Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kusan hakane dai don wai ashe sun bukace shi da yatafi ya buga masu ball a kasar ghana.
Amma sai yace wai gida an hana,shi zuwa shine nace ni dai ban sa zancen ba amma kila ita uwar shi ta san da zancen?
Eh na sani tabashi amsa amma kuma na fada mai hakan baiyoyuwa.
Kada ma ya kara min zancen shine yake ta faman fushi a kwanaki ai har yaje yai wanan aika aikan.
Kai amma hajiya maijidda baki kyauta ba gaskiya.
Ai wanan abin alfahari ga kowan mu nan ace an samu haziki daga gidan mu .
Amma may yasa ni ba a shawarce ni ba kika yanke hukunci ke kadai, maji tace Alhaji naga baka ra,ayin wanan kwallon da yakeyi ne.
Sannan kuma yana nan ma a,tare da mu yaya aka kare ballw yatafi wata uwar duniya can, inda babu mai kwaba mashi.
Haba kwabo fa daga Allah yake mu itakarmu dashi addua ne a duk inda yake, amma ai wanan wani babban abin alfaharine idan Allah yasa mashi hannu inji hajiya kubura.
Nikan gaskiya sai naga kamar hakan zai kara jefashi cikin mugun halin da yasa kan shi a cikine.
Alhaji yace yanzun dai idan ya shigo kafin na fita kice ina magana dashi don inji yaya zancen yake ne.
Majibata,dade da barin gurin maigidan na suba sai ga sadauki ya,shigo don yau sammako zaiyi ya fita saboda yana process kan fita service din shi.
Bayan sun gaisa ne maji take cewa yaya akayi Alhaji yasan zancen zuwa kwallon da kai min bayan na fada maka cewa ban ra,ayin hakan tun farko.
Cikin muryan ahi ta,rowa yace wallahi Maji ban sani ba don bamuyi maganan da kowa ba a gidan nan.
Ta ka godewa Allah da uwarka hajiya kubura don naga ta dauki abin haikan ita akan dole sai anbarka.
Na ko san tunda tai magana Alhaji yarda zaiyi ba fashi amma ya,dai ce idan ka,shigo kasamay shi yana nemanka wai.
Baba ke nema na maji tace eh ba,wanj abu bane wai yana,son jin kan maganan daga bakin ka ne.
Sadauki bai tsaya ba ya mike don zuwa kiran mahaifin shi da yake mashi,
Yana kaiwa kofa yaji muryan bakuwar yarinyar nan cikjn yar siririyar murya tana fadin Allah yasa baba ya,yarda yatafi wallahi.
Juyowa yayi ya maka mata harara yafice daga dakin yarinya karama,sai bakin iyayi ina,ruwan ta dani ne
Yarinyar nan bata,san halina,ba,sai watarana na gwada mata,zata gane kuren ta gidan nan.
Yafita yana magana,shi kadai a ran shi yana fita hajiya kubura tana kulle kofan part din ta zata fita ya ke cew mummy ina kwana.
A,a sanda sadauki sabda gagare ashe ana ganinka ni yaushe ma rabo dana saka a idona ne wai.
Yai yar murmushin shi yace ban zama,sosai ne yanzu shi yasa ba,a gani na,
Tace tau akula dai don Allah a daina rashin ji kaji Umar Allah ya tsare muna ku Allah kuma yai maka,albarka.
Yace amin yabarta taba,ci gaba da,rufe kofan dakin ta shi dai matar batai mashi komai ba amma kuma ya kasa sakin jiki da ita,
Dan dama,ma,yau har ya tsaya sundan yi dogon magana dashi ko shi don irin halarcin da ta nuna mashi ne ranan yasa yadan sake mata yau.
Da Umma ya hadu tafito tana sauri don ta makara kauce mata yai nufin yi don kada,su hade amma sai cewa tayi wallahi haukan yaro yakawo gareni da,uwar yaro zanyi a gidan nan.
Bai ko gaisheta ba ya,wuce abinshi gurin mahaifin nasu don amsa kiran da yake mashi.
