Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

sai yadda tayi da kowa agidan baki daya.
Hjy kubura ce kawai bata samu ta mallake yadda ranta ke so ba amma ko ita din ba laifi don bata iya kifar mata da,gwaunati a gurin mijin su ba.
Amma wanan munafukan Hauwa,u zamani amarcin ta Alkah daine yanufi takai wanan lokacin a gidan Alhaji don gaba daya hankalin shi ya koma ga majine kamar ita kadaice mace.
A ganin su Umma ke nan a lokaci amma kuma a gurin Alhaji tausayin Maji yake jin don ya dakatar da ita ga karautun ta yadauko ta ya hada cikin matan da ke aikin gwaunati suna da abin kansu.

****** ********* ******
Yanzu abinda ya,rage bukina baifi wata bakwai ba don an dagar da zancen bukin da babana yai ciwo ne shi ya roka abari har guri ya sha iska sai ayi.
Haka kawai kwatsan ranan muna zaune sai ga sadauki ya shigo ya fito daga cikkin garine fun safe safe ya fita sai da yamman nan ya shigo gida.
Suna hira ne da maji yayin da mu muke harkan gaban mu can ya sa murya ya kira sunan Amirah ta amsa da sauri tana fadin na,am yayana.
Yace zaku iya yin aiki hajji bana kuwa don tare nike son in tafi daga club din mu na samu kyautan kujera har har biyar.
Kinga dani dake da maryan nake son mu tafi sai tsagal Maryan tace da Bintu ko?
Tsit falon yayi don sun san maryam tayi tsaga da fadi gaskiya.
Yace wanan bakauyan taje mijin ta ya kaita mana nidai ni dake da Amirah nace kina min gayyan wasu takarce can daban.
Kai ban son rashin kunya Fatima ce takarce kuma yace ba tana da miji ba taje ya kaita.
Ai dai kasan zai iya kaita tunda yana da halin shi shima maji ta fada mai hakana.
Don Allah dai yaya ka hada,harda Bintu mu tafi ita ma ta sauke don Allah tana fadin cikin dan marairaicewa kamar karamar yarinya.
Yace maryam ashe ke karamar yarinyar ce yaya zai kai ta saudiya bayan tana da miji idan yai karana fa na kai mai mata saudiya bada sanin shi ba.
Don haka ki bar wanan zance don Allah nikan da naji ta matsa zance ina duke kaina akan littafi.
Nace Anty maryam bar zancen nan nima ban faye saka kaina inda Allah baikaini ba.
Nafi kowa murna yau dajin yan uwana zasu gabas su sauke farali at early age din su.
Muryan maji ne tace ai yadda Allah ya bashi ikon , biya wa yan uwanki ko ke haka zai bashi ikon ya biya maki atafi dakw kafin kiyi aure.
Maji na fada maki wanan kujeran kayautan su na,samu nima daga wa ni kungiyan mu dake can kasan Dubai.
Jin nan babana ban son tsaya wani kace nace kawai ka bari yaran nan su tafi da yar uwar su .
Kai kanka kasan da cewa, bamu taba tsan manin irin haka ba a rayuwan mu.
Shiru yayi har maji ta gama fadan ta baice uffan ba nidai takaicin irin wanan halin da yakw min sun kai min ko ina amma indai har nai aure na bar gidan su na huta da komai ma.
Can ya dan furzo iska yace yauwa Maji na dade ina son in tambaye ki naji sai abubuwa sukai min yawa ban samu lokacin tsayawa tambaya ba.
Fadi ina jikin muma dai shiru mukayi muna saurarwn shi sai da dan garani ina kokarin yin abindake a gabana ne alokacin.
Yace Maji wai akwai wa ni tsoho da naje gurin shi kwanaki bashar ne yakaini gurin mutumin
To da zan dawo sai yake cewa idan nazo gida na fadawa mahaifiya na kada ta manta da alkawarin da tayi na cewa zata kaini da kanta gurin da aka bukaci ta kaini.
Ni din nan inji maji ta fadi cikin dan murmushi da mamaki a fuskan ta a lokaci guda.
