Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Nasan bakya jin dadi amma ki kara tausayawa kanku please badon ni ba for the sake of our baby please.
Idanuwa na na dago sun ciko da hawaye nace yaya ina son ci amma ko naci din fitina yake zama min nai ta amai sai na fitar da abinda naci nake dan samu lafiya.
Ya dora kanshi saman goshina ta yadda muke iya shakan nufashin junan mu.
Yace sorry my baby nasan kina wahala wallahi dada halin karban ciwon nan a hannuki da na karba maki kin huta ke ma.
Hawayen da nake dannewa ne suka silalo daga idanuwana a hankali.
Yasa hannu ya goge min yace ko bakya son na tafine Fatima?
Sai na barsu mummy da sagir su tafi su kadai na zauna nai jinyanki da kaina.
Nace cikin kada kai tare da bude bakina da kyat nace no yaya Baba yafi bukatan ka a hanlin yanzu.
Tausayin ka kawai nake jin irin yadda rayuwa yazo muna cikin wanan dan kankanin lokaci haka komai ya jagule a lokaci daya.
Yace cikin dan murmushi tare da rugomoni zuwa jikin shi da kyau yace duk bawa yana da tashi kalar jerabawan a kullun don haka wanan wani sabon gwajin Imanin bawa ne yazo muna.
Ki kula da rayuwan ki don likita ta fada min kina matukar bukatan hutu sosai saboda kalar mahaifan ki ba mai daukan wahala bace haka.
Nace insha Allahu yaya zanyi yadda kace Allah ya tsare min kai a duk inda kace yace amin cikin dadin rai.
Yace Fatima wanan baby ya wahal da maman shi da yawa udan yafito ashe bazan yi punished din shi ba kuwa?
Dariya nayi dama shi yake son ji gare ni kafin ya tafi nace ni har cewa nake a cire min shi na huta wallahi.
Sai naga ya sake ni ya lame kwance saman gado yana fitar da numfashi tare da furzo iska daga bakin shi.
Yace Fatima ko bakya son nawa ne da gaske da har kika iya furta wanan kalman haka a gabana ?
Nace haba yaya kaima ai kasan ina son ka wahala dai ne yai min yawa wallahi yaya.
Yace to kiyi hakkuri please ki haife min shi nai maki alkawari baku kyakyawan kulla dake da ko maynene a tare da ke insha Allahu nace naji yaya.
Kudi ya ciro masu yawa yabani yace karbi wanan ki boye a gurin ki don ban san abinda baya zai yi ba.
Nace ni may zan saye anan wanda akace zai kwana biyu a cikin asibiti yace karbi dai ki rike a hannun ki in case zai maki amfani.
Ya rugomayni na dan tsawo lokaci ya mike yana cewa zamu tafi nima kokari saukowa nake daga saman gadon da nake kwance.
Ina kuma zaki tafi na dan marairaice nace ina son ganin tafiyan baba ne yaya.
Ido ya kura min kamar zaiyi magana sai kuma ya mika min hannun shi alaman nazo mu tafi tare muka fito bayan na saka dan silifas a kafana tare da saka hijjib dina.
Tare muka fito daga dakin yana rike da hannuna nan naga kowa na gidan mu yana gurin maza da mata manya da yara.
Idanuwan su akaina har muka karaso suna gaisawa dani bai saki hannu na ba har lokacin muna tare muka shiga inda Baba yake kwance harkaf an shirya shi kamar ace ya tashi ya tashi.
Har bakin gadon muka karasa yaya yadan duka daidai kan shi yace Baba ga Fatima tazo tai maka sallama.
Yadan jawonin zuwa kusa da Baba nace Baba Allah ya tsare hanya Allah ya baka lafiya ka dawo cikin mu lafiya.
Ikon Allah sai kawai baba ya dan bude idanuwan shi a hankali wanda sunce ya kwana biyu bai bude idon shi ba.
Yana bin mu da kallo a hankali na kara cewa Baba Allah ya baka lafiya ka dawo ka dauki jikan ka da hannun ka.
