Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

su gaban ta ya fadi don in akwai abinda ta tsana shine ta koma gidan su mai tarin rikici a cikin sa.
Maryam tun bata karaso ba take fadin haba Bintu may akai maki zaki tafo gida batare da sanin kowa ba kin tayar wa Maji da hankali yau sosai wallahi.
In ba don yaya sadauki ba da ya shigo yana fadin yaga lokacin da kika dawo nan gidan.
Amira tace Bintu nasan akwai abinda ya faru ki fada muna ba boyewa zakiyi ba a ranki.
Don in har baki fadi ba ba,a san may yasamay ki ba balle asan ta inda za,a bullowa maganan.
Maimakon Bintu tayi magana sai kawai ga hawaye sun fara zubo mata shar nan ta fashe masu da kuka mai tsuma zuciya.
Duk yadda suka so tai magana Bintu taki fada masu komay ye matsalarta da har ta guje su haka a lokaci guda.
Haka suka koma gida da sanyin gwiwa suna fada wa uwar su yadda suka yi da ita a can.
Hakalin Maji yai matukar tashi si dai kuma gashi babu halin ta fita zuwa gidan don maigidan yana kasuwa a lokacin.
Gashi kuma itace zatai girkin gidan ranan nan abu ya taru ya rikice mata akai.
Itako mummy tana can hankalinta a kwance, don tasan yanzu bata da matsala don Bintu zatai mata komai kafin ta dawo gidan.
Sai yamma lis ta shigo tare da yaranta da takai suka sayo abubuwa a wani shago.
Ganin kofan ta a rufe yasa ta tunanen ko Bintu ta shiga gurin hajiya Maijidda ce sai take fadi a ranta dole nasan yadda na hana wanan yarinyar shiga gurin matar nan.
Sai dai tana shiga taga ko ina tsab an gyara amma babu alamar an dafa abinci a part din.
Don haka tafito da kanta har kofan dakin Maji tana fadin hajiya ina ya ta tashiga ban samay ta,ba a daki dana,dawo.
Tun lokacin Maji tadan fara tunanen duk yadda akayi akwai wata magana a kasa.
Maji tace hajiya ina yarda da fahinta yasa nabar wanan yarinya a gurin ki da zanyi tafiya.
Eh haka ne amma kuma ai haka ba yana nufin yarinyar bata da yancin kanta da zata zabi inda take ra,ayin zama bane ko?
Oho yanzun nagane inda matsala take ke nan ashe akwai abinda ke faruwa a gidan nan bayan tafiya na ban sani ba.
Babu komai sai alheri inji hjy kubura tace kawai dai mun shirya da yarinyar zata dinga min aiki ina biyan su, aikin san babu boyo a tsakani na dake.
Hmm tau Bintu dai bata gidan nan yanzun haka don ta kwashe kayan ta tabar gida ta koma gidan su.
Kai amma ban zaci haka,ba daga gareki hajita maijidda.
Ban taba zaton zaki yi min bakin ciki ba irin haka yanzun don kada yarinyar ta taimaka min kika kore ta a gidan nan.
Hmm ke ma kin san hakan ba halina,bane ra,ayin kantane takwashe batare da,sanin kowa ba tabar gidan nan don kanta.
Ikon Allah inji Mummy kamar zatai magana sai kuma ta juya a fusace tabar gurin zuwa part din ta ranta a bace wai Maji tai mata hassada.
Kai duniya kan yanzun ba gaskiya babu tsoron Allah a cikin ta,wai ita da za,aiwa zargin rashin gaskiya amma itace ke ganin hakan akaimata.
Maji nashiga daki Maryam tace amma kuwa Bintu munafuka ce yanzun saboda kwadayin duniya har ta uya yiwa mutane haka.
Amira tace aini tabani mamaki wallahi.yanzun ita tana ganin taiwa mutane wayo ke nan ko.
Aitazo indai Mummy ce dan abu kadan zatai mata sai duniya taji su .
Matar da bata da,yarda ko kadan inba diyan taba ita batasan kowa ba aduniya shine kwadai zaikaita gurin ta.
