda ke hannu na kwata kwata baifi dari uku ba ma in har sunkai shine kuma nake dan juya muna.
Rufe min bakin ka kai baka ji kunyan fada min haka ba kai dan gidan Alhaji Abubakar deller shine har zaka fada min haka ?
So kake na yarda da karyan ka kana nufin haka zan zauna dakai ba wani karuwa sunan ina auren dan mai kudi ko may wai ?
Kaji na fada maka in har kana son zaman lafiyan kakan ka nemo min wanan kudin dana fada maka.
Ehe, don shine kawai kwanciyar hankalin ka don a zauna lafiya kawai kaji abinda na fada maka daga haka ta mike tashige dakin ta tare da rufo kofan dakin garam da karfi yamike yana fadin Jamila Jamila tsaya mana ki saurare ni.
Amma ina har da key taiwa kofan dakin nan ya dafe kan shi yace oh my god wanan balin na jamila da may yai kama ne wai.
A falon ya kwanta saman dogon kujeran su a takure haka ya kwana shida gidan shi ya koma kwana falo don masifa.
Washe gari ma da masifan suka tashi a gidan don yana zaune ta hado abin karyawa duk dashine yasayo amma yana zaune, yana kallo tana shan shayi da kwai a gaban shi har ta shanye tass
Ga jamila bata wasa da ci duk yawan abin nan zata iya cinye shi tas ita kadai yace a ran shi shiyasa take mulkan dan bura uban kiba haka tana curewa ita kadai.
Shi ko sai rama yake yana aje dan dogon wuya kamar matikin lema dashi ganin babu sarki sai Allah yasa shi mikewa don fita ya dan samu abinda zaiciwa ran shi tun jiya da ya karya bai ci koma ba don fitan jamila a kan shi yai yawa .
Gidan su ya nufa gurin mama Asiya don ya dan samu abin karyawa a can , duk yasan kullun yaje neman abinci sai mama tai mashi korafi kan shi matar shi da bazata girka mashi ba shi ke nan kullun zuwa gida cinye masu abincin su.
Yau ma yadda yai tunanen masifan mama hakane a kan shi don fada ta haushi dashi tana fadin sai da nai maka gudun haka amma ka dage kai sai wanan yar daban matar taka zaka aura yanzun ga shi ko abinci ba ta iya baka sai ka kama labe labe gidajen mutane.
Bai damu shi dai yace Rukaiyya ta debo mashi abinci kawai yaci nan ya hago kayan tsaraban da sadauki ya labto masu a gida.
Yace kai mama har yanzu tsohon nan yana sayo maku abinci haka mai yawa ashe.
Tace wani tsoho kanin ka dai sadauki shine ai yanzun zance mai muna sayen abinci duk wata.
Kamar Alhajin ya barshi da wanan nauyin ne kasan su da son neman suna da iyayi waishi gamai hali kowa zai gwadawa hali .
Dama ba musan uwarshi bace matsiyaciya yar taulali kawai su suka sani da shegen iyayin su wai su ga yan iyawa ke nan.
Nan dai ya kwashi abincin shi sai da yai kat dashi yana ta sake sake a zuciyan shi.
Sai da ya gama yamike yana cewa zai shiga gari yaga may gari ya waya yau kuma.

******

Please Login or Register in order to submit comment