Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

zata shigo dakin tace ai har ina batun shiga na samay ki kada ki tayar dasu da ga barci.
Nace kai haba mama, may zai sa na tayar dasu suna hutun gaji tare da su.
Nace zan tafi mama sai na dawo muryan ta ne naji tana cewa yaki Rahama.
Najuyo zuwa inda take tsaye tana kokarin kwance haban zanin ta data kulle kudi a cikin sa .
Naira ashirin ta miko min tana cewa karbi wanan kyaci tara dashi indan kin tafi can.
Take fuska na ya sauya nace cikin marairaicewa mama da kibar shi wallahi yau ai Inna ta tabani Naira biyar zai isheni na sha ruwa a can.
Tace ruwa kawai Rahama bayan nasan ko karyawa bakiyi ba kika fito daga gida?
Nace dimamay mama laure tace baida yawa don haka su dake gida zasu ci abinsu wai idan naje can ban rasa abinda zanci.
Mama Altine tace shine kuma ita Inna ki ta baki Naira biyar kacal ki sai mai da naira biyar din.
Muryana na tausa kada wani yaji ni nace mama kin san idan tabani da yawa mama fada take mata wai tana lalatani da yawa shiyasa mama ta kafa doka wai Naira biyar kawai za, a dinga bani ya isheni .
Kai amma dai laure takai muguwa wallahi nace mama barin tafi kada na makara yau ina son naga assymbly don na manta yaushe rabo da ayi shi dani.
Najuya ba tare da na karbi ashirin din hannun nata ba nafice daga gidan da sauri tana kirana amma bai sa na tsaya ba .
Koda na isa makaran ta nayi dace da abinda nake son gani ina shiga ana kada kararawan assymbly yau ba duka gare ni zan kuma ga assymbly din mu.
Kowa ya ganni sai mamaki daga dalibai har malamai suna cewa, sarkin late yau lafiya kuwa ?
Sai dai nayi masu murmushi kawai na wuce haka muka zauna nai matukar jin dadin samun darasin safen da nayi yau.
Allah Allah nakeyi a tashi daga makaranta na koma gida na samu anty na yar birni don ni gaskiya ban gajiya da kallon ta ita da yarta mai kyawo.
Har zuwa lokacin tashi ranan saurin da nayi har yafi wanda nakeyi zuwa daukan talla na a kullun.
Na shigo gidan mu da hakki alaman nayi gudu ko sauri a lokacin sai dai may na samu a gidan mu mama lauratu na sana,an fadan ta da ta saba yi idan fitinan ya motso mata.
Duk da har taci ta sude babu mai biye mata indon ta inna tace zata iya kwana tanayi bata tanka mata ko uffan.
Sai dai idan baba yana gida ne wani lokacin zaibi ta kanta suyi ta tonon asiri a junan su.
Wanan haushin da naji tayi yayi dalilin da na fasa shiga cikin gidan namu na dan daka ta ina sauraren ta don naji akan may take fada kuma.
Daga inda nake sauraren fadan nata na fahinci fitina take da Inna na wai akan kudin da aka bani inna bata nuna mata ba taba babana ya dan kara jarin shi.
Sai zuwa can naji muryan Inna tana cewa yaya kiyi hakkuri dan Allah ni bawai na nuna bakece kika haifi Yarinyar nan ba .
Naga kin san da zancen ne tunda boyar Allah nan a gaban ki ta furta cewa ta dauke ma yarinyar nan yin sana,an ta.
Ai fa yanzu sai kiyi kwana nawa ne idan bakin ciki kikeyi dani akan ki zai kare Asiya don wucewa yar gidan Altine mai kuli zatayi.
Kuma kowa komawa zaiyi ga turken shi mai cabo ai har kudin nawa ne da suka rufe maki ido haka ?
Maimakon na shiga yadda nai niyar yi da farko sai kawai naja na juya zuwa gidan mama altine mai kuli.
Tafiya nake kamar banda lakka a jiki Allah ya taimake ni naga kanina zai shiga gida na mika mai jakkar makaranta na nace ya kai min dakin mu.
