Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tana fadin munafuka kawai wakike boyewa maganan ku indai yayanane baki taba fari a gareshi.
Ina shiga daki yana fadin dan baki da kirki da tarbiya shine koki kira kiji yaya na isa balle yaya nake ke wai wata irin yar kauyen yarinya ce haka ?
Nace da iska zan kiraka ko da guguwan nomba zan bugo maka ?
Yace dan rashin kirkin ki bazaki iya tambayan ko Amira ta baki nombana ba ki gaidani.
Nace banga zan iya wanan ba don ba damuwa kayi da asan lafiyan juna ba ai ?
Yanzun kuma da ka damu aika kira kaga na samu lamban idan zan iya sai nakira.
Ke baki da kunya wallahi idan kika fada min maganan banza ko a waya ne wallahi gobe zan shigo garin nan naci maki mutunci son raina.
Nace kai dade idan kaso ma ka taso yau din nan ka iso anjima ba sai gobe ba dip naji ya kashe wayan tashi.
Tun ranan bai kara kirana ba nima dai haka ban kara kiran nashi ba har lokacin.
Maryam ce ta ishe ni da korafi inda ta matsa min akan sai nakirashi a gaban ta kokuma wallahi mu bata da ita.
Ba yadda na iya dole na dauko wayana daga cikin hand bag dina na kira wayan na shi a lokacin kuma shi yana zaune tare da Linda.
Sai ganin kirana yashigo a wayan shi da sauri ya dago kanshi tare da cewa hello,
Nace wa,,alaikum sallam.
Ina wuni yaya ya amsa da lafiya a takaice sai nai shiru maryam dake gefe na ta kafeni da ido don jin may zan kara fadi kuma.
Jin nai shiru yace min kuna lafiya dai ko?
Lafiya muke na bashi amsa a lokacin naji muryan mace tana tambaya cikin harshen tiranci da wa yake waya ?
Naji yace mata sister din shi ce .
Lafiya dai ko naga kin kirani yau?
Nace ai kaji matsalar sai ba lafiya zan kiraka dama ni sai anjima kawai.
Dakata sai na tsaya ina sauraren shi yace nasan wani ni yasa ki kirani dole ko?
Nace eh.
Anty maryam ce gata a zaune tace sai nakiraka ko mu bata da ita shiyasa na kiraka.
Ok
Maryam dake gefe na tace shit ta karbe wayan daga hannuna tace hello yaya ta damay ni fa da zancen ka shine nace takiraka mana taji lafiyan ka.
Murmushi yayi yace maryam kin san fa yar kauye ce bata san darajan miji ba balle ta san kiran shi taji lafiyan shi.
Daga inda nake a zaune nace, gara zama da kauyanci da hurda muranen banza ai muryan mace naji tana magana dakai yanzu.
Dariya magana ta tabashi don ya fahinci nasan kishi ke nan nima don har na kasa boyewa na fadi a fili.
Yace maryam fada mata Linda ce my wife to be nake tare da ita ba irinta yar kauye da batasan komai sai kauyanci da rashin kunyan su na yaran kauye.
Haushi naji nace komai kauyanci mu dai mun san darajan kan mu da mutuncin iyayywn mu dip maryam ta kashe wayan tana fadin.
Kinji halinki ko Bintu ke wanan bakin naki wai bai mutuwane nace cikin fada wallahi muddin bai daina kirana yar kauye ba bazamu taba shiri dashi ba kinji na fada maki.
Tace kai Bintu ada kema kice mashi kowa ma kauye ne asalin shi don mu kauyen mu fa har yanzu babu ko titin mota ba wuta ba ruwa.
Nace nagode anty aiko zai rana kanshi don daya fada zance mai munfi mutane kauyen tureta ai.
Ranan daga school maryam tace min mu tsaya salloon din dake kusa da school din mu gyara kan mu baki ba don da wuri muka tashi.