Maryam tace bataga daki yana kyalli ba kamar aljannan duniya dole ta gudu nan inda ba komai ai.
Kai ya isa haka dan Allah kubari muga yatinyar muji may ke na kafi ku yanke hukunci ku fara zaginta.
Da zata zauna da ita aida tun tuni tayarda da zugin da tai mata, ina jiya kince da kuka taje kwana dakin dana tura ta.
Koma may nene duk nice najawa Bintu din haka don ni nakaita da hannu na cikin rashin sani.
Maji dama aikin san mummy ba mutunci ne da ita ba don ita kanta kawai ta sani amma wanan rashin gaskiyan haka ai ya zama cin fuska.

Da yamma da maigidan yadawo maji takai masa abinci lokacin ya tafi sallah sai tadawo dakin har in ya huta ta samay shi akan ya bari ta shiga gurin Bintu taji may ke faruwa.
Amma tana zuwa gurin maigidan saita samu hajiya kubura tana mayar mai da magana akan karya da gaskiya.
Wai taimata bakin ciki akan yarinyar shine har ta koreta bayan tafita daga gidan.
Shigowan Maji ya sashi cewa madalla ga Maijiddan ai ta shigo ma dama yanzun nake nufin kiran ki.
May ke faruwa ne akan yarinyar nan ta gurinki don hjy kubura ta samay ni da wani magana sai dai ban fahinta,ba.
Murmushi maji tayi tace nima dai ban fahinci maganan ba sai takai zaune yayin da mummy tacika ta batse da Maji din.
Nan ya kara tambayan ta ta fara fada mai tun farkon barin yarinyar da tayi a gurin mummy da kuma yadda jiya akayi kafin ta tafi gurin ta ta kwanta kamar yadda mummy ta bukata.
Maji tace ni a zatona ko don a jiyadin muka dawo yasata cewa tazo ta kwanta.
Sai yau tun safe yarinyar ke daki tana kuka dana tambaye ta take cewa wai kanta ke ciwo.
Wallahi Alhaji dafa haka ban sani ba bayan nabata magani ashe ta faki idon mu ta kwashe duk kayan ta a gidan nan ta sulale ta fita ba wanda ya sani.
Saidana tura yaran ban,suka ce tana gidan su dakin gwagon ta ita kadai a gidan.
Subbahanallahi yanzun dai ina yarinyar take tana gidan su ita kadai a gidan.
Yanzun nake batun na rokeka naje naji ko may ke faruwa da ita tai muna haka amma kuma sai dazun ga hajita kubura tazo tana wani maganan da ban san dashi ba mani.
Yanzun dai ba,wanan ba ahin kun san hatsari ne abar yarinya karama kamar wanan ita kadai cikin gida babu kowa a wanan zamanin da muke ciki.
Hakan yasa fa uwarta takawota gurinki don ki rike mata ita har lokacin da zata dawo.
Don da kanta mai masa sai da taimin magana akan zaman yarinyar gidana shine ma dalilin da yasa na barta kowan ku bai sani ba.
Amma kubura kin bani mamaki wallahi yardane fa yasa maijidda ta barta a gurinki.
Yau ina wayon ki da iliminki ya tafi ina suka shiga da zaki turawa yar mutane wanan akidar na bijerewa.
Alhaji nifa ba,a kyauta zan dauketa ba kudi zan bata ita da iyayyen ta don ina bukatan taimako.
Wani irin tsuki yaja ya dauki wayan shi nomban Amira ya kira tare da babban dan,shi yace su zo yanzun falon shi.
Ba,a dade ba sai gasu yake cewa ya raka Amira tazo da Bintu yanzun nan suce inji shi.
Bintu har ta rufe gida da daki ammajin da tayi anata bugawa tare da kiran sunan ta yasa ta bude kofan tafito.
Duk ta fyde ta ramay lokaci guda da ita ta canza don fitinan daya samay ta.
A tsiwance Amira tace da yaya Imirana muke Baba ne yace muzo dake yanzun nan.