Da sallama na shiga gidan suna zaune su biyu ga kwanon dan wake da mai da yaji tana ci cikin irin cin abincin su na yan gayu.
Mama altine ne tace a, a yar gidan anty har andawo bokon ke nan nace eh mama cikin kada kaina.
Zama nayi tare da gaishe su naci gaba da tunane a cikin raina wai yaushe ne Inna ta zata samu saukin rayuwa ne agidan mu?
Duk abinda tayi batayi daidai ba gurin mama, damu da ita duk bamu da wani yancin kan mu sai abinda mama laure tace.
Na sauke ajiyan zuciya ina fadi a raina yaushe ne wai muma zamukai ga namu yancin kan ne agidan mu , ?
Jin ajiyan zuciyar dana sauke karama dani yasa hankalin su ya dawo gare ni mama altine da anty sa,ade har suna hada baki ita mama na cewa may kuma ya faru yar gidan anty ita kuma nacewa Rama na duk gajiyan ce haka wai ?
Nace a hankali mama ni halin mama laure ne yake min ciwo ace kullun duk abinda Inna tayi ita a gurin ta ba daidai bane ?
May kuma ya faru yanzu?
Nace mama bakiji haushinta bane har nan gidan wai akan kudin da anty ta bani shi ne Inna nasan tabawa baba kudin ne ga Mama can ta saka inna a gaba da masifa akan may tabashi kufin bata bata ba.
Ikon Allah waiko laure na da hankali kuwa mama altine ne ta fadi hakan.
Nace mama akullun wanan halin na mama ya damu na inna sam bata da sukuni a gidan mu.
Wanda kinga abin har muma ya shafe mu muda ita bamu da incin kan mu ko kadan.
Nan kata tunanen yaushe ne wai muma zamu zauna kamar kowa agidan.
Nace mama fa har ikirari takanyi da cewa sai dai mu zauna a haka mu da uwar mu don bazata zauna tana ganin ita da mijin ta ba wasu banza can suzo su shige mata gaba.
Duk da Inna tana hakkuri da ita kalamanta badu damunta nake gani amma baisa mama ta watsar da wanan halin nata ba har zuwa wanan lokacin.
Wai mama kin kuwa san duk saba, an da nakeyi kudin mama laure ce ke karbe su a gurin Inna da sunan wai zatai min tari ko kuma tace wai ta ara.
Kuma bawai zata biya bane sannan ni har yau banga wani tari da ake min ba agidan.
Wani lokaci idan tace abata kudin na hana don sai yakai ma bamu da jarin da zamu juya awataran.
Data gane ina hanawa yanzu shine take cewa idan ina ganin nai wayo ne na kama kaina don dagani har uwana da uban nawa bamu fi karfin ta ba don haka in ina shiga hankalina mu zauna da ita lafiya nayi .
Idan bazan iya ba wallahi ko yaushe kofa a bude yake mina dagani har Inna muyi gaba.
Anty ce tace kai ashe haka take ina ganin ta a hakan ?
Mama tace wa laure da kike gani bata da dama komu makwabta sai munkai zuciyar mu nisa da ita ake zaunawa lafiya.
Nace muma hakan muke zaman takura da tsangwama a tare da ita kullun sai ta kirkiri sabon jidalin da ta dora akan Inna don dai ayi fitina kawai.
Anty tace kuma shi mahaifin naku duk yasan da haka Rama ?
Nace cikin kada kai kamar wata babba dani yasani mana anty may zaice tunda baya iyayin musu kullun da ita baya kuma jayayya da ita sai abinda tace don azauna lafiya.
Sai idan abin ya ishe shine yake magana kuma maganan ba amfani zaiyi ba ai.
Balle ma yanzu nagane baba yana matukar gudun bacin ran mama sosai sai abinda takeso akeyi agidan mu.
Don kinga kan tallah mu ba yadda baba baiso mu bari mu kama boko da islamiya ba amma mama ta hana.
