Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yayi yace idan ma baki taba ba ai yau gashi kinyi ko?
Amma anyway zan baki bashin na yau don kin min alkawari a baya don haka nima ya kamata nai maki uzurin na yau.
Nace aini ba don ka nayi ba don mama nayi amma ba saboda kai ba sake min hannuna na wuce.
Yai dan murmushi kadan abinda bai saba yi min ba yace ba abinda yakamata kice ke nan ba Fatima kice dai kin boyeni don baki son ace ni din mashayi ne ko ?
Amma ko banza dai ni koma maye aikin min alheri ko Fatima don haka nima zanso ace nadan yi maki ko na rana guda nane kamae yadda kikai min din.
Cikin wani shu,umin murmushi yace min tafi sai kin jini nan gaba, nima,
Na dan kalli hannuna da yai ja saboda riko da yasha a hannun shi nace mugu kawai ashe yajini yace may kikace da gudu na zura zuwa cikin gida kada ya kamani sai ganin mama nayi a gaba na tsaye.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,


ALLAH DUK WACCE TA KARANTA BATA BIYA BA KAINE SHEDA INA BINTA BASHI,,,,,



Zaune take duk abin duniya ya damay ta a ranta ga shi yanzu daga ita har dan ta sun zama abin magana a gari.
Ko a gaban ta zataji mutane suna bayar da labari yadda ma ba,ayi abin ba haka za,a zake ana labarata shi.
Kowa da,kalar abinda yake fadi a bakin shi ba dama yaron ya fita sai yara abokan wasan sbi su fara gudun shi kaman sunga dodo.
Haka zai dawo gida yana kuka yana fadin abinda yara yan uwan shi sukai mashi.
Abin duniya ya ishi mariya a ranta tai kuka har tagaji ta hakkura don kan ta babu wanda zata kai kukan ta gare shi.
Gashi zaman gidan kawai takeyi tun lokacin da aka dawo da ita daga gidan su daya tura ta manyan suka zo suka bashi hakkuri.
Ba don yaso ba ya hakkura da ita haka na amma zama takeyi ba abinda ke shiga tsakanin su.
Koma cefane ne idan ya shigo dashi sai dai ya aje mata a kofan daki ba tare da yai magana ba.
Idan kuma tana son wani abu sai dai ta tura yara su fada mashi abin da ake bukata a gidan.
Ranan dai taga yana ta gyaran wani kangon dakin shi a zaton maria shine zai koma ciki don ya bar masu dakin su sai bata kawo komai a ran ta ba.
Don dai tasan ba aure zaiyi ba mutumin da ko kudin cefane sai ya fita ya nemo masu abinda zasu ci.
Ranan wani laraba ta zaune tana wanke wanke taji wasu mata su biyar sunyi mata sallama.
Suka gaisa da ita sai suke fadin wani ne dakin da aka gyara daya daga cikin su tace, tana ganin wancan ne da ke da sabon siminti.
Basu bi takanta ba suka nufi dakin suka shiga ciki suna dan dubawa anan suka barta tsaye da mamaki.
Bata iya masu magana ba suka fita sai gasu da kaya suna shigowa dashi.
Kasa daurewa maria tayi tace wai bayin Allah daga ina haka bakuce min komai ba kun kama shigo da kaya cikin gidan mutane.
Dayar matar tace a,a shi mai gidan bai fada maki yai aure bane yau matar zata tare ma.
Ai mu amarya muka kawo yanzun haka munzo gyaran dakine ma kagin anjima mu kawo ta.
Allah ne ya taimaka maria bata fasa ihu a gaban su ba amma sai ta fada dakin ta can ta fasa abinta ita kadai tana fadin na,shiga uku yanzu da wani zanji halin da nake ciki ko da zancen kishiya kuma?
Bata fito ba sai da taji fitan matan daga gidan mayagin ta ta dauko sai gidan su ga girkin da ta dora a saman wuta nan tabarshi ta fita.
