Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

mukayi dashi a lokacin.
Mama tace aima jikin yai sauki yanzu gata har tana dan fitowa falo yanzu aida ko yaushe tana daki a dunkule.
An ko koma asibiti da ita kuwa ya tambaya ?
Yau sati daya ke nan da aka kara mata ruwa da magani ai abin yazo mata da akasi wallahi haka nan nai cikin maryam kusan duk sati biyu uku sai na sha ruwa ga zafin jiki da ciwon kai duk na kare a lokaci sai dana haihu kamar anzare min kaya naji komai ya wuce.
Iyya tace hjy ashe maishi ya biyo gwagon shi ke nan da ga jini wani ciki kara gare shi sosai wallahi.
Ya mayar da hankalin shi gare ni tare da tausa muryan shi yana tambayana may nakeji ajikina ne wai ?
Nace ba komai yaya ai naji sauki nace mai yaya hanya yace cikin bata rai Alhamdullahi.
Sannu yaya jikin to yanzun kuma nace da sauki yaya.
Maji ko zan fita da itane waje idan nan basu gane may ke damuwar ta ba ?
Dariya sukayi mama tace ji shirmayn ka ciki may ye bai zuwa wa mace dashi kowa da kalar daukan cikin ta ai.
Yadda ya mai da hankali akaina muna magana kus kus yasa Anty Amira jin haushi matuka tana gani idan da dane daya dawo itace yar gaban goshin shi amma yanzu tunda ya shigo hankalin shi yana a kaina baima ko yi mata wani magana ba bayan gaisuwan da sukayi kawai.
Mikewa tayi tare da tsuki tabar falon daidai lokacin da yake tambayan ina kuwa cin abinci yaga duk na ramay gaba daya haka,?
Baima san tanayi ba tashige tana gunguni wai an asirce shi yanzu bai ganin kowa da gashi sai ni da yan uwana kawai.
Mama tace mai bata cin komai sai ruwan kunu kaganshi nan a gefen ta aje koshi bai ludayi uku ba idan ma tasha din ke nan ai.
Nan ya fara tambayana zakici abu kaza ko na sayo maki kaza ne nace yaya ban son komai Iam ok haka ma na koshi.
Ya dan tsuki tare da kura min ido yana tausayawa halin da nake ciki sosai can mamatace mai.
Matar dan uwanka fa tana gidan nan kasan na fada ma ta haihu banda gobe suna.
Yace au a gidan nan take zaune ne mama tace eh daga asibiti uwar su tace a kawo ta nan.
Yace amma naga maryam ita a dakin ta ta haihu ai bata dawo gida ba ?
Mama tace kasan kowa da irin ra,ayin shi nata ra,ayin ke nan yin haka din Alhaji ma ido yasa masu don yasan ba a wanyewa lafiya indai yaya ne.
Sun dan yi hira ya mike zuwa cikin gida dakin Umma idan ya duba jaririya.
Ya samu su umma da uyalin ta a falo yai masu barka suka tambaye shi hanya yace Alhamdullahi.
Da zai tafi bayan maijego tafito sun gaisa da ita yakawo kudi masu yawa ya bata yace ta sai wa yarinya sabulu dashi.
Yana fita yaji Umma tana tambaya nawane halan ya basu ta nuna masu raffan yan dari biyar sabbi tace akawo a kara ga laluran buki dashi.
But Nafisa dake daki tafito tana cewa a,a Umma ki bar mata kudin ta don Allah don dai ita aka ba itama ai tana da abin da zatayi dasu ko?
Umma tace kada ki kawo min diban albarkan ki da kika saba yiwa mutane wani lalura gare ta wanda yafi namu kuma ?
Ita dai Shafa,tu mikawa Umma kudin tayi amma sai Nafisa ta rike tana cewa wallahi ba,a bayarwa tunda ita akaba.
Ai ya ganki baice maki gasu ba ya mika mata idan yabaku naku da ita zaku raba ta shige cikin daki da kudin a hannun ta umma tana kwalla mata kira amma ta kyale ta.
