Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

gidan har su uku bata tunanen cewa abinda take wa yar mutane zai iya faruwa akan diyan ta.
Mata bamu tunanen cewa mu uwaye ne masu diya duk abinda ka shuka shine kake girma a rayuwan ka.
Muryan mijin nata ne ke fada mata cewa tazo gida ga Aisha, yar su ta dawo gida da matsala.
Wanan maganan da taji ne yasa ta dafe kirjin ta tana cewa zata tafi amma zata dawo don bata karasa maganan da ya kawo ta ba.

****** ********* ******
******
Tun da farar safiya muryan Jatau ne ya tayar da mutanen gidan da balain da yazo masu.
Yake cewa mama tafito bazai yarda ba tasan yarta honko ne ta dauka takai mashi gidan shi don an raina shi.
Shi za, aiwa wullakanci ko may da za, a dauko honkon akawo maigida don an mai dashi tsoho.
Gaban mama ne yai mugun faduwa haka ta daure tafito zani na faduwa mata gashi har mutane sun fara taruwa don gulma.
Tace a ranta bari ta rufe ido tai mai na mahaukaci kawai a wuce gurin gaba daya.
Ta na lekowa take cewa kai Jatau kada ka dauka ko tsoron ka ake ji duk haukan da kakeyi kyaleka na keyi.
Mata kace kana so mata kuma na baka banga dalilin da zaka taso tsofai tsofai dakai ba kazo muna kana wanan magana abin kunya.
Tace ankai maka honko din sai ka turo min yata yau din nan na fasa auren bazata zauna ba a gidan ka.
Da Jatau yaga mama ta fishi iskanci da hauka dole ya kwantar da nashi haukan yace baki da hurimin daukan min mata, don mata zamana take yanzu.
Matar ka da kace honko ce ai daga yau ta gama zama dakai a gidan ka don dama kudin bazawara ka biya bana budurwa ba.
Yace a shekeke yo ina budurwan take anan kin kai min hinkon diyar ki aiko sai ga su Rukaiyya sun fito daga cikin gida.
Mama ta juya garesu tana cewa maza kuje kuzo min da Lawisa gidan nan yanzun nan.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , ,


IDAN KIN BIYA KI RIKE AMANA DON NAUYI GARESHI YAR UWA KADA KI TURAWA WANDA BAI BIYA BA DON GIRMAN ALLAH, , , , , ,


Da taimako na muka kanmala aikin girkin rana da muka samu anty ta dora don muna cikin hira na mike don jin kaurin abinci danaji.
Kofan danaga ta nufa dazun dauko muna abun sha na nufa sai dai ina shiga kaina ya daure yadda naga kayan girkin zamani ya cika kitchen din ta ko ina.
Na rasa yaya zan duba abincin da naji yana nuna alaman ya dahu a lokacin.
Gurin gas din na nufa da tsoron tabawa fal a zuciya na don ban taba amfani dashi ba sai dai cikin karfin hali na bude tukunyan dake saman wuta.
Na samu abincin har ya tsotse na sauke sai dai ban iya kashewa ba ganin kayan miyan da tai blandinga cikin blander na juya na dora a wutan sai kamshi ne ya ziyarci hancin su a falo lokacin kuma suka fahinci bani falon tun dazun da sauri anty ta mike zuwa kitchen din ta samay ni a tsaye.
Cikin mamaki take cewa dani Rama dama kin iya girki da gas ne ?
Kaina girgiza mata tare dacewa yau ma na fara ganin shu ai, tace min kiyi a hankali nan take min bayani kan komai na kitchen din muna aiki a tare da ita har muka karasa tana gwada min komai sannu a hankali har na fara fahinta har muka gama aikin na zubo ma mama dani , mukaci mukasha muka koshi.
Suna hira da mama nake fahintar akwai matsala a gidan nasu yadda naji tanawa mama bayanin komai dake faruwa.
