Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Mama don mahaifiyan sadauki zanyi wanan auren don ba zan iya mussa mata fa bukatan taba a gare ni.
Mama ta katse ni tace amma kin bani kunya wallahi yarinyar ga ina iliminki da tarbiyan ki ya shiga da har kike ganin ba zaki iya taimakawa hajiya ba yau.
Tace da kikaga hjy ta zaboki a cikin dubu ta bukaci ki auri dan ta kina zaton don kyau kine ko arzikin ki ko wani abu can.
Tayi hakane don tana hasashe watakila tagare ki zata samu nasaran raba dan ta da waban halaiyar tashi.
Bafa don bata sonki ne tace ki auri dan ta ba suna da kudin da zasu aura mao duk macen da yake so a duniyan nan.
Amma kikaga ta nace akan sai dai ke din take so ki zauna dashi, nasan kuma tai hakane don tana ganin ke ce kila zaki iya kawo karshen wahalan nashi.
Shi fa hanyan sabon Allah shiga rai ke gare shi sosai, daga lokacin da akace wanan abin baida kyau haramun ne, sai kiji zuciyar mutum na tura shi aikata shi a ko wani lokaci.
Shiyasa akace an zagaye wuta da abin sha,awa wanda zuciya ke so, an kuma zagaye aljanna da abubuwan ki wanda zuciya bata so.
Don hakane duk wanda ya kama hanyar aljanna zai ta haduwa da abubuwan da zuciya bata so, haka kuma shi wanda ya kama hanyan wuta zai hadu da abubuwan da zuciya ke so.
Shiyasa akace daga cikin hakkurin da ake son mutum yayi shine harda biyayya ga Allah da manzon sa dama
magabatan mutum da kuma hakkurin gujewa sabon Allah.
Hana zuciya aika ta sabon da ya ginu a kanta farat daya abu ne mai wahala so sai sai mai hakkuri.
Idan kana da hakkuri zaka iya jure jawo hankalin mai yawan sabon Allah sannu a hankali ta yawan nasiha da lurar da mutum illar abinda take aikatawa.
Uwa uba kuma addu,a da nasiha ga mutum har Allah ya bada sa,a ya bari ko ya rage.
Yin fushi da mutum ko kaurace mashi baya hana mutum sabawa Allah sai dai ma ya kara kangarewa kawai.
Amma jan mutum zuwa jikin ka shike sa mutum ya rage watarana har ya tuba ya daina gaba daya.
Don haka ita hajiya taga cewa, kece kadai zaki iya taimaka mata gurin wanan yakin.
Don haka yaki babba a gaban ki yar ba don hajiya ta dora maki nauyi mai girman dauka gare ki.
Fushi zagi gori da kawar da kai ga abinda yake aikatawa yanzu ba naki bane yar baba.
Don haka wani kawar da kan ki gare shi ko ki kyamace shi ba naki bane yanzu.
Don idan kinyi haka tankar kin kara tura shi ga halaiyar da yakeyi ne na kyamata da uwarshi bata son ganin shi a ciki.
Hajiya ta wuce ki watsar mata da bukatan ta gare ki, sai dai ki kara runguma kawai da hannu bibiyu.
Zata ci gaba da magana gwagona ta leko tana cewa fito mana Bintu, dare fa ta soma kin san ba wuta garin.
Haka yasa nai sallama da mahaifiya na tana ta jero min addua irin da yadace duk uwa taiwa yar ta da zata dakin auren ta.

****** ********* ******
Waagegari tun da safe wata mota ta iso da kujeru da rumfuna suka shiga hakawa sai kuma fa mota da abinci ruwan sha na gora da leda sun iso.
Inna ta bawa ranan ta arare ta yafe itace kirjin buki arziki ya sauka mata a gida sai yadda tayi zuwa tara da rabi sai dirin motoci ke tsayawa a kofan dan gidan mu.
Haba take guri ya kaure da yan ma,abba sai kirari sukeyi fa Alhaji wani ga Alhaji wani yazo.
