Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kalar kayan.
Tun daga fitowa na yake sakar min murmushi, sai dai wanan karon ya dan kara min hasske da kiba kadan.
Barka da fitowa, kalman da ta tare ni dashi ke nan da na iso inda yake tsaye,
Tuni naji wani wani kunya ya lulubeni saboda tafiyan da nayi ban fada mai ba kuma,nan garin mu da nazo ba,services ko dayaushe.
Na dan rusun na kadan na,gaishe shi, tare da,tambayan shi yaya hanya.
Cike da,fara,a yace hanya Alhamdullahi mai gaskiya,
Murmushi nayi nace gaakiyan may kuma nayi har ake kiran min ita cikin kunya na,fadi hakan.
Sai murmushi naji yayi ya dan kalleni ya kada kan shi kawai,
Yace wallahi Fatima baki kyauta min ba haka,kawai ki kama hanya ki wuto baki fada min ba ko a waya,
Sai kawai da naji shiru natura a,diba min ko lafiya ake ce min wai ai kin dawo nan.
Gashi kuma ban samu zuwa ba,don an turani wani course a lagos sai last week na dawo gaskiya banji dadin yadda kikai min ba.
Cikin yar muryata nace to kayi hakkuri nima,tafiyan tazo min bashiri ne.
Yace gaskiya banji dadi ba don sai ma na,fara zargin kodai ban samu karbuwa bane a gurinki shi yasa.
Dan satan kallon shi nayi tukun, san nan nace a kunyace ,a,a ba hakana ne gaskiya.
Sai naji ya sauke ajiyan zuciya yace tau Alhamdullahi,
Amma kuma kin shirya zaki iya auren mai mata har biyu ki zama ta uku?
Dammm naji gabana ya fadi don an tambayeni abinda nafi kowa tsoro yanzu watau kishiya.
Na dan kwantar da murya cikin dakewa nace idan Allah yayi hakan ne ai ban isa naja da ikon shi ba.
Sai ya dan zuba min ido can yace tau kin gama magana ke nan ai tunda kince Allah.
Ban nuna wani alama najin tsoron maganan shi ba amma sai nace ai Allah shike komai dama.
Nan dai muka dan taba hira dashi yana min karin bayani a kan, shi.
Yace matar shi ta farko yar uwarshi ne garin su daya auren gida akai masu shida ita duk da dai su suka hada kan su.
Azuciyata nace kaji matsalar ba yace sai tabiyun ita soyayyace ta hadani da ita kaunar abokina ne dake sokoto lokacin ina,aiki a sokoto kafin na koma Abuja mukayi aure da ita yanzun yaranta biyu dani.
Ya,kare da,cewa sai kuma yanzu da wata farar tantabara ta,sace min zuciyana a lokaci guda duk da can baya banyi niyar karin aure ba ina ganin matana biyu sun isheni rayuwa.
Sai gashi ganin farko da nai maki naji kin kwanta min a zuciyata fiye da tsanmani na.
Dafatan zan kara samu karbuwa a gurin ki bayan mun dan taba hira yake ce min zai koma don gobe yake son ya koma,sokoto ya dauki matar shi tare suka,shigo amma ya barta sokoto taga gida.
Yace min ina zan samu yara su sauke min kaya a,bayan motan shi
Nace cikin yar murya lah, dama ka barshi zuwan da zakayi gurina shine harda dawainiya.
Yace ai nasan baku rasa ba amma ni ban saba zuwa guri babu tsaraba ba.
Yaran makwabtan mu dake wasa a kofan gidan su na kira inda suka shiga da kayan cikin gida.
Nayi sa,a mama tafita zuwa uguwa don bata zaci lokacin zai tafi ba nasan da bata fitaba a lokacin.
Kafinta dawo nida Farida yarinyar da take riko muka tsince kayan tea da su indomie muka,boye inda bata gani.
Sauran muka barsu kofan dakinta inda inta dawo zata gani.
Tana ko shigowa tai tozali da kayan sai cewa tayi cabdi jam wanan kayan alherin kuma haka fa nake gani.
Farida tabata amsa dace wa Bintu aka kawowa su, mutumin da yazo kafintai wani magana sai ga babana yadawo daga gona shima tambaya yake.
Tace yarka aka kawowa su sai ka tambaye ta ko waye nidai in kun kwaso rigiman birni babu ruwana.