Daga haka Amira bata sake cewa komai ba ta tsaya jiran ta ta shirya su tafi.
Jin Alhaji da kanshi ke nemanta yasata dauko hijjab dinta zuwa amsa kiran inda tabiyo bayan su simi simi har falon Alhajin.
Shikan Imirana bai san komaiba ya na cewa gata nan yajuya abinshi ya fita falon shida Amirah.
Guri ta samu ta zauna a makure duk ta kode lokaci guda da ita fuskan ta duk ya wani kode mata.
Gaba dayan su kallonta sukeyi take taba Alhaji tausayi yace Fatima may ke faruwa ne.
Sai tai shiru ta dukar da kanta kasa tare da sako wasu hawaye masu dumi daga idon ta.
Ganin bazatai magana ba tasa Alhaji cewa may kike a gidan ku ke kadai baki tsoron dare wasu miyagu bata gari su shigo maki ke kadai a gida karamar yarinya dake.
Nan ma Bintu sautin kukanta takara batare da tai magana ba sai tsoron da ya kamata a cikin ran ta lokaci guda don ita batai ko tunanen hakan ba.
Yace kin fadawa maijjida abinda ya faru tsakanin ki da hajiya kubura ne.
Da sauri ta dago kai tare da cewa cikin kuka ban fadawa kowa ba Baba.
Baki kyauta ba Fatima don kinga amana kike a gurinta agurin mu ma baki daya idan wani abu ya samay ki damu uwarki zatai kuka.
Baba kuyi hakkuri amma ni na guji hafin hasumi ne akaina shiyasa na kona gida.
Baki kyauta backe nan baki rike maijida a matsayin uwaba gareki tunda har zaki iya boye mata maganan ki.
Da sauri tadago kai ta dan kalli maji tace ba hakana bane Baba ban son wani abu ya faru ne a tsakanin su don naga akwai yarda a tsakanin su.
Inda mummy take zaune ya dan kalla yace kinga karamar yarinya ma tafiki tunane wai mai ya samay kine kubura da zaki wanan danyen hukunci wa kanki haka.
Maganan nan ba abin kunya ne gare ku abokan zaman ku suji shi an yarda dake abaki amanan yarinya sai kuma ki mata wanan danyen aikin haka.
Kituna fa kema kin haihu idan wani yaiwa yaranki haka zaki ji dadi bafa rashi gatane yasa kika ganta nan ba lalurace takawo ta gurin mu.
To amma Alhaji aini naga ,,,,, dakata don Allah wallahi baki kyauta ba kuma kin bani kunya yau ace kece kikawai maijida haka a gidan nan.
Ke tashi ki koma dakin ku kuma na kashe wanan zancen a gurin nan kada naji shi wani guri don ranku zai baci.
Daga yau ke maijjida nabar maki rikon yarinyar nan a hannunki koda uwarta tadawo zanyi magana da ita kada na kara jin zancen nan ko nan gaba.
Bintu ta mike jiki ba karfi tana fadin nagode baba cikin kuka tana fita taji yana cewa ke kuma kubura wallahi duk naji kin wa yarinyar nan wani muvun kallo gidan nan sai na saba maki ta yadda baki zata ba.
Bintu tana shiga dakin da dan muryan sallama duk su Amira suka kalleta a wulakance bata gane masu ba.
Bata jima da shiga ba saiga maji tashigo tana cewa Amira hado mata tea mai zafi tasha tasha magani.
Nan taje mayar masu da yadda maganan yake sai ko suka shiga zagin hajiya kubura sai da ta tsawata masu.
Ta juta kan Bintu tanacewa Fatima ashe baki dauke ni uwa ba da gar zaki iya biye min magana irin haka tunda badawo.
Cikin kuka tace mama ban so kuyi fitina ne shiyasa naga gara kawai nabar gidan gaba daya.
Nan maji tai mata fada sosai tare da kara bata shawara akan mutanen gidan gaba dayan su.
Bintu a ranta tace nafiki sani komai yanzu ai mama nan dai su Amira ma sukai mata magana sosai akan zaman duniya.
