Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tsiya.
Bashar yace sai dai yanzu kuma ka rufe daki da Fatima amma bani ba Bashar ba ya juya yafara tafiya yace bari ma na shiga cikin nai ma maji godiyan wanan babban albishir din da kai min.
Da sauri sadauki ya jawo shi ta baya yave kada ka farashi wallahi har ta zaci ko nayi na,am ne da zancen har ina farin ciki da zancen ne.
Farin ciki kan ka kanayin shi komai dadewa zakace na fada maka ai.
Wallahi kada ka fara kaje gurin maji na fada maka, Bashar yace mai da yukan ka a kube kamanta nima maji sarakuwa tave ina kunyan ta yanzu.
Kaima kuma ya kamata ka fara kunyan ta daga yau dan ta zama sarakuwar ka kaman ni daga haka yafita dakin da sauri don yana iya shakoshi ta baya yadda yaga ya hasala.
Dan iska da ka tsaya kaga tsiya a dakin nan ya dade tsaye dafe da bango sai tsaki yake shi daya a dakin.
Sai can yaji taahin motan Bashar daga gidan ya sauke ajiyan zuciya kawai



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,,


IDAN KIN KARANTA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA ALLAH NE SHEDAN HAKA MUNA BINKI BASHI,,,,


O lala ka kai mara mutunci sadauki ka gwada min baka da tarbiya yau, dana so nace sai na bi ra,ayin Fatima akan wanan zance amma yanzu tunda haka ne abin bari kaji indai har ni ce na haife ka ko bana raye sai ka auri Fatima.
Kuma idan ka sake ta ban yafe maka ba a rayuwa na, ba sadauki ba har ni da ke tsaye sai da nakai zaune cikin kuka ina fadin.
Don Allah mama kada ki min haka wallahi bashi ba koni ban ra,ayin wanan hadi bani son shi mama na tsane shi kamar yadda na tsani mutuwa na.
Inda nake ta karaso tare da dafa ni kadan tace Fatima, bani son ki da fadin haka nasan baki so amma don ni da Allah dashi kan shi mara tunanen abinda zai je ya dawo idan ya auri wata can sabba zakiyi.
Kaina na noke a cikin kafafuna ina rusa kuka wanda baka yasa mama ta kasan lalashina a lokacin.
Sai ji nayi tana fadin kafita min a shiya tunda ban isa da kai ba baka kaunan farincikina baka damu da rayuwan ka ba balle nawa.
Zai yi magana tai mashi alama da hannu ya rabu da ita don Allah ya dan tsaya jin sai yaja kafan shi ya fita daga dakin.
Kaina ta dawo ta zauna a gefe na tare da dafani tace Fatima ina fatan kin fara fahintar manufana na son yin wanin hadin danake kokarin yi.
Don haka nake son fada maki sai kin jajirce sosai a cikin wanan al,amarin don akwai aiki sosai ja a nan gaba kafin komai ya dawo muna normal life.
Cikin kuka nace mama ni ba zan iya ba don bazan iya zama da miji mai duka ba bai da tausayi mama bai san darajan mace ba ko kadan.
Tai dan dariyan manya tace zaki iya Fatima zaki iyane na fada maki kuma ko bani raye zaki fadi da bakin ki, taimon da zaki min ke nan daya a rayuwana shine ki auri sadauki.
Don ke ce kadai yanzu nake ganin mafita a gurin ki, kece wace zata kwato min shi daga duk wani sherin rayuwa dake bibiyan shi.
Don Allah Fatima ki daure ki kanne ki fitar da duk wani shakku dake damun zuciyar ki, ki saka a ranki zaki sadaukar da rayuwan ki ne don Allah don ni kuma.
Sai naji ta fara kuka a hankali cikin kukan tana fadin Fatima ban da wani mafita da yafi wanan a yanzu haka yasa kike ganin ban tausaya maki ba.
Wanan hukuncin dana yake insha Allahu shine zai kawo karshen azzalumai masu bibiyan shi dashi wanda ba wai sun fasa ba ne har yanzu.