Ya samu yana gap da fita ya,shigo falon da,sallaman shi suka gaisa yake cewa hauwa ta fada maka ke nan ina neman ka ko.
Don nasan inbashiba bazaka zo mu gaisaba ai anya Umar kana kyautawa kanka kuwa?
Baba kayi hskkuri lokacin da nake fitowa sai na samu kafita ko kuma lokacin da zan fita baka fito ba tukun.
Ba sanan ba idan maka gyara don kanka, yaya zancen dana ji na batun fita kwallon ku yake ne?
Don ban son abinda zai je ya kara saka sha shan ci kuma a bayan idon mu, anan ma muna nan kafara haka inaga babu kowan mu.
Baba insha Allahu ba,zanyi wani abinda zai bata maku rai ba ko martaban gidan mu,
Hmm daga baya ke nan amma sadauki yaushe kuma,ai kayi waka an amsa maka ko.
Don tunda harka bari kishiyoyin uwarka suka fahinci halin da kake ciki ai abu ya baci ko saidai Allah ya kyauta kawai.
Nan dai sadauki cikin dukar da kai yai ma mahaifin shi bayanin komai yadda abinyake ya kuma fahince shi.
Ga mamaki shi sai yaji Uban na cewa Allah yasa haka yafi zama maka alheri gare ka da ma muma iyayyenka.
Ya amsa a sanyaye da Amin baba insha,Allahu alheri ne ma hakan da yardan Allah.
Kadaikula don Allah ka kula,da rayuwan ka don mu shine adduan mu a gareka ko yaushe Allah yasa ayi a cikin sa,a Allah ya tsare ya kare.
Yakara amsawa da fadi a sanyaye cikin farin ciki da jin dadi nagode baba yace tare da mikewa yabar dakin cikin farin ciki.
Ya shiga dakin mahaifiyar shi da murna yana fada mata duk yadda sukayi da uban nashi.
Yace maji don Allah ke ma ki samin albarka don in baki yarda ba gaskiya babu inda zan tafi ni kan.
Sadauki Allah yai maka,albarka Allah yasa a,tafi a sa,a adawo lafiya cikin nasara.
Har kasa ya kai yana fadin Maji nagode nagode maku dake da baba nagode ma Allah baiko tsaya cin abinci ba yafita daga dakin zuwa club din su ya,sheda masu yardan mahaifan shi akan tafiyan shi.
Maji tabi bayan shi cikin tausaya mashi irin na da da mahaifi, tasan kwanaki akan bakin cikin rashin yardan su yasa shi zuwa ya sha manyan kwayoyi yazo masu gid a buge

Yau tasan cewa duk abinda yaro ke ra,ayin yi indai babu illa acikin sa tauka kyale shi yayi sai dai kai naka kabishi da,adduan da fatan alheri shine mafita.
Amma idan ka hana sai suga ba,a kaunar su bari kawsi su sha abin kawar da hankalin su ko zasu samu relief akan maganan.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,


Baby yaya zamuyi ne ina son ki rakani zuwa lagos don ina da seminar da zamuyi a can, kuma dake nakeson zuwa.
Shiru Raiha tayi tana nazarin zancen shi a cikin ran ta don tasa abu mai wahala ya dauko mata.
Yaya zatayi da uyayyen ta a gida may zata fada masu ina zata ce masu zata tafi.
Muryan shi ne ya katse mata tunanen ta yana cewa naji kin yi shiru mana ko baki san rakani ne wai?
Hmm ba,wai hakana bane kasan in da hali koma ina ne zan iya raka ka amma ban san yaya zanyi da iyayyena ba may zance a gida.
Haba baby sai kace wata local can dan karya kawai zaki shirya masu mana kice zaki gurin wani dan uwan ki koda kauye ne kinga indan munje mun dawo sai na kai ki garin ko kwana daya kiyi sai ki dawo ko?
Nan ma,Raiha shiru tayi tana tunanen akan zancen shi don tasan abune mai wuya abarta zuwa wani guri ita kadai.
Gashi kuma tana son bin shi sosai a ranta don batajin yanzu zata iya rabuwa dashi ko na dan lokaci kadan ne.