Wanke min akai akayi tare da zuba min kayan kamshin da tazo dasu masu kyau sai nace a dan gyara min kafana da yatsun hannu na haka akaimin gyara nafito wata yar birni dani.
Sai da zamu rabu take ce ban sa zamu hadu ba sai zuwa next week amma ina son ranan Friday don Allah kiyi girki mai dadi ki gyara gida da kanki sosai yadda yaya zai gane cewa yanzun ke ba bakauya bace don ina sa ran Friday din nan zai shigo garin suyi waya da yayana yace yana Abuja.
Muka rabu ina shigowa gida Amirah ta kasa boye haushin gyaran da nayi a zuciyar ta tace sai dai kikare haka Bintu miji kan sai dai kamahi shi.
Murmushi nayi a raina nace kai kodan na kure anty Amira dole nabi shawaran maryam.
Friday na yi kamar yadda tace sai bina da kallon mamaki Amirah keyi.
Kasa hakkuri tayi tace wa da ni yau wani kuma sheri kike son yi a gidan nan ne haka ko bakin yan kauyen ku zasu zo ne wai?
Nace anty ashe kin gane bakin kauyan mune zasu zo yau gidan kuma anan zasu kwana tare da mu.
Na gama komai na koma daki ganin biyar saura nan na bata lokacina gurin gyara jikina zakace wani gasan gwajin kyau zan tafi a lokaci don har musa kanina saida na bashi sabbin kayan da na,sayo mai ya saka yai aski irin ta matasa.
Falo muka dawo muka zauna ganin haka yasa Amira fitowa daga daki nasan ta hake ne taiwa bakina wulakanci a lokacin.
Bamu dade da zama falon ba da kamshi ke tashi cikin shi mukaji ana nocking din kofan shigowa don a rufe yake musa na tura ya bude kofan.
Yayin da Amirah ta sako idanuwan ta don ganin mai shigowa falon a lokacin don a shirye take da cin mutunci a ran ta.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKK8N WASU PLEASE,,,,


IDAN KIN BIYA KADA KI TURAWA WANDA BAI BIYABA,,,,


Shine ya shigo gidan kai tsaye yana saye a cikin kananan kaya farare cikin mutunci musa da ya gane shi yake mashi sannun da zuwa .
Murna da yar tsalle Amira tayi sai a gaban sho tana fadin yayana ashe kana hanya shine ban sani ba tun da,safe.
Yace common yanzu ba gashi kin sani ba what else ?
Har lokacin yana tsaye daga kofa yana rataye da yar jakar shi ta maza mai dogon igiya da suke ratayawa,a,kafadar su.
A hankali na karaso garesu cikin tako daidai har na iso gare su jakar kafadan shi na sa hannu ina cirowa daga kafadan shi tare da mashi sannu da dawowa cikin wata murya sai ido ya bini dashi cikin shagala da kallo na.
Da kyat ya iya amsa min da hanya lafiya saboda hannu na da ya dan taba jikinshi ya sakar mai da wani irin kasala lokaci guda.
Daga inda Amira take tsaye tare dashi sai kallon mamaki take binshi dashi a cikin mamaki, can ta saki wani irin ajiyan zuciya jin haka yasa shi saurin juyowa gareta daga shagalan da yayi ga kallona.
Tace yaya na ko shiga baka karasa yi ba mun barka tsaye a kofa tau matar gidan ce wata barkatatta da ita can.
Ya saki ajiyan zuciya a hankali tare da lumshe idanuwan shi cikin wani yanayi yana shafo fuskan shi da hannayen shi .
Cikin falon suka karaso tare dashi inda suka zauna akan kujerun dake falon gaba dayan su har musa kani na dake tsaye daga gefe daya.
Drinks ne mai sanyi na jera a wani dan tiren silver mai ruwan golden da cups din shi ture din tafiya nake zakace wai sallon jan aji nakeyi wanda ban san dalilin kara shagalan da yakeyi ba haka.