Zuwa can wani mai murya ke sanar da jama,a ta lasifikan shi Allah yayi lokaci yayi yau an daura auren Umar faruq da Fatima Bintu akan sadaki naira dubu hamsin.
Sai wata matar babana ta rangada wani irin guda tana fadin yau Fatima Binta kin gwada muna kin haihu a zariyan Ibrahim da maimunatu don kin jawo muna arzikin da bamu taba sanin akwaishi na garin nan.
Allah yasawa auren ku albarka yakawo muna zuri,a dayyaba masu albarka arayuwa.
Bayan dan lokaci muka ji mata na fadin ance ku gyara ga angonne nan zasu shigo gaida ku cikin gida.
Ina can boye kuryan dakin Inna tabawa naji matan tsakar gida na fadi wanan na tsakiyan dogon ai shine angon lalai Bintu kan kin yi sa,an miji wallahi da ganin shi ba karamin mutum bane.
A raina nace baku san komai ku kumbu a rufe ganin kyaun dan maciji kuke mashi haka dahi nanan cikin shi.
Ba wani bata lokaci matan da aka zo dasu suka fara cewa wai a fito da kaya zamu tafi take na saka wani sabon kuka mai tsuma zuciya.
Bashar ne ya dauko ni a motar shi sai kaunan mahaifiyata wata malaman arabiya ce ita sai gwagona dana zo birni a wurin ta, kawa yena su biyu haka muka shigo mota daya dasu.
Tun da muka fara hanya ina a dunkule sai kuka nake rusawa a hankali gwagona tana min fada wai zan jawa kaina ciwon kai a banza kamar wace za aika gidan mugun abu.
A raina nace kyace haka mana tunda kin ja min mugun rayuwa a sanadinki duk na fada cikin wanan rayuwan haka ai.
Bashar yace gwago kyale Fatima tai kuka yau don zata fada sabon rayuwa kuka ta zama dole gare ta.
Magana ce yai mata a cikin magana wanda duk cikin motan nasan sai ita kadai ce zata fahinci hakan kawai.
Gida ya cika yacika ya batse kamar may yan uwa da abokan arziki nisa da kusa birni da kauyen an hadu.
Muna na isa aka fara futowa zuwa taron mu yan uwan mama da yan uwan mahaifin su yan uwan umma da mama nasu suma ya ishe su ranan.
Ga Nafisa tayi halinta suyi party tayi tatil haka tashigo gida tana ta watsewan ta gidan Amarya yaya Ahmad kuma suma suyi nasu bushewan sai tir da Allah waddai akeyi masu ta ko ina.
Part din maji ne ba wani abin asha da akaji don bukin yaran ta neat akeyin shi cikin mutunci da sanin ya kamata.
Ina rike da hannun kaunan mahaufiyata da yan uwan ubana don atare muka iso da sauran yan kawo ni daga garin mu,
Wanan kauna mamana ta dan duko tace saka kafan ki na dama ki ja basmalah kafa ashirin da daya tare da karanta, (fihizuma, wa huwa ala kulli shai in kadirr,,,, kafa ukku)
Nan mukaja muka tsaya kaman muna wani abu na karanta tace kin gama nace eh tace ubangiji Allah yasa ki shiga da kafar dama Fatima.
Mama tana jin mun shigo ta taso da kanta tazo ta tare mu ta rungumoni jikin ta tana maraba da diyata sannun ku da zuwa.
Dakin mu na shige da kawaye na na samu su maryam dakin ya cika da kawaywn ta.
Suna ganina ta saka ihu tare da shekowa ta tareni da murnan ta nan muka zube na hira ni dai ban da kuzarin bata amsa sosai a lokacin.
Zan iya cewa ni dai tunda aka fara shagalin bukin mu ban saka Amirah a idona ba har naje na dawo din ban gan ta ba ga gida ya cika ya make da mutane.
Nace niko banga Anty Amirah ba fa tace wa tana can gidan yayan mu da wasu baki ma, ana dai ince maki tana gidan ki can ta tare yau tun safe suke can da kawayen ta wai suna wa bakin shi abinci.