Da kuka ta samu uwar ta tana fada mata abinda ya samay ta nan uwar tashiga zagi tana fadin amma Atiku ya cika tsohon macuci wallahi.
Yanzu da yake nan yana yawo kaman almajiri ashe har yana da kudin da zaiyi aure, bamu sani .
Nan sukai ta kullawa ita da uwarta a tsakanin su har dare ya soma ta fito zuwa gida.
Koda ta koma ta samu har girki ta ya kone wuta ya mutu don kan shi nan dai ta kwashe shi haka na don bazata iya girka wani ba yadda take ji a lokacin.
Atiku na shigowa gida ta tare shi da masifa da jidali nan ya dakatar da ita yace.
Maria ki shiga hankalin ki wallahi kada na bata maki rai a gidan nan kin dai san ina da haushin ki dama to ki iya kan ki dani wallahi ko ayita a akare a gidan nan don dama kin kai min ko ina wallahi.
Nan ta shiga zage zage tana kiran shi macuci azzalumi dama ashe yana da kudi yake ce masu baida shi yanzun ina ya samu kudin aure.
Yace wanan aure kikace dole na samo shi don naji dadin rayuwa na kuma duk mata ta shigo gidan nan kikace zaki daga muna hankali wallahi sai dai ki koma gidan ku kinji na fada maki mara mutun ci da tausayi kawai.
Ke abinda kikai min a duniyan nan har kina da bakin magana don zan kara aure.
Kuma ai dole na kara aure na samu wace zata kwantar min da hankali na wadda zanji dadi da sanyin rai a gurin ta.
Ba irinki da kikai shekaru da shekaru kina gwada muna boni ni da diyana ba a gidan nan.
Don tsaban iya cutan ki harda dan ciki kika zalunta dakanki da kanki kin mayar damu abin zunde da kwantance a gari saboda tsaban kwadayin ki.
Yana fadin haka yai alwala ya fita, daga gidan ran shi a bace yana kutawa shi kadai.
Bayan sallan magariba kaman masu jiran a idar da sallah sai ga yan kawo amarya da gudan su sun shigo gidan.
A zaton maria za,a kawo mata amarya dakin ta irin na al,ada sai taga sabanin haka.
Sai ma jin da tayi lokacin yaran ta suna cin abinci a,waje matan na gardama a tsakanin su cewa.
Ko wanan ne akaiwa fyaden cikin su dayan tace karamin ne fa akace sai dayan tace a,a fa ance babban ne mai sayar da pure water uban ma bai ko san tana aza mashi tallah sai ranan da abin ya faru ya sani.
Kai amma wanan matar ta cika azzaluman mace ita tajawa dan ta wanan bakin sunan haka har ya mutu ana kwatance dashi a gari.
Wani irin zafi da radadi maria taji a ranta take ji kaman ta fito ta basu amsa amma kuma ita kadaice a gidan kada su taru su yi mata tsinanen duka don taga a tsaye suke su ma.

****** ********* ******
Haka kawai ranan na tsiro da tafiya kauye ba,shiri nacewa mama dake shirin zuwa gidan buki zan tafi garin mu yau.
Da sauri ta juyo ta fasa daurin dan kwalin da takeyi tace zaki kauye Fatima ?
Na dukar da kaina a kasa nace eh mama mamana ce bata da lafiya jiya ake fada min a waya da dare.
Tace assha amma gaskiya ban son tafiyan ki a motan kasuwa yanzu da zaki bari zuwa jibi idan angama bukin nan sai nasa a kaiki.
Nace mama yau nake son zuwa don na dawo da wuri insha Allahu ba abinda zai samay ni mama ki kwantar da hankalin ki.
Ta je gun jakkan ta na hannu ta dauko min kudi sun kai dubu goma tace gashi kiyi kudin mota dashi idan min tafi yadda kika samu jikin nata sai ki min waya nace nagode mama.