A gaban su na girke tire din ina masu bisimillah tare samun dan guri daga gefe daya na zauna na dan zamo daga kujera inda saboda dan dukawan da,nayi gaban rigana ya baiyyana suran jikina a fili, da sauri ya lumshe idanuwan shi da sauke ajiyan zuciya a hankali,
Cup din da na tsiyayawa abin sha na dauko na mika mashi ina fadin ga ruwa mai sanyi yaya.
Yakarba ba tare da ya juyo gare ni ba nace abinci fa ko sai kai wanka ne zakaci cikin wata irin yar siririyar murya da ban san ina da ita ba a lokacin.
Ya dan girgiza kan shi tare da kara lumshe idanuwan shi sai dai fuskan shi a dauresuke mai yadda,na,saba ganin shi a koda yaushe.
Kamar da kyat ya iya furta cewa bari nai wanka idan na dawo daga sallah zanci abincin kafin na kwanta.
Yana dan kurban drinks a hankali yana wani lumshe idanuwan shi abinda ya daurewa Amira kai ke nan ta kasa fahintar yayan nata gaba daya.
Shi da kan shi yai masu bisimillah tare da cewa musa bissimila dauki mana may ma sunan kane please
Musa ya bashi amsa cikin dan murmushi da fadin musa yace malam musa ke nan naga kaman kai ustaza ne ko?
Musa dai murmushi yayi saboda ba sabawa sukayi ba bai sake jiki dashi tukun.
Dawowa nayi falon tare da dafa kan kujeran da yake zaune nace yaya ga ruwan wanka can an hada maka magariba yana kusan towa.
Duk da yana mamakin ganin sauyi a tare dani amma sai yake daukan hakan a matsayin wani sabon yaudara ne na ke kula mashi don naga Amira a gidan.
Amira bari na je nai wanka yace mata tare da kokarin mikewa tsaye daga falon zai shige ciki.
Yana shiga daki mamaki ya kara kamashi ganin yadda dakin yasha gyara ga kamahi ko ina yana tashi daga dakin.
Jiki a sabule mashi yadan bi ko ina na dakin da kallin mamaki gaba daya tarasa may nene dalilin wanan sauyin da ya gani a gare ni lokaci guda haka amma zai natsu ya fahinci may abin ke nufi ne wai.
Daga Amira ko maryam ko kuma dai akwai wani plain a kasa nake boyewa.
Haka ya shiga wanka zuciyar shi fam da tunane a cikin ta na tambayan kan shi may ke faruwa ne haka akwai yaudaran da nake shiryawa a boye.
A lokacin na juya zuwa cikin dakina na bar falon da suke zaune sai da na kwatanci ya shige bayi na budo turare a jikina, sun kai kala uku nafito falon sautin takalman dake kafana, yasa Amira saurin dago kai tabi ni da idanuwan ta.
Sai ga kamshi yana taron hancinta a lokaci guda sai taji wa ni irin wani abu ya tokare mata makoshin ta a lokaci daya.
Dakin yaya sadauki na nufa nai sa,a na samu ya shiga bathroom a lokacin cikin sauri na bude wardrobe din kayan shi, na fito mai da doguwan jallabiya fara kal mai laushi da,santsi jikin shi na bishi da turaren shi masu kamshi na fashe rigan, na aje mai wani wando gaje daga cikin kayan shi dake wanke na tafito nabar dakin kafin ya fito.
Yana fitowa kamshi ya daki hancin shi sai lokaci yaga komai da zai bukata na aje mai a saman gadon shi ko.
Musa kaje kayi alwala na fadi tare da shigewa dakina na muka barta a falon zaune ita kadai kamar manya.
Tana batun mikewa don ta gane nice silar a,watse a,barta a gurin zaune ita kadai sai taji motsin kulle kofan dakin dan uwan nata.
Da fara,a a fuskan shi yake cewa Amira kina nan zaune ne bari na dawo mosque nazo mu zauna ko ?
Tare da musa suka wuce zuwa sallah mukuma kowan mu ya,shige dakin shi a lokacin.