Sai cewa tayi zan yi shawara don nasan abinda zan yi akan tafiyan.
Huci yayi don jin dadin yasamu yadda yake so daga gurin ta nan ya shiga yi mata abinda yasan tafi bukata daga gare shi har suka kai ga,watsewar su a hotel din da ya kaita.
Da zasu rabu ne yake jadfa mata cewa next week ne fa sunday tafiyan su kuma da jirgi zasuyi tafiyan, don haka yana son yasan idan zata tafi ya sai tickets din su shida ita.
Ba matsala tabashi amsa zansan yadda zanyi mu tafi din tare insha Allahu.
Wani shu,umin murmushi ya,sauke tare da,shafan dogon fuskan shi ya na cewa dat is my baby shiyasa nake kara,son ki.
Tun dawowan ta gida take ta faman sake sake a ranta sai kullawa take tana warwarewa ita kadai a ranta.
Can wani dabara ya fado mata a rai tai wani murmushi daidai uwarta ta zo shigewa take cewa, mama ina fa son zuwa kamba gurin su kaka na dubo su.
Kamba Raiha kedawa zaki tafi har kamba ? Raiha tace haba mama sai kace wata karamar yarinya ni ko makka ai ina iya zuwa ni kadai yanzu.
Kai Raiha wai may kike daukan kanki ne yanzu har nawa kike da zakice zaki iya kai kanki makka.
Yanzu dai mama da na shiga mota daga nan sokoto ba sai jega ba daga jega ga motocin zuwa garin kamba nan sai na,shiga kawai.
Eh lalai ashe ko zaki iya aiko kin kyauta bari malam ya dawo na fada mai Allah yasa ya barki dai ki tafi din .
Raiha cikin marairai cewa take cewa don Allah mama ki tayani rokon shi ya barni ba dadewa zanyi ba sati daya zanyi nadawo kawai.
To shike nan bari yadawo din muji yadda za,ayi idan zai yarda sai ki shirya ki tafi aini wallahi kin kyauta min nasha kulla tafiya na dubo su amma sai abin bai yuyuwa.
Yanzu kinga ai inkije sai ki taimaka min nasan halin da,suke ciki a can din.
Sai da,dare bayan mahaifinta ya dawo ne take sheda mashi bukatar yarsu na,son zuwan ta kauyen zu garin kamba wanda ko anje kambadi sai an shiga mota ko mashin zuwa can.
Haba nana yanzu kamar Raiha ne zamu saka a mota daga nan har kamba ita kadai a,wanan zamanin da muke ciki.
Malam insha Allahu zata iya ai yanzu tasan hanya zata iya kai kanta ita kadai bada wani ba.
Nan dai suka kama inyafito nan tafito mai nan abin mata da miji har ya yarda da zasu tafi ya bata kudi tayi sayayya da kudin mota wanda zai kaita.
Sosai Raiha taji dadi a ranta nan take ta kira Nasir take sheda mashi halin da take ciki.
Yai murna yaji dadin samun nasaran da sukayi don haka washe gari yaje yai saya masu ticket din tafiyan su.
Bayan kwana biyu suka shirya sai air port inda suka tashi zuwa garin lagos ita da shi.
A wani katafaren hotel ya sauke su ita dashi inda tun ranan ya fara nuna mata wane shi, don dama can ashe a sannu yake binta.
Bata da hutu a gurin Nasir don kusan a kanta yake kwana har gari ya,waye.
Tun tana iya jurewa halin Nasir har Raiha tafara raina kan ta da kanta don yanzu yakai bar ta baya yake ne manta.
Da farko takiya amma da tasha duka a gurin shi dole ta yarde mashi yana yadda yake so da ita.
Idan sun gama kuma ya dauko kayan maye ya dirka mata sai ta futa hankalin ta .
Sati dayan da sukayi Raiha tagan shi kamar shekara daya ne na,wahala da ukubar zugubar namiji a gare ta.
Sam babu tausaya tsakanin ta da nasir ko kadan kamar ba soyayya ce ta hada su ba don yi yake kamar ya samu boya.