Don haka kada ki zargeni a zuciyar ki na nuna son kaina a gare ki yadda na haifi Amira da maryam haka nake daukan ke ma din nina haife ki da cikina.
Don duk abinda uwa ko da zaiwa mahaifiyan shi Fatima kina min a rayuwana may zai sa na bari wanan daman ya wuce wanan yaron ina kallo yaje ya dauko min wata sabuwar fitina cikin dakina.
Dan uwan mahaifin shi ma yakasa bashi yarshi kan halin da yake ciki balle wani bare can sabba ya ba shi nashi a zauna lafiya.
Hakan da nayi shine daidai a gare mu baki dayan mu sai dai a yanzu kurciya ba zai bari ki fahince ni ba.
Ba dago fuska na dake shabe shabe da hawaye nace mama na yarda insha Allahu duk abinda yaya zai min zanyi hakkuri na zauna dashi saboda Allah da kuma ke.
Ta rungumoni zuwa jikin ta tana fadin na gode Fatima na gode yadda kikai min Allah kema ya baki zuria masu albarka a rayuwan ki.
Insha Allahu bazakiyi dakin sani ba ga wanan auren da yardan ubangijin mu.
Tace tashi kije ki gyara fuskan ki kada wani ya shigo ya samay ki a haka a dauka ko wani abin ne can daban.
Yadda tace haka nayi na mike na shige dakin mu sai dai ban fito ba na zauna cikin dakin kawai.
Amirah dai ba ruwan ta dani don tamafi yayan ta daukan zafi akan zancen don kwata kwata ta daina min magana gaba daya a gidan.
Sai harara da habaici kawai ne a tsakanin mu da ita, maryam kan ce na fita zancen ta na kyale bata da wayau ne da bata biye wa son ranta ba.
Ina ji ina gani yanzu na koma wata abin boyo a cikin daki ban zama falo ko yaushe kunshe nake a cikin dakin mu ban san komai da akeyi ba a gidan.
Karatuna ne kawai ya tsayar dani garin don da na gudu na koma kauyen mu gurin iyayyena da zama amma kuma ba daman haka don karatuna zai iya tabuwa.
Ranan dai da dare na ce bari na dan fito cikin su a falo na dan zauna kadan na samu daga Amira sai maryam zaune suna hira.
Maryam na ganin na fito take cewa a,a matar yaya yau kin gaji da boya ne kin fito ki sarara ke ma kina wani shigewa daki kina kumshe kan ki a ciki kamar lalle kafa.
Nai dan dariya ina zama nake cewa anty maryam yanzun dai ke ake ji zama nake ina karatu don exam da ya kusa.
Kwadayi dai mabudin wahala ne wallahi, in mutum yace ba zai iya tsayawa inda Allah ya aje shi ba ai yana tare da wahala a ran shi.
Zaman daki kan yanzun aka farashi tinda mutum yace shi dan shishigi ne ya kai kan shi inda Allah bai kashi ba.
Ban yi magana ba sai samun guri nayi na zauna da kyau, tare da mayar da hankalina ga TV dake aiki a falon a lokacin.
Kada dai mutum ya manta matsayin shi ga Allah ya dauki kan shi ya kai inda Allah baikashi inji maryam.
Anty maryam please bar zancen nan don Allah kada mama takai ga jin may mukeyi a falon nan.
Idan ma taji ai haka kike so ke don yanzu nasan abinda ya kawo ki cikin mu kuma kuke kullawa keda munafukan gwagon ki.
Nai matukar jin zafin zancen sai na dan ritse idanuwa na tace yanzu basai ki zauna ki auri maji din ba tunda shi wanda ki ke son mannewa din ya tafi sai muga wanda zaki aura yanzu.
Ko shekara dubu zai yi a can dole dai watarana ya dawo gida aiko?
Zasu ci gaba da sokawa juna magana sai ga mama tafito daga dakin ta da waya a hannun ta tanayi.
Da wata kawarta take waya tana cewa Insha Allahu ranan laraba mai zuwa za,a je kai kayan shiyasa na bugo na fada maki don ki shirya.