Kin san ita yar ba ruwan mu ne daga cikin mu adole a bayan yaya take bata san zatai kunya ba idan yaya ya shiga hannun wanan matashiyar matar tashi da nake gani.
Nace kai anty zaki fara ko tace wallahi Bintu bakiga yadda kika koma ba yau gaba daya kamar wata yar kasan etopia can.
Kin san sune yakar kyayo acikin jin sin na yan adam.
Karfe daya da rabi a kaje daurin auren yaya Ahmad wai na yaya Imirana tun bakawai na safe aka daura don su haka akeyi gidan matar shi.
Biyu da rabi aka daura auren su Anty maryam da Anty Nasmatu diyar mama, ita ba ruwan ta da sha,anin kowa a gidan mu irin masu akidar ra,ayin rikau ne ita.
Muna nan akace wai za,ai dinner da karfe bakwai zuwa takwas na dare.
Haka yasa ana idar da sallah magariba mummy tace kowan mu ta fito dama muna cikin shiri tun yamma kowa ta kimtsa tafiya gidan ta.
Nice farkon kaiwa don tare aka fita dani da maryam anty Nasmatu yan uwan uwar ta suka kaita ita ma.
Jin an dakatar da mota yadan sani bude fuskana kadan gidan da nagani sai da gabana ya fadi don zakace ba cikin garin sokoto kake ba a gidan.
Hankalina yai balain tashi ina yaya ya samu kudin da yai wanan gida haka ba dai a ball kawai.
Ina jin Inna tabawa na fadin dankari ba fashi wanan gidan haka shine dai gidan Bintu ko kuwa?
Ina makalle ga hannun kaunan mamana wacce dama ina ganin don haka yasa tazo daga bangaren mamana.
Tace idan zaki saka kafan ki akasa ki karanto fatiha kafa uku, ko wani da bissimillah.
Sai ki karanta Basmalah irin na dazun kafa ashirin da daya ki karanta falaki da nas ki hada da ikilas uku uku Allah ya sawa aure albarka ya kare muna ke daga duk wani abin ki na cikin aure.
Ina idarwa ta kama hannu na tare da rada min ki dinga karanta Hasbunallahu wani imal wakeel har mu shiga ba adadi.
Muna tafe masu guda sunayi masu suraitai nayi niko ina saman bakina har abinda batace ba idan yazo min janakeyi na neman tsarin daki.
Nan aka shiga bin gidan da kallo mun samu yan uwan mama acan sune suka tari amarya.
Muna nan dai akace afito akai maryam nata gidan ba nisa sosai don unguwa daya muke.
Wata kawar anty Amira mai makeup ce tashigo dakin bayan an watse tace amarya nazo nai maki makeup na fita dinner ne.
A hankali na kware rufin da ke kaina sai naga tare da su Amira suke da kawayen ta naji mai makeup din tana fadin masha Allahu friend wanan ce kike kira da yar kauye haba waban aiko a fashion sai haka mana.
May kuma ake bukata ga mace ga kyau ga wayewa duk a gurin nan tsoki tayi tafita daga dakin tace ma sauran su fita su bar mu.
Ta busu tarufo dakin tace na taso na saka kayan da suka shigo dashi a jikina kallin kayan nayi da mamaki nace wanan kayan zan saka tace eh shine angi ya sayo na dinner.
Ba yadda na iya dole na saka kayan hakana a jikina ba don naso ba sai da zan saka nagane akwai wani daga ciki mai tare jikin mutum.
Tana min kwalliya tana min gulma wai may yasa Amira take ta faman kusheni ne haka ita bata taba zatin haka zata ganni ba.
Don Allah kada na damu da duk abinda Amira da yan uwan ta zasuyi min hassadane kawai take gani yana damun Amira.
Nace haba anty kin taba ganin mutum yai hassada da dan uwan shi nima fa kaunan tane halinta dai ne baku sani ba amma haka take ita.