Wanka nayi na fito nai sallah tare da canza sutura a jikina irin da ya dace mace taiwa na miji shiga dashi da dare tankar wace zata halartan wani bukin dinner can.
Dogon rigane mai hannu kamar ta shimi za,a iya ganin hammatan mace a fili daga ciki sai zuwa kasan riga an matse shi an fitar da sharp din mace sosai wanda ko wanene yaga wanan shiga sai ya yaba da shiga na daure gashina da ya sha gyara a cikin dan kyallen riga mai kama da ribbon din daure kai.
Ba yaya saudauki ba har anty Amira da muke zama koyaushe a gida guda,
Ina fitowa falon wanda shigowan shi ke nan daga sallah nafito ina kamshi ina fadin sannun ku da dawowa tun da nake da Anty Amura babu wanda yasan cewa na iya wani yare sai yau din nan dana canza harshe da musa ina mashi yaren uban su wanda nima da karfin hali na iyaren mutanen Niger din.
Kallo biyu suke min na mamaki kwalliya na da kuma jin canza harshen da nayi wanda basu san ina da,wani yare a,harshe na ba sai yau din nan.
Inda yake zaune na nufa sai da,na kai zaune gefen hannun kujeran na fara gaidashi tare da kara mashi sannu da zuwa .
Amirah ta cika fam tun zamana a gurin ta wani hade rai hankalina ya dauke ga kallon tv gaba dayan mu duk wani film din action ake a lokacin.
Sai da aka gama gurin da ya dauke muna hankali na dan juyo gare shi cikin kwantar da murya nake cewa abinci fa yaya.
Yace kin shirya daning din din ne nace mai eh tare da mikewa yace malam musa muje muci abin ko.
Ko ba komai ni dai sai naji dadin yadda ya kula min da dan uwana batare da nuna mai yadda nazata ba daga gare shi.
Sai da suka mike da musa yake cewa Amira taso mana sister ta wani bata rai tace naga kaman ka fara mantawa danine ai yaya.
Kai haba Amira wani irin magana ke nan kuma yace mata kin taba ganin mutum ya mata da dan uwan shi ne ?
Sai bayan sun zaunane nazo na fara zuba mai abincin sai wani faman lumshe idanuwan shi yakeyi don kamshi da desire dake damun zuciyar shi.
Kujeran da yace itace nawa na zauna akai tare da dan zuba abinci kadan a plate wanda zanci .
Bai wani ci abinci ba amma yasha fruits salad din dana zuba mai sosai da ruwan kayan yajin da nai mashi drinks din hausa dashi.
Yana ci aka bugo mai waya nan hankalin shi ya dauke da hannu ya yafuto ni da alamar nazo sai na zo inda yake ya daina waya yana ce min ki dauko liptop dina ki dan dafa min kafin na kwanta zan sha.
Dakin shi na nufa naga liptop din gasu nan da yawa kala kala na dauko wani mai steberry na nufi kitchen dashi.
Musa yana gamawa ya mike tare da komawa gurin tv yaci gaba da kallon shi.
A flask na zuba mai tare da daukan cup na nufi dakin shi da ruwan shayin zalla ba madara a ciki na kai mashi.
Ban fito ba sai da,na kara gyara dakin tsab nafito don na samu kayan da yacire a,watse inda yake ajewa na feshe dakin da airfreshiner.
Dakina na koma don nagaji gani na san tunda yana gari gobe dole akwai aiki gare ni.
Sallah nayi tare da dauko rigan barci na na saka har zan kwanta sai na tuna ban sallami MUSA ba .
Nafito a cikin yare nai mashi magana cewa idan ya gama kada ya dade yaje ya kwanta yace min to Allah ya bamu alheri.
Duk da zani ne saman rigan ya san shirin da nayi alokacin na kwanciya ne.
Daki na koma ban dade da kwanciya ba naji barci ya fara dauka na gashi ban sawa kofa key ba yadda na saba sawa nufi idan na falka zanyi sallah sai na rufe kofan.