Saura kwana uku ta dawo ya shiga da ita gari shida wani abokin shi suka je zaga garin da ita.
Yai mata sayayya sosai na abinda duk tagani tana so a fitan nasu taci kayan ciye ciye masu kyau sosai da tsada.
Bayan sun dawo sai taga wanan dayan abokin nashi baida niyar tafiya kamar yadda tai zaton tafiyan shi.
Ashe bata sani ba aun hada plain a tare shida Nasir zasuyi amfani da ita gashi shi ba ko musulmi bane dan uwan ta.
Nan suka samay ta da ihu da komai suka kwana a kanta suna juyata yadda suke so.
Tai kuka har tagaji tahakkura ta kyale su suka gama don kan su ka barta, abokin nashi yata yaba ma dadin ta har yana rokon Nasir da ya bar mashi ita for ever amma nasir din yaki yarda da hakan.
Yake cewa Michael ai ba,addinin su daya ba don haka ba,zai yarda ya zauna da ita ba.
Bai san bayan sunyi barci Michael ya dauki wayan Raiha ba ya saka layin shi yakira nan ya samu nomban ta.
Sun dawo arewa kwanan su daya a garin sokoto takaita garin kakan nin ta ta kwana washegari ta dawo sokoto ita dashi dake jiran ta a birnin kebbi.
Maman ta taga ta sake maimakon taje kauye tayi baki amma sai wani haske ta dan kara sai dai tayi dan rama amma fa tayi mata kyau a fuska sosai.
Yanzu ke Raiha kada dai kinje kin cinye ma yan tsofi kajin su wanan irin haske da kikayi haka anya kuwa ba barna kikayowa tsofin nan ba.
Raiha kuwa sai rankon barcin wahala takeyi don sai yanzu ta samu hutun wahalan da tasha gurin Nasir a can Iko.
Sai dai shi bai sani ba ta riga da ta yanke a ranta cewa ta gama zama dashi ke nan don yai mata wullakanci a can dama lalaba shi tayi har ta samu su dawo arewa.

****** ********** *****
Ganin yanzun ba wani ciniki take samu ba sosai yasa ta yanke shawaran samun dan almajirin da zai dinga mata talla tana bashi abinci da dan kudin sabulu kamar yadda da yawan almajirai sukeyi yanzu.
Duk almajirin da ya shigo zatai mashi tayin talla amma sai su zille suce malam ya hanasu yin talla ko kuma suce dama shara ne ko wanke wanke zasu yi amma ba talla ba.
Sai wani yaro ne tasamu yace mata zai yi Allah ya taimaketa yaron yana da kan talla sosai don da yafita kamar ya kifar ne zai dawo ya kara wani.
Haka yasa tagane fita da sana,a waje yama fi cikin gida sosai samun ciniki .
Maigidan ta yaga almajirin yai mata magana akan ta dai kula da bashi hakkin shi don kada Allah ya tambaye ta akai.
Amma,saboda dadin baki irin nata bata bari yakai karshen nasihan shi ba ta shiga bakinta akan zancen.
Maigidan dai ido ya,sa mata baice mata komai ba sai cewa yayi bani abinci nashi kada na makara zuwa daukan karatu.
Yana cin abincine yaran shi suka zagaye shi suna fada mashi makarantar su ance a,sai masu shocks da takalma.
Yakai loma,a bakin shi yana cewa aiko sun dauko min aiki yanzu hada kudin safa da takalma ai aiki a cikin wanan daman da ya fara.
Kuyi hakkuri insha Allahu zan sayo maku nan bada jimawa ba da yardan Allah.
Yana gamawa bai tsaya jiran komai ba yafita zuwa gidan babban malamin shi inda yai karatun allon shi.
A nan yake zuwa daukan karatu gurin malamin duk dare idan ya,dawo daga gurin neman kudin shi.
Yana fita ymta jawo bankin kudin ta tafara lissafawa inda taga irin ribar da ta samu gurin tallan almajirin ta.
Tayi murna kwarai don ba karamin cabawa tasamu ba ga wanan tsarin sai fadi take ai wallahi mama ta taimakeni da wanan shawaran nata.