Na bu gidan da mamaki gashi da girma da kyau babu ne kawai babu a gidan amma wai zasu bar gidan bada dadewa ba.
Ganin ina zaune a takure na kasa sake jikina yasa ta kallon inda nake tausayi nake bata matuka idan ta kalle ni yadda rayuwa yazo min ina yar karama da ni.
Anty ke cewa na taso ta gwada min dakin da zamu zauna a part din ta nan na kwashi kayan mu na kai dakin sai da na tsaya na gyara shi tas na shiga nai wanka tare da yin sallah.
Don a kauye na tashi amma ina da matukar tsabta sosai naki jinin ganin daki a ya mutse ko kadan.
Kafin wani lokaci nai ma gidan kwal don dama gyara yake so bai samu ba ita gashi tayi tafiya sauran matan gidan kuma ba zama sukeyi ba a gida koma sun zauna basu iya gyara ko kadan don son jiki.
Tun wanan ranan da na zo anty tasan ta rage matsala ta wanan fannin sai misalin biyar saura yaran gidan suka dawo daga makaranta su hudu na gani uku mata daya namiji.
Na sheda yaran anty daga cikin su, don na sansu kwanaki da taje dasu ina gidan garbati.
Biyun yan matan ne ban san su ba sai ranan na fara ganin su don haka nake kyautata zaton diyan maigidan ta ne su din, don akwai dan kama na jini tsakanin su da diyan anty din.
Nan suka kewaye ta suna mata hiran makaranta sai can anty tace bakuga Grandma tazo ba da Anty Rahama.
Gaba dayan su yaran suka juyo inda muke muna masu kallon sha,awa da namijin ne ya juya yana kokarin cire school bag din shi dake goye a bayan shi cikin rashin damuwa da abinda uwar tace mai.
Duk da yara ne an koya masu gaisuwa sai yaran da ba nata bane suke muna wani irin kallon mamaki.
Nasir baka gaida Anty Rama ba fa ya dan juye fuska a daure yace ina wuni ?
Muka amsa mai a tare da mama lokaci daya sai dayan yarinyar ta dan kwanta gefen hannun kujerar da anty ke sama tace mummy are they going to stay with us ?
Gaba daya yaran suka juyo suna son jin amsan da uwar tasu zata bayar a kaina maman tace dasu i think so, cikin jin dadi suka saka ihu lokaci daya suka samu waje suka zauna suna surutu.
Kamar yadda nake wa kannena a gida idan sun dawo school zan sa su tube uniform din jikin su na kwasa na wanke na basu abinci kafin su wuce islamiya.
Tsab na mike daga inda nake na ce da Amira oya Amira zo na cire maku uniform kuci abinci.
Duk sukayo kaina suna rige rigen zuwa gare ni cikin jin dadi a tsakanin su, anty tai murmushi daga inda suke zaune da mama suna kallon mu tace dani ku shiga daga ciki dayan dakin kayan su yanan an kowa ta nuna maki nata aini kin ceceni yau wallahi.
Komai na gama masu har abinci a sama sukace zasuci don haka can na hau dashi sukaci muka gyara gurin kamar basu bata ba.
Cikin kwana biyun da nayi a gidan na dan fahinci abubuwan rayuwa na gidan yadda take gudanar dashi a tsarin ta.
Kaman tashi da wuri da safe a girka abincin yan makaranta ai masu wanka a shirya su a hada masu abincin zuwa makaranta sai rakiya har bakin motan da zai kai su school.
Haka yasa ta samu sauki sosai a dan zuwan da mukayi da nayi motsi kadan zata fara cewa wai Rama na nagode nagode kinji idan naji ta fadi hakan.
Sai dai nayi murmushi nace kai haba anty wanan har wani aiki ne mai yawa ?
