Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

a zuciyar shi a lokaci guda.
Yace su waye haka kika tara min a gidana sai cewa tayi yaya sadauki salma ce fa diyar gidan baba prof da take mutuwan son ka wace nasha fada maka zancen ta tana karatu a london yanzu itama tagama ne ta dawo gida.
Wani mugun kallo ne ya watso mata yace kina da hankali kuwa Amira look kwashe min wanan mugun tarkacen da kika tara min a gida don yanzu na gama sanin inda kika dosa.
Salma da ta zage akan ta aamu shiga tunda ta samu kaunar shi nason ta sai yadda tayi dasu.
Dalilin ma da aka kitsa ke nan su dinga zuwa gidan don ta san halina da kuma yadda zata saba da gidan kafin ta shigo.
Haba UF inji salma data mike tsaye tace kaima kasan da ina son ka shi yasa kaga har nazo gidan ka kawai .
Amma daba, son ka nakeyi mai zai kawo ni wanan nan gidan nazo na zauna har wanan yar matsiyatan daka aje tace zata kawo muna raini kawai.
Don mun sauki cups din amfanin ka ta kama muna haushi ai badon Amira da ta dauki mataki a kanta ba da na so na gwada mata koni wacece.
Wani irin kallon mamaki kawai yake masu take idanuwan shi suka rikide zuwa ja kamar gauta a lokaci daya.
Yace cikin wani irin murya please get out in my house before i take a desition on you.
No no UF kada kace zakai min haka please already mun riga mun gama maganan nan da kai ko.
Tazo har inda mukw a tsaye tana cewa tare da nuna ni da hannun ta wa an yar kauyen matar taka bata dace dakai ba don tafi dace wa da masu gadin ka kawai.
Fauuuu muka ji kara mari tace ido rufe maza su kwashe subar mai gida mara sa kunya fitsararu ko mata sun kare a duniya mai zaiyi da ita mace da taje london ta gama watse wanta zai dauko ya kawo wa kanshi fitina a gida .
Tas yai masu suka fice simi simi da kunya wai su tantire sai gashi su hadu da wanda ya fisu iya fitsara yai masu tas gaban matar shi.
Wanan karon tare da tsaraban ahi ya shigo gari don koda su salma zasu wuce wata hilux data kwaso mai kaya daga airport tana sauke kayan a kofan gidan mu.
Ana shigo da kayan ciki yai tsaye yace Amira tafito ta wuce zuwa gida sai ya zo zai nemai ta a gida.
Aiko Amira ta ce yaya may kake nufi korana zakayi don munafukar matar ka tai muna hadi a gurin ka hau kazauna akai.
Babu inda zan tafi sai ka bude kayan nan a gabana kowa ya gani haka wancan karon nazo nai zaman banza komai baka ba.u ba yadda ka saba ta kwashe takai kauye inda,ba,a san darajan su ba ma.
Amira waiko anya kanki daya kuwa, ina dai gani kanki ba guda bane kawai don hakan da kikeyi abin naki ya zarce sanina gaskiya.
To bazan bude ba kuma maza ki kwaso kayan ki tun ban bata maki rai ba a gidan nan.
Idan Fatima ta kwashe abina nakine ta kwasa ko nawa ina ruwan ki da kayana Amira Fatima matatace ko kina da abinda zakiyi kan zaman ta matata.
Yaya ta furta tana mashi kallin mamaki tace kan Bintu kake fada min haka yaya Bintu fa Bintu dai.
Yace Idan na kara jin kin kira Fatima da Bintun nan da kuke kiranta dashi don rainin wayo wallahi sai kinyi mamakina Amira fito kawai ki tafi gida zan zo zamu hadu agidan ai.
Haka yai mata kora na kaskanci kan abinda tai min wanda tun yana can Bashar ya fada mashi komai duk irin halin da muke ciki da Amira a gidan, da bayana ranshi yai matukar baci shine ya zo muna a bazata batare da ya fadawa kowa zuwan shi ba.