Nafisa ke kan ke kan wallahi Allah ya waddaran hali ir8n naki na tir da Allah waddai tace daga ciki ban dai bayarwa wallahi.
Bai dade ba yace zai tafi ya kwanta don a gajiye yake lokacin mukai mai sai da safe ya fita daga gidan.
Ji nayi kamar na bi bayan shi da zai fita sai dai babu halin yin haka dole na zauna a gurin mama don nan ya samay mu.

****** ********* ******
Kwanan shi biyu da dawowa sai faman sintiri yakeyi bai gidan mu baya gidan maji gurin mu.
Yau an tashi da bukin sunan matar yaya Imirana inda yarinya taci sunan Umma kowa na kiran ta da Ummi don sunan ta na Umma da taci.
Sai naji kawai ranan ina marmarin alale na gwangwani don haka na fadawa Iyya Rabi abinda nake son ci.
Baita kasa a gwiwa ba ta shiga shirin yi min alaila ta samo gwagwani gurin wani mai shayi a unguwan ta hauyin alalen da nake son ci.
Ba bata lokaci ta gama min ina daki ina shiyawa zan fito falo yau na kokarta na yi dan kwalliya a jikina don jama,an da suka cika gidan.
Cikin atamfar super nake dark blue dinkin shi mai shara sharan hannuwa half gown na daura dan kwalin kayan a kaina.
Cikin dake jikina kayan yasa yafito don lokacin ya kai wata shidda a jikina sai dai ba kowane zai iya ganewa ba sai wanda ya sanni da farko.
Nafito falo na zauna Iyya Rabi tace yauwa yanzun nake batin kiran ki kifito kici shi da dan zafin shi kada kuma ya fita ran ki.
Zama daidai da shigowan maryam gidan da ita da kannen mijin ta da suka rako ta gurin sunan.
Suna dauke da danta a hannun su sai wata makwabciyar ta data rakota kuma again don ita tana hurda da makwabtan ta sosai.
Suna zama aka kawo alalen da ita muka hada hannu muna ci a plate daya naji dadin shi sosai muna ci muna hiran yaronta irin yadda yake yawan alolayi sosai.
Muryan Baba mukaji a tsakar gida yana kwalawa matan shi kira cikin tashin hankali.
Gaba daya suka fito daga dakunan su sai gidan yai tsit kowa nason jin kiran don daji bana lafiya bane.
Mama Asiya tana fitowa ya kalleta yace Asiya kuncuce ni kunci amana keda dan ki bazan taba yafe maku ba a rayuwana.
Mummy ce cikin karfin hali yadda taga Baba a rude take cewa wai may yafaru ne Alhaji kuma ?
Yace Ahmed ya sayar da gidan nan yau wata uku ke nan ban sani ba ashe ?
Salati kowa ya saka sai ihun mama Asiya kawai mukaji daga waje abinda yasa mu fitowa ke na daga dakunan mu duk wanda ke gidan sai da yafito don tashin hankali.
Baba yaci gaba da fadin yanzun haka wanda yasai gidan yana waje yace yazo ne yabamu notice din tashi don anyi dashi nan da wata uku zamu bar gidan wai .
Lokaci daya aka saka salati masu kuka sunayi masu salati da tir sunayi a lokaci daya.
Sai ganin kawai akayi Baba yai suuu zai fadi da sauri mama da mummy suka tare shi bai kai kasa ba sai dai ba rai.
Idanuwan shi a waje inna lillahi wa inna alaihim rajiun,,,
Ihu da tashin hankali a ranan mun gane shi a gidan da gudu wasu suka kwasa zuwa kiran maza a waje.
Yaya saudauki yana tare da yaya Bashar suna hanya kiran maryam ya shigo wayan shi .
Yace kai munafukan matar kace fa ke kirana yanzu, bashar yace wa maryam lafiya kuwa ya dauki kiran tana kuka take ce mai yaya don Allah kazo gida Baba.
Cikin wani irin murya yace Baba may fa ?