Sai da na gama shiri na tsab na fito falon lokacin su Amira ne kawai a falon ganina da jakka kamar may shirin tafiya suke tambayana.
A,a gaki kamar may shirin tafiya mana Bintu ?
Nace eh anty zani kauyen mu ne yau, gurin mamana har ma gurin babana zan leka na kara dubo shi insha Allahu.
Maryam tace yaushe zaki dawo nace sai na kwana biyu gaskiya to Allah ya kiyayye hanya.
Har kofan gida inda zan hau Napep din da zai kai ni tasha maryam ta rako ni na tafi.
Sai dai a cikin ranta bawai ta yarda da zanyi tafiya bane don ganin mahaifiyata kawai dai na gudu ne don kaucewa yayan su sadauki.
Amma sai ta sa a ranta zata saka ido taga shi wani reaction zai yi akan tafiyan nawa.
Takira Bashar din ta take fada mashi da kuma abinda itama take kullawa yace haka daidai zan tayi saka ido nima insha Allahu.
Ban isa gida ba sai da yamma don ban fito da wuri ba kuma motan bata tashi da guri ba.
Ina isa gida sai ganina mama tayi kwatsam tace a,a ke kina hanya ne ashe nan muka gaisa nafito da dan tsaraban da na kawo masu aka shiga rabawa.
Dakin da bakowa suna aje tarkace a cikin shi sai wani dayan kani na da ya dan tasa ya dan girma.
Nan na gyara na kai yar jakata a ciki tare da shimfida tabarman kaba sabo da mama ta bani na dinga kwantawa akai.
Ranan haka na kwana ina juyuyi don yaushe rabona da kwana saman tabar ma, zaman birni ya fara bata ni yanzu.
Sai tunane nakeyi ko may su maryam suke yanzu don nasan dai basu kwanta ba saboda a can dare baiyi ba sosai kila suna can suna kallon season film din da muke bi a zeecilmer .
Miskili jarababbe mugu azzalumi na furta a fili nace yanzu ai sai ka samu wata ka lalata ba dai ni Fatima Binta ba kuma.
Nace ko hutu ya kare ban dawowa sai naji ka tafi kabar kasan zan dawo macuci kawai.
Allah kadai yasan irin iskancin da yakeyi can bariki idan ya tafi babu kowa nan ma gida ya yi shaye shayen shi balle can inda babu kowa tare dashi.
Mazina ci kawai mai boye kama ashe shiyasa yake wani kallon mutane duk shakiyai ne irin shi gashi kirkiri ya rabani da Usman ba wai ban son usman bane amma saboda bakin zargin shi dole na rabu da Usman din ba don naso haka araina ba.
A haka har barci ya dauke ni ban sani ba sai washe gari kiran sallah da ya tayar dani a lokacin.
Bayan na idar da salla ban kwanta fitowa nayi na gyara gidan ko ina don yana bukatan gyara.
Ga karan gidan da akai danni duk ya tsufa har ya dan dadare daga yadda aka jera shi da farko.
Makewayin su ma haka tsufin tsumane na wani tsohon babban riga aka tare bayin dashi.
Ga kwata ya taru sai diyan sauro da kuda da gurin ya tara ya wani canza launi duk da kasa ne yashi amma rashin samun gyara yasa gurin ya canza launin shi.
Nan ma sai dana gyara nasa musa kanina ya debo tsakuwa da yashi muka zuba ya dauko wani falalen dutse muka kara dagwarawa a saman gurin don mutum ya samu gurin hawa yai wanka.
Kafin dan wani lokaci gidan ya koma tsab dashi kaman bashi kaca kaca da farko na dora ruwa muka dama kunu ina gamawa na dora sauran tuwo na gyara ma ma yaran don dashi suka saba karyawa.
Sai dana gama nai wanka na shirya tsab dani dakin da nake na gyara kafin lokacin sa girkin rana yayi.
Sai da mijin mamana naji ya fita daga gidan don bai tashi sai rana ya raba wani lokaci ma alokacin zaiyi sallah.