Sai ya dan sake murmushi a hankali wanan yasa kowa dake gurin jin dadi sosai har likitan dake tsaye yana gyara shi yace gaskiya da za,a samu irin wanan da yake so a tare dashi ko yaushe za,a samu improvement sosai ga lafiyan shi.
Nace muyi addua kafin a wuce nan na gyara na dinga kwararo mashi adduoin samun lafiya ana karbawa da Ameen.
Muna tsaye aka fito dashi aka saka shi a ambulance din asibiti zuwa airport.
Sai da aka rufe motar yaya ya dawo har inda nake bai damu da,wai mutane suna gurin ba yai hugging dina a jikin shi yana dan bubuga min baya kamar yana lalashi na tace be strong Fatima Allah ya baku lafiya.
Ya juya ya tafi kowa sai kuka yakeyi don yadda aka fita da baba ko mutum baida Imani sai ya tausaya mashi.
Da gata na kwato bawa daga hannun Alah da gata ya kwato Baba cikin wanan halin rayuwan da yake ciki a wanan lokacin.
Gaba daya diyan shi yan uwanshi abokan arziki jikoki saraikai duk suna gurin tsaye cikin tashin hankali a lokacin.
Rahama tana gurin da iyayyenta a gaban idon ta komai yafaru tana kallo.
Wani kishi ya rufe mata idon ta don ganin yadda yaya yake wani jiji dani kamar diyar wata da wani.
Tace sai tayi magani na sai ta mayar da wanan son tsakanin mu ya koma kiyayya watarana a cikin ranta take zancen ta.
Uwarta ma kishine ya rufe mata ido suna hanya take magana cewa jifa yadda yaron nan yake wani jiji da yarinyar nan.
Ai don dai baki tare dashi ne idan kina gidan wane ita yar talkawan tsiya kawai.
Baban yace ai barshi da gaiyya zan daura masu aure inga yadda zai yi da ita idan nakai mashi ita gidan shi.
Muna kallo suka fice daga asibitin suka barmu nan aka fara watsewa daya bayan daya ana mai fatan samun lafiya.
Na kalli duk taron nan watsewa zasuyi su tafi su barni a cikin asibitin ni da Iyya kawai .
Sai naji wasu hawaye sun zubo min Nafisa ta kama min hannu tace kada ki damu matar yayana Allah na tare da ke.
Tare da ita muka koma dakin da nake bayan nayi sallama da mutane mama da maryam da mijinta ne suka biyo ni zuwa dakin.
Sun dan jima a gurin mu sukace zasu tafi sai dai da safe idan sun dawo kuma insha Allahu.
Nafisa tace ita yau a gurina zata zauna mama ta zaci wasa takeyi sai da tace Allah maji yau a nan gurin Fatima zan kwana na debe mata kewan yayana.
Nan mama ta tafi tabarta sai dai mama bataso haka ba don tasan halin Nafisa na watsewa.
Amma batai komai ba wallahi sai hiran da mukeyi akan matsalan baba kawai da zamu kwanta ta hau dogon kujera iya tasa bargo a kasa ta kwanta sai safe.
Washe gari da muka tashi Nafisa bata tsaya an kawo abin karyawa ba ta wuce gida.

****** ********* ******
Sun isa Germany da baba lafiya an kuma duba lafiyan shi har ana samun sauki sosai suna isa yaya yake kiran layina tare da tambayana karfin jikina.
Ganin an wuce da baba yasa yaya Ahmed fitowa daga maboyar shi ya na komai nashi normal.
Sun buga suna fadawa sadauki fitowan shi yace abar case din har ya dawo don kotu ta fadawa dan masani cewa bai da hujjan tayar da maigida a gidsn shi sai ya samu lafiya an yi sharia.
Sadauki baya son ayi maganan kan zancen sayar da gidan nasu na gado da akayi duk da zancen ya karade gari anji labarin abinda Ahmed yayi wa mahaifin shi.
Mama Asiya hankalinta yai matukar tashi yadda taga kowa gidan ya tsane ta ita da danta.