Nikan a guri na ai wanan ba wani aiki bane don banga abin wahala ba a cikin sa amma ita sai take ganin babu taimakon da yakai wannan tunda gashi tana samun hutu da yin barci da safe wadattace yadda ake bukata a gareta.
A kwana biyun da mukayi kawai shakuwa ne sosai ya shiga tsakanin yaran matan gidan dani sai Nasir ne har yanzu bai sake jikin shi dani.
Sosai nake mayar da hankali ga taimakon rayuwan anty a gidan ko ina na gidan sai walkiya yakeyi don yana samun gyara.
Idan yara sun tafi zan gyara falo har kitchen na dora abincin rana sai na koma part din anty na hada mata ruwan wanka na dan zauna da ita muna hira har ta mike ta shiga tai wanka sai nai saurin gyara mata dakin kafinta fito daga wanka na koma kitchen gurin girkin rana, kafin wani lokaci na gabatar masu da abincin rana ko.
Kafin mu cika sati daya komai na kan gidan nasan yadda akeyin shi zan kuma yi mata shi tsab haka yasa suke samun hutu daga anty har mama sun dan canza a wanan lokacin.
Duk wani abinda nasan bata so ko zai bata mata rai da yaran ta basu so, zan gujewa wanan abin .
Na zomo mai kafa kafa a kan komai na gidan bana shiga shirgin dabai shafeni ba don ko yaushe ina busy ne.
Ganin yadda yanayi na yake bana jin kiwar ko kyashin aiki komai idan ina yi, yawan shi bai damuna don ni a gare ni yar kauye tashin kauye har ina aikin yake anan bisa ga namu na kauye mai wahala sosai.
Sai dai ita anty ko yaushe cikin yi min fada take wai na dinga hutawa sai dai nayi murmushi kawai idan ta fadi hakan mama kan ce ai gareta wanan ba aiki bane.
Tana matukar bani kulawa ta bangaren ta sosai don tana nuna min kamar cikin mu daya da ita idan tana nuna min so.
Yau ma zaune take falo ta mike kafa saman dan stol din katakon dake gefen kujera wanda ta jawo zuwa gaban ta, dauke da waya take hannun ta tanayi tsawon minti goma da fara wayan ta kamar ba kudi ake akashewa ba.
Sai tv ke ta aiki shi kadai a falon don mama da suke zaune tare gyangyadi take yi lokacin a zaune ba kallo ba, ai dole mama tayi gyangyadi, taji sanyin AC na ratsa mata jini yanayi ya sauya sai barci duk inda ta zauna.
Ferfeson kodan kaza zalla tace nai masu yaji kayan yaji don hadin kauye nai masu take kamshi ya gauraye ko ina na gidan .
Na zuba mata shi mai yawa tare da dorawa ga ture da goran ruwa sai dai ba mai sanyi ba nazo gaban ta inda take waya na aje mata kayan abincin naji tunda safe tana cewa tana son cin bread da shi ferfesuf irin dai kwazaban mace mai ciki abinda, bai yuyuwa tace shi take so.
Sai ganin na hado mata shi komai kamar yadda take muradin son cin shi kusan kwana biyu ke nan da take marmarincin hakan.
Ta manta waya takeyi sai cewa tayi kai masha Allah Ramana Allah yai maki albarka duniya da lahira ya kare ki daga sherin masheran ta.
Yanzu abinda nafi kusan wata ina son nayi na zauna naci kamar may shine daga kinji na fada kika hada min yadda nake so.
Murmushi nayi ina gyara aje mata kayan abincin da kyau take cewa anya Ramana idan mutanen gidan nan suka dawo zasu gane ni kuwa wanan irin kulawa dana samu a yan kwanakin nan haka.
Sai da taji dan murya cikin waya yasa ta tuna waya take tun farko abincin dana shigo mata dashi ya katse ta.
Daga cikin waya ake tambayan ta wacece take zukawa albarka haka ne wai ?