Tana min magan ganu akan rayuaan mazan yanzu abinda zakayi wanda zaka kama miji da sauri a hannun ka ni dai umhumm kawai nake ce mata har muka gama komai da ita.
Ba matar ba ni kaina nasan na hadu haduwar da ban taba sani ina da shi ba irin haka sai yau.
Sai tara da rabi akazo daukan mu zuwa gurin dinner wata irin haddan motace aka bude min baya in shiga.
Duhu bai bari mutim ya gane ko mai a ciki sai da na shiga na zauna a zatona zamu je daukan shi inda yake ne .
Sai da mota ta fara tafiya a hankali naji an matse min hannuna dana dauka kujeran motan ce na dafa.
A hankali ya kare tankware hannun nawa yace welcome to ukuba house baby Fatima.
Wani irin faduwan gaba naji amma na dake yakara cewa da fatan dai kin shirya danmaran taron abinda kika fada a shekaran jiya ko?
Nace shirye nake tsab da su don nasan cikin shi na shigo dama yace good baby good.
Haske fitilon da ya haska gurin zakace rana ne a lokacin motoci kanan duk motan dake garin aka kwaso ranan.
Zaka ji kida na tashi daga duk inda kake a farfajiyan gurin da kewayen shi.
Sai dan wani lokaci wasu mace da namiji suka zo inda muke dafa baya na gane summaiyace kawata da mukaje kauye da ita sai wani da ban sani ba namiji.
Sadauki yadan rankafo daidai kunne na yana fadin idan kika bani kunya da halinku na kauyawa wallahi nima sai na disga ki a taron nan kinji na fada maki.
Tare muka jera dasu zuwa wani dan karamin kofa shiga wani guri a hole din sai ganin maryam da Bashar din ta nayi.
Mune a gaba shiga hole din suna bayan mu naji bashar na fadin Ubangiji Allah ya sakawa maji da gidan aljanna da wanan hadin da tayi haka.
Muna shiga saida gabana ya fadi don irin taron da na gani a gurin mutane sai kace ana wani taron addinine.
Nace hasbunallahu wani, imal wakeel a hankali.
Wani haske da kamshi da wasu abubuwa ake watso muna take guri ya dauki ihu up U F kayi daidai wallahi.
Sai wani dan washe baki yake kamar da gaske yana so mun zauna aka fara event yadda akeyi a ko wani buki na dinner.
Gurin yanka cake a tare mu duka hudu muka mike ko wani ango yana rike da hannun amaryan shi,
Sai dai ni nawa angon rikon keta yai min don yatsuna duk sunyi ja saboda matsa da yayi masu na kyata.
Shine ya fara yankawa yabani ba dan guntsura kadan aka hau tafe sai ni kuma na yanko kato na kai mai a bakin shi mugun sai ya hada da hannuna ya tauna sai da nai kara aka saka ihu.
An fitar da mu wai muyi rawa ni dai ina tsaye shine dai ya dan taka kadan sai lokacin nasan wai yan kwallon su na kasa sunzo taya shi murnan aure ashe.
Nan suka zagaye mu suka fara ruwan dollars akan mu suna fada mashi wai yaya akayi ya iya zaben mata haka gani kuma very young dani.
Duk wanda yazo zai mashi farin ciki akan ya iya zaben mace komai nashi a sa,a yake shi.
Sai sha biyu da rabi nace nifa barci nake ji gaskiya zan je na kwanta ga photo da muka sha har nagaji ranan.
Hakan yace wa Bashar akai mu gida naji bashar na fafin kaifa yace yaya zan tafi nabar abokaina ka kuma san ina da bakuwa sai na lalabata fa yace kadaiji tsoron Allah wallahi.
In banji tsoron Allah ba bashat tsoron ka zanji kafasan yanzu wallahi surukin ka nake ka tuna.