Don laifin Ahmed ya shafe laifin duk wani laifin yaron dake gidan gashi Alhaji bai ko yarda ya gaisa da ita a waya.
Ko yana waya akace ga mama zata gaida dashi zai kashe wayan yaki dauka.
Balle ga mummy kusa abin nema ya samu dama ba shiri a tsakanin ta dasu ko kadan.
Duk da baba yana asibiti cikin halin lahulai amma idan mutum ya shiga gidan zai ga kamar hankalin su a kwance yake.
Irin yadda suke busha shan su agidan ba wani damuwa a tare dasu a lokacin.
Ga wani shakuwa da yashiga tsakani na da Nafisa yanzu don ko wani lokaci tana gurina a asibiti muna tare.
Wani lokaci anan kawayen ta ke samun ta nan zasu wuni suna debe min kewa.
Banda matsala dasu wani lokaci idan suna hiran busha shan su a gabana nakan ce haba anty kamata yayi ace cikin maneman ku ku cafke daya ku aura.
Nura kance ke kaunata nifa mijin ki nake so na aura nakance aiko danaji dadi anty idan har zakiyi aure ki zauna ba sai mu zauna lafiya ba.
Kin sanni na san ki kinga ba fada a tsakanin mu sai so da kauna mu rike mijin mu tsakani da Allah.
Nuriya wallahi idan kina wanan maganan zamu sami sabani sosai wallahi Raiha ke fada mata haka duk lokacin da tai irin wanan magana.
Nafisa kuma takance may zaiyi da honko haka may ya rage jikin ki baya cus kin sha burga kamar rijiyar kwakwara da ke.
Nace ba komai zamu gyara ko anty Nura ai mace mai gyara bata baci ko ?
Raiha takan sha toka tace please abar wanan zancen bata so su ko watace sukaji mijina yana nema sai inda karfin su ya kare akai.
Tace Fatima kin muna fa wata matar aure ce zata sake jiki damu haka abinda ake gwada muna kyama keko kin muna rikon tsakani da Allah kamar wasu yan uwan ki naji fa kika mayar damu.
Yan uwan mu ma naji yanzun haka basu hurda damu don kaaai wanan halin da muka tsunci kan mu a ciki.
Mutane suna manta cewa ko su Allah yana iya jarabtan su a kan haka?
Duk lokacin da ya tashi yin ikon shi a kan mutum na tabbatar da yan gulma suna fadawa mijin ki kina hurda damu haka amma sanin koke wacece yasa bai damu ba duk dai yana halarci ne akan yar uwar shi dake cikin mu amma duk da haka Fatima kunyi muna wallahi.
Nan zamu wuni da su ai ta shiririta suna matukar bani tausayi ina yi ina masu gyara.
Yau ma sunzo mun jima muna hira dasu sosai har barci ya kwashe ni na barsu da Iyya suna hira sun sayo nama mai zafi da drinks sun baje suna ci.
Amira ne tashigo dakin da nake kwance wanda yanzu ya zama min dakina na komai.
Suna gaida ita amma,sai wani basar dasu takeyi sukaci gaba da harkan su kawai.
Bakin gadon da nake kwance ta karaso tana tayar dani daga barcin.
Iya da Raiha ke cewa haba kin san tana son hutu barta mana tai barcin ta kada ki tayar da ita.
Tace waye zai hanani tayar da ita Rabin dan musa ko wa wai takai hannu ta tabani na bude idanuwana.
Ina kallon ta nace anty kin shigo ne ashe tace a wulakance may wa yan nan sukeyi a nan ne haka ta nuna su a wulakance.
Sai sha,anin su sukeyi kamar basu san da ita ba afurin ko tanayi ma ba wanda ya kulata.
Na dan kakaro murmushi a fuskana nace anty kawayen anty Nafisa ne fa.
Tace and so what Nafisan may can kuma wai kinga bani son na kara ganin su a tare da ke kinji na ffada maki ko?
Tace sai dai ban sani ba ko kema harkan taku dayane dasu don banza bai kai zomo kasuwa.