Na shiga gurin ta na samu tana nade kayan wankin da na samu tayi jiya da na zo.
Nace ta bari dakin na zo na gyara mata dama nan kuma na shiga gyara nafito da tulin shara daga dakin don irin gyaran da ake mai na sama sama ba,a kwakwalo komai da kyau.
Dakin sai gashi yafito tsab dashi kamar dakin mace nace mata may za,a girka ne da rana
Tai murmushi tace ai bamu girki rana sai dai da yamma idan ya dan samo muna sai mu girka jiya ma da kikazo ai sa,a ki kayi yasayo muna dawa shine nan nai muna tuwon shi har kika samu.
Haushi ne ko tausayin ta zai kamani na rasa may mama ta zaunayi gidan wanan mashayin har lokacin nan.
Yanzu gashi har sun kai ga tara yara har shidda dashi babu zancen fita gare ta kuma ke nan.
Bance mata komai ba nafita na kira musa ya sayo muna rogo da zogala a bakin yar kasuwan su.
Nai zaune na gyara shi kowa yaci ya koshi muka sha ruwa abin mu nayi hakane don mu kyale mugun mijin ta da baida katabus ga iyalin shi ko yaushe.
Dan na lura yanzun idan nazo komai bai saye in an tabaye shi sai yace a tambayi Bintu ko tana da canji a sayo.
Yana ko dawowa yake tambayan ba,a gika komai bane a gidan mamana tace ka kawo abin girki ne halan ?
Yace baga Bintu tazo ba bata sayo bane a girka din ?
Naga idan tazo takan dan yo muna dabara yanzun aci shiyasa yanzun nake farin cikin zuwan ta furin mu ai don nasan idan tazo hankali na a kwance yake da kayan bani banin ki.
Tace to bata sayo ba yau don haka sai ka canza tunanen ka kafita kasamo muna.
Yace kin tambaye tane tace maki babu a gun ta da zaki ce na fita in na fita ina zan samo tunda ba sana,a nakeyi ba ni.
Sai kawai naji yana kirana ke Bintu Bintu fa na amsa daga dakin da nake nace na,am Baba na fito.
Yace cewa nayi baki zo muna da komai bane wanan tafiyan don naji shiru har yanzu bakice muna komai ba?
Nace ban zo da shi ba a takaice.
Kallona yake don jin yadda na bashi amsa duk nima ban so bashi amsa a haka ba don ko banza mijin mahaifiya na ne shi.
Ina fafin haka na juya ban tsaya ba balle naji may zai kara fadi kuma tunda ba ta ido ne dashi ba.
Yanzun kai bakaji kunyan tambayan ta wanan magana ba haka wani sana,a takeyi ne a can kokuwa itama ba karshin wasu take bane wai ?
Yace na dai fahinci abin akwai rainin hankali watay kin hada baki da uwar ki kada ku taimaka ko to oho akan ku zai kare ai munafukai kawai.
Idan naga abin rainin wayo ne sai yarinya ta koma gidan uban ta wallahi tunda nan ba gidan su bane ?
Zance ke nan kake fadi ai matsawan ina gidan nan dole ne yarinyar nan ta zauna a gidan nan ita ma.
Yafita yana fadin oya shege ka fasa ni daku kuwa a gidan nan mama tace ai ni wallahi dana huta ta wanan wahalan.
Ni dai ina jin su nace mashayin banza kawai a raina a haka zaka kare har girma yazo maka baka bar tabara ba har yanzu.
Muryan kani na musa dake zaune ta waje naji yana fadin ni wallahi mama da ma kin gudu din mu huta da halin baba mu koma can birni gurin yaya Bintu muma mu huta kawai.
Daga daki nace kai musa baka da hankali ne ina ruwan ka da saka baki ga maganan man ya ne wai ?
Da yamma muka shirya nace su rakani unguwa duk da ban fadi inda zan tafi ba sai gidan su marigayi Kabir naje gaida mahaifiyan shi.