Bashar yace nima ai surukin ka ne tunda kaunata kake aure kaga munyi one one ke nan ai.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,


IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANI MUN BARKI DA ALLAH,,,,


A LOKACIN MUKE,,,,


Maria ta rasa may ke ma rayuwan ta dadi yanzu don gaba daya hankalin Atiku na gurin sabuwar amaryan shi da tashigo mashi da sauyin yanayin rayuwa.
Duk wani ladabi da biyayya na aure amaryan maria ta iya shi haka yasa take ta sace zuciyan Atiku don dama haka maza ke so .
Gashi da ita da dan ta abinda ya faru dashi na kaddara yaki gogewa gare su.
Kusan kullun sai yaron da akaiwa fyade ya dawo mata gida da kuka wani yai mashi gorin abinda ya samay shi.
Itama dai din idan gidan buki ta tafi ko unguwa haka mata zasu dinga cewa Allah sarki ashe itace abin ya faru da dan ta.
Abin kunya harda yan uwan ta na jini sai su dinga fadar maganan yadda hankalinta zai kara tashi taji kaman a ranan abin ya faru da Aliyu.
Ga maigidan ta da yake yawan musguna mata a gida duk abin da tayi bata iya ba yanzun gareshi.
Saboda tabon abin da ta aikatawa dan shi ya matukar tsaya mashi a zuciyar shi sosai.
Ta ramay tai baki sosai gashi sanyi ne yanzu bata cinikin ruwa ko kadan kuma ko banza bata da mai mata talla yanzu.
Wanan bakin cikin da take ciki da yai mata yawa yasa ta tafi gurin mahaifiyan ta cikin tashin hankali.
Nan uwar take ce mata ai sai ki zauna ki ta hadiyan bakin ciki, in kina fidda kudi, kije ai maki aiki ki samu kan mijin ki ki fitar idan kuma kin boye su sai dai ki zauna kina hadiyan bakin cikin da namiji kina kallo zai zama mijin ta ita kadai.
Hakalin maria yai mugun tashi da maganan mahaifiyan ta nan dai ta bata shawaran ta dawo akwai inda zata kaita don mutumin aikin shi kaman yankan yukane saboda gwanancewan shi da iya aikin shi.
Take maria taji kamar an cire mata damuwan ta don sai take gani kamar har tayi nasara ma ko a lokacin.
Ta dawo gida da farincikin ta ta samu har amaryan ta ta gyara gida sai kyali ,gidan keyi don ko yaushe a cikin gyara yake yanzu.
Tai ma Maria sannu da dawowa ta amsa mata a tatsune ta fada dakin ta don ko sallah batayi ba a lokacin.

****** ********* ******
Ina idar da sallah na fito na fara gyaran gidan kafin wani lokaci gidan ya dauki kamshi gaba daya, nan na fada kitchen for the first time don na fara girka abinci da akaina.
Kayan aikine na electronic gasu nan kala kala a kitchen din na fara tunanen wani simple abinci zan yi a lokacin.
Ina bude store din kitchen din naga kayan abinci da na,shaye, shayen, kwali da sauran duk abinci da sha tap a store din.
Na dan dade tsaye ina bin kayan da kallon mamaki don abin yayi yawa sosai a store din.
Dankalin iris na debo tare da kayan miya nai tunanen yin dan fate mai ruwa na sa naman koda dake cikin fridge din na dan yi amfani da danyen attarudu.
Sai ruwan shayin dana dafa yaji kanunfari kamshi na tashi daga cikin shi.
Ina tsaye a dining ina gyara kayan abinci naji ya shigo gidan cikin kayan motsa jiki yake.
Ban san baya gidan ba sai da naga dawowan shi daga inda nake tsaye nace mai ina kwana.
Lafiya kawai ya amsa dashi ya shige part din shi kai tsaye inda ya shiga wanka.
Nima wanka na shiga na gyara jikina ina tsaye bakin wardrobe dina da hijjab dina don sai da nai sallah walha, zan dauki kaya naji an shigo dakin.
Na juyo a firgice ina ganin shine nace cikin daure fuska don may za,a shigo min daki haka ko sallama babu kuma.