Amira ta kasa kannewa da uwar ta gama waya tace kayan wa za,a kai maji ?
Kayan auren yayan ku mana.
Can kauyen ko ina?
Ki tambaye shi mana kiji daga bakin shi ko?
Amirah da ta cika ta mike zuwa daki cikin kunan rai, waya ta dauka takira dan uwanta kira daya ga na biyu ya dauka.
Yace Amirah yaya akayine?
Tace yaya yanzu nake jin maji na waya wai ranan laraba za,a kai kayan auren ka kauye.
Dariya taji yayan natayi yace as maji wish zan kyale ta tayi duk abinda zatayi don lafiyan ta da kuma gujewa fadawa fushin ubangijina akan hakkin ta da ke kaina.
Amma ai nine mai auren ko let the vegan come into my house zata rena,kanta da kanta barni da yar iskan yarinya kawai.
Amira tace amma ni gaskiya yaya ina son ka dauki mataki gada ma ayi wanan auren kwatakwata wallahi don ina jin kunua ace wai Bintu ce matar ka gaskiya.
Class din ka ka kare ga wata Bintu can yar kauye wallahi nayi hating din yarinyar nan baka ga yadda ta wani kara komadewa bane ma yanzu.
Dariya yayi yace common Amirah fita zancen kawai ki bar su maji da munafukan nan maryam da Bash duk sune masu kara zuga maji ai zata zo ta same ni ne.
Suna gama wayan da Amira sai yaji gaban shi yai wani masifan faduwar gaba don ua tuna maganan maji da sukayi kaeshe dashi kan zancen auren.
Yadda ke kullawa zai wa Fatima muddin ta shigo gidan shi ga maji tai mai sharti akai.
Domin yadda yake ji a cikin ranshi a lokacin zai iya aiwatar da komai kan wanan manyar yarinyar dake son taiwa rayuwan shi karan tsaye.
Shi yasa ma yai saurin kashe wayan da sukeyi da Amira don maganan ta na kara tunzura mai ziciyar shi ce.
Duk yadda yake son yaiwa mahaifiyar shi biyaya akan auren zabin ta da tai mashi bai tsanmanin zai iya yin adalcin aure akan wanan yar kauyen dako Abuja bai iya fita da ita balle wani uwan duniya.

****** ********* ******
Kamar yadda maji ta fada haka din ne cikin satin da ya zagayo aka kawo lefen auren mu gidan mu.
Muna school har masu zuwa kai lefen suka taru suka dauka zuwa kauyen mu gurin kai kayan.
Akwati ne har guda goma sha biyu dankare da kayan irin na zamani, tsayawa fadar abinda aka zuba acikin akwatinan, sai abin ya zama tankar kauyancine saboda babu kadai ba asaka a ciki ba.
Nan abin yazama turiruwa ga matan kauyen zuwa kallon abin arziki.
Su gwago da yake sun san yadda ake a birni su ma basu bari abarsu a baya ba don suna tallakawa, suma sunyiwa yan kawo lefen abinda ya dace suyi.
Rago gassa abin sha da sauran takarce na kauyawa irin su fura da nono dakar hannu mai kyau cikke a raba mai marfi.
Yan kai kaya suka dawo suna yaba karamcin da akai masu a kauyen mu cikin jin dadi nan su hjy kubura aka shiga rabawa masu zuwa abinda aka samo don ita mama tabarwa yuka da naman zancen.
Har da su Umma da basu tafi ba ankai masu nasu sai dariya sukeyi wai ana gaba an koma baya.
Duk matan dake cikin gari yan gayu diyan masu kudi sunki dole an koma kauye inda ba asan ciyon kai ba an dauko yar kauye.
Amirah ta bugawa dan uwanta waya ta fada mashi duk abinda akeyi a gidan nasu har zagi da dariyan dasu umma keyi saida ta fada mashi.
Sadauki ya kira waya don ya shedawa mahaufin shi shifa gaskiya ba zai iya auren Fatima ba don yana da wace yake so Linda.