Wanka ya shiga don ya rage gajiyan jikin shi ina kitchen ina hada mashi abinda zaici na juya zuwa dakin na shi inda na samu ya fito daga wanka na yana saka kaya a jikin shi.
Jin motsin shigowa yasa shi dan juyowa yana kallo na tare da sake murshi a fuskan shi.
Yace batare da ya dago kan shi gare ni ba mai yasa kika boye min halin da kuke ciki a gidan nan da Amira.
May yasa tun wancan zaman baki fada min ga irin rayuwan da kukayi da ita a gidan nan ba.
May yasa ki ka bari Amira ta tara yan iska suna wullakanta min ke ne haka a cikin gidana.
Ya dan dago kai kamar a fusace yake magana yace may yasa zaki boye min irin wana mugun halin da Amira taita gwada maki.
Nace yaya Anty fa yar uwatace komai tai min kanta taima bawai, ni kadai tai wa ba don wata rana zai bata mata rai yadda tai min din.
Nace yaya duk abinda Anty ke min a saboda kaine don taga ban cancanci na aure ka ba saboda matsayina bailai na hakan ba.
Sau dayawa nakan rasa laifin may nai wa anty Amira take min haka yanzu , sai da ta fada min akan gangancin da nayi na auren ka yasa take min wanan halin.
Hawaye ya gangaro min a fuskana nace yaya sadauki nasan nayi gangancin auren da matsayina baikai gare shi ba.
Haka kuma wanan ba shine irin rayuwan da ya dace dani bayar tallakawa kamata bata dace da irin ku diyan masu kudi da matsayi ba a duniya.
Ya sadauki kaima kanka kasani bankai matsayin da za,ace ka aure ni ba kasani ba irina ce ta dace dakai ba a gidan nan kamar yadda anty Amira ke fada min nima yanzu nasan gaskiya take fadi don ban kai matsayin hakan ba a gare ku.
Yaya kayi yadda yan uwanka da masoyan ka ke son ganin ka tare da,diyan attajirai irin ku masu matsayi a duniya bani yar takawan kauye ba Fatima.
Ba so tsakanina da kai sai zumunci na wa yanda suka tashi a daki daya irin na yan uwantaka kawai.
Kamata yayi ace na auri maigadin gidan ku ko wani dan aikin gidan ku wanda baida matsayi irina.
Sai faman kallona yakeyi kamar talabijin da mamaki ya lura ina a cikin damuwa da kuncin rayuwa mai yawa don bai taba ganina acikin irin wanan yanayin ba haka.
Sai na fashe da wani irin kuka mai tsuma zuciya a lokaci guda na durkushe a bakin gadon shi ina rusa kuka.
Cikin kuka nace Allah kadai da mama suka san dalilin wanan hadin da sukai muna.
Amma da zaka daure ka auri wacce tafi dacewa da zama a matsayin matar ka hakan zai matukar saka anty Amira farinciki a rayuwan ta.
Hankalin shi yai matular tashi a lokaci guda yace tabbas Allah ba zai yafe min ba Fatima tunda nine yakamata na daukakaki a idanuwan mutanen duniya tun farko Fatima amma na kasa yin hakan.
Matsalar duk nawane da na kasa fitowa fili na nuna cewa ina matukar son matata batare da duniya na mata kallon wacce aka tilsata min da ita ba.
Dole ne komai yacanza daga gareni yadda kowa zai iya fahintar Fatima ta wuce yadda suke tsanmani a gurina.
Ahankali ya tako zuwa inda nake a tsugun ne ina kuka shima ji yake kamar ya fashe da kuka a lokacin.
Ya dago ni tare da kokarin mikar dani tsaye ya rigumay ni zuwa jikin shi muka zauna saman baki gadon shi a hakan.
Yace Fatima ki kwantar da hankalin ki ki saurare ni dagani har ke zan iya ce hada mu akayi amma kuma ba bisa kuskure ba.
Maji ta fahinci kiyayyan mu ba kiyayya bace illa kainace mai wani sabon launi ta hango abinda mu bazamu ita hango aa kan mu bane a lokacin.