Don dai kawaiba zauna lafiya a gidan da ita ko kwanaki an kawo karan Lawisa amma mama ra hana yayi magana dole yai shiru ya kyale ta hakana.
Anty tace Allah ya kyauta ni dama zai ban ke mu tafi birni muyi zaman can ki shiga bokon ki yadda kike so daya kyauta min.
Nace wai anty idan na tafi birni na zauna waye zai kulla min da Inna ta ko kudin sayen sabulu kawai ya isheta ai.
Mama tace balle ma laure bazats bari ba dakike ganin ta na tunda ba yayan tane zaki dauka ba.
Ai duk wanan fitinan da kikaji tanayi da ace tare da yarta kike da baza, a ji shi ba sam.
Halin Laure sai ita dubi yadda Asiya ta koma kamar ba ita bace ta tashi a garin nan abin sha, awa ga kowa.
Amma mahaifinta ya hana ta zabi yacs sai malam Abubakar zaiba don zumuncin dake tsakanin shi da mahaifan ta.
Yarinya da gatan ta amma dubi yadda duk ta zuke takoma kamar ba Asiya ba, lokacin da tai yan matancin ta babu wanda zai ganta bai kyasa mata ba.
Yanzu gashi tun auren ts gidan nan dubi duk yadda ta tsiyaye babu komai gajikin ta sai tarin hakkuri da zaman sunnu kawai.
Anty tace mama ashe mahaifiyan ta takwaso gurin kyau ke nan ?
Kai wane ita da kyaun Asiya wanan da bata gyara kai zaikai wata biyu ba kitso kafa ba lalle kamar ba matashiyar budurwa ba da ita ?
Nace kai mama duk wanan gyaran da nakeyi zakice haka ina wanka fa sau uku ko biyu a sati 😆
Dariya ne sosai ya kumshe anty tace kai Rama na wankan ma har sai an kidaya kwanakin yin shi kuma ?
Nace anty ai nayi kokari bakiji har ana yaba tsabtana ba don fa ina da tsabata wasu ke sayen sana, ata sosai.
Dukan su dariya suke min akan maganata niko ko ajikina ban damu ba sai mama ce tace nidai bari na zubo maki abinci kici da wanan bakin surutun naki haka ?
Na gyara zama ina ta kawo min dan wake ranan har da ruwan goran da anty ke sha nasha azatona yana da zaki amma sai naji shi salaf kamar ruwan rijiya.
Ina gamawa na gyatse dama nasan ko naje gida tuwo ne zai tare ni don haka ban rage komai ba harda sude kwanon nayi.
Anty tana ganin haka tace dani ko a karo maki ne idan baki koshi ba nace sai zuwa anjima Anty yanzun kan Alhamdullahi.
Tace oya zo na banye maki kanki nai maki kitson shi duk da take na manta ko yaushe rabona da yin kitso a duniya.
Ina bude kaina saida tai wani irin ihu tace Rama subbahanallahi kanki ne haka nace shine anty yayi yawa ko ?
Tsuki naji taja tace haba Rama kamarki kuma kinkai har secondary ace baki gyara jikin ki sai yaushe zaki koyi gyaran jiki kuma ?
Haka zaki dingayi agidan mijin ki idan kinyi aure ki dinga zama da kazanta yace kina wari.
Kunya maganan ta yabani na tsune kaina akafa nace aure Anty ina nai aure wazai zauna da inna ta yana taimaka mata da diban ruwa da tallah kuma ?
Kinaji na idan kina son mu shirya dake daga yau duk sati ki dinga kitso da kunshin da mama tace idan ba haka ba wallahi wanan kazantan zai sa mu bata dake.
Nace insha Allahu anty zan dinga kitso bani son mu bata dake ko kadan a rayuwana.
Tace dakin kyautawa kanki haka taci gaba da sance kan har wani gari ke zuba a cikin don dankarewan dayayi.
Dama asalin haduwan mu da ita shine yawan gashin da nake dashi.