Don haka yake shirin fada mai ko zai samu mahaifin nashi ya fahince shi ba da son shi maji ke shirin wanan auren ba.
Don a kullun zuciyar shi taki yarje mashi Fatima a matsayin mata a gare shi abokiyar rayuwa.
Babs ya dauki wayan tare da sallama yana cewa Umar sanda babuga sadauki.
Sai kaji irin alheri da taron da mutanen arzikin nan gidan su Fatima sukayiwa yan kai kaya ko?
Ai ni nasan ban taba dana sani akan ka sadauki bar wa yan nan wawayen iyayyen naka su Atika suna zaton auren wayayya shine zani ga aure.
Sai gashi su gidan nasu sarakan ko ruwa ba,a mutane sun sha ga wullakancin da sukai wa yan kai kayan sai kiran babu babu kaza a ciki sukeyi.
Nasan dakai da mahaifiyan ka dama mutanen arziki ne ba yau ba don komai naku a cikin nazari kukeyin shi.
Yace lafiya dai ka kirani yanzu ko?
Sadauki da ya rasa may zaice a lokacin don duk jikin shi yai sanyi sosai dajin yadda mahaifin shi yake a cikin farin ciki yace.
Dama kawai na kiraka ne mu gaisa naji lafiyan ka don bamu samu gaisawa ba jiya.
Nan dai mahaifin ya shiga sa mashi albarka tare da fatan gamawa da duniya lafiya.
Suna gama waya da mahaifin nashi ya kira mahaifiyar shi sun gaisa sai kuma shiru sai uwar ke fadin kaji dai ankai lefen ko kuma sunyiwa mutane halarci sosai a can.
Cikin murya mai nuna damuwa yace Maji ni may zance akan wanan magana tunda zabin kine.
Yanzun ma nakira Baba na fada mashi zancen nawa auren na zabina da nake so sai shima yake min magana akan wai ankai kayan lefen ko amma ni ban so akai kayan nan duka ba tunda ba wata bace can da suka san darajan kayan.
Sadauki wace irin banzan magana ce wanan kuma ko kayi shaye shayen naka ne kake son mayar da mutane kananan yara ?
Jin dadin da kayi ne yasa har kake son watsa wa mutane kasa a ido ko may.
A kan wata arniya can har idon ka ya rufe kake son yimin cin mutunci ko may ?
To wallahi kaji na fada maka, ko da wasa nakara jin zancen arniyar nan a bakin ka sai na bata maka rai fiye da yadda kake tunane.
Don haka idan an aura maka Fatima sai kai gunduwa gunduwa da ita ka zuba a buhu ka kawon gawan ta nan.
Sakaran banza mara tunane an maka gata shine kake son yiwa mutanr rashin mutuncin ka da ka saba ko ?
Haka ya kashe wayan ran shi a bace yasan dai yanzu baida wata mafita yadda mahaifan shi suka hau zancen sai anyi wanan auren dole.
Da kyat ya ja kafan shi zuwa bakin window dakin da yake zaune cikin wani katafaren hotel na kasan LasVegas.
Tun ranan kuma baida sauran wata walwala a tare dashi ga Amira ta ishe shi da kiran waya tana mashi kwarmato wai taga maji ta karbi keys din gidan shi a hannun Bashar zasu tafi da mummy su duba gidan.
Idon shi ya rufe da jin wanan bakin labarin suka soma canza launi, zuciyar shi ya dinga mashi wani radadi da zogi ya mike tsaye ya nufi fridge din falon shi nan ya bude ya dauko wani dan mitsitsin kwalba ya kafa a bakin shi.
Yana shaye abinda ke cikin kwalban ya wurgashi kasa gefen shi kwalban ya tarwatse.
Dafe kan shi yayi yana wani irin huci mai fitar da zafi daga bakin shi, yana fadin why maji why zakiyi min haka please?
May zanyi da wanan yarinyar da ko na yini daya bata iya daukan lalura balle na zama dindin din.
Kai ba shakka wannan yarinyar ta zama mashi kafen ka al,amarinta ya na matukar caza mashi kai.