Tace bari kai dai heartbeat sister na da suka zo da mama ne ta hada komai na gidan nan ta hutar dani daga barci sai ci sai wanka sai ko kallo.
Yace good da kyau amma ko na gode mata wallahi tayi min maganin ki tace wallahi kamar ka sani, kafin duk na gama barci na, zan samu komai is ready yarinya karama bata jin nauyin jikin ta ko kadan.
Yace kai amma wanan yarinyar ta kyauta min wallahi ki min godiya gurin ta tunda ta kula min da bugun zuciya na.
Dago kai tayi inda nake duke ina zuba mata ruwan miyan a plate tace Ramana kinji ana maki godiyan kula dani ko ?
Murmushi kawai nai mata na fara kokarin zubawa mama nata na mika mata, lokacin kamshi ya tayar da mama dake zaune tana gyangyadi a saman kushin.
Yaran da yake weekend ne na sauko dasu cikin hikima nazuba masu suka zauna ci don abinci bai damuwan su sai dai kayan kwadai kawai shine abincin su.
Ganin Nasir yaki saukowa yasa na diban mai nashi zanje nakai mai murya anty ne dake shan ruwan miya da cibi take tambayana da cewa wanan na waye ?
Cak na ja guri daya na tsaya tare da juyowa gare ta da hannuna dake dauke da kayan plate dana shirya.
Nace anty na Nasir ne yana kwance bai taso ba shine zan kai mai nasa a dakin su.
Tace cikin tabe baki Allah yasa ya karba waban yaron halinsa sai shi wallahi ya faye yawan bakin rai zakace bani na haife shi ba.
Ni dai juyawa kawai nayi zuwa dakin koda na shiga dakin yana kwance rub da ciki da littafi a gaban shi yana rubutu a ciki.
Abincin na aje na dawo gefen shi ta gaban shi na zauna na dan shafo kan shi nace Nasir tashi kaci abinci kaji rana yayi.
Ban ci yace batare da ya dago kai ba nace haba Nasir ka tashi ko kadan ne kaci kaji kada mummy tai muna dariya dama tace min bazaka ci ba nace idan na baka zaka ci don ni abokiyar ka ne.
Dago kai yayi ya kalleni sai ya duka yaci gaba da abinda yake a littafin, nace ni kasan duk cikin ku nafison ka don halinka na da kyau nasir baruwan ka da rigima.
Kaga ko dole na soka na kuma damu dakai gaka yaro mai kirki da kai ko anty ma ta fada min kana da kirki sosai shiyasa take son ka ita da daddy.
Sai ya sake dago kai ya kalle ni nace cikin daga kai hakane yace ba ai kazanta ba ga abincin ?
Banyi magana ba sai bude mai plate din nayi kaman mai tunane sai naga ya mike zaune tare da jawo plate din a gaban shi ya dan diba kadan yakai a bakin shi sai ya fara danci a hankali amma hankalin shi na wurin littafin shi.
Ruwan da nazo dashi na tsiyaya mai na mika mai ya karba ya dan yasha.
Ina zaune tare dashi ban daga ba har sai da ya turo min plate din a gabana a raina nace kai lalai maganan Anty ne wanan yaron akwai miskilanci gare shi.
Na mike tare da kwashe kayan nace dashi na gode Nasir ya bini da kallo har na fice.
Ina fitowa da kayan zan kai kitchen ta bini da kallon tace ai na fada maki ba zaici ba daga inda nake tsaye nake cewa da ita yaci.
Na shige da kayan sai dana wanke su komai da aka bata ina yi ina tuna kalamin Nasir watau kazan ta na cikin abinda bai so ke nan yaro dan kimanin shekara shidda wai yasan kazan ta haka.
Sai da na gyara komai na fito daga kitchen din na nufi daki direct gurin kayan Nasir na nufa na gyara mai komai nashi tsab yanayi yana kallo na.