Watarana tazo garin inna takaini an min kitso ya sauko har bayana taga mun shigo gidan mama Altine sayen mangyada take cewa kai wake wanan fine girl din a kauyen ga kyawon yarinyar na ace a birni kika fito da kinsha gyara yarinya.
Tace zo nan ban mata kiuya ba nazo ta rugumay tana cewa kina so na na kada mata kai alaman eh.
Tun rana muka shaku da ita da zan koma ta saya min biscuit da sweet naje dashi gida amma mama tana gani ta kwace ta rabawa yayan ta lokacin ni kadai ne a gurin inna ta ban da kanne baya na.
Wassh nace don jin zafin kan da anty taja min da karfi tace yaya akayi kuma nace babu komai idanuwa na sun ciko da hawaye da zata gani kila zata barni don akwaita da tausayi sosai.
Tana gamawa ta sa asayo mata clean ta wanke min kan tas dashi sai da naji wani iska yana shiga na sosai acikin kaina.
Mun zauna tafara min kitso ke nan sai ga Rakiya diyar mama tashigo babu ko gaisawa tace to akwadaita mama tana kiran ki.
Nace cikin daure jin zafin kitso kice kitso ake min gani nan zuwa idan angama min.
Tace mama tace tana kiran ki shine zakice wai ana maki kisto ne barin je na fada mata kince bazaki zo ba.
Anty tace bari na sake maki idan kin dawo sai mu karasa ko ?
Nace taci gaba don nasha zafi daya yanzu idan na tafi bazata bari nadawo maza ba.
Ban tafi ba Rakiyan ma bata dawo ba daga sakon har aka gama min kitsona nai wanka wasu kaya daga cikin tufafin ta sun min yawa sosai amma haka tasa na saka su na fito wata shar dani.
Sai da na gama komai na kama hanya na nufi gidan mu nan na tar da balain dake jirana na mama.
Ina sallama tako haukaina da balainta tana fadin mai kwadai baji dadi ba wallahi yanzu don kina isar sa ke kinga gurinci shine na aika kizo kikace ace min bazaki zo ba sai kin gama kwadayin ki ko.
Bari mahaifin naki ya dawo gida yau ai ayita akare don wanan abin baku kadai da uwarki za, a zaga ba harni sai an hada dani an muna suna indai kauyen gane.
Kuma ki tafi ga diban ruwa can yana jiran ki tunda babu bawan ubanki da kika aje da zai debo maki ruwa ai aiki dashi.
Ban tanka mata ba don nasan ko na fada mata yadda mukayi da Rakiya ba yarda zatayi ba.
Kayan jiki na na cire na daura tsuman zanina na fara diban ruwan don nasan idan banyi har inna ranan sai ta yabawa ayya zaki.
Saida na cika mata randunan ta na fara cika na Inna na don ban isa na fara zuba a namu ba naja bala,i kuma.
Ban koyi rabin randan mu ba sai ga Lawisa tafito da roba tana diban ruwan rabi a cikin roba rabi a kasa .
Kasa daurewa nayi nace haba lawisa wanan ai hainci ne idan ma zaki dibane ai ki tara roban dakyau mana amma kina diba kina zubarwa akasa don baki san wahalan diban ruwan ba ko ?
An zubar din ko zaki hanani amfani da ruwan ne kuma tunda wuyanki yai kwari yanzu ya isa yanka don kina ganin kina hurda da yar birni ana hure maki kunne kiwa mutane rashin kunya.
Nace ashe hurda da yan birni isa ne ai ban san kina hassada da hakan ba sai da kikai magana yanzu?
Kafin tabani amsa sai ga mama tafito daga dakinta tsagal tace eyye Rahama lalai kuwa ashe wuyan ki ya isa yanka yanzu yarki kikewa shamaki akan ruwa don ta diba.
Saboda kina kurin kece kika debo ko may ai kafinki fara diban ruwa su suka fara kuma akai amfani dashi.
Kamar ince bako ga Inna ta ba don da wayo na akai fadan ruwa agidan mu wai don may babana yake debowa innata ruwa.