Duk yadda suka yi da mummy ta kwashe ta fada masu komai suka shiga tsinarta da kwashe mata,,,,



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,


A LOKACIN MUKE,,,,,,


Nocking din kofan take a hankali yayin da take jin sautin kida ya na tashi daga dakin, sai dai ba a da niyan bude dakin a lokacin.
Kara sautin nocking din da takeyi tayi sai ji tayi ana cewa wai waye please ke damuna haka.
Mai dakin tana bude daki sai suka fara kallon kallo a tsakanin su don ba wanda yasan wani a cikin su.
Kina neman wani please ?
Har lokacin tana tsaye ta tare kofan dakin nata ta inda mutum zai iya shiga dakin.
A,a gurin ki dai nazo.
Ni kuma ta fadi cikin dan mamaki a fuskan ta tare da dan sake fuska tana dan kada idanuwan ta cikin mamaki.
Eh duk da dai nasan baki sanni ba amma dai gurin ki din ne nazo ai.
Ok tau shigo daga ciki mana ko ?
A tare suka shiga dakin a lokaci guda suna nuna a jere da junan su.
Kujeran dake dakin ta nunawa Raiha ta zauna inda Raihan ta gane nufinta ta ta zauna kamar yadda ta bukace ta da yi.
Juyawa tayi zuwa ciki sai gata dauke da kwalin juice da cup a hannunta inda Raiha take zaune tazo ta aje drinks din tana cewa bisimillah.
Raiha ko sai bin dakin take da kallo wanda dakin yai mata kama da ta mai zaman kanta ko kuma wace tazo karatu a garin.
Idon ta ya kai akan kwalaben syrup din maye dake saman wani dan table can gefe guda.
Kisha mana bisimillah ko sai takai idon ta akan kwalaben da Raiha take kallo, tace,
Ko kema dai yar hannu ce na miko maki ki surka dasu ne?
A,a barshi kawai ni sai dare nake sha idan zan kwanta yafi min caji don ina gudun mutane su gane ina wanan harkan.
Dariya Nura tayi har fararen hakoranta suka haska daga bakin ta tana cewa.
Kai har kin bani dariya wallahi ashe da sauran ki ke har yanzu dasha da rana da dare ai ni duk daya na dauke su a gurina.
Haka dai kika ce amma akwai banbanci gaskiya baki dai ganewa ne kowa da nashi irin ra,ayin nake gani.
Kurba biyu Raiha taiwa juice din sai ta aje cup din tana kallon Nura cikin murmushi.
Nura tace ni kin barni a duhu ban fa gane kiba gaskiya har yanzu gashi kuma kince guri na kika zo.
Raiha tace eh gaskiya baki sanni ba nima haka Sunana dai Raiha amma mutane suna kirana da Raihanatu musanman ma iyayyena.
Ok ni Nura nake karatu ne yakawo ni wanan garin ina karatu a dan fodio university ne.
A ran Raiha tace shikan karatu kikazo kika buge da harka ke nan a garin da ba,a sanki ba.
Raiha tace cikin murmushi ko kin san Nasir Habbib mai aiki a sokoto cement ?
Nura tace a ranta au budurwan Nasir ke nan ta biyoni don nai mata snatching din shi a gurin ta ko?
Aiko yarinya kinzo gida wallahi don zan maki wankin babban bargo yanzun nan kuwa.
Amma sai ta kyale a fili tana cewa nasan shi kuwa kwarai da gaske anjima kadan ma zaki ga yazo nan ai idan ya taso daga gurin aiki.
Raiha tace good zan iya kiranki da Anty Nura don ko ba,a fada ba nasan kin girmay ni.
Dafatan zaki saurari maganan da nazo maki da ita da kunnen basira batare da kin fassara min zance na ba da wani abu.
Ok ke nake saurare ina jinki ai.
Da farko dai kamar yadda na fada maki sunana Raiha kuma ni haifafan wNan gari ne muna zama a uguwar arkilla ne nida iyayyena.