Allah ya,sauwaka babana yace sai ya samin kira nafito ina mashi sannu da zuwa.
Yakece sai na dawo na samu wanan uban kayan haka na tambaya akace waikece aka,kawo wasu.
Nace eh Baba Kabir ne dan hakimin Rabah yakawo min su dazun dayazo.
A ina kika san shi Bintu, Baba ya tambaya cikin son jin inda na san Kabir, nace Baba da naje gurin mamane shine muka hadu dashi a can.
Allah ya kyata yace inda ya isa gurin kayan buhun shinkafa dan gote sai jarkan mangyda da doya mai yawa sai tumatur din leda katon guda da taliya leda biyu,
Dankari inji Baba duk wanan din muke dashi haka nace eh Baba mu yakawo wa tsaraba yace,
Baba yace Bintu idan kin san bakya son shi kada muci kayan shi yazo yai muna,tasau watarana nidai k8nga banda,shi.
Shiru nayi ban yi magana ba baba ya juta zai futa nace baba zan dauki doya da taliya naba su Ama don su suka kwaso min kayan zuwa cikin gida.
Yace hakan na da kyau ki baau yadda ya dace azato mama tabawa bazata kalli kayan ba amma dana dauki doya manya zai kaiwa su Ama sai ji nayi tace kai amma kedai baki san ciwon kanki ba,
Wana abin duka zaki basu don kawai sun kwoso maki kaya maza rage su kinji nace to mama.
Nan aka,shiga sha,ani da kayan mukan mun boye namu bata sani ba ni da farida mun samu na karyawa safe da yamma mu faki idon ta,muyi amfani da abin mu.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,,


A LOKACI MU KE,,,,,

Zancen neman da Kabir yake min ya kewaye kauyen mu,sai ga yan uwan shi har gidan mu sunzo gaidani wai kuma suga ko wacece ni din.
Gami kuma da nuna goyon bayan su dari bisa dari akan neman da dan uwan su ke min.
Kamar yadda,dangin miji suke nuna goyon baya idan dan uwansu ya,tsiri aure, komai mutuncin da akeyi da uwargida sai an samu masu hakan daga dangin shi.
Nima hakane ya kasance dani don yan uwan kabir maza,da mata haka suke shigowa ganina,tunda ance masu nima ba a kauye nake zaune sokoto nake zama.
Basu san cewa ko a,sokoton labe nake zaune a gidan mutane kamar kuku.
A gaskiya da farko naso Muhammad Kabir kodon na samu inda na labe na,rufawa rayuwa na,asiri na huta da guzuban mama tabawa da nake ciki.
Yakan zo kusan duk karshen wata gida cikin irin zuwan da yakeyi sai yazo har garin mu da dan tsaraban shi na abin arzki yakawo muna.
Wata rana Kabir yazo wurina sai dai wanan zuwan bai dade ba kamar yadda ya saba dadewa idan yazo inda nake.
Ya ce zai koma na ya bude mota ya miko min wasu kaya dinkakku yake ce min anko yai min tare da,sauran matan shi.
Na karba nai godiya sai kuma ya kawo kudi masu yawa ya bani, amma sai nace ya,bar kudin kayan ma,sunyi min.
Amma sai ya,aje min kudin saman hijjab dina ya,shiga motan shi sai horn din shi naji na,dan daga kai ya sake min murmushi tare da jan motar shi yabar gurin.
A dakin mu saman tsohuwar katifan kadan da muke kwana akai amma na,gyara, shi mutum bai sani tsohuwace ta yagalgale saboda bed shirt da na,sa na,rufe shi lif ba,a ganin sirin ciki.
Dinkin kayane irin ta yan birni jakkuna da,takalma masu tsada sosai, sai kayan makeup set mai kyau dasu turaren suma masu kamashi sosai.
Kayan abinci yadda ya,saba kawowa haka ya ke jibge su a,kofan gidan mu yanzu tabawa shiru kake ji tsakani nada ita,sai lalashi.
Afili amma,a,kasan zuciyar ta,tankar ta soke ni takeji a rayuwan ta don kishi na take balain ji duk kiyayyan da,takewa uwana ya koma a kaina yanzu. Sai dai tana dan waye wane kawai don tasan wani lokacin nima nakan dan tsula mata tsiya yadda naso.