Sai kuka takeyi tace don Allah yaya kazo Baban mu ya rasu inna lillahi wani irin burki ya taka da ya daki motar dake kusa dashi.
Ga you turne din sokoto da tsawon tsiya haka ya kwashe su da gudu Allah dai ne ya tsare su sai gida cikin yan mintina suka kawo.
Irin mutanen da ya hango sunyi cincirindo a kofan gidan su cikin tashin hankali ne yasa hankalin su ya kara dagawa sosai.
Wani irin mugun parking sukayi ya bar mota a bude ya nufi cikin gida da gudun shi irin na yan kwallo bashar tana bayan shi.
Sai wani yaro makwabcin su ne ya kashe motan ya gyara parking gefe yana shiga get su Sagir sun dauko Baba ya tare su tare da kamashi suka fita zuwa waje da shi sai asibiti cikin tashin hankali.
Suna zuwa emergency aka nufa dashi nan aka samu da kyat ya farfado duk ilahirin iyalin shi suna gurin sai yaya Ahmed ne kawai da matar shi basu gurin.
Koke koke kawai ke tashi tashin hankali ne ga duk fuskan wanda ka kalla a lokacin.
Muna tsatsaye tare da su anty maryam da anty Nafisa don tare muka zo asibitin da su.
Wani iri nake ji dole ssuka samomin guri na zauna ga alalen da naiwa mugun ci sai taso min yakeyi ina jin zanyi amai a lokacin.
Maryam ce ta dafani take cewa Fatima ko zaki koma gida ne kinga baki da lafiya fa a jikin ki gaki da lalura kada tashin hankali ya kamaki kuma ?
Nace ba komai ai anty aiko sai aman da nake taushewa ya taso min nan na duka naita sharara shi hankalin mutane kuma ya dawo a kaina.
Daga cikin daki da Abdul ya shiga inda su yaya suke a kan Baba da ake neman jijiyan shi yake cewa ga kuma Fatima can wallahi ita ma a waje sai a hankali sai amai take shararawa kawai.
Da sauri suke cewa harda ita da bata da lafiya tazo ne yaya sadauki ya dago rai bace yace may yakawo ta ita da bata da lafiya kuma ?
Bashar ya fita da sauri halin da ya samay ni ciki yace su maryam su kamani muje gurin likita.
Muna zuwa likita mace ce muka samu tace ina bukatan bedrest a lokacin nan nima aka kwantar dani asibitin.
Dole rabin yan uwa suka dawo gare ni barci ya dauke ni mai nauyi sosai har ban san inda nake ba ma.
Da kyat aka samu baba ya farfado tana kiran Ahmed Ahmed ka cuce ni wallahi ka cuci iyalina Ahmed.
Nan sadauki yake cewa haba Baba yi hakkuri a samo lafiyan ka tunkun na koma may nene please.
Sagir ne ya jashia gefe daya can kusurwan gadon da Baba yake kwance yace yaya sadauki baka san may ke faruwa bane ko ?
Yace may kuma ya faru ne Sagir ?
Sagir yace wai yaya Ahmed ya sayar da gidan mu shine ya jawowa Baba wanan matsalar haka.
Cikin wata murya sadauki yace what Ahmed ya sayar da gida fa kace nan dai Sagir ke fada mai duk yadda abin yake don a gaban idon shi akai komai.
Yace mai gidan yazo da bukatan yana son a kwashe a bashi gidan shi don wa,adin aka bayar ya cika.
Innalillahi sadauki yace may yasa Normal yai wanan mugun aika aikan haka da lafiyan shi kuwa ?
Waye ya sayi gidan ya tambayi Ahmed cikin dago kai da idanuwan shi suka kada sukai ja a lokaci daya.
Nan Bashar ya shigo yanayin da ya gansu ne ya tayar mai da hankali ya karaso yana fadin may ke faruwa ne kuma man ?
Yace humm bari kaidai man wani sabon labari nake ji wai Normal ya sayar da gidan baba ga wani mutum.
Yace what da dan karfi yace no warder ake ce min yanzu anga yana bushasha da kudi ya samu lafiya.