Tace kai mutane akwai yaudara wallahi ko sai mutum yai karya ne zai samu abu daga gurin mutane ?
Shiru nayi idona akan littafi amma kuma zuciya ta tana nazarin wani zance can a baya tun farko.
Amma maji wanan mutumin wallahi tsoho ne sosai kuma ban tsan mani yaudara bane yadda yai min maganan
Don zanfita cikin murmushi yace nacewa mahaifiya na tayi niya ta tafi inda tai alkawarin zata kaini da kanta in ba haka ba gaskiya akwai matsala,babba nan gaba.
Don tana tunka ana walwale mata ne za,a mayar da hannun agogo baya sosai .
Mai makon naji maji ta tuna alkawarin da tayi a baya sai naji sun buge da zagen tsohon mutane kawai.
Suna kiran macuci ne ma yaudari don taci kudinw yake fadin haka Allah yasa dai ni ba mai zuwa gurin malamai bane da yan tsubbu neman taimakon su na dogara ga Allah.
Amirah tace ba dai maman ba kan yaje can ya yaudari wasu gaba amma ba nan ba kan.
Batare da na kalle su ba don shima mai maganan kanshi na duke ne kawai alaman surutun su yai mashi yawa.
Sai muryana kowa yaji a falon ban juyo ba ban dago kai ba nace mama kece ba karya mutumini keyi ba.
Da sauri sadauki ya dago kai yana kallona itama uwar hakane ixo ta tsura min don ban taba mata haka,ba duk zamana da ita.
Tace Fatima kikace nine nace zan kai sadauki wani guri ban kai shi ba nace eh mama ,
Kai Bintu yau kuma maji zaki kullawa sheri haka maryam ke nan ke fadin haka cikin dariya.
Na girgiza kai na nace bazan taba yiwa mama sheri ko wani nataba har abada.
Dan tabe baki yayi daga inda yake zaune yana wani game da,wayan shi na,wasan driving.
Don yakan dan taba wasan mota a America tare da,samari yan uwan shi don nishadi kawai haka har kudi suke sakawa ko kyautan wani abu ga wanda yaci.
Mama tace dada,Fatima kikace nine nai alkawari na kara cewa eh mama sai dai bazan tuna maki ba sai wani lokaci in kuma kin tuna shike nan.
Amira tace a to dama dai ba,a shiga tsakanin Bintu da maji don sun fi kusa, kila tare da ita akai zancen.
Nace ai harda ke anty don gaba dayan mu musan da zancen sai dai mantuwa kawai .
Dan dariya yayi yace wanna yarinyar Allah munafukace Maji baki dai son ana fadi ne kawai amma ji daurewa wai kowan ku yana gurin.
Dakata Babana tunda Fatima ta kuke da haka akwai magana ke nan ya mike tsaye yana fadin ni kan na fita don bsn iya sauraren shirmayn yarinyar nan gaskiya.
Yana ba da baya na,shake murya nace mama kin manta maigani yace kikai mashi sadauki inda gwago mai masa ta tafi.
A,a,a anyi haka Fatima shiku jin ina kus,kus da maji yasa shi juyowa ta ce tabbas anyi haka Amirama,tace wallahi na manta muna zaune kuwa aikai maganan.
Cikin wani fargaba Maji tace babana dawo ka,zauna don Allah da mamaki yake kallon mahaifiyar nashi don bai san may shu,umar yarinyar na tafada mata ba a lokaci guda yaga ta birkice.
Tace don girman Allah ka fada min yadda aka fada maka ka fada min a take ya kara nanata mata, sakon da tsohon ya fada mai.
Tace inko ba wani ikon Allah ba yaya akayi wani yasan wanan zancen don dai ba,a nan akayi shi ba.
Mamakin yadda maji ta rude a lokaci guda haka ya bashi mamaki matuka yace Maji injin dai lafiya ko yace cikin kallon fuskan ta ido cikin ido.
Take ya fahinci da akwai matsala ke nan yace please Maji may ke faruwa ne wai?
Ko zancen mutumin gaskiyane dai yake fada don ni ban dauki zancen da wani muhinmanci ba kada haka ya tayar maki da hankali.