Don ban san ya,akayi tasan muna boye wasu kaya,ba,sai ranan ta zaci ko yanzu iri dane da,zata kwace min abina tabawa diyan ta har yan agolan da tazo aure dasu gidan mu sun fini dara a lokacin.
Sai ganin Tabawa mukayi a kofan dakin mu tayi tsaye kerere ta re da,daga labulen dakin cikin tijaran ta na yan iskan matan kauye take cewa,
Ke Bintu kwaso sauran kayan nan da kika,boye wanda aka kawo muku wai ke munafuka,shine kika boye kayan shayi wai don kada na,sha,
Ti jiya banyi barci ba ina jinku kuna sha ke da muna fukan can Farida, don haka na leka naga may kuke don haka kifito dashi nan.
A zatonta zan mike na dauko mata kamar yadda da can nake mata cikin rawan jiki.
Amma,sai taji murya na yau ina cewa,
Eh ko kingani fa,
Sai may,
Ina dai ba,sata,nayi ba,nawane ni aka,kawo wa ko ?
Don haka sai yadda,naga dama da abina Farida ce idan kince na barbata abarta mana yunwa ya kasheta.
Baki bamu abinci yadda ya dace sai dai kibawa diyan ki
Don Allah yai muna mafita shine kuma zaki nuna halin ki na hassada haka.
Eh lalai kuwa Bintu sai yau na,kara yarda kin shiga Birni tunda har ina fadi ki fadi haka,
Nace mama kece kikaja hakan don yakamata ace yanzu na ci ragowa gareki ko dan dan girman da na,kara.
Amma ke kullun sai kokari kike kiga kin mayar dani baya kin tausheni kin ha,ince ni kin fifita diyan ki a kaina.
Don banda,uwa agidan ai ina dai gidan gidan ubanane dole ko abarni na zauna ciki.
Nan tafara rafa hannayen ta cikin mamaki da lalami tana fadin eh lalai zaman bariki ya nuna kan shi yau kan.
Baba yana dawowa tafara fada mashi bata kai karshen zance ba yakwala min kira nazo, nace gani ba.
Yace Fatima yanzu na dawo gida maman ku ta tare da,zancen da ban san halinki bane.
Nan na koro mai duk kan maganan har karshen yadda mukayi da ita,da,safe.
Ya juya gurinta yana cewa Tabawa kiji tsoron haduwar ki da Allah horo da,yunwa ko dabba,ba,ai ma,shi balle mutum dan adam mai tunane.
Yanzu ba gashi a,sana din ta alheri yana sauka muna duk karshen wata sai yaron ga dan gidan hakkimi ya kawo muna abinci ba.
Nan dai har sun hau da Baba ko may ta gani sai gata ta sauko don kanta ta, dawo tana cewa haba Bintu ke diya tace kada ki yarda mutane su zuga ki ki min rashin mutunci suyi dariya.
Nace komai ya,wuce amma da safe indan Baba ya fita sai ta turo yaran ta da,kwano wai na yan mata kayan shayi ta dan kada.
Da,nafita iyawa sai na,zuba mata dan kadan a cikin roban nace akai mata hakana,baida yawa.
Shine samun saukina a gidan mahaifina da mama tabawa yanzu kadaran kadaham muke da ita.

****** ********* ******
Shine yau da Kabir yazo ya,tafi da,wuri ashe tare da,matan shi yazo sun zo yin bukin wata diyar yayan shi ne a,Rabah.
Shine yazo da iyalin shi gaba daya amaryan shi bata zama a,kauyen sai dai tazo ta,wuni takoma gidan su.
A nan aka,samu wata,tsegumama ta tsegunta mata zancen neman auren da kabir keyi yanzu.
Nan ta,tayar da,hankalinta sosai har ta tambaya,akai mata,kwatancen gidan mu sai gata,ita,da,kannen zawarori biyu.
Ni dau ina daki kwance ina kallo a,wayana,da,aka,karbo min caji sai ji murya mukayi ana,cewa,da karfi sallamu Alaikum ko nan ne Kabir Rabah ke neman aure a fitsarance suka shigo muna gidan.
Eh nan ne inji Farida da,bata san da may suka shigo muna ba,
Eh lalai ashe dole a haukace a so mai mata,biyu an matsu a,tashi gidan haki akoma alminium zalla.