Don gashi kwana kadan na hada,waban uban kudin haka nan ta,ware nata ta cire ma,almajiran ta nashi.
Har yaran sukai barci amma ita hankalin ta yana ga sakan zucin da takeyi itta kadai a lokaci, na ganin ta hada kudi ta sai fili da sunan nata.
Sai karfe goma mijin ta ya dawo gida ya samu yaran saman shimfidan da ya tashi ga sauro na cizon su.
Yacee haba maryama da wannan sauron kikabar yaran nan haka a cikin shi suns cizon su gani ba kudi gareni ba idan maleria ya kama su da,wani zanji.
Sayen abinci ko sayen magani da zuwa asibiti gashi yanzu zazzabi idan ya kama mutum kamar ba zai barka,ba sai ka hada da,asibiti dole ko chemest.
Nan ya shiga kwasan yaran zuwa cikin dakin kwanan su gaba dayan su saida ya kwashe su ya kaisu daga ciki.
Maria na gama abinda take ta nemi guri ta kwanta don dama a ganiye take don tun safe bata huta ba tana gudun tai barci masu sayen ruwa ko wani kayan sanyi su shigo.
A gaakiya ta godew haduwan ta da Muda almajirin ta don yaro ne ma hazaka gashi da amana.
Koda gurin lissafi tai kure zai dawo mata da canjin ta, ya bata abinta, bai sa ta gode mai ba.
Ko da daga gurin talla ya dawo bata barin ya dauki abinci komai yunwar da yake ji.
Sai yai mata shara da wanke wanke, da yan sauran aiyukan gida kafin ta sallamay shi.
Hakan ne ke batawa yaron Muda rai yana yawan yiwa yan uwan shi almajirai korafi sosai.
Wanan shine matsalar da ke damun yaron mai mata talla koda zai makara ga karatun shine sai yai mata aiki bayan kuma akan talla sukai alkawari kawai dashi.
Wata rana yana fita daga tallan ne sai gashi ya dawo jiki na makyarkyata yana jin sanyi ba lafiya.
Maimakon Maria ta ji tausayin yaron sai cewa tayi shine baka sayar ba kadowa min dashi ya tsiyaye ga banza.
Cikin rawan sanyi yaron ke fadin banda lafiya ne maman Abba sanyi nake ji sosai.
A je katafi tunda yau baka son yin tallan ke nan nagani, maman abba in kina da magani don Allah ki bani nasha.
Tace cikin tsawa banda shi kaje gurin malamin ku yabaka shida ya dauko ka mana.
Yai shiru kamar mai nazari can yace don Allah ki taimakeni da koda cikin kudina ne na biya shago nasai magani.
Babu su tafadi a cikin fada da,dan tsawa yaron yafita yana dan makyarkyatan sanyi don fever ya damay shi.
Yana zuwa makaranta ya rabke da ciwo maleria ta kama shi sosai nan malamin su ke tambayan shi ina kudin tallan shi ya bayar a,sayo mai magani yasha.
Da kyat yaron ke iya magana yake cewa na tambayi matar tace wai babu kudin.
Malamin ya hasala yafito yana tambayan wayasan gidan da Madu ke talla ya aike shi.
Suka yaran wasu sukace sun sani nan sukatafi gidan don su karbo kudin shi hannun maria.
Amma sai tace a tafi ita babu kudi a hannun ta sai dai idan ta samu zata aiko mashi dasu.
Almajiran basu fita ba suka tsaya yi mata tsageranci, akan sai ta bayar da, kudin sukai wa malamin su.
Sun dade basu samu ba dole suka bar gida taki bayarwa kuma tabi su da zagi.
Suna fadawa malamin yace kada wanda ya koma gidan subarta da Allah a bar maganan.
Shi yakai yaron asibiti akai treating din shi ya biya kudi har yaron ya samu sauki.
Bayan Muda yaji sauki yaki zuwa gidan ta nan almajirai yan uwan shi kewa makwaciyar ta hiran shi tace akawo shi ta dauke shi aiki.