Maji a sanyaye ta,ke ce mai gaskiya Babana akwai matsala saboda akwai wani mutum da haduwa kawai nayi dashi ranan ina asibiti ya shigo gaida mu yake cewa kana da matsala don Allah nayi kokari nazo dakai gurinshi ya ganka.
Nai alkawarin zan kaika amma kuma kaga na manta shaf wallahi inba yanzu da Fatima ta tuna min ba.
Ban san lokacin da na sauke ajiyan zuciya ba jin yadda Maji ta canza maganan a lokaci guda.
Don dama ina gudun ace daga gwagona zancen yafito yace zata koya wa uwarsu bin bokaye nima yana iya sakani gaba da zagi don nasan halin shi.
Yace amma Maji kin dauki zancen serious ke nan ko?.
Tace idan ba serious matter bane yaya za,ayi zancen ya fito daga gurin wanan tsohon.
Kaga ke nan maganan mutumin gaskiyane tunda ga zancen yafito a gurin ka.
Jikin maji yai sanyi sosai a lokacin don sai ta shiga tunane watau ke nan masu sherin basu daina ba ake nufi ke nan.
Tai mamaki da taji yace yanzun za,a tafi gurin mutumin ke nan tace ya kamata gaskiya .
Zan samu lokaci sai mu tafi kafin na koma ke nan don na kusa tafiya ba kuma zan dawo ba sai nazo daukan yaran nan mutafi don ta inter national zamuyi tafiyan.
Maji tace amma na fada maka da diyata za,a atafi baice komai ba har ya mike zuwa kofa sai lokacin ya ke cewa Maji sai ki shirya mu tafi dake kenan don bazan kwashi wa yan nan ba duka su zama min wahala a can.
Don nima ina son nayi inganttacen ibada banda lokacin taulali dasu gaskiya don kin san yar ki bakauya ce matar bakauye kuma.
Yana fadin haka Fita yayi daga dakin nima sai yau banji haushin shi ba don ya gama min komai a duniya.
Mutumin da adalilin shi zai shiga kasa mai tsarki ai yagama min komai wallahi ko a duniya dole nayi hakkuri dashi don iyanzu na fahinci halin shine haka gwatsale mutum a take don bai son raini.
Nikuma yar kauye ce baruwan mu da banbants babba da karami gurin fadin magana.

****** ********* ******
Maji ta tsara Baba hat ya yarda cewa zadu duba jikin Baba na ne akauye don haka muka fara shirin zuwa gurin da akai magana.
Don ta kira gwago ga waya sunyi magana akan tafiyan mu kuma gwago taiwa dan uwan nata magana yasan da zuwan mu gurin shi.
Sadauki ne dai bai san cewa da mu za ai tafiyan ba sai lokacin da za,a tafi yaga duk mun shirya tafiya yake cewa
Wa yan nan fa kuma Maji ?
Tace dasu zamu tafi don suma ina son na kaisu gurin mutumin ya gan su.
Kaman zai yi magana sai kuma yai shiru yana tsaye tsakar falon ya harde hannayen shi guri guda.
Can yace sai dai da Bashar zamu tafi ban tsan mani motar zata dauke mu ba fa.
Tace ai zamu iya matsawa mu hudu a bayan dukkan yace da yake ita wanan yar fillon ba jiki gareta ba ko?
Yadda maji tace hakane mu hudu muka matse a bayan motan muka kama hanys sai garin.
Tun shigan mu mota banyi magana ba don idan na shiga mota amai nakeyi ko yanzu shi ke damuna.
A hankali na bude ledan da na riko na shige cikin hijjab dina naita kwarara amai tun ina yi a boye har Maji ta gane da sauri tace subbahanallahi.
Fatima amai kikeyine ?
Da sauri ya juyo yana fafin oh shit,
Don Allah Bashar parke motan da sauri kada ta damay mu da wari a mota.
Fada yake yana fadin kin san baki da lafiya don gulma shine sai kin biyo mutane kuma?
Yaja tsaki aka fito da sauri na samu guri nai ta shara amai mama tana a kaina sai sannu take min.