Fatima komai nawa ya canza a rayuwana adan zaman nan da mukayi dake tunane yanayi da komai nawa yanzu ya canza min a dan lokaci guda.
Don haka ki fitar da zance su Amirah da wanan salman a ranki ,kimai da al,amarinki ga ubangiji don shi yafi mu sanin me ke boye yafi kowa sanin abinda bamu sani ba gaba dayan mu.
Sannan ina son ki saka a ranki daga yau ni Umar faruq sanda ina sonki Fatima, ina kuma kaunar ki fiye da tsanmanin ki Fatima ke alheri ce babba a gare don ko nina tabbatar da hakan da kaina.
Ina maki so na hakkika Fatima wanda ban taba tsanmani akwai wata mace bayan uwata da zanyi wa wanan irin son ba a duniyan nan.
Ni Umar Faruq nai alkawari har ga Allah zan rike amnan da mahaifana danaki suka bani akanki zan .
Zan taimakawa rayuwan ki naga kinyi abinda kikayi niyaryi, zan taimaka maki tako wace hanya inga burin ki yacika akomai.
Ki sani yaya sadaukin ki nai maki alkawari Fatima muddin muna a raye insha Allahu zan maki komai don wanan Umar din zuciyar shi da gangan jikin shi wanan kirjin da kike son kwanci akan sa duk nakine ke kadai Fatima zarah,.
A kullun zaki kwanta akansa kuma zan share maki hawayen ki harta inda baki zata ba Fatima.
Fatima muddin ina a raye duk abin kike so shi zan maki don haka ki share hawayenki Umar nakine ba wani wanda zai shiga rayuwanki ni da ke , sannu a hankali muddin ni mijin kine kina a matsayin matata zakiga gurinki suna cika daya bayan daya.
Yana dan buga min baya yake fadin Sadauki nakine zan maki duk maganin matsalolin ki don zan share maki hawayen ki.
A hankali na dago kaina na kara shigewa cikin jikin shi ina fadin cikin kuka nagode yaya sadauki Allah yabar min kai a rayuwana yabamu hakkurin zama da junan mu.
Yace Amin Fatima nima nagode Fatima da kika fahince ni a cikin sauki tashi muje ki bani abinci naci yunwa nake ji banci komai ba tun jiya dasafe don kawai nazo naci girki yar matata naji dadi.
Murmushi nayi tare da mikewa ina gaba yana bina a baya mukaje falon sai da ya zauna na zuba mai abincin ya fara ci.
Mikewa nayi na fara gyaran falon da suka bata kaca kaca wanda a kullun sai nayi gyaran shi fiye da sau uku suna batawa.
Yana cin abinci yana kallona a fakaice yana tinanen ashe zancen da bashar ke fada mai Fatman shi ta koma kamar boya a gidan kan abinda Amira ke fada mai.
Bayan na saka kamshi ko ina yafito neat ya mike ya dawo saman kujera yana waya.
Daki na shiga na kara wanka na gyara jikina tas nafito falon ina kamshi inda yake zaune na nufa da hannu yai min nuni da nazo saman kujeran da yake a kai na zauna.
A hankali yakai hannun shi saman jikina yana waya yana wasa da part din jikina a hankali.
Yana gama wayan yake cewa idan kin huta zuwa dare ki bude kayan nan da nazo da su, naki ne sunfi yawa daga ciki sauran zaki iya zabawa maryam da Amira sai kuma wanda kika so aba.
Nace mai mama fa yace atamfar Holland ce sunan nan zaki gan su kema ki zaba tunda naga kina son su sosai amma ki min dinki da zai fitar min da suran ki a fili.
Nace kai haba yaya abinda ake fadakar da mutane ba,a son anayin su yanzu yace ba ani zaki sawa ba ko wani ne zakiyiwa kwalliya bani ba.
Nace an gama yaya indon wannan ne kawai mikewa nayi na shiga fitar da kayan ina matukar yaba yadda ya iya zaben kaya haka kamar mace.