Kai amma guy din nan baiyi ba wallahi wanan ne ya jawo wa Baba matsala ke nan ko ?
Bai bashi amsa ba sai cewa yayi yaya ita Fatima din kuma take yanzun ?
Yace itama an bata gado tana bukatar bedrest wai sukace .
Yace o my god wata sabuwa kuma again Allah gamu gareka yace a zuciyar shi amma a fili cewa yayi tana ina yanzun kuma ?
Tana gany room a can suka kwantar da ita har tayi barci shine na fito zuwa nan don gaskiya tana jin jiki sosai wallahi.
Sai da yaga komai ya saitu wa baba ne ya fito zuwa dakin da nake kwance ina barci maryam da Nafisa sun sakani a gaba suna kallo na.
Shigowan shi yasa suka juyo suna kallon shi tare da tambayan shi jikin bana yanzu.
Yace masu ya farfado idanuwan shi a,kaina ya kura min ido ina barci cikin wahala ga ruwa daure a hannu na lokacin.
Takowa yayi zuwa bakin gadon ya dan tabo fuskana ban ma san yanayi ba don nai barci sosai.
Ya dade a tsaye baiyi magana ba ya juya tafita daga dakin ya nufi gurin Baba shima barcin yakeyi yasa shi fitowa don likita yace kada a shiga dakin abarshi ya huta haka yasa akabar su mama da umma da mummy kawai.
Fita sukayi daga asibitin shi da bashar bai mashi magana ba shine dai ya karbi key yajasu barshar din.

****** ********* ******
Ina muka nufa yake tambayan shi kai tsaye yace kaini gidan Normal please inji daga bakin shi.
Sai gidan yaya Ahmed bashar ya tsaya suka fita gidan yana a rufe amma akwai mutum don kara kidan disco daya karadw erea din a lokacin daga gidan.
Nocking din kofan gidan sukayi kusan sau uku kamar baza,a bude ba can jamila tabude kofan gidan.
Tana cikin wani matsatsen wandon jeans da ya matse ta da wani dan riga ja mai guntun hannu a rubutawa rigan crazy girl.
Tana ganin shi ne tace up UF yau kaine gidan da kanka cikin wani yanayi na farr da idanuwan ta.
Yace mai gidan fa a taice ?
Baka ma bari mu gaisa sai tambayan dan uwaka watau shi ka sani kawai ko ?
Yace please ina Normal yake nake tambayan ki ?
Normal kan baya kasan ya tafi kwatano dauko mota tabashi amsa ganin da tayi ba wasa a fuskan shi.
Ok kawai yace ya juya yabar gurin bashar yabi shi a baya mota suka shiga suka bar unguwan .
Baiyi magana ba da suka fara hanya sai sa hannu yayi ya dafe goshin shi da hannun shi daya kawai.
Zuciyar shi tana mai wani irin suya don bacin rai hankalin shi a tashe yake lokacin.
Bashar ne yace yanzu kamata yayi mu nemi mutumin mu fara jin yadda sukayi dashi first.
Yace wa yasan mutumin sai bashar yace bari mu nemo Sagir ko yasan labarin mana ?
Asibiti suka dawo har looacin Baba yana kwance sharkaf dashi sun dan dade a kan shi ba wani motsawan da yakeyi sai dai numfashi kawai da zai nuna ma yana raye.
Fita yayi ya kira yaya Imiran da Sagir din shima Abdul ya biyo bayan su dashi da bashar.
Yace wani mutumine ya sayi gidan baba din hannun Normal Sagir ?
Gaskiya ban san shi ba sai dai ina gani a GRA kamar nake ganin motan shi idan naje gurin aboki na dake can.
Abdul daga bayan su yake cewa wanan guy din da suka zo dazun yace eh shi yace dan masani ne mana guy din nan mai sayen gidaje dake GRA ko ?
Mota biyu suka tafi dashi gidan mutumin sai dai baya nan ance masu yafita cikin gari .
Yanzu yaya kuke ganin zamuyi ke nan ?