Da ya tsaya min muka shiga mukaci gaba da tafiya, an fara tafiya cikin jan tsuki yace i hate naga ana amai wallahi.
Bashar tace kasan wasu mutane idan sun shiga mota sai su dinga amai don warin petror.
Da kyat naga,mun kawo garin kaina yana,duke sai ciwon kai dake damuna a lokacin sosai.
Gida ne irin ginan kauye na haki da itattuwan dake basu innuwa manya manya a kofan gidan.
Suka tambaya kamar yadda aka fada masu wani yaro ya shiga yai masu iso akace a shigo daga zauren.
Maji ce tafara shiga taiwa mutumin bayanin komai yace to a shigo babu komai dama irin matsalan nan sai anyi wa mashi dabara.
Dattijone fari dogo dashi baida jiki sosai sai dai yana da fatin gemu mu bamu shiga ba muna zaune a bayan mota.
Sai Bashar dake tagaba sosai bai shiga ba har sun shiga sadauki ya fito yai mashi hannu daya biyo su mana.
Sun zauna aka gaisa yake tambayan shi yaya jama,a ya aiki ya amsa tare da bin zauren da kallon irin littafan dake tare a cikin zauren da ido.
Malam ga yaron kamar yadda kai umurnin nakawo maka shi yace nagan shi hjy.
Hannu ya mikawa sadauki inda shima ya mika mai azaton shi gaisawa zasuyi sai yaji ya rike hannun nashi idanuwan shi ya lunshe yana fadin ikon Allah.
Can yace umm,umm Allah mai iko, aida sun barka da sun sha alheri fiye da tsanmanin su.
Sai ya sake hannun sadaukin yana girgiza kai yace mutane basu da imani yanzu duniya tai nisa wallahi.
Agida akwai matsala sosai hjy hakama a,waje akwaishi.
Sai dai ita matsalar ta waje ba wani matsala bane akan harkan samun shi ne.
Nan ya dago kai yacewa sadauki ka na iya gane wani bakin mutum daga cikin ku mai dan saje a fuska sai dai ma naga kaman ba musulmi bane.
Yace akwai ranan da yaba wani abu a cikin leda fari kai kadai baiba kowa ba.
Sai dai anyi sa,a kana zuwa gida ka manta bakaci ba sai bayan kwana biyu kaga ledan ka bude amma sai kaga abin ya zama baki.
Shiru yayi yana son ya tuno wanan ranan sai zuwa can yanisa yace anyi haka malam,
Amma Daniel ne abokin wasa na ne saida iyamurine shi ba musulmi bane.
Yace nagani ai .
Yace Allah ya kareka da kaci yadda wanan anin ya koma baki da haka jikin ka zai koma ayi maganin duniyan nan sai dai Allah gaskiya.
Yace amma idan baka yarda ba abinda zan baka yanzu idan ka gwada zakaga insha Allahu ba yin mu ba da yardan ubangiji bazai yarda ko hannu ya kara hadawa dakai ba.
Burin shi shine saboda kaine bai daga ba kakai mashi ko ina don yana ganin kaine ka,tare mashi wuri.
Ikon Allah inji maji tace ko ina da matsalan dai, malam yace yanzu muna A LOKACIN NE,
Ai yanzu duniya ba,ai mata hawan kawara sai dashiri ake shigan ta don mutum yana barci ana mashi nasari ne.
Bashar yace kaji abinda nake fada maka kullun amma kai baka ganewa ne shiyasa.
Shi dai nisawa kawai yayi.
Hankalin shi na gurin tunanen Daneal kawai yasan bai kaunan shi tun farkon haduwan su suka fara samun matsala amma daga baya sai ya daina tsanar shi.
Yace hjy sai zancen gidan ku gaskiya bazan boye maki ba akwai matsala sosai a gidan.
Nan ya fara basu bayani tiryan tiryan amma bai fada masu sunayen masu wanan aikin ba kamar yadda yaiwa gwago bayani a baya dama kuma,shirin da suke a yanzu.
Har kan yaranta mata da aka,asirce mata su akan suyi ta zama ko kare bai kaunan su balle mutum.