Gaba daya gidan su sai dana fitar wa kowa da nashi kaso har yaran mummy da suke kanana sai da suka samu tsaraba haka yasani fahintar tafiyan da yayi akwai sa,a sosai a cikin shi ke nan don haka yakeyi duk yai tafiyan da yayo nasara zamu sha tsaraba masu tsada muma a gidan.
Ranan kan naji jiki a gurin yaya sai dai daurewan danayi kawai don iyan zu na fara sabawa da halin shi ko.
Da safe bayan mun karya ne yafita zuwa kai tsaraba gida bayan na rubutawa kowa suna a nashi yadda zai gane.
Ranan kowa ya fahinci na fara jan ragamar aure na a gidan sadauki don ganin kayan kowa da sunan shi a jiki.
Dakin su Umma cewa mama Asiya tayi waiko kin gane cewa wanan yarinyar itace ta zabawa kowa kayan nan don ga suna kowa a jikin su .
Rukaiyya ta tare su da cewa amma kuma mama ai atamfan duk suna da matukar kyau wallahi don ni sun bani shawa,awa sosai wallahi.
Ke rufa wa mutane baki ke may kika sani ba sai tazabi na iyayyen ta yafi kyau ba ta bamu matasa kyau.
Kai haba mama wallahi haka baida kyau fa ina laifin Fatima gida su yaya ko tsuki sun taba kawo maku ne yakamata ku daina irin wanan halin wallahi inji yaya Sagir.
To sannu uban mu inji Umma yan uwan naka zakaiwa gori kuma don bakin kwadayi.
Mashayi dai ne ba wata tsiya ba can don har yanzu ba fasawa yayi ba ai tana cikin fadin haka sukaji hayaniya daga tsakar gida.
Nafisa ce tayo mugun sha take ta watsar da duk abinda tagani a waje da sauri suka fito hardasu mama dake dakin su cikin tashin hankali.
Ga kayan jikin ta yai futu futu sai ashar take zubawa tana fafin nagane duk munafukaine gidan nan don babu wanda ke sona.
Sai kuma tasa wani ihu kamar wata yar daji da taje farauta tace yau zan ci kazar uban duk wanda ke gidan nan munafukan banza xa wofi kawai.
Kuke nan kullun ku shige daki kuna kulla yadda zaku kashe UF ko wooo UF ko yafi karfin ku wallahi sai UF up up UF buga muje yayana ikon Allah .
Umma tafito rai a bace ta nufe ta tana fafin Nafisa abin naki kuma ya koma haukane ko may .
Tace Umma ni kika ceqa ma haukaciya yau ko zan gwada mamu ni ma ma mahaukaciyace a gidan nan saiko ta dauko tabaryan dake yashe a tsakar gida tayo kan Umma gadan gadan dashi.
Ganin da gaske zata rotsawa umma ne yasa umma juyawa da gudu saiko ta fadi kasa ku caaa gap da ta rotsa mata Sagir dake daki yafito jin yadda kowa ke ihu yayo kanta yakai mata shuri sai da ta fadi kasa takife bakinta ya fashe.
Kara dagowa tayi tana fafin wallahi yau sai na kashe ka gidan nan ni zaka daka haka ?
Nan ya samay ta yai ta jibga saida aka tare shi ganin haka yaran mummy suka sa ihu maji ta jasu zuwa dakin ta taboye su a ciki.
Yaran duk sun tsorace Umma tayi tayi ta tashi abu yaki kafa ya rike mata ashe tayi targade ne ba,a sani ba.
Ganin haka yaran ta suka saka ihu suna kuka neman taimako ga uwar su.
Mama Asiya ta bugawa Maigidansu waya yazo gida ba lafiya suna tare da sadauki dayaje gurin shi kasuwa.
Tare suka iso gidan cikin rudewa gashi an taru akan umma sai hawaye take tanaji kamar zata mutu.
Mummy ma dawowan ta ke nan ta samu wanan tashin hankalin daukan mama akayi dakyat zuwa asibiti sadauki da sagir da mama.