Bashae yace lauya zamu fara nema mana shine farko don nasan dole abin sai ya hada da lauya ai.
Wani lauya kake gani duk garin nan zamu iya samu ya tsaya muna kan wanan magana don ba karamar case bane fa ?
Nan suka fara kawo sunayen lauyoyi da suka san cewa yakai lauya da zai iya tsaya masu karshe dai suka tsaya akan barister Nuraddeen mohammed moroki dake zama a gusau zamfara state.
Shine zai tsaya masu a matsayin lauyan su matashine wanda yasan aikin shi da sanin darajan tallakawa akan aikin shi sosai.
Sun samu lamban lauyan inda suka kira shi tare da mashi bayanin komai dake faruwa shima yana tambayan su wasu abubuwan da ya dace ya sani daga cikin maganan.
Haka aka shigar da kara a koto ranan basai ma gari ya waye ba don da zafi zafi ake buga karfe.
An aikawa dan masani da sammacin sayen gida ba bisa kan kaida ba a hannun dan maigida da yayi.
Yana karantawa yai dariya yace shi may ye nashi sana,anshine ba yau aka fara irin wanan ba ai Allah ya kaisu kotun lafiya.

****** ********* ******
Falkawana yai daidai da su Mama suna dakin lokacin ma magariba ya gabato sosai na bude idanuwa na a hankali.
Sai naji suna sannu Fatima yaya jikin naki nace a hankali da sauki na daga ido na kalli gurin daki ne na asibiti ashe nake ciki a lokacin.
May ke damunki yanzun Fatima mummy ta tambaye ni ?
Da kyat na bude baki nace mata juwa nake ji tace bari a kira likitan ya dubaki.
Likita sun dawo tare da su yaya nan suke gaishe mu likita yace su dan rage daga dakin nan aka barmu ni da yaya da likitan kawai.
Bayan yan tanbayiyi idanuwa na suna a lumshe yai yan rubuce rubucen da zaiyi ne yake cewa dole sai nayi bed rest a cikin asibiti don yana gani baby dake jikina yayi weak sosai zai iya fitowa indan an matsa mai wanda hakan babban hatsari ne sosai gare shi.
Idanuwan shi ya runtse tare da tausaya ma halinda nake ciki lokacin nan dai aka yanke shawaran zan zauna asibiti har wani lokaci a gani.
Iyya Rabi ce zata zauna a tare dani don dama tare muke itace ke ta fama da lalura na ko a gida.
Hankalin kowa a tashe don yadda baba yake matukar jin jikin shi ko matsi bayayi sai na,uran taimako da,aka saka mashi ke aiki.
Zancen karan da akayi an tsayar da magana dole sai anga Ahmed anji ta bakin shi za,a,san yadda za,ayi.
Gashi har lokacin bai dawo garin ba kullun akaje gidan baya gari Jamila take fadi.
Ashe ta dawo ya samu labari gurin wani abokin shi shine yake boyewa kada su ganshi.
Sai dare sosai yake komawa gida ya kwanta tun da safe ya bar gidan ya koma maboyan shi ya boye.
Duk wani dan gidan hankalin shi a tashe yake yadda baba ake hasashen ya samu faralazy ne barin shi guda na dama.
Gashi har zuwa lokacin yana unconscious bai san inda yake ba sai cewa likitoci keyi akwai improvement ga lafiyan shi.
An yanke shawaran za,a fita dashi waje wani abokin sadauki likita yace a kawo shi gurin su su duba shi a Germany.
Komai an cika na tafiyan su waje da baba lokaci kawai ake jira na fita da mummu kawai sai shi sadauki da,Sagir aka shirya tafiyan da za,ayi.
Ina zaune Iyya tana tsaye a kaina ta wade min lemo zan sha ya shigo dakin zai min sallama.
Tana ganin shi ta fara gaudashi tare da mashi yaya maijiki yace Alhamdullahi Iyya zamu tafi yau da,daren nan lagos gobe da safe zamu daga dashi.