Kuma alhalin ita bata bari yaranta su diban ma Inna ruwa anata randan haka inna zatai ta zama ba ruwa koda kuwa girkin gida ne zatayi.
Tun ranan baba bai sake diban wa inna ta ruwa ba sai dai ta dinga tarataran yaran mutane suna dibo mata.
Tun ban kai munzalin iya jan ruwa arijiya ba dole haka na fara zuwa bakin rijiya wanda yaga Allah ya taimaka ya zuba min har na samu Inna ta dan samu na aikin ta.
Muryan mama ne ya katse min tunane na tana fadan ta da cewa yanzu don kinga kin girma kin iya hassada da kyashi irin na uwarki shine zaki hana ai amfani da ruwan ko ?
Ni dai ban kara magana ba na fita raina bace daga gidan sai magariba na gama diban ruwan a gurguje na shiga naiwa anty sai da safe.
Tana ganina a jiki cikin tsuma babu dadin gani tace yaya haka kuma Rama na ?
Na turo baki gaba nace ba mama bace saida tasa na cika duk kayan ruwan dake gidan mu kuma ban gama ba Lawisa tana diba tana zubarwa nai magana kuma ta hauni da zagi wai don naga ina hurda dake ne nake wa mutane rashin mutunci.
Kai ikon Allah yanzu har nima na samu shiga cikin ran mama daga zuwa na ko ?
Nace ai har yaranta bakin ciki suke da ke wai don naga kin fito daga birni nake lake maki ina kwadayi.
Allah sarki ni may nake baki da zasu ce haka Allah dai ya rufa asiri wallahi shaf na manta da zancen ki da sun ga aikin gaiyya kuwa.
Nafita da sauri na koma gida kada aga na dade inna tai min fada don ni ko tallah naje bani kai magariba koda kuwa ban sayar ba ne.
Sai bayan sallah ishai baba ya dawo daga kasuwan kauye yana jaye da wani dan karamin rago da yasayo daga can kauyen da yatafi.
Baya ya daure ragon wanda ya cika muna gida da kuka irin na dabbobi kowa yasan an shigo da dabba.
Mama tafito daga dakinta tai mashi shimfida inda yake zama yaci abinci ya huta idan ba zai fita ba hiran dare wanda shi ba kasafai yake fita ba don yafi fita ne idan suna siyasa ko wani abu mai muhinmanci a garin.
Bayan ya zauna muka dinga fitowa muna mashi sannu da zuwa wanda zance kusan mu yan dakin mu ne keda wanan halin.
Sai nice nafito karshe don ina sallah koda ya dawo lokacin na gaishe shi na juya zan wuce ne naji Mama tana fadin dama kai nake jira ka dawo tun dazun.
Yace to ai gani kuwa Allah ya dawo dani lafiya cikin ku tace dama akan Rahama ce .
Don dakai da uwarta kun daure mata gindi akan bakuwar birni da tazo don kunga kudi idanuwan ku sun rufe .
Shine take ganin kowa tana iya takawa ta zauna lafiya yanzu wai har na aika don ta samu daurin gindi daga uwar ta tace min wai bata zuwa tana kitsone.
Ni zata gwadawa kitso tunda tun uwarta bata san duniya ba nakeyi a kaina.
Yanzu dai may tayi baba ya katse dogon sharhin data fara cikin tambayan ta ba, asi don baison suyi jidali daita gashi ranan itace da girki a gidan.
Yasan idan yaja zance cikin shi tayi don daren shi ke nan zai kashe a ranan.
Tace ruwa fa zata debo bayan tasan cewa itace da alhakin diban ruwan gidan nan akanta amma uwarta najin amsan da ta aiko min bai sa ta dauki mata ki ba jifa ?
Yanzu ita Asiya da taji abinda tace bata dauki mataki ba akai ?
Tace ta dauka ran yar gwal din ta ya baci ita ma nata ya baci, yanzu ta debi ruwan ko bata debo yar kwal uba ?.
Tace ta debo amma kuma sai rashin mutunci yabiyo baya nan tai muna tas nida Lawisa wai don may tana wahala ana zubarwa jifa wai aikin gidan ubanta ne wahala ?