Yaran mummy suka fito dakin a tsorace suna ganin uwar su sukayo kanta suna kuka.
Ta rugumay su tana fafin yau kuma wanan iftila,in ne yazo muna agida haka kai Allah ya kyauta kawai.
Nafisa na cikin dakin uwarta sai ashar take ta zubawa da tonon asiri wa uwar ta.
Alhaji yana tsayevsai zufabke karyo mashi na tashin hankali mama da mummy suka nufe shi suna cewa yashiga ciki ya zauna kada kuma yajawa kan shi matsala.
Sai wani lokaci aka dawo da Umma duk ta jirkita ga uban bandejin da aka lailaiye mata kafa dashi.
Baba najin muryan su sun dawo yafito da sauri yace Atika kada ki shiga min gida dauki mahaukaciyar yar ki kubar min gidana.
Cikin yashin hankali aka shiga bashi hakkuri amma ina ya hau baji alokacin da kyat sadauki dasu mama suka samu ya koma dakin shi.
Umma tace tana kuka ai dama nasan shetine wallahi sai Allah ya isar muna duk wanda keda hannu cikin lalata min rayuwan yata.
Kai kaji kuma wani wauta wa zai tsa yiwa Nafisa wani sihiri kuma ga abin kwarai ba ai masu ba sai wanan barkatatan taki.
Haba hjy kubura a dai bar zancen ai Allah ba azzalumin kowa bane duk mai wa wani sheri ai zai girbi abinshi tun anan duniya don Allah bai barin bashi yanzu.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,


A LOKACIN MU KE ,,,,,


Ba karamin jiki umma taji ba sanadin kafan nan ta abu ga mai babban jiki irin ta.
Duk halin da take ciki bai hanata makirci ba daga zaune take kulla sheri kulun.
Ranan mama Asiya tazo tanawa Umma gulma wai taga maji da wani sabon waya tana ganin Sadauki yazo mata dashiba cikin tsaraba.
Umma tace shine mu bai bamu ba ya mayar damu mutanen kawai ko indai waya ce kowa ma na iya saye ai.
Asiya tace wallahi kona sa sace wayan ma gaba daya mu batar dashi kowa ya huta.
A dole ita yanzu ga mai da mai hali komai sai dai mu ganshi gareta ina haka ma wallahi bai yuyuwa ko alama.
But Nafisa dake daki tana shirin ta tana sauraren su tafito tace kaikayi dai koma kan mashekiya.
Kullun ku ke nan cikin kullawa matan nan sheri ita da diyan ta Allah na kareta ya na komawa kan diyan ku amma baku fasawa ku daina.
Don haka yau wallahi sai na fadawa maji wanan sherin da kuke kulla mata don ta kama wayan ta.
Yaya sadauki ya nuna min so da kauna wanda duk duniya yanzun ban da kaman shi don ni ko bai min komai ba ya bani so da kauna na yan uwan taka da ba wani dan uwa da ya taba bani shi.
In kin yi haukan e da gaske yau ina son ki gwada min kije ki fadawa Hauwau din ga abin da muka ce mata.
Murmushi tayi ta koma dakin ta kawai taci gaba da shirin ta har sai da ta gama tsab tafito tace to ni zan fita.
Ba dama Umma ta hanata ta ci mata mutunci tunda baba ba gida yake zama ba shi don shi gar yanzu tana dan tsoron shi.
Tana fita ta samu mummy da mama a tsaye suna magana kan wani makwacin su da baida lafiya suna son zuwa gaida shi.
Nafisa na fito mummy ta bita da ido caaa maji na kallon ta saudaya ta kawar da kan ta tana fadin a zuciyar ta Allah ya shirya kayan shi.
Maji sai ki kama wayan ki don gasu can ciki daki suna kulla yadda zasu raba ki dashi kowa ya rasa.
Don kin san su kullun cikin kulla sheri suke basu bari ki kama kayan ki don tun da suka ce sai sun dauke shi sai sun daka din don ba yau suka fara sheri ba.