Iyya tace kai duniya gaskiya wanan yaron wallahi bai kyauta muna ba wallahi wanan sallon yaudaran nashi yayi yawa ina zai kai alhakin wanan bawan Allah da,sanadin shi ya mayar haka ?
Ya tako zuwa inda nake ina tsotson lemun da Iyya ta wade min a hankali yace yaya jikin naki Fatima ?
Nace naji sauki yaya yaya jikin baba din yake ya dan lumshe idanuwan shi a hankali yace yaji sauki yau insha Allahu zamu tafi.
Ki kula da shan maganin ki Fatima kin dai ga yadda kike fama ban how long zaki yi ba anan yadda likita yai min bayani zasu dan rike ki suga yadda jikin naki zai kasance kafin su sallamay ki daga nan.
Idanuwana na lumshe ina jin wani ba dadi yace naso mu aikawa mutanen gida don su san halin da kike ciki amma maji ta hana tace kada mu tayar masu da hankslin su suma.
A bari har aga yaya jikin naki zai kasance tukun sai a fada masu amma ni naso su sani kila za,a samu wanda yazo daga can ya zauna dake.
Shiru nayi ban da ta cewa sai dai naga aiko yayane ya kamata a basu hakkin su a matsayin su na mahaifa na.
Don idan sunji bazasuji dadi ba daga baya sai dai banda yadda zanyi don ban da tacewa ni yanzu.
Muna tare muna hira jefi jefi dashi wanda na lura bai a cikin hankalin shi a lokacin.
Yace zai tafi gida ya shirya ya bar zancen makarantan Sa,ade a hannun bashar yana ganin zuwa wani Monday za,a kaita makaran ta.
Musa ma Bashar zai kula da zuwa mai visiting kamar yadda ya saba zuwa mai.
Nace na gode a hankali ya mike yace zai tafi ya dawo idan ya kimtsa nace Allah ya tsare ya fita.
Da yamman ne wani abokin bashar ke fada masu cewa yaga yaya Ahmed yana garin don sun hadu dashi da rana a,wani shago yana sayayya.
A gida kuma mama Asiya da yan uwanta suna cikin matukar tashin hankali sosai don tana gudun wani abu ya faru da mijinsu a sanadin dan ta.
Wanda tasan ba zasu yafe mata ba don halin da danta ya jefa gidan ko yanzu bata da shakata a gidan kowa sai zagin su yakeyi tanaji tana gani babu yadda zatayi akai sai hakkuri.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,

IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BAKI GA ALLAH YA SAKA MUNA AKANKI YAR UWA,,,


Ya dawo acikin shirin shi ina kwance Iyya tana kokarin fita da ta gan shi yace, Iyya ni zan tafi don Allah mutumiyar ki a kulla da ita sosai naso ace ina garin don na bata kullawa sai dai hakkan baisamu ba.
Nasan ban da matsalar hakan don ke da maji kuna kusa da ita bana son tana wanan rashin cin abincin da batayi yana matukar damu na sosai ko ba dadi abata koda kadan ne please.
Iyya tace uban dakina kada ka damu tsakani da Allah nake zaune tare da ku zanyi wa Fatima duk abinda kasan zan iya yiwa yar cikina shi insha Allahu.
Ya ciro kudi masu yawa yabata yace ga wanan ki rike a hannun ki ku dinga lalura dashi a nan din.
Tai mai godiya ta fita daga dakin ta barmu mu biyu dagani sai shi a dakin.
Isowa yayi inda nake kwance yana cewa na,shirya zamu tafi yanzu bakin gadon da nake kwance ya zauna ya kamo hannuwa na.
Yana fadin Fatima don Allah ki kula da kanki ki tausayawa abinda ke a jikin ki please.
Idan baki ci abinci ba yaya zaki samu kuzari har baby na ya samu shima please ki tausaya min ko ba dadi ki dan dinga cin yan abubuwan gina jiki don kuzarin ku.
Kune rayuwana Fatima kune zan kalla nayi farinciki don kune jindadin farin cikina.


Please Login or Register in order to submit comment