Yasan idan baiyi da gaske ba zuciyar shi na iya kamuwa da wata lalura da zai ja mashi komawa baya ga harkokin shi.
Yana kwance ya saman dogon kujeran falon ya dinga karanto addu,an samu sauki a cikin mayen da yake.
Ya jawo dan filon kujeran dake gefen shi ya rungumay filon a kirjin shi tare da rintse idanuwan shi.
Yadda rayuwan shi zai kasance da zama da wanan yar kauyen yarinyar a gidan shi, wacce ko kwaliyan kirki bata iya ba kullun tana dunkule,a cikin hijjab.
A haka zazzabi mai zafi ya rufe shi, ga dubin damuwa da kadaici daya ishi zuciyar shi.
Duk da shi ba likita bane yasan gap yake da BP shi ya hau a lokacin.
Don irin yadda yake jin kan shi yana mashi sai matsanacin kasalan dake damun shi,.
Gaba daya sai ma yaji zaman garin ya ishi ra shi baki daya tankar ana hura mashi wuta.
Haka ya wuni kwance a dakin shi ko wasan motsa jiki ya kasa fita yayi sai shawara yakeyi kawai ya koma gida ai koma maye a gaban shi zaifi mai.

****** ********* ******
Sosai mama ta mayar da hankalin ta gurin gyaran mu a cikin hikima irin ta manyan mata.
Ta hayan gyaran jiki da kuma magunguna na hausa da zasu karawa mace, ni,ima a jikin ta.
Lokaci guda duk da damuwar da nake ciki da tashin hankalin wanan kaddararen auren.
Amma haka bai hana ni canzawa ba nai matukar kyau, tankar ni nai kaina a lokacin.
Cikin dare ya iso garin muna folo a zaune gaba dayan mu har mama dake ta waya da kawarta kan wasu kaya da take son a hado mata.
Da murna suka tare shi duk da dare ne amma hasken fila ya haska kowan mu.
Saudaya ya daga kai, ya kalleni inda nai mashi sannu da zuwa kaman yadda kowa yai mashi sannu din.
Cikin dan sakin fuska kadan mama tace kai kana hanyane ashe bamu sani ba?
Yadan kai zaune a kasale yake cewa wallahi tafiyan dai gatanan kaman ba shiri nayi ta nima maji.
Maryam tace Allah yasa ka dawo ke nan har a gama buki yaya don idan baka nan ba zamu ji dadi ba.
Maji ta kwantar da murya cikin tsigan lalashi tana fadin haba ya dawo ke nan mana ina kuma zai koma ai gara ayi komai dashi yana garin don jama,an arzikin shi.
Amira ta saki wani irin tsaki tana cewa kai maryam ke wallahi baki da kunya sai kace kanki ne farau din aure.
Maji tace basu bane farau saidai su yanzun ne zasuyi dole suyi dauki kuwa.
Sai kuma Amira tai fushi wai da ita maji keyi don ita bata tashi aure ba yanzu a matsayin ta na babba cikin mu.
Ta mike cikin fushi zata shige tana cewa, Allah dai yasa ni ban iya kutsawa aso ni ba balle na kawo wanda bsi sona.
Maji tace cikin takaici wawiya kawai mara hankali shekaru yakai bata sani ba sai hauka.
Sadauki da idanuwan shi suke mai a lumshe yana sauraren kowa sai dan murmusawa yayi yace,
Maji ba dake take ba ai da maryam mai shegen rawan kan tsiya take magana ai.
Zaka ci abinci ne inji mama data ga dan nata cikin alaman damuwa yake.
Yace ban jin cin komai yanzu maji dan dama dama dai ko tea na dan walwale hajina dashi kawai.
Maji tace Fatima hado ma yayan ku tea mai kauri ya sha don yafi mai zama haka nan.
Na mike don dama a takure nake zaune a gurin na shiga kitchen don hado tea din.
A fakaice ya bini da satan dan kallo duk abinda yakeyi akan idon mama amma tai tankar bata gan shi ba.