A,a sannun ku da,zuwa sai wani kallon banza suke watsawa,mutane su ga yan birni a dole.
Ina, ita gajar da kabir din ya,wullakanta kanshi yazo har nan gidan wai neman aure.
Saye nake da,wani dogon riga baki cikin wanda yaya,sadauki ya,sayo muna,ghana, a jikina don dashi naiwa Kabir kwalliya da,yazo don haka ban cire ba yana a jikina.
Nai rolling din kaina,da dan kwalin kayan tsaye nayi harde da,hannuwa,daga kofan dakin mu ina kare masu kallo irin wanda,suke ma gidan mu da yan uwana .
Sai da suka juyu ne mukai arba dasu, gaba dayan su ido suka tsura min,
A cikin min kallon kurrullah tun daga kafana gar zuwa kaina o lalai kice min farar fata yabiyo mana kin sanshi maye farar mace ce ko manyace.
Nace ballw ba,farin ya,jawo shi ba,nan sai hali, don may yuyuwa yaga abinda ya,rasa,a,gida ne yazo nan.
Ke kama kanki don ko ba,a,fada,ba,nasan kece yake nema don kece ki kadan yi kama,da zubin yan birni kadan.
Ba shirmay ya,kawo mu ba ni matar Kabir ce ta biyu na,zo ne nai maki kashedi akan mijina,wallahi,
Don ko ita bakauyar dake gida, ban dauke ta wata tsiya ba balle ke dake shirin kawo kanki.
Nace hmmm mijin ki ko mijin mu yar uwa, ba,a kara aure aka,auro ki ke naga dani dake din duk ba,matan gado bane,
Balle ki manta ki kirashi da su nan wai mijin ki aikin makara da,baki tsaya kin auri wanan mai matan ba da,sai ki tsaya,ki auri wanda baida mata,a kiraki matar mai shi.
Yanzu ko tunda mijin wata zamu aura da ni dake kinga kalman mijin mu ya,shigo ke nan.
Ke wallahi, kama kanki dama ku yaran kauye haka kuke da iya magana tankar tsofafin mata.
Nace mazan mu da matan mu kuwa din shi kika gani ga bakauyen mijin ki har ya,rude ki kika,aure shi.
Sosai mukai musayan harshe da su su fadi in fadi wai tana min kashe di na rabu mata da mijin ta,inva haka ba zaki shigo ki samu balai a gidan shi.
Nace kai dama baki zo ba da,ban san balai ke gidan Kabir ba
Don da ma kabir bai a,raina saboda bai min ba amma yanzu zuwan ki sai naji ina,matukar sha,awan auren shi na zama koda ta hudu ne.
Gaskiya,zuwan ki yai min rana sosai din haka kikoma,ki fara shiri nima zan shigo da shirina sai na zo.
Ina fadin haka na juya zuwa cikin daki dama gidan ya fara cika da,mutane don jin hayaniyar da akeyi yayi yawa.
Mata ko suka,saka,su gaba da ihu da,tur da,Allah waddai da halinsu kishi wai hauka,ne da zaku zo gari wa gari ku na kishin hauka wa mutane.
Sai bayan naji tayar da motan su na sauke ajiyan zuciya saboda karfin halin da nayi don duk a,tsorace nake, kada suyi min dan banzan dukan tsiya tunda nice banda gaskiya, nike bi masu mijin su.

Lokacin da,labarin cin mutuncin da matar shi tazo har gida tai min hankalin Kabir yai matukar tashi sosai tunda safe sai gashi kofan gidan mu.
Da Baba na yafara ganawa, kafin daga baya asa a kira ni nafito ina daure da fuskana tamau,
Tun fitowa na,Kabir ya kura,min ido yana kallon yanayin da,na,fito dashi don yana son fahinta da sauki ko akwai magana.
A mutunce na durkusa na gaishe su sannan na koma gefe nace Baba gani,
Mutanen da Kabir yazo dasu suna zaune saman tabarman da aka,shimfida masu idanuwan su a,kaina karrr,
Baba yace Bintu Kabir ne ya samu labarin abinda matar shi tazo hannan gida tai maki shine yazo ya,bada hakkuri akan sabanin da aka samu da ita.