Wasu hawaye suka zubo min nace haba anty cin fuska baida kyau haka wani abu mukeyi banda mutunci da zumunci kawai.
Tai mun wani kallon wulakanci tace zaki gane wallahi Nafisa tace Amira wallahi yadda kike da Fatima nima haka nake da ita don haka baki isa ki rabani da ita ba don bakece kika hadamu ba.
Tace yanzu ko da yake ba mamaki tunda naga yazama dan uwanku don abin hannun shi ai.
Tajuya tare da yi min wani kallon mamaki na wullakanci tafita daga dakin.
Tana futa tun a haraban asibitin ta kira dan uwanta cikin fada take mai batanin karya da gaskiya.
Yace Amira badai zuwa kikayi kika tayarwa Fatima da hankali ba tana fama da kanta ba nan tace don may zata dinga tara wa yan nan yan iskan haka tare da ita.
Yace kin san halin Fatima fa Amira bazata taba bari tayi wani abin asha ba insha Allahu a rayuwan ta.
Kuma ai don Nafisa suke zuwa tace min nafusa ko yaushe tana gurin ta tana debe mata kewa ke da baki son su zo may yahana ki tare a gurin su.
Lalai ma yaya dama ba yau ba nasan cewa Bintu ta gama dakai gaba daya baka son a fadi abinda tayi don ta shanye ka.
Baiyi magana ba don ranshi yakai kololuwar baci mama ya kira yana fadin daga yau kada Amira ta koma gurin mamatata don bata san zafin ta ba.
Don may zataje ta tayar mata da hankali bayan ta san irin yanayin da take ciki likita yace a bata hutu.
Kai wai may ke faruwa ne haka wai nan dai ta kwashe yadda sukayi da Amira ya fadawa mama komai.
Mama tace ji mahaukaciya kawai Nafisan da koda Fatima ke a gida tana nan like da ita ko yaushe a dakin nan.
Ko ranan da kuka wuce fa a gurin Fatima Nafisa ta kwana tace bazata dawo gida ba zata tsaya ta debe mata kewa.
Yace balle zaman Nafisa da fatima Allah ne ya hada su ai maji.
Mama tacs kuma tun yayatana fada har ta gaji yanzu ta daina ta saka masu ido tsakanin su don waya sani ko hakane zai zama silan shiryuwan ta ma ?
Nan dai sukayi magana sosai ta kashe wayan tana jiran dawowan Amira gidan.
Mummy dake kusa dashi taji fadan da yakeyi tace kai Amira ma dai ita fa bazata iya tsayawa tayi yadda ya dace ba Fatima da yanzun take son wai raba tsakanin Nafisa da Fatiman.
Zaman Fatima da Nafisa fa yakawo sauyi sosai yanzu a rayuwan Nafisa fa don yanzu kan zaman Fatima a gida zata iya kwana barkatai bata fita waje ba.
Aiko wanan abin sai ace abune na dubawa sosai wallahi tabar irin wanan cin fuska haka baida kyau ga dan adam wallahi.
Baba ta najin su wanda yanzu bakin shi ya dan fara budewa yake cewa Fatima Fatima ai alheri ce a cikin zuria ta wallahi.
Amira na shigowa gida zata fara fadawa maji mama tai cikin ta da fada sosai har sai da ta raina kan ta a lokacin.
Ta shige tana cewa indai kan Bintu ne wallahi bazan sake saka kaina ba a al,amarinta da yardan Allah kuwa tashige ciki abinta.

****** ********* ******
Amira na fita wasu hayen bakin ciki suka zubo mata nace yanzu ni may laifina kuma?
Idan naki Nafisa kuma zagina za,ayi ace bani son dangin mijina balle ni Nafisa tsakani na da ita yanzu sai hamdala kawai.
Duk da ta girmay ni amma idan nai mata magana takan daina abinda takeyi a lokacin.
Amma may zai sa Amira tace wai kila harkan mu daya dasu bayan ta san koni wacece takuma san halina din.