Kallon mamaki yai min tare da daure fuskan shi sai kuma naga ya dan dara yace dakin ki fa kikace yarinya?
Nace au nan din dakinkane ko kaga ni nashiga naka dakin ne da zaka ce nan din ma nakane?
Yace lalai yarinya kina da karfin hali wallahi ni da gidana kuma yau ake son kafa min doka akai.
Yace to bari na tunatar dake in har kin fara shagala kin samu gidan zama.
Ki sani duk wani abinda ke cikin gidan nan gaba daya har ke mallakana ne don baki san yadda na samay su ba.
Saboda haka ina son ki shiga hankalin ki daga yau don kada ki wani mike kafa wai ke ga maigida tunda kinga banza ko ?
Ashe shiyasa jiya nida gidana da kayana har kika sawa daki key wai ke ga mai daki ko?
Nace saukin abin dai nima ba kasuwa aka dauko ni ba dai yace towa kuma yasani sai anbincika wanan.
Raina yai balain baci nace kamar yadda kaima akwai alaman bincike akan ka dole.
Sadauki yai murmushi saboda yaba ma karfin halina yace yarinya idan zamuci gaba da haka zanfi kowa farin ciki da hakan a gidan nan.
Yace ai duk macen da zatayi abinda mijin ta ke so ana kyautata zaton samun sakamako mai kyau a gurin ta.
Don haka mu zuba dake a haka a gidan nan aga wanda zai sha wahala.
Ya fara tafiya yake cewa sai ki fito muci abinci don ban yarda dake ba kada ki kashe ma uwana ni.
Nace bazanci ba idan kaci sai ka mutu don kai ke tsoron mutuwa yanzu kuma ma na kashe ka nakai tarin zunubin ka ina ?
Yai murmushi yace ban dai yarda ba na fada maki ina jiranki a falo don nasan halin yan kauye da son banza don a gajewa uwata da yan uwana dan abinda aka gani.
Ya sa kai ya fice daga dakin yana dariyan keta raina yai balain baci haka na karasa shiryawa ina mitan maganan shi a raina.
Kaman bazan fita ba amma kuma sai tsoro ya kamani kada yazo wani abu ya samay shi ace nice nafito tare da dan saka takalmin na tare da daura dankwalin rigana ga kaina sai karamin hijjib na saka iya kafada na.
Saye nake a cikin redmaid din dogon rigan abaya maroon color nafito nima sai kamshi ke tashi a jikina.
Yana zaune yana waya yana jin motsin fitowana ya kura min ido da sauri naga ya kawar da kan shi gareni.
Ashe gaban shi ne yai wani mugun faduwa ganin yadda na sake mai a lokaci guda.
Naja kuran dake gefe zan zauna yace kaji min yar kauye yana kashe waya yake kallona yace wancan kujera zaki dinga zama mai fuskantar wanan don kada wani ya shigo ya samay ki cikin zaman kauyawa ace yar kauye na kwaso gida na.
Ban zauna ba sai jawo plate din da nayi na fara zuba mashi abinci komai da ya dace na dan zuba mai yadda muka saba zuba mai a gida.
Na koma na zauna a inda ya umurce ni yana daukan spoon yace one warning again daga yau idan ina gidan nan bana son ganin wanan takunkumin hijjabin naki kamar zaki cin kasuwan kauye dake.
Nace ai ni ba don ka na saka ba don Allah nake saka abina dama.
Yace kin makaro da wanan dakin zauna gidan ku sai kita faman saka abinki amma ba gidan Umar ba kan.
Haushi ya kamani ganin ya kura min ido yana jiran na cire hijjab din dake wuyana.
Dole na dan sa hannu na zare hijjab din daga wuya na gaba daya surana yafito a fili.
Sai lokacin naga ya fara cin abinci nikan na kasa sai naji yace may kike nufi ko dai da gaske kinyi barbaden ne a ciki wai?
Nace banda gadon wanan amma

Please Login or Register in order to submit comment