Sai kuma tai shiru tare da dan kallon saman silin din dakin zuwa dan wani lokaci, Nura tace ke nake saurare fa kada mu bata lokaci.
Ba zancen bata lokaci ai don magana ce mai muhinmanci da zata amfane ki nazo dashi.
Tace ok ai ina sauraren ki ko?
Raiha tace kafin Nasir ya nemay ki ni Raiha ya fara nema amma sai Allah ya tsallakar dani daga mugun nufin shi a kaina.
Kamar ya mugun nufi kuma Nura ta tambaya a cikin mamaki da son karin bayani ga Raiha din
Raiha tace niyar shi na shigewa yan mata ya sace zuciyar su da so da kauna kamar yadda yake maki a yanzun haka.
Amma fa daga baya zaki zo ki sha mamaki don ba nufin shi ke nan ba a kanki.
Nura tace a gatsale Allah ko ?
Hmmm Raiha ta dauki cup din drinks din da ta aje takara kaiwa a bakin ta tadan kurba kadan sai ta juya gurin Nura tace.
Wallahi wallahi ifan bakiyi hankali ba a karshe zaiyi safaran ki ne zuwa kasa shen turawa ya tura ki karuwanci a can ya kuma karbe passport dinki duk gudin da zaki samu sai dai dila ya turo mashi ta account din shi.
"Ke
Kada ki maisheni karamar yarinya mana kedai kinzo da tsigar nabar maki Nasir don ki yaudareni da wanan magana naji tsoro nace ban son ki sai ya koma maki ko ?
Allah sarki babu ko daya wallahi don idan da na yarda da yanzu nima nazama tarihi a gurin iyayyena da yan uwana a nemay ni a gari a rasa inda na shiga.
Amma sai Allah ya kare ni da yake banda rabon wahala nasamu wani abokin shi ya tausaya min ya fada min ainihin gaskiyan abinda ke nan.
Raiha ta mike tana cewa ni zan tafi tunda naga kamar baki yarda dani ba yanzu amma nasan watarana zaki tuna da wanan dan zaman da mukayi dake.
Ni zan tafi kuma ban tsoron ki fada mashi cewa nazo gurinki don yanzu a shirye nake da na tona mashi asiri a harkan da yakeyi .
Ta juya tare da daukan jakarta dake saman kujera tana cewa idan kin shirya saurarena sai ki nemay ni.
Har Raiha takai kofa zata murda kofan Nura tace kinga dawo ki zauna ai bamu gama magana ba tukun ko?
Baki da niyar saurare na shiyasa kina ganin kamar kishin Nasir na tare dake yasani zuwa gurin ki ko?
Ba haka na bane amma akwai wasu yan tambayoyi da zan maki ina bukatan amsa daga gareki in naji su daidai kinyi gaskiya.
Raiha ta dawo ta zauna tana kallon Nura ido da ido tace ina sauraren ki ko?
Hmm wai ma ta ina zan fara tambayan ki ne duk kin sani a caji wallahi.
Duk ta inda kika fara in na sani zan baki amsa insha Allahu.
Ok tau dan Allah kunkai kamar tsawon wani lokaci dashi Nasir din a tare dashi.
Ummm gaskiya mun kai kamar wata takwas muna tare inda a sannu ya fara koya min wasu abubuwa na rayuwa.
Kallon ta Nura tayi da kyau tace hmmm lalai ma amma ce min yayi tunda matar shi suka rabu bai kara neman wata ba bayan ni.
A,a karya yai maki don kafin ni akwai wasu da har yai galaba a kan su yanzun haka suna waje on behalf of him suna karuwanci a Spain.
Kai wai da gaske kike da zancen ki ni yar uwa wallahi ba karya a magana ta sai tsabar gaskiya kawai.
Ok ya taba zuwa dake tafiya ne ke dashi kubar garin nan zuwa wani waje?
Tace kwarai mun je lagos da sunan yatafi aiki ashe yakaini ne gurin yan commuty din su sugan ni idan zan yi sai ya dawo ya shirya tafiya na.