Can cikin barci naji kamar ana tsaye a kaina duk da rufe nake a cikin bargo bai hanani jin nauyin mutum aikana ba.
Da sauri na bude bargon dake rufe har kaina yana tsaye ya harde hanbayen shi biyu a saman kirjin shi ya dan jingina jikin shi da bangon daki haka ma kafan shi a harde suke mai.
Ganin shi a dakin yasa nai saurin mikewa zaune cikin dan rudewa nake cewa wani abu zan makane kuma?
Ke dakata yace min cikin daure fuskan shi tambayan ki nake son yi .
Wani muna funci kike kokarin kulla min a gidan nan kuma ?
Cikin mamaki na dago kaina tare da dan kallon shi ganin ni yake kallo ido da ido yasani dukar dakaina a kasa.
Yace tambayan ki nayi may kike kullawa akaina don ban fahinci wanan bakin ladabin shegun da naga kinayi ba tunda na dawo gidan nan.
Murmushi nayi kawai tare da kokarin mikewa zaune da kyau banyi magana ba sai da na mike tsaye da kyau tare da manta yar rigar barcin dake a jikina.
Sai da naga wani mayen kallon da yai min nai saurin koma da sauri na zauna tare da jawo zanin da ke saman gado na kara dan rufe jikina dashi.
Idanuwan shi na a lumshe yake ce min ke nake saurare zakiyi magana ko sai na saba maki yanzun nan.
Nace laifi ne kuma idan mata ta kyautatawa mijin ta ashe nace kada ka manta nauyin ka yanzu a kaina yake.
Duk wani nauyi da nasan naka yana a kaina shi nake kokarin ganin a matsayina ta matar gidan nan na sauke shi a kaina ko kuma hakan shima sabawa ne ga Allah.
Bai yi magana ba bai kuma fita daga dakin ba sai lumshe idanuwan shi kawai da yayi a lokacin.
Can naji ya furzo iska daga bakin shi yana fadin idan kika kuskura kika kulla min wani makirci har na fahinci haka wallahi sai na mugun saba maki kinji na fada maki.
Daga haka naga ya juya yafita daga dakin hakan yasa na mike nabi bayan shi na sakawa dakina key kawai.
Amirah da taga shigan shi guri na shiru shiru taga bai fito ba ta mike cikin bacin rai ta shige dakin ta sai sauke ajiyan zuciya takeyi kawai.
Tana cewa a ranta may yaya sadauki ke nufi da wanan yarinyar badai yana nufin har ya mika kan shi gareta bane mai zai gane gurin wanan bakauyan yarinyar da maji ta nace a kanta.
Tace kai yayana ban taba zaton haka ba daga gareka gaskiya kai mai tsadane kai mai daraja ne sai yar manyan mutane ta dace da irinka.
Bintu bazan taba bari ki samu farinciki ba a zuciyar yayana har abada sai dai ki zauna zaman gadin gidan nan kawai

****** ********* ******
Washe gari kafin kowa ya tashi na gama hada komai na gyara ko ina na gidan sai kamshi ke tashi na koma ciki na gyara jikina tare da saka kaya wani dogon riga Afr abaya mai simple design.
Ina zaune gaban mirror wayana yai kara na dauka ina mamakin mai kira na da safiya haka.
Anty maryam ce ina dagawa tace amarya kina kamshi fa, yaya labari.
Dan tsuki nayi nace kai anty maryam ni dan Allah ki rabani da wanan zancen kinji.
Tace cikin daga murya may kike nufi wai wallahi Bintu kiji tsoron Allah duk wanan nasihan da nai maki kina nufin baki dauka ba ko may ?
Nace haba Anty yaya kike son nayi da mutumin da baidamu dani ba zargina mafa yake wai bai yarda da sauyin da yagani gare ni ba.
Dariya naji tayi tace bashi bane ya fara kamuwa ke nan kedai kawai yi yadda na fada maki shi da kan shi zai kawo kan shi gare ki sai dai in ba mace ta haife shi ba.