Ina daga daki daga ni har Inna ta muna sauraren maganan da mama keyi karya da gaskiya .
Cikin bacin rai ya kwala muna kira ni da Inna ta bamu dauki lokaci ba muka fito inda yake zaune.
Tambayan dalilin dayasa Inna tanajin sakon rashin kunyan da na aikowa mama dashi taki daukan mataki a lokacin.
Cikin murya mai sanyi Inna ke magana tana cewa haba malam yanzu don ban da kunya zan saka baki ga maganan yarinyar nan da maman ta ?
Aikuma sai ace nayi rashin kunya kuma baba yace ke nan kina nufin karya Lauratu tai mata ba amsan banza ta aiko mata dashi ba ke nan?
Inna tace ni bance karya yaya tayi ba dakai da ita sai ku dauki hukuncin daya dace akanta basai kun fada min ba.
Au to haka ma zakice ke nan ko ?
Inna tace idan ba haka zance ba ni may kake so nace yar tace tana iya daukan matakin daya dace akan ta duk sanda taso.
Mama tai karaf tace wace ni na dauki mataki abi gari dani ana nazalunci uwa da yar ta don cin amanan dana iya
Sai ranan naji Inna ta ba da amsa mai ingaci da tace uhumm zalunci kan ai sai dai kada a kara don kullun a cikin sa muke raye, sai ranan da mai ramawa zai rama muna idan ba yafewa mukayi ba.
Ai Inna ta na fadin haka da ga baba har mama sukoyo cikin ta da masifa kamar zasu cinye ta danya a ranan.
Wai tayi masu Allah ya isa shi da mama ke nan take nufi akan yar ta na suka sakata gaba da wullakanci kowa yana fadin albarkacin bakin sa.
A take naji jikina yahau tsumi ina ta dan karkarawa daga inda nake a tsugune kamar na tsoma masu baki ga zancen su wata zuciya ta haneni da hakan.
Na rasa yadda zanyi a inda nake yadda ake ciwa uwata mutunci yau akaina gaba daya kwanakin nan baba ya karkare birkicewa akan mama a gidan.
Duk abinda ta fada ya zauna ke nan daram ba canji cikin sa .
Nasan idan na saka bakina ga zancen abin zai kara muni gashi yau alama ya nuna inna ta fara gajiya da halinsu har takai ga fara bada amsa da bakin ta .
Don haka na mike tsam na juya zan tafi daki muryan mamace ke cewa dani ina zaki rasa kunya an sallamay ki ne ?
Bari ta nuna min ta isa mana tunda uwarta ta daure mata gindi inji baba yake fadin haka.
Ke maza shiga daki kada ki dawo gurin nan kinji na fada maki so kuke da ni da ita ku turke mu kuyi muna wankin babban bargo don bamu dagata kuke gani ko?
To bari kuji gatan muni dayara na Allah a gidan nan da duniyan nan kai nagaji da wanan halin cin amana kullun mune dai masu laifi a gidan nan ku bakwa yi.
Idan wani laifi ne ai babu dan da baya laifi ni dan wa nataba kawowa kara duk da urin kuncin rayuwan da ake min a gidan nan ina sa kafa ina takewa daga haka ta juya tabi bayana zuwa daki.
Ranan daga ni har Inna babu wanda yaci abincin dare ba, a ma taya muna balle muci.
Shekaruna da kurciya na bai hanani fahintan ranan Inna tana cikin kunci da bakin ciki akan dalilina.
Daga inda nake zaune takure bakin gadon karfen ta na mike zuwa inda take zaune saman tabarman sallah ta na tsunguna nace.
Nace Inna don Allah kiyi hakkuri duk nice na jawo maki wanan bacin haka da ba don ni ba bazaki shiga wanan bacin ran ba yau.
Batai magana ba sai na kara cewa don Allah Innan mu kiyi hakkuri ki yafe min.
Tace ke nagaji ne da irin cin

Please Login or Register in order to submit comment