Nan kan ran sadauki yai matukar baci cikin bacin rai yake fafin wai Maji may mukaiwa wa yan nan mutane ne haka a duniya.
Kagin tai magana malamin yace hassadane kawai don sun san kokai waye shiya kawo haka kawai..
Maji tace yaran suna nan nazo dasu ai yace na sani don nagan su su uku ko?
Sai dai dayar bataki bace Allah daine yakawo maki ita cikin hikima irin na ubangi wanda duk abinda kaga ya tsara ba,a banza yake tsara shi ba.
Zaman ta gareki alheri ne sosai koda yake bama sai na fada maki ba ai kema kin sani.
Sai dai zatai aure amma dai auren yanzu gaskiya sai Allah don banga yuyuwan shi a halin yanzu.
Malam daga gurin mijin ne ko kuwa yace Allahu,a,a lamu sai gaibu sai lillahi gaskiya.
Cikin ran sadauki yace aidama nasan wanan mutumin yaudaran tane zaiyi sai yaji malamin na fadin amma akwai abinda zanba kowan su insha Allahu komai zai walwale da yardan Allah.
Sauran ma insha Allahu mazajen su zasu fito bada dadewa ba ai.
Nan dai yaba yaya sadauki abubuwan da,suka dace tare da kara jaddada mai yadda zaiyi amfani dasu.
Sai yace ace mu shigo idan mun fito sadauki ya shigo shi kadai sai uwarshi akwai maganan da zai yi dasu wanda siri ne.
Nan dai yai muna duk abindaya dace da kowan mu muka fito da yan ledojin kulin maganin daya bamu daga zauren.
Ni a lokaci duk a galabace ma nake don ni ban san wai ina da matsala ba,su dai ne na dauka masu matsala kawai.
Muna fita sukai magana ta siri sosai da mana ta fada mashi damuwan ta yai kuma alkawarin taimaka mata.
Sadauki ya shigo ya zauna mutumin ya kalle shi yace kai babban mutum ne watarana zaka tuna da magana na matsalan ka dayane shine wanan shaye shayen da kakeyi.
Duk da naga abinda sauki yanzu sosai akan ka don abin yarage maka fiye da baya can.
Yace sai kuma ka kara da hakkuri don ko yaushe biyayya na iyayye yana kai mutum ga alheri.
Yai mashi nasiha sosai akan duniya tare da kara mai wasu yan abubuwa irin nasu.
Inda yace ya tabbatar kagin ya tafi gurin neman shi yayi abinda ya bashi din.
Kudi masu yawa ya ba mutumin sai yai dariya yace ba haka nake ba ni dari biyar kawai zaku bani ko shi kada kuce naki karba ne da ban karba ba wallahi.
Sunyi mamaki sosai muka kama hanya sai sokoto koda zamu dawo naita kakarin amai saidai da yake cikina ba komai sai kumfa kawai nake zubowa.
Bashar dasu mama suna ta faman yi min sannu amma,shi ko kallo ban ishe shi ba.
Da la,asar muka iso gida tun lokacin kowa ya fara abinda aka bashi yayi daga gurin bawan Allah.
Don har bashar saida ya anso nashi shima don mutimin shi da kan shi ya bashi taimakon.
Tun dawiwan mu nikan ina dunkule saman dogon kujera harda barcin wahala saida nayi.
Anty maryam ce ta dafo min liptop da lemun tsami na dan sha shine na dan ji dama sosai.
Ya shigo falon yayi wanka ya,sauya kayan jikin shi a lokacin yasa wando da rigan na maza mai dogon hannu.
Gani a kwance na dunkule yasa ya dan tsura min ido sai yaji na bashi tausayi sosai.
Yace ke may ke damun kine yanzu kuma?
A sanyaye nace cikin bata fuska kaina ke min ciwo.
Bari in nafita sai a sayo maki magani kisha.
Nace nagode.
Wanan gidiyan da nakan yi mai idan yai min alheri yakan ji matukar dadi a,ran shi don shi mutum ne mai son yaji ana godiya gare shi.
Sosai ya mayar da hankali shi ga maganin shi da mutumin ya bashi don yai matukar yarda da zancen mutumin ba din komai ba,rashin amsan kudin su da mutumin baiyi ba.