Yayan ta ma ya ganni dasu bai ce komai ba don shine ta jawota gare ni .
Allah sarki yaya sadauki mutumin kirki mutum mai adalci wanda ta san ya kamata .
Muryan su naji suna fadin sister indai don muna hurda dake zamu jawo maki matsala zamu daina zuwa gurin ki gaskiya.
Nace akan may anty wanda ya ajeni baiyi bakin ciki da zamana da ku ba sai don anty tazo da wani zancen ta can na daban.
Nace ba inda zaku idan dai ba maigidan da kanshi yace min bai son hurdana da ku ba.
Wayan shi ne ya shigo a lokacin jin ina kuka yasa shi cewa Amira tazo ta bata maki rai ko?
Yace ina Nafisa take nace mai gata nan yaya yace bata waya na mika mata wayan nace yaya yana magana da ke anty.
Ta karbi wayan daga hannu na yan uwan suka tsura mata ido don son jin may zai fada mata a lokacin.
Mun dai ga tana cewa ai ba komai yaya duk abinda tai min yar uwata ce ita tace ba komai komai ya wuce ai don badon ta muke zuwa ba ai dama.
Sukai sallama ta miko min wayan ya tambayi jikina nace naji sauki ni so ma nake a sallamay ni na koma dakina wallahi.
Yace sallama Fatima likita yace min sai kin haihu zasu sallamayki fa don bazasu bari ki fita asibitin nan ba hakana.
Banji dadin wanan zancen ba ina cikin asibiti har tsawon wani lokaci ni wani irin ciki ne dani haka wai ?
Gashi muna batun fara exam haka nake karatu a asibiti sai idan lokaci yayi zasi yarda na tafi na zana koshi tare da wata nurse zamu tafi suka ce.
Yadda suka fada ko hakane haka zan shirya da safe yaya bashar yazo ya dauke mu zuwa school dani da,wata nurse da aka dauka haya don dubani ba dama nayi wani dogon motsi dana gama zamu juyo zuwa asibiti tare da ita a sauke mu.
Bai tafiya gida sai yaga anbani magani na kwanta zai bar asibitin har na kare exam dina da mukayi.
Gaskiya yaya bashar mutum ne don yana bani duk wani kulawan da ya dace wanda zai sa banji kewan mijina ba gurin kula.
Haka zai kawo min maryam mu wuni da ita muna hira sai dare sanan yazo ya dauke ta.
Mama ma takanzo sosai kuma abinci dare da rana yana saman hanya ana kawo muna duk abinda muke so.
Ba laifi don yanzu da cikina yake wata shidda da yan kai saura kiris ya cika wata bakwai ina dan iya cin abinci kadan.
Sai dai ba mai yawa ba don idan har naci mai yawa ranan sai na fadawa aya zaki gurin wahala.
Haka dai nake zaune Iyya tayi min halarci matuka a rayuwan na don komai itace ke min shi iyakana naiwa kaina wanka kawai.
Bayan shi duk wani abin bukata na itace mai aiwatar dashi da kan ta zatai min komai.
Yan uwa sai faman zarraiya suke zuwa gurina duba ni zuwan Baba na biyu yana duba lafiya na a,asibitin.
Haka ma a bangaren mamana saida sukayi mota daya ita da abokan arzikin ta da yan uwa sukazo duba ni.
Don haka ban da wani damuwa a tare dani sai na kadaicin mijina a kusa dani kawai zance yana damuna.
Acan ma Germany ya wuce gurin buga wani wasa da akayi mai zafi inda kuma team din su na basilona da yai ma,wasa yai nasaran lashe wasan da suka buga.
Ba karamin kudi ya kwaso ba sai dai bai dawo gida ba ya koma gurin su baba asibiti.
Baba yanzu ya dan samu lafiya don likita yace zasu iya dawowa dashi nan da sati biyu masu zuwa idan an tantance lafiyan jikin nashi da kyau.
Sai kuma ga,wasa ya taso mai zai tafi arabian kingdom ya bufa,wasa wanda ake tsanmanin zasu samu makuddan kudi idan har sunyi nasara ga wasan da zasu buga.