Ita ta rike yaron zaman amana kamar itace ta haife shi haka yasa Maria jin wani irin kishi kamar zatayi hauka

****** ******** ******
Kamar yadda mai masa taiwa Maji alkawari haka din ne don batai sanyi a,gwiwa ba ta shirya sai wani kauye can gaba da kauyen su gurin wani malami.
Malami irin malamai na kwarai bai damu da wani kudi ba don a kauye yake kuma ita dashi yan uwane ta mahaifiyar su.
Yana ganin ta ya shiga murna da nuna jin dadin ganin ta nan yasa ai mata girki na musan man kamar yadda yan kauye suke yi idan sun ga bakon birni yazo gurin su.
Sai da dare suka samu kebewa dashi da ita suka kara gaisawa sosai, nan take, sheda mashi dalilin zuwan ta gurin shi.
Ya jijiga kan shi yana cewa matsalar ku ke nan yanzu yaran birni don kwanaki akwai wani da yazo tun daga kano har nan gurina akan wanan matsalar.
Amma yanzu ba abinda zamuyi sai dole munyi istihara don naga daga inda matsalar take, don kinga ba dama muzo muna aiki inda muka dosa daban abinda ke damun shi daban.
Don haka ki bari sai zuwa gobe da safe sai nai maki bayani, mai masa tai mashi godiya sosai nan suka dan taba hira na yaushe rabo da junan su.
Washegari tun da,sauran duhu aka kaiwa gwago ruwa masu zafi tai wanka tana fitowa ga koko mai zafi da kosai da masa irin tasu ta kauye da badin shi.
Tace wani abu sai kauye mu a,birni ai yanzune ma,wata mace ke gyara kwanciyar ta.
Sai da ta karya tashiga ko wani lungu na gidan suka gaisa da mutanen gidan sai ta dawo dakin da akai mata masauki .
Ba a jima ba malam ya,shigo gidan ya shigo dakin da mai masa take ciki suka gaisa yai mata ban gajiyan tafiya da bakun ta.
Can yace Asmau nayi duba akan matsalar ku amma gaskiya akwai yar matsala a cikin harkan.
Don shi wannan yaron gaskiya akwai hannu ga harkan shi.
Don tun yana karami aka soke shi don haka su abubuwan bayin kan sa bane.
Yaron nagani yana da taurari masu haske sosai a rayuwan shi don hakane akayi kokari dakushe masa su don kada ya haska.
Anje anyi tambaya a kan shi amfadawa wa masu shi cewa zai zama wani abu ga rayuwan shi shine suka,sa ai mashi wanan aika aikan.
Kuma al,amarin ga yadda nagani ba wai mutum guda bane yai masa haka ,a,a suna da yawa kowa kuma da irin aikin da akai mai.
Ga miyar kifi aka bashi wanan abin shaye shayen yaci shi.
Matane da namiji guda sai dai ba zaso na fada maku su ba don gudun hadin hasu mi.
Yanzun mu matsalar mu shine mu san mafita akan zancen mu san yadda zamu nemo makaru mu kara wanan asirin na jikin shi.
Don muddin yana tare dashi ba,zai taba zama wani abin kwarai ba ga rayuwan shi.
Kin ga yadda nagani matar tana da yara uku a,raye shine dana farko a gurinta.
Su ma sauran diya matan nata biyu wallahi ba,a barsu ba don suma suna da nasu asirin sai dai suyi ta zaman gida ba aure.
Koda ma an dace sunyi auren bazasu zauna ba zasu fito don zasuji auren ba dadi.
Yan da zaai sha rubutu ne kinga sai na rubuta maki wani rubutu ki fara,zuwa masu dashi har uwar tasu tasha.
Kafin kwana biyu nan da sati biyu ki dawo lokacin na,shirya,sauran abinda da zan baku.
Gwago tace zai sha mana malam ai kasan wanan dolene asan yadda za,a bashi yasha.
Yace kin san yanzu yayin izalar nan ta sa matasa basu son shan irin abubuwan nan.
Kuma mutane ne basu gane ba ai shi a addini musulunci da kike

Please Login or Register in order to submit comment