Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

******
Sai washegari bayan na,tafi ne sadauki ya uya,shigowa cikin gida a,falon maji ya zube bai jin karfin jikin shi ko kadan sai yawan jin amai da yakeyi.
Yakai awa biyu baiga gilmawa na ba yace maryam maryam daga inda take zaune ta amsa mashi ta mike tazo gurin shi.
Sai da ya dan jima kadan kamar wanda yake wani tunane can ya nisa yake ce mata.
Wai ina yarinyar nan take ne ?
Maryam jin tambayan nashi tayi a bazata mata sai mamaki ya kamata tace wata yarinya ke nan yaya ?
Yace wanan dake nan dakin mana gurin maji.
Tace oho Bintu daidai maji tana shigowa falon ke nan
Tace wallahi ta tafi gida jiya Baban ta aka bugo waya baida lafiya shine ta tafi yace
OK,
Maji tace wa yake tambaya ne wai ?
Maryam tace wai Bintu yake tambaya.
Tace yau kuma lafiya kake tambayan min yarinya kodai wani aikin zaka sata ne?
Yace No ban gata ba dai ne kawai tunda na tashi shiyasa maji tace jiya ta tafi gida mahaifin ta ba lafiya tace anbashi gado a can kauyen.
Yace subbahanallahi a kauye kuma za,a kwantar da mutum ga asibiti a gari.
Tace ba,sai suna da halin kawo shi garin ba Alhaji ne ma da zata tafi yabata dubu hamsi su sai magani tace dashi aka kwan tar dashi din.
So nake ka kara jin sauki sai na roki Alhaji ya bari na tafi nag jikin nashi kauyen.
Don Fatima na da kokari wallahi sosai yarinyar tana da kirki ga dadin zama ai mijinta ya dace wallahi.
Bai yi magana ba sai idanuwan shi da ya lumshe tare da dora hannayen shi saman fuskan shi yai makari dasu.
Bai dade falon ba ya tashi ya fita part din shi ya,shiga yai wanka jin karfin jikin shi yasa shi cewa bari ya fita ya dan zagayo ginan shi yagani don ya kwana biyu kwance bai fita ba.
A can kauye kuma jikin na Baba na gayanan dai ga kaman shi sai dai muce Alhamdullahi kawai.
Haka karama dani, nice komai akace nake kokarin yi ga dan kudin dake hannu na ya,soma karewa,saura dubu uku kawai a hannu na.
Gashi yau tun safe mun rasa,gane kan jikin baba yaki mashi dadi sai nishi yakeyi kawai .
Hankalina duk a,tashe yakw munyi waya da Kabir yace zai turo da sako akawo min daga kauyen su.
Gashi banga dan sakon ba har yanzu kusan karfe dayan rana ake bida a lokacin .
Nafito daga wajen asibitin na samu gurin saman wani dutse gindin bushiyan dake farfajiyan asibitin na zauna, tare da kifa kaina saman gwiwayu na nai shiru ina tunane.
Kaman daga sama nakw jin muryoyin yan gidan mu Maji tana cewa ko wani daki sukw ma ?
Da sauri na dago kaina nace lah mama sannun ku da zuwa ashe kuna hanya tafe ne yanzu.
Tace Fatima kece nan zaune yaya mai jikin maimakon na bata amsa sai kawai na fashe da kuka nace mama Baba kan sai yadda Allah yayi kawai don jikin sai munga kamar yaji sauki sai kuma ciwo ya dawo.
Sam ban san dashi suke ba sai ji nayi yace to may na kuka kuma haka ?
Zaki tari mutane da kuka ki tayar muna da hankali inane dakin da aka kwantar dashi na shiga gaba suna bina a bayan su har muka je dakin da yake kwance.
Baba na yana kwance sharkaf dashi sai nishi yake guda guda suna mashi sannu kafin ma nai magana mama tabawa tace kai Bintu akwai ki da,shiririta wallahi.