Amirah ta koma ne nace tana nan what wani gulma ya tsayar da ita kuma a gidan ku amma dai Anty bata da kunya wallahi.
Yanzu zan sa maji ta aiko a dauke ta tunda ita bata san ya kamata ba don may zata zauna maku gida ta haku walawa.
Shi musa nasan namiji ne ba zai tsaya saka maku ido ba namaji yayana na fadin makarantan kwana yake so ya sama mashi nagari ya kai shi.
Wani mugun dadi naji a raina nace da gaske Anty tace wallahi jiya naji yana magana cewa yana nan yana mai process don baya son ya koma kauyen nan kuma don yaron nada kirki.
Nace wai ban ma san urin godiyan da zan ma yaya Bashar ba wallahi na dade ina tunanen mafita akan kannne na anty don haka suke zaune ba karatu wallahi.
Tace a sannu duk sai ai masu mafita yanzun dai mu samu kan wanan baudaden mijin naki tukun shine mafitan komai.
Nace nifa anty ba wai ya damay ni bane kawai ko hakan ma da muke is ok ai.
Tace kina da hankali kuwa Bintu mace baliga kamar ki zaki zauna danamiji sai kallo ni na fada maki sa ido kiyi kallon yadda zamu kamashi wallahi.
Mun dan kai wani lokaci muna waya da ita tana kara fada min abinda zanyi, mukai sallama da ita.
Muna gama waya ta kira mama tana cewa bayan sun gaisa ko anty Amira na kusa na kira wayan ta bai shiga ba tace ba tana gidan yayan ku ba ko kin manta ne ?
Tace bata dawo gida bane mai takeyi a gidan kuma bayan maigidan ya dawo ?
Yaushe ya dawo inji mama tace jiya da yamma mana ya shigo gari haba dai ita ko gidan amare mijin mutum ya dawo may zata kuma zauna yi masu a gida?
Maji tace ai yanzu zan tura Abdul ya dauko min ita bata da kunyane da bata zauna a tsakanin su ba ai.
Bayan sun gama waya da Maryam mama ta kira wayan yaya tana cewa ashe ka dawo ne Baba na?
Kunya yaji da ta fadi haka yace cikin dan kamay kamay wallahi yanzun nake shirin nai wanka nazo gida ai.
Tace babu komai ka huta abinka har zuwa yamma ka shigo ai wanda ke da iyali kuma ina zaka da dawowanka.
Sai dai ka fadawa kaunan ka ga Abdul nan zuwa yanzu ya dauke ta maza ta dawo gida.
Ban san may ta tsaya yi maku gida ba kuma bayan tasan kana bukatan hutawa da iyalinka.
Murmushi yayi kai haba maji jiyane fa na dawo ai ba komai takeyi ba zata dawo anjima idan zan zo .
A,a maza yanzu ga Abdul nan zuwa zai dauko ta dawo gida haka na ladan ya isa kuma.
Suna gama waya da mama ya shiga wanka sai da ya shirya tsab cikin kanan kaya kamar yadda ya saba shiryawa, ya fito daga dakin shi sai annuri da kamshi ketashi gare shi.
Amira ce zaune a falo nan ya zube gurinta suna gaisawa da ita sai wani shan kamshi take wai tana fushi ya shiga guri na amma shi bai ma fahinci may take nufi ba da hakan.
Yace maji tace ki shirya ga Abdul tafe yanzu zai tafi dake wai.
Bata so batace tunda safen nan kamar abin kora kuma ?
Yana zaune idon shi na akan kofana amma babu alaman fitowa na a lokacin.
Mikewa yayi tsab ya nufi dakin nawa tsaye nake ina shirin fitowa ke nan Allah ya ingizo shi dakin.
Ina ganin shi na zube kasa ina fadin ina kwana yaya?
Yace ba tare da ya amsa ba Amira zata koma gashi kayana basu

Please Login or Register in order to submit comment