Ya dawo ya,sayo min magani harda na amai da kuma drinks mai sanyi na kwali.
Ina kwance na na dunkule a saman kujera su na kallo ni kuma gani kwance a dunkule sai dai ba barci nakeyi ba idona biyu.
Muryan shi naji yana tambayan su ita wanan barcin takeyi har yanzun ne ko jikin ne ke damun ta?
Maryam tace tace kanta kawai ke ciwo yanzu yace ke tashi ga magani ki sha ko zai lafa maki.
A hankali na mike zaune daga kwancen da nake sai dai still ina dunkule ga hijjab ga kuna blanket dana yafa ajikina.
Na karba tare da bare maganin na kai abakina saida na dago kai naga ya tsura min ido ashe ni yake kallo daga inda yake zaune.
Da sauri na dukar da kaina kasa bban tsaya shan drinks din ba yake cewa bazaki sha juice din ba ne?
Nace a,a ban iya sha yanzu sai nakai kwance daga inda na tashi yamike zai bar falon yana cewa idan bai bari ba sai akaiki asibiti ke nan.
Ya fice daga dakin na lumshe idanuwana tare da komawa barci a lokaci guda.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,


IDAN KIN TURAWA WANDA BAI BIYA BA BAMU YAFE MAKI BA ALLAH YA ISAR MU NA AKAN KI,,,,



Tun kawo laife na yaya sadauki ya kara tsananta min a gidan su, dan abu kadan zanyi ya dinga min fada cikin hasala da bacin rai.
Wanda shi kanshi bai san dalili yi min haka ba haka,kawai yake jin haushin yarinyar a ranshi.
Duk da maji tana mashi fadan haka amma ya kasa rangwanta kiyayyan da yake ji nawa a ranshi.
Idan yana gida ban fitowa falo sai naji ya fita daga gidan zan fito falo don nima haushin shi nake ji yanzu don a matsayin mugu macuci nake ganin shi.
Nasan kuma don saka mai idon da nakeyi ne abaya shine yasa yake jin takaicina haka.
Maji sai shirin bukina dake kara matsowa takeyi a hankali, irin su kayan kitchen da wasu uan abubuwa su take sai min.
Kabir yace idan anyi aure a sokoto zan zauna a gidan shi na garin sai idan anyi hutu zan diga zuwa gurin su Abuja.
Maji yakira ya fada mata tsarin da yayi akaina da ta tambaye shi kan al,amarin karatuna da nakeyi.
Sadauki ya shigo ya samu mama tana wayan da Kabir yana jin duk abinda suke fadi a karshe Kabir din ke cewa mama ko tsarin bai maki ba haka?
Maji tace gaskiya naji dadin hakan Allah ya albarkaci rayuwan auren ku, ya amsa cikin jin dadi da Amin mama.
Mama tace Kabir don Allah ka rike min Fatima amana don Fatima yarinyace dake bukatan kulawa yace insha Allahu mama kada kiji komai nima nasan da hakan.
Yana zaune ya fahinci da wa mama take waya ya lumshe idanuwan shi jin hiran nasu yake kamar a fili Kabir yake ya shake shi.
Sai tsuki yayi lokacin suna sallama zata kashe wayan yace tsohon banza kawai.
Kaidawa kuma kake tsuki anyi wani abin ne ko may?
Yace cikin daure fuska kawai dai nayi ne don wanan shirmay danaji anayi.
Shi waye da zai dinga yiwa mutane barazana kamar wani attajiri can.
A,a ikon Allah waikai sadauki ina ruwanka da zancen nan ne?
Ina da ka mayar da kanka abin kwarai agurin kane za,a zo neman auren yaran nan.
Yace wani maji da ban bashi ba kawai mutum ya tsufa amma yana halin yara .
Idan aure yake so bai zuwa ya samu bazawara su shirya sai yafake zai bata yar mutane.
Ya juya inda nake zaune raina yabaci don abinda yake min yafara isata, yace jita don Allah daga kawai ance mutumi a abuja yake

Please Login or Register in order to submit comment