Daga haka ta juya,ta,wuce abinta, mamaki ne ya kama su maji da mummy suka shiga magana kan Nafisa.
Mommy ne tace aiko tunda kika ji sun fadi haka wa yan nan macutan su na da niyar yin hakan don haka sai kiyi taka tsatsan da kayan ki ba waya ba komai manaki sai ki dinga hankali dashi don wa yan nan mutanen basu da imani ko kadan.
Bai wa mummy ba da baba ya dawo sai dai ta fada mai abinda Nafisa ta fada ma su.
Ran Baba yai matukar baci ya mike sai dakin Umma don a zaune take kafan ta har yanzu ba lafiya.
Yana daga labule suna zaune tare da mama daga kofan ya tsaya yake cewa to muna fukan Allah .
Duk wanan isharan da Allah ke nuna maku bai maku ba sai kunci gaba da kulla makirci don baku da imani.
Shege ya fasa sace wayan maijidda a gidan nan daga ku har muna fulan diyan ku da kuka lalata da mugun abu.
Yau gashi abin kuya ke Atika yar cikin ki da Allah ya mayar haka tazo tana tona maki asiri akan sherin ku.
A na dai kallon Nafisa haka amma ke Atika kece silar mayar da rayuwan, Nafisa haka kuma har gobe dake nake kuka a gidan nan.
Ku biyun kune silar duk wani balain da yarana suke ciki gaba dayan su don duk da hannun ku ga lalacewan su.
Allah ya isar min akan da duk wani da nawa da kuka lalata min a gidan nan kada kuce ban san duk wani sherin da kuke kullawa bane.
Wallahi nasan komai na dai barku ga Allah ne kawai ya fitar min da hakkina a kan ku.
Daga haka ya juta rai a bace yana fadin Allah ya isa tsakani na daku.
Tunda baba yafara magana jugun sukayi duk kunya da bakin ciki mamaki ya baibaye su sosai.
Yana ficewa mama Asiya tace yanzu yaya ashe saida ja,iran yarinyar nan ta fada masu zancen nan.
Amma ko nafisa takai la,ananna wallahi kidaina zaginta haka kada aji tsakanin mu idan la,anewan yafi haka kuma a kanta yaya kike son nagan ta ne.
Duk fa kece kika jawo muna wanan tsinuwar haka wallahi ina zaune zamana kika shigo min da wanan tsurkun kinga sabon waya hannun Hawau,
Ni yaya ina nasan wanan mai bakin tsiyan tana dakin bata fita aida ba zan soma maganan komai ba wallahi tun ita ta zama abinda ta zama.
Umma tace sun dai zama gidan nan waye baida abin fadi tab a tsuliyan shi sai dai na wani yafi na wani kawai.
Anan dai sukai ta yaba wa junan su bakar magana dama a haka hitan nasu ke kare a karshe kuma a dawo a samu sun shirya kafin wani dan lokaci.

****** ********* ******
Yana dai zaune Abuja ne amma kwata kwata hankalin shi yana a kan yar matan shi da yanzu yake jin ta ta zama mai wani rabin rayuwan shi.
Wata rana yankayi matukar mamakin kan shi don bai san lokacin da har son Fatima yai mashi illa ba haka a rayuwan shi.
Murmushi yayi ya mike daga kwancen da yake tare da dan murmusawa tunanen yake yadda har yanzu kunyan shi bai fita a idon Fatima ba.
Ya kamata ya san yadda ya fitar mata da wanan kunyan nata hakana lokaci yayi da ya kamata yai wani abu akan ta don kawar da kunyan dake idon ta dakuma sauran yarintan dake cin ta hakana.
Yana son mace wace ta san kan ta tasan hanyar da zatabi ta gyara mashi shimfidar shi.
Fatima zata zata iya zata iya mana, kwai dai wanan bakin kunyan nata ne ke hanata aiwatar mashi da yadda yake so da ita amma yanzun kan dole ne ya san yadda zai batar da kunyan nan nata.


Please Login or Register in order to submit comment