Matan bata gane mu ba sai da muka shiga har dakin ta muka gaisa da ita, sai dan shiru can tace ban ko gane ki ba.
Nai dan murmushi nace Fatima ce diyar Hausin dan Amo, tace Allah sarki Fatima kuwa haka akayi gaskiya ban gane ki ba wallahi.
Nan ta,rasa inda zata sani don murnan gani na tace yaushe kika zo garin namu nace mata jiya nazo Inna.
Nan muka zauna muka kara gaisuwa dasu da sauran matan gidan suna kara jajanta min mutuwan Kabir din.
Nan suke fada min iyalin shi yanzu suna sokoto zaune don karatun yaran shi daya bari.
Nace Allah sarki aiko ban sani ba dana shiga inda suke tace min dama ai a uguwar GRA yake da gida an raba gado anba kowa nashi shind ita Saude da yaran ta suka samu gidan .
Nan dai nan dan zauna har zuwa dan wani lokaci nai mata sallama muka bargida bamu ratse ko ina ba sai gida.
Mun shigo bamu dade ba sai ga yaron gidan ya biyo mu da sakon wai inji mahaifiyan su.
Ana wata ga wata sai ga wani dan kanin Kabir da suke uwa daya dashi ya aiko wai yana so na da aure yana son ya maye gurbin yayan shi da ni.

****** ********* ******
An wuni an kwana har dare duk shigowan da yakeyi a gidan baiga Bintu ba a ran shi yake tambayan wanan ko lafiya take ne ban gan ta ba duk kwanakin nan ?.
Yana son ya tambaya sai daibai son raini ko tuhuman wani abu ga tambayan da zaiyi na ina nake kwana biyu baya gani na.
Da yamma ya shigo gidan baiko shiga part, din shi ya wuto cikin gida direct nan ya zube a falon mahaifiyan shi.
Wayan shi ya jawo daga aljihun shi, bayan sun gaisa dasu rasa may ke mai dadi shine ya ciro waya.
Ya fara yin game da ita sukosai hiran su suke suna kallo hankalin su a kwance abin su sabanin shi dake a cikin damuwa.
Can yace maryam
Ta amsa da na,am yayan mu .
Yace wai ina wanan yarinyar take ne kwana biyu bana ganin ta ?
Tace yaya sadauki Fatima kake nufi ?
Yace ita din mana.
Tace ta tafi kauyen su yau kwana uku ke nan taje gun mahaifan ta ne wai zata kwana biyu a can.
Wani irin faduwan gaba yaji a lokaci guda, yace a ran shi kodai saboda abinda ya faru ne a tsakanin mu ta bar gidan nan don ni.
Duk sanyin AC dana gari da akeyi bai hana ahi feso wani irin zufa ba a lokaci guda.
Take kamannin shi ya sauya a cikin, lokaci guda, idanuwan shi sun sauya kala zuwa ja a lokaci guda.
Tankar wanda aka watsa wa barkono yace a kasale yaushe tace zata dawo ne wai ?
Tace zata kwana biyu a can don haka ba rana ke nan sai dai idan mun ganta kawai.
Yace ba kun kusa komawa school ba shine zatai tafiya taje ta zauna har wani lokaci.
Maryam tace ai muna da sauran lokaci ga hutun mu yaya kila sai hutun ya kare zata dawo ai?
Maryam tace lafiya kuwa yaya kake tambayan ta cikin son kara tuhuman ta akan shi.
Yace No babu komai dama zanyi bakine shine nake son ta hada min wanan abin dama yan wasu abubuwa.
Daga haka yaja tsaki ya mike tsaye yabar falon a lokacin maryam ta dan matsa gurin Amira bakin ta tab da gulma tace a hankali.
Cikin yanayi irin ta mai rada tace wai anty may kika fahin ta ga yayan mu da yake tambayan Bintu.