Tun dazun ga mutumi yana wahala kin tai kinyi zaman ki baki dawo ba nace mama wanda zai kawo min kudin ne baizo ba har yanzu.
Tace ba Kabir din yace ya basuwa ba shiko mi tsaidashi hakana wai ?
Muryan yaya sadauki dake kallon dakin cikin kyankyami yake cewa wai may sukace yana damun shi ne?
Sai lokacin nace mama ga mamana nabirni da nake wurin ta ta sun zo da yaranta.
Tace ayyo Allah sarki kuna sannun ku da zuwa to a,a hanya yaya sauran jama,an gurin ku,
lafiya suke inji maji, ta amsa mata akaice.
Kara tambaya yayi tare da matsawa gurin Baba ya kura mai ido a ran shi yace ashe agun shi wanan yarinyar ta,kwaso fari haka.
Ga mutun cikin wahala amma farin shi yana nan bai gushe mashi ba natural skin ke nan
Yace wa Babana may ke damun ka ne Baba?
A hankali Baba na ya nuna maran shi da hannun shi da kyat.
Yace shit kun aje mutun haka a kazamin guri haka yana ra wahala ciwo daban magani daban .
Ina likitan yake naji may sukai mai anan don musan inda za,a dora akai.
Yajuya zuwa gurin likitan muka taka mai baya ni da maryam har zuwa,dan dakin da likitan ke zama ko shi a kazance yake gurin.
Yana ganin mu zai fito yafara,washe bakin shi duk goro yasa shi yana fadin ,a,a malam Bintu yau baki mu kayi ne ?
Sun zo duba jikin Baba na ko ?
Yaya sadauki da haushin yadda dattijo kamar wanan ke wasan baki wai yaga yan mata yace don Allah likita muke nema?
Yace mallam ai ni incharge din gurin ka wani kallo yaya,ya,watsa mai yace ina,son in san may ke damuwan bawan Allah nan mahaifin yarinyar nan ya nuna ni sai malamin asibitin yace Fatima Bintu yar ma,aiki.
To gaskiya dai munan in munce ma ga ciwon daka damun shi munyi karya abu gudana dai mun bashi taimako don ya dan samu karfin jikinai kawai.
To idan babu damuwa zamu tafi dashi birni yau aje aga may ke damun shi a can yace gaskiya na hakan yana da kyau sosai walleh.
Ko ina zamu iya samun motan da zata dauke shi ya tambayi likitan yace in anyi sa,a za,a iya samun mota bakin yar kasuwa inda motoci suka tsayi.
Bai tsaya jin komai ko gidiya ba yajuya muka bi bayan ahi sai likitan ke cewa ,a,a Fatima Bintu yau tafiya za,ayi abar mu.
Daga inda yake munajin tsukin shi mudai bamuce komai ba muka bishi maryam ta shiga gaba ina baya sai inda motoci ke tsayawa a kauyen namu .
Munyi sa,a kuwa don mun samu mota daya a layi zasu tsaya dogon jinga dashi yace ko nawane zai biyasu azo a tafi kawai.
Muna zuwa ba adauki lokaci ba muka kama hanya sai sokoto da Baba dake kugin ciwo ba barci kwana da kwanaki gareshi dama mu masu jinyan shi.
Direct asibiti muka nufa dashi yashiga ya fita nan da nan likitoci suka taru kan babana suka,fara binciken matsalar shi.
Sun fara bashi taimakon gagawa tare da,wasu allurai da suke ganin ya dace dashi sai gashi ya samu barci cikin dan lokaci kadan.
Muna nan har dare yana barci sai ga yaya da,wasu samari biyu yan uguwar mu yaran shi ne don nakanga suna mashi abu yace muna mu tashi muje gida jinyan namiji sai maza.
Komai ya,sayo ya masu na bukatan su da ma wanda zasuci jiki ba karfi na mike nabisu muka tafi har da mama ta bawa mukazo gida da ita.




ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,

IN KIN TURA MA WASU DA BASU BIYA BA DON KIN BIYA , ALLAH YA ISAR MUNA AKAN KI,,,,


A LOKACIN MU KE,,,,,



Tun da safe na farka na shirya abin karyawa, da za a kai asibiti na tayar da mama tabawa,ta shirya don mu tafi tare.
Dakin mama na leka har lokacin zaune take saman salayan ta ta azzakar a gurin.
Na fara gaida ita nake cewa mama zamu tafi asibiti mu dubo Baba na kuma shirya abin karyawan su.
Kai ta,gyada min tare da daga min hannu alaman a dawo lafiya ta nuna min post in dauki kudin mota a ciki.
Mun fito lokacin duk su Amirah suna barci abinsu hankalin su a kwance sukan.
Ban san ya akayi ba ko yaga fitowan mu ne, muna tsaye daidai inda zamu samu abin hawa sai ji nayi ana horn daga,bayan mu, ban so juyawa ba amma jin horn din yai yawa yasa ni dan waigawa.
Sadauki ne zaune cikin haddadan motar shi yana saye da kayan wasa farare sai dai wadon dogo ne har kasa haka ma rigan maidogon hannu sai jan da,aka,sa,daga gefen kafada zuwa hannun rigan layi biyu.
Fuskan shi a,daure tamau dashi kaman bai taba dariya,ba ganin ya,tsaya,a gaban mu kuma baiyi magana ba na gane may yake nufi.
Bude motar nayi nace wa mama ta bawa ta fara shiga, ta sa kai tana fadin bissimillahi rahamanin rahim, ina kwana Alhaji ?
Bai amsa mata ba don baiyi tsan manin da shi take ba, sai da ta gyara zama da kyau nima na shiga bayan na zauna tare da rufe marfin kofan mota,
Wani kyatci naji yayi tare da,furzo, iska daga baki irin na jin takaicin wani din nan.
Ya wani fisgi mota da karfi yan mintina sai gamu bakin UDUTH asibitin koyar da,kwararun likitoci na wanan nahiyar.
Na bude wa mama tabawa ta fara fita daga cikin motan nazo zan fita tare da daukan basket din da muka zubo abinci a cikin shi yake cewa.
Yarinya,baki sanni ba har yanzu zaki rena min wayo bakauyar banza kawai ni driver gidan ku ne.
Naji zafi zagin da yai min amma sai na,share don dan ni ya,taimaka muna nakuma zo abin kunya ana jin harshe na sama tare dashi bai yi ba.
Amma badon taimaka wa mahaifina da yakeyi ba da yau ba abin da zai hanani rama zagin da yai min harda cewa gidan mu.
Gidan mi koda muke tallakawa ai muna da mutunci a idon duniya don bamu da abin da za,ai muna fade, a kanshi sai talauci halittan Allah kawai.
Mu, muka fara shiga dakin da babana yake kwance aciki muka samu mata san suna mashi wanka dole muka dan zauna daga waje har agama mashi wankan.
Muna nan zaune shi bai karaso inda muke ba sai zuwa can na hango shi tafe da leda a hannun shi ya nufo dakin.
Bai muna magana,ba ya zo ya,shige kamar nace kada ya shiga a gyara baba ne ashe yasan an gama,shirya shi, shine yazo kai tsaye ya shige dakin.
Can dayan matashin ya leko yana fadin ance ku shigo angama muka mike sai cikin dakin baba yana zaune Sadauki yana gaban shi yana mika mashi abinci a plate.
Mamaki nayi dana samu ya na tsaye a gaban gadon yana shayar da babana abin karyawa da kan shi.
mamaki ya rufe ni a cikin raina yadda sadauki mai daukan kai, mai izzan tsiya, mai fadin rai kamar wani mugu can akoda yaushe ba alaman rahama a fuskan shi ko kadan.
Amma kuma wai shine tsaye yake shayar da babana mutumin kauye tallaka mai jiran Allah ya kawo aci.
Tun daga kofa mama tabawa cikin muryan yan kauye ana magana a na daga murya take fadin a,a malam kan jiki yai kyau wallahi kaga ikon Allah.
Nan muka shiga gaishe su tare da,matasan nan biyu da suka kwana da Baba na a daren jiya sai lokacin na fahinci cewa wata kila hayan su akayi don suyi wanan aiki, a