Jirgi ya samu ya kammala komai akan tafiyan su Mummy da baba sai yaya sagir da zasu dawo gida.
Ya basu kudi kowa ya sawo tsaraban da zai zo gida dashi inda,zasu dawo tare suka fita dashi ya kaisu sukai sayayya inda yaya sagir ya kwaso laptop da kudin shi zaizo dasu ya,sayar itako mummy kayan yaranta da,wasu abubuwan anfanin ta ne ta sayo acan kasan.
Ranan da zasu dawo kowa yana cikin farinciki da dawowan su gida anshirya ma dawiwan baba din sosai yanzu.
Muna asibiti labarin dawowan shi ya riske mu sai dai ance bari dayan baba bai aiki gaba na ne ta yanke yafadi ras.
Amma Rukaiyya tace min sai dai gaskiya idan kin ganshi ya samu lafiya sosai wallahi.
Tun bayan fitanta nake jin marana yana dan yanka min kamar zanyi period nake ji.
Sai ban damu ba don nasan tunda ina da lalura mai zai tayarwa kaina da hankali dashi.
Wasa wasa ban daina ji ba har cikin dare sai barci ya gagare ni ina kallon iyya da ta samu barci tana barcin ta hankalinta a kwance abinta.
Jin mara din ya matsa min ne na mike zaune aiko zama yace bai sanni ba can da naji wani iein ciwo na sauko na kama karfe gadon na dan nisa tare da murde bakina don dan zafin danaji a lokacin.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,

IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH YA SAKA MUNA,,,


Kukan dan jarin da ya fado ne ya saka Iyya dake kwance dan bude idon ta a hankali.
A lokacin da nake fadin Iyya Iyya tashi ki gani abin cikin cikina ya fito Iyyah ko na haihu ne ?
Tamike tana fadin subbahanallahi ikon Allah uwar dakina kin sauka ne ?
Sai kuka yaron dan karami dashi sosai yake tsalawa duk Iyya tabi ta rude taje inda ake kunna wutan dakin ta kunna tana cewa.
Kinko haihu wallahi uwar dakina amma sai dai killa bakwaini ne kika haifa don yaron yai kankanta da yawa.
Ta dan taba yaron yakara tsala ihu tace namiji ne sai dai bakwaini ne da sauri tafita daga dakin zuwa inda nurses suke kwana ta kira su.
Sai gasu da saurin su sun shigo tare da ita taimakon gagawa suka fara ba yaron nan suka rabashi da uwar tafiya Allah yasa akwai reza da na anty Raiha ta sayo min sai ta sayo parked din shi gaba daya.
Dayar nurse din taje dakin doctors takira likita mace wacce tai adimin dina a,asibitin ranan ita ce akan duty.
Tana zuwa ta danyi dube duben da zatayi ta tambaye ni banjin komai na fada mata komai bana ji.
A cikin daren akaiwa yaron wanka nima nai wanka Iyya tace a kira gida ne a fada masu nace tabari harda safe sai a kira gida don yanzu kowa yayi barci hankalin su zai tashi tunda ina lafiya.
Sosai likitan taita gwada yaron tace min lafiya yake sai dai premature baby ne idan da rabo zai rayu insha Allahu.
Nace daga inda nake zaune a bakin gado anty zai rayu kuwa ?
Tace insha Allahu zai rayu ai seven months ne yanzu kike da kwana biyu.
Sai dai da,safe zan so muyi shawara muji idan zai yuyu sai a dan saka shi a kwaba yadan kara tasawa tukun.
Bamuyi barci ba sai da,asuba muka dan runtsa kadan shigowan nurse din dakin ya,samu falkawa Iyya ta tafi sallah ni kuma ina kwance ina kallon yadda sukewa baby din.
Bakwai da yan mintina Iyya tashigo dakin nace ta bani wayana , numban mama na fara kira har ya kusa tsunkewa ta daga da,sauri ba ko

Please Login or Register in order to submit comment