Na fahinci rashin hayaniya hhalin yaron ne haka hallita ne mai haka Allah yayi shi amma ko ma maye a sannu zan gane komai nasa.
Abincin dare na girka nagama da wuri na sa a kula ganin yaran na waje suna lesson yasa nace da Anty nima ina son zuwa na saurara.
Anty tace kaman kin shiga raina dama ina son magana da lesson teacher din akan ki don nasan karatun kauye ba wani waya ta dauka kafin na fita tai mashi bayani a kaina.
Cikin sati daya na fara fahinta da yake na dan san wasu abubuwa dama don haka ban sha wani wuya ba gurin fahintan karatun.
Gashi dan zamana dasu na fahinci halin ko wani yaro ina kuma jan su a jiki sun sake dani sosai.
Wanda hakan na fahinci yana matukar yiwa anty dadi a ranta niko a guri na naga ba komai ba ne hakan don tafi haka a gurina ni.
Banda abin su na masu hali ni banga wani aiki da take yawan cewa yai min yawa ba amma gashi ita ko wani lokaci sai gode min takeyi.
Sosai yaran suke sake jiki dani gashi har Nasir na dan fahinci halayen shi haka yasa yauma tun dawowan su na fahinci yaron bai jin dadin jikin shi amma ya kasa fadawa kowa sai kwanci yake yana mika.
Mun dawo lesson nake cewa dashi Nasir bari na hada ma ruwa mai zafi ka gasa jikin ka dashi bai ce dani uffan ba har na hada ni da kaina nai mashi wanka na gasa shi da ruwa mai zafi na shirya shi har da robb na shafa mai na rufe shi da bargo.
Na fahinci yaji dadin yadda nai mashi don naji ya sauke ajiyan zuciya dakin anty na nufa don karbo mai magani.
Na tura kofan na shigo da sallama tana zaune saman gadon ta ta baje kanta babu dan kwali akai.
Tana gani na take cewa dani cikin murmushi maman yara kin samu kanki ko kin gama komai.
Nace eh anty yanzu ma nazo ne in da magani ki bani naba Nasir.
May ya samay shi kuma nace ina ganin zazzabine ke dan satan shi amma ba wai ya fada min bane nan dai nai mata bayanin komai.
Tace wanan yaron sai kinyi hakkuri halinsa sai shi wallahi don ni halinsa na rasa ina ya samo shi.
Ta nuna min inda magani yake na miko mata tace Allah yasa yasha don miskili ne wallahi.
Murmushi nayi nace haba anty ba kudai fahince shi bane amma yana da saukin kai ai idan abin shi a sannu.
Tace ai yanzu kunfi kusa dashi Allah yasa dai ya sha maganin don bai son magani sam.
Nashiga dakin na samu yana kwance yadda na barshi da farko na dafa goshin shi jikin ya dan yi sanyi a lokacin ya bude idanuwan shi yana kallona.
Nace Nasir dina tashi ga magani ka sha kada jikin ya matsa ma sai naga ya ya mutsa fuskan shi nace ko na jika mane ?
Sai ya gyada min kai alaman eh yana son haka na dawo da cup da ruwa a hannuna a gaban shi na jika na nasa spoon na juya na bashi sai ya karba yasha yana ya mutse fuskan shi na bashi ruwa yasha.
Ina gyara mai kwanciya sai ga uwar tasu ta shigo dakin tana tambayan yasha ko akai shi asibiti yaga likita nace ya sha anty.
Matsowa tayi ta zauna a bakin gadon da yake kwance sai take bin dakin da kallo komai na dakin tsab dashi.
Tun dai gurin kayan Nasir komai a natse yake tace dani kai ashe ba karamin aiki kisha ba dakin nan ne haka Rama ?
Nace kin san zama da kazanta ba kyau anty gashi yara ne sai anyi hakkuru ana gyara masu dakin nasu.
Kakarin amai yaron keyi yasa hankalin mu ya koma gare shi kama shi nayi amma kafin na dago shi har ya bata min jiki da aman .