Tace eh nima nai mamakin jin yana tambayan Bintu don naga shi bai damu da kowa ba ai.
Hmm baki fahinci komai ba,wallahi amma ni nasan yaya yafara kamuwa da son Bintu wallahi.
Kai haba wata Bintu can wanda ke shiga duniya yana ganin mata kala kala shine zai tsaya son wata Bintu can.
A ganin ki ba tunda ke baki san so ba har yanzu kina nan zaune a na soyewa a gida baki sani ba.
Ke dai wallahi akwai ki da shirmay tsiya maryam may zaiyi da Bintu wace kullun cikin fada suke a gidan nan .
Mugun takaicin ta fa yake ji shine ke ko yar kayan soyayya kike ganin kamar shi suke yi.
Maji da tasamu suna firan tace waye wai,?
Amirah tace wai yaya sadauki take cewa wai soyayya suke da Bintu kila a boye haba may zaiyi da Bintu ga yan mata yan gayu iri iri a gari ko ina.
Eh tun da ita Fatiman ba mutum bace ko ke kin fita kama mai kyau ba da zakice hakana.
Shi damay yafita ?
Ai da ta taimakawa rayuwan shi wallahi dayayi arziki in ya aure ta.
Ita Bintu din dai maji ?
Oh baki san shi al,amarin aure ba ke nan ashe da sauran ko ke tunda baki da fahintan komai.
Ni na dade da sanin abinda yakeyi kyaleshi kawai nayi kada najawa yar mutane matsala.
Kai haba maji don Allah kubar wanan zancen mana kada ku ja wani matsala kuma yarinya na zaman zaman ta yasa ta agaba.
Kai amma dai anty Amirah nan .
Watarana kice na fada maki ai.
Ita dai Amirah jin su takeyi kawai don tasan haka ma bazai taba yuyuwa ba ai.
Wata Bintu can yar kauye kuma ba diyan kowa ba, a gari.
Sai ma taji ranta ya ba i kawai da zancen don abin haushima ya bata ita a ran ta.
Yaya sadauki na barin falon dakin shi ya shiga ya fada kan gadon shi yayi lamo saman gado.
Tan kar wanda yake barci, sai dai ba barcin yake ba yar damuwa ce da bai san dalili ba ya dami zuciyar shi kawai.
Can ya tambayi kan shi wai may yasa har yake son damun kan shi akan yar karamar yarinya hakane.
Gashi a yadda ya lura da yarinyar bata ma gama sanin komai ba na rayuwa don akwa childish a tare da ita har yanzu a rayuwan ta.
Karancin shekaru uwa uba kauyanci bata san ko inaba daga sokoto sai kauyen su kawai.
Shi dake son mace nagani nafada na gwadawa tsara shima ya faso zai tsaya ga yar kauye kuma karama haka dako twenty bata cika ba har yanzu.
Sai yaji take wata zuciya tana gargadin shi dacewa kai baba ina kai ina wanan tunanen kuma wai ?
Washegari tunda safe yashigo yana cewa shi zai tafi Abuja yanzun nan maryam tace a,a yaya wai ya zancen bakin da kace kuma zakayi har ina shirin masu abinda kace ai masu din.
Yace No maryam ki barshi kawai sun fasa zuwa din zanyi tafiya ne nima yau din nan.
Bashar yana jiran shi a kofan gida nan suka samay shi da suka rakashi, Bashar ko a,gaban kowa bai ita boye kaunan shi ga maryan yanzu sai ya baiyana shi a fili.
Don suna fito tana dauke da yar jakan tafiyan yayan ta, da ta karba ta saba a kafadan ta.
Daga cikin mota da Bashar yake zaune suna karasowa idon shi akan maryam yake cewa Madam how far?
Ita ko tai wani shake murya tace bakomai yace ya su mama tace suna lafiya.
Har sadauki ya zauna a mota Bashar sai soyewan shi yake yi hankali a kwance.
Dallah malam ja

Please Login or Register in order to submit comment