Nafito da tea din hade da jug din ruwa cikin dan karamin tire dan madaidaici nakawo mashi gaban shi.
Na samu ya rike goshinshi dake damun shi da halbawa da hannun shi daya.
Nace cikin dakewa ga tea din yaya, ya bude idanuwan shi da kyat yai min alama da na aje a gaban shi.
Sai da ya ciro magani daga aljihun shi ya bare tare da hadewa tukun ya fara dan kurban tea din a hankali don zafin shi.
Baja jin dadi ne naga kasha magani mana mama take tambayan shi da hakan ?
Da kyat yasha cokali kamar shidda ya aje cibin tare da mayar da jikin shi saman kujera ya kwanta da bayan shi a hankali.
Muryan maji yaji don a lokacin na koma cikin dakin mu, maji tace mashi.
Ka sa damuwa a zuciyar ka ko dubi yadda duk ka lalace lokaci guda, kana ganin zan cutawa rayuwan ka ne ko may sadauki?
Ya dago kai tare da bude idanuwan shi yace namay kuma maji ?
Tace akan auren da kake gani ina son tirsasa makayi ba da son ran ka ba mana.
Yace maji ni fa banda zabin daya wuce naki a rayuwana akan may zan tayar da hankalina ga abinda kike shirin yi min gata.
Mama taji dadin kalamin shi sosai a ran ta har fuskanta ya dan baiyyana murmushi kadan.
Nan ta shiga mashi nasihohi akan hakkin aure tare da saka mashi albarka kwando kwando na mata biyayyan da yayi tana mashi fatan alheri.
Sosai ya dan ji sasauci a zuciyan shi dan kasancewan da sukayi da mahaifiyar ta shi na dan lokaci, abinda ya dade baiga hakan ba a tare dashi tsakanin su.
Ni dai tun wanan lokacin ban kara bi takan komai ba don ko kallon inda yake banayi balle nasha harara.
Hakan yana matukar bata mashi ran shi sosai yakance a ran wai wanan abar ce zata zauna da mutum har ta farauta mashi ran shi yaji dadi a haka?
Mace komai bata iya ba ban da dunkulewa a cikin hijjabi kulun kaman munafuka ko muguwa.
Wama yasani ko maganan Amira gaskiy ne asrice maji sukayi don suci arzikin su.
Don shi baiga abinda maji tagani gacwanan yarinyar ba har take kokarin yi mashi baki a kanta inba hasken fata ba kawai.
Gashi baida yadda ya iya dole yasawa zuciyar shi hakkuri da wanan auren kaddaran don ya dadawa mahaifan shi rai kawai tunda suna so amma shi kan yasan an tsere mashi gurin matar gwadawa tsara kan.

Ta ko wani bangare na gidan kowa sai shirin buki yakeyi banda mummy da babu nata ko daya a cikin bukin don ita yaran ta kanana ne kwarai agidan.
Sai dai kusan tare suke harkan bukin bangare mama da ita don ta saka kanta tsunbul a ciki inda su umma ke fadin wai kwadai ne kawai ya kaita ciki don taga gurin ci.
In bashi ba ai su ma yaran su ai diyan mijinta ne may sa zatafi bada karfi a dayan shiyan kawai.
Ta bangare na ni kan ba wani abinda na shiryawa aure sai harkan bukin Anty maryam kawai nake yi kamar nima ba amarya bace,
In dan anyi min magana nakance ni ba wani bukin da zanyi sai dai dan dama dama walima indan zan samuyi.
Su mummy sun tafi sun gyara gidajen mu yadda ya dace duk da ba wasu abu za akaiba mai yawa saboda ko wani ango yasaka kayan komai a nashi gidan.
Baba yai fadan haka yace don may zasuyi mashi haka da su bari shima yai wa diyan shi nashi bajinta da ko wani abu kewa yar shi idan zatayi aure.
Kayan aiki ne aka kai muna irin na amfanin mata ko shi ba wasu masu yawa ba don sauran abubuwa irin

Please Login or Register in order to submit comment