Nan uwar ta haushi da fada tana cewa haba Nasir wanan sakaci ne ai zaka batawa Anty jiki da amai kuma ni ba batun kaina nake ba sai kokarin kamashi muka shiga bandaki yai amai sosai a ciki na gyara shi muka fito har lokacin tana zaune inda muka bar ta.
Nace bari na canza mai zanin gado tace haba goge gurin kawai ya kwanta mana.
Nace bari dai na canza mai tunda wanan din ya baci yaron cikin san murya da nuna fushi a fuskan shi yace kai mummy please go now.
Tace cikin dariya dama abinda yake so ke nan shegen tsabta gare shi kaman ba karamin yaro ba.
Sauran yaran ne suka shigo dakin suna cewa anty is time for prayer mun zo muyi sallah ne tare da ke nace tau ayi alwala.
Tace masha Allahu ashe har jam,in sallah ake a dakin lalai an samu ci gaba.
Suka ce anty ta fada muna cewa idan bamu sallah za, a kona mu ne wai da wuta.
Tace gaskiya ta fada maku oya aje zuwa alwala kafin anty tazo nan suka shige bandaki kafin su fito na fitar masu da hijjab din su.
Anty ke cewa idan mun koma wancan gidan zakuji dadin shi don yafi wanan girma sai dai aikin zai karune don haka nace a samo min wata yar dattijuwa mai dan dama don akwai dakuna da yawa sosai a kowani part gidan babbane kwarai.
Nace cikin mamaki anty yakuma fi wanan girma da kuk ciki tace babban gidane sosai Rama sai in kin gani zaki sheda .
Ba karamin kudi ya kashe ba gurin gina gidan don har ginan yaso ya taba mai aikin shi da kasuwan cin shi don mutane nata magana akai.
Nace ashe harda babban gari akwai tsegumi kamar mu kauye tace inane babu gulma yanzu haka duniya ya koma fa.
Ranan itama a dakin mu tai sallah tana kallo yadda muke sallah da yaran sai sun kalla sun ga abinda nayi zasu kwaikwaya suma suyi hakan.
Muna gamawa taji mun fara karatu duk sun haye min jiki na amma haka muke karatun tai mamaki jin har mun kai kulhuwallahu da yaran don tare muke hadda dasu da baki.
Abin yai matukar bata sha, a take cewa lalai munyi kure dole a samo malamin mai koyar da addini koda da dare ne sai yazo a dan taba.

****** ********* ******
Fitina yakai fita don Jatau ya saka mama da baba a gaba daya samu labarin bani garin.
Haka magana har takai gidan maigari dole sai da aka kira mama taje da kanta.
Nan dai ya koro bayani mama tai tsuru tsuru sai kamay kamay takeyi tarasa na cewa gashi babu kudi don har kudin sadakin ta kashe wai tayi sayayya dasu na aure.
An basu sati biyu kacal su kawo mai kudin shi ko su dauki hukunci kan ta nan suka bar gurin kan wanan magana.
Suna dawowa gida ta saka baba a gaba kan sai dai ya tafi birni yazo dani a daura aure akai ma jatau don bata san inda zata samo mai kudin shi ba cikin sati biyu.
Yana gama sauraren ta yace amma kina da wani magana ni ina zanje cikin kano na dauko Rahama ?
Altine ce tasan inda ta kaita kuma suna can tare ban san wanda zan tambaya inda suke ba yanzu don ba wanda yasan gidan yan uwan nata.
Hankalin mama ya kara tashi sosai har gurin Inna ta taje cikin kwantar da murya take cewa a tsaya a fahinci juna kada abin yakai ga bacin rai.
Inna tace rai shi ya dade baici ba ita ko kano bata taba zuwa ba balle ta ce tasan inda muke.
Su dai da suka ci kudin shi sai

Please Login or Register in order to submit comment