Mikewa tsaye Nura tayi tana fadin ikón Allah na ko yarda da zancen ki don duk inda muka tafi sai naji ana cewa she is ok,
Very pretty you will get a high level on dis pretty,
Sai da nai mashi magana ya daina kaini ana fada min hakana don ban son jin wanan kallaman daga bakin arna.
Murmushi Raiha tayi tace a can bai nuna maki true color din shi ba ne ko ?
Kamar yaya Nura ta tambaya.
Murmushin takaici Raiha tayi tare da fara fada mata duk yadda yayi da ita a garin Iko din.
Mikewa Nura takarayi tsaye tace umm ummm na yarda da zancen ki gaskiya don nima ya jawo wani abokin shi akan na tarda mu kwana tare dasu su biyu amma bai san ina jin lokacin da suke maganan haka ba sai na bijire mashi tun kafin dare nace period yazo min.
Mikewa Raiha tayi tace nasan koke can akayi shiyasa nasa a saka min ido a kan shi nai alkawarin duk yarinyar da yai niyar batawa sai na kwatota daga halaka hannun mugu azzalumi mayaudarin banza macuci kawai.
Nan suka zauna sukai ta hira akan yadda zasu dau mataki a kan shi don kada yaci gaba da abinda yakeyi.
Tun wanan ranan suka kulla kawance da junan su inda ta rako Raiha tana mata godiya.

****** ********* ******
Tun daga kofa yake kwala wa mariya kira har zuwa cikin gidan, maria wace ke duke tana wanke wanke taji kiran a bazata yai mata yawa.
Ta mike tana fadin gani nan babban Abba lafiya dai ko kira haka daga waje babu kakautawa.
Yace cikin hasala yanzu naga malam a kasuwan mu yake ce min wai yaran nan yanzu basu zuwa makaran ta ko yaushe.
Shi Abba ma sai ya makara kullun kafin yaxo in ma har yaje din yace yai magana yan uwan shi suka ce wai talla yake zuwa.
Tace tallafa tallan may wani kallo yai mata na ban yarda dake ba fa.
Tace ba gaskiya bane in zai yi talla ai ban dora mashi ban fada maka ba balle ma nasan ba yarda zakayi ba.
Shi dai kila yara sunyi mai yawa yanzu bai gane zuwan su da rashin zuwan su shiyasa ya fadi hakan.
Yanzu ina suke ya tambaye ta tare da tsureta da idanuwan shi tace sun tafi tin da karfe hudu suna can.
Yace ai zan tafi nagani ko suna makarantan ya mika mata ledan ce fanen da yayo ya dauki buta zuwa ban daki.
Nan ta samu tafa leken zaure ko Aliyu yana tafe saiko gashi ya sayar rataye da roban shi na talla a wuyan shi.
Da sauri ta tare shi ta karbi roba da kudi tai mashi magana kuskus a kune yaron ya juya da sauri yabar gidan.
Kafin maigidan ya fito ta boye roban da kudin da sauri a dakin kayan su ta kama aikin ta.
Yafito daga ban daki yana fadin yanzu zan tafi nagani idan suna can ko kuma wasa suke tsayawa yi a hannya.
Yafita tana ce mai a dawo lafiya bai amsa mata ba don a cike yake ran shi ya baci sosai.
Don shi bai wasa da hakkin iyalin shi a kan shi don haka yake matukar saka ido akan al,amarin yaran shi dama ita kan ta matar tashi.
Tun daga nesa ya hango su a zaune gaba dayan su don haka sai bai karasa kusa ba ya juya zuwa kasuwa ko zai dan kara samun wani abin tabawa a can.
Kafin ya dawo yaran sun rigashi dawowa gida Aliyu da yuwan taci ta ishe shi abinci yafara nema yaci sannan yai wanka zakace bai tafi ko ina ba .
Taja ma yaran kunne akan duk wanda yace Aliyu yana fita talla sai ta yankewa yaro kauna a gidan.
Bayan maigidan ya dawo ne yake tambayan yaran inda suke

Please Login or Register in order to submit comment