Kaina na sadda kasa nace cikin yar murya Baba gaskiya ayi hakkuri da wanan zancen don tun ba,a shiga ba an fara irin hakan
Ina ga in an shiga gidan baki daya sai ai marus ke nan lokaci daya sukace ,a,a wanan ma,ai baiyuyuwa sam.
Duk da sun fahinci kan zance na ina nufin nafasa ke nan sai suka shiga ba da baki da gyaran zance .
Shiko kabir yana zaune yai shiru kawai abin duniya ya,kai mai ko ina abinda matar shi tazo tayi ta bashi kunya.
Baba dai da yaji irin yadda suke bada hakkuri ni kuma na kafe akan sai dai a,rabu.
Sai baba yace Bintu tashi jeki ciki kawai ma,karasa,maganan dasu.
Namike nashige ina jin yadda Kabir yake sauke ajiyan zuciya daga inda nazo wucewa ta gaban shi.
Ban kara jin zancen ya tashi ba sai bayan kwana hudu sai gashi yazo har lokacin bai sake jikin shi ba dani.
Na fito saye da zani da rigar atamfa mai ruwan jan kalla, dinkin shi yai matukar karban jikina da kyau.
Son in mashi kwalelenka, ranan gyale na yafa ajikina sabanin hijjab din da ko yaushe nake rufe jikina dashi.
Na durkusa na gaida shi a cikin ladabi da biyayya tare da,tambayan shi gajiyan buki.
A,sanyayw yace Fatima kinga yadda kika,wahal dani da,kalman ki dakike fadin wai kin fasa aurena.
Don Allah Fatima koda nine nai, maki laifi, kada kice kin fasa aurena, don baki san irin wahalar da na,sha ba na ganin za,a raba ni da wanan kyakyawan halittan mai suran larabawa a hannu na.
Don Allah Fatima koma may ye kada ki kara cewa zaki rabu dani akan wata, wacce dama ita bukatan ta ke nan nayin haka.
Wallahi ranan da,muka,bar nan nayi tunane dubu a raina don sai na kasa banbance so na yasa kika ce hakan ko kina.
Nan yadan zubo min ido yanaxmai kare min kallon kurullah , akunyace na dan rufe fuskana da hannayena .
Yai ajiyan zuciya yace nagode Fatima don ko hakan ma,sheda ce ta kin sauko zaki yarda dani.
Mun jima muna hira dashi yana bani labarin irin fitin matar tashi saratu yadda sukw kwasan masifa da uwargidan shi a kan lalai ita ala,dole abar mata miji ita kadai
ko da ya zo tafiya sai yace kin hana ni shakat wallahi Fatima gashi haka nazo ban riko maki komai ba.
A hankali nace mai babu,komai, ko haka,na gode ai,
Ya ce sure ?
Nace, mashi insha Allahu.
Haka yatafi ba don ya,so ba yana ta,faman bani hakkuri ya,wuce abinshi.
Anyi wanqn rikicin da Sati biyu ina gidan mu gaban iyayyena hankali a kwance abina na fitar da komai a raina,
Ina zaune ina gyaran ganyen da mama,tabawa tasayo lanbu zamuyi miyan dare dashi.
Ina cikin gyaran ganyen ne sai naji karan diran mota ta tsaya a kofan gidan mu.
Dan dakatawa nayi da aikin nawa ina sauraren ko anyi bakine gidan daga bisani dai naci gaba da aiki na.
Gwago na ce ta shigo gidan da sallaman ta saura kiris na zubar da ganyen da nake gyarawa don murnan ganin ta danayi.
Fuskanta dauke da yalwatacen fara,a take ce min dana karaso gurin ta cikin daukin ganin ta.
Bintu baki da kirki banzaci zaki zo ki share ki zaman ki haka a kauye kin bar uwar dakin ki sai damuna take tunda na koma.
Ledan dake hannun ta na karba daidai lokacin da mama tabawa takw dawowa da makwabtan su.
Mama tabawa tace a,a yau gwagon yara ce a garin kwana biyu kin shige birni abinki.
Nan dai suka dan taba wasa tsakanin su sai kuma gwago take tambaya yayanta yana gona ke nan ko bai dawo ba har yanzu kuma tana son ganin shi.
Ba ,a jima,ba Baba na ya dawo daga daji, sun jima suna hira da babana wanda akasarin hiran akan yar uwar suce da gwago tai jinya takare.
Can tun ina jin hiran su sai na bar jin tashin muryan su, ma,ana dai za ai magana ta,siri a tsakanin su ke nan.
Zuwa can Baba na ya daga murya ya kira ni nazo, na,samu guri dan nesa dasu kadan na,tsugun na.
Baba na yace Bintu gwagon ki tazo tafiya dake ne akan umurnin mijin uwar dakin ki, na can.
Don haka,sai ki harama ki shirya ku kama hanya don kinga mota,sukutun ya bayar azo a tafi dake don ba,ayi zaki zo ki zauna haka,ba harki dade.
A take na bata rai na,tare da,dukar da kaina a kasa, baba na yace ko baki ji may nace bane Bintu.
Cikin yar karamar murya nace naji Baba yace tau yau din nan ki hada kayan ki ku tafi tunda sunyi mutunci haka nima idan na samu lokaci wuri yasha iska zan shigo naga inda kuke.
Na dago kai din nai magana gwago ta watsa min harara dole na noke kai bance uffan ba.
Namike jiki ba karfi idanuwa na,sun ciko da,hawaye amma,ba,wanda ya kula da damuwa na nafara ashirya kayana.
Kafin sallah magariba haka gwago tace sai muyi hara man tafiya kada muyi dare sosai a hanya.
Nan na,dauko yan abubuwa nabawa Farida yarinyar da zantafi na bari cikin uku ban mama tabawa,
Komai da muke boyewa,nabar mata,ban dauka,ba, sai kudin dana,bata ta boye ta tafi garin su dashi idan taga wuya,zai kashe ta a gidan.
A sanyaye na gama hada kayana raina a bace don kwata kwata ban son komawa gidan su maji don bani bukatan zama cikin wanan babban gida mai cike da tarin rikici a cikin shi.
Saboda wancan karon ma banji dadi ba don a tauye nake cikin su sai dai na kulla a raina wanan karon kan zasuga canji sosai a gare ni don su barni na,dawo kauyen mu.
Munyi sallama da kowa mun kama hanya sai dai kallo daya ya ishi mutun sanya alaman tambaya a kaina din yadda nai kicin kicin da raina.
Sai ranan naga mama tabawa ta,tausaya,mun tana fadin haba baban binta in bata son zuwa abarta mana.
Daga Baba har gwago na ba wanda yabita kanta sai kyaleta sukayi kawai.
Mun hau titi da kyau mun saki hanyar dajin mu gwago ta kalle tana cewa Bintu kin bani mamaki sai kace wace za,a kai mugun guri.
Acikin wata raunaniyar murya da take gap da,narushe da kuka nace gwago bawai mugun wuri bane.
Amma zama gidan da,baka,da,alaka da kowa,sai zaman girma,da,arziki kawai, shine nake jiyewa.
Tace da kika zauna wancan karon anyi wani abin ne sai da na nisa kadan nafara fada,mata,duk yadda aka,kwashe da,bata,garin.
Tace ni na sani ai ba yau ba Hajiya kubura munafukace ta,karshe wallahi ko.
Tsayin lokaci muna,tafiya muna hira har muka fara hango cikin garin sokoto.
Unguwan sama road muka dosa inda muka tsaya a kofan gidan Alhaji habu.
Lokacin dare yayi ko don har anyi sallah isha,i don haka cikin gidan muka shiga kai tsaye.
Na zaci gidan mu zamu shiga amma,sai naga sabanin hakan kawai mun shiga gidan masu hali.
A dan tafiyan da,nayi na,samu canji na sauyin launin gidan sosai an canza abubuwa da dama a gidan.
A kofan da aka,sake wanda ban zaci na,maji bane muka tsaya tana sallama daga kofan shiga.
Muryan maryam ce naji tana a,a mai masa,oyoyo harkin dawo ashe?
Sai tafara leken bayan gwago tagani ko ita kadaice tazohangini tayi ina,saye da lace din da Kabir ya dinka min da matan shi cotton lace ne mai laushi sosai da duwatsu caaa a jikin shi.
A razane tace maji yau kan ga yarki ta dawo gare ki gwago ta cika alkawari kowa ya huta dada.
Da sauri ta karaso gareni ta rugumay ni cikin jin dadin ganina a lokacin.
Jin

Please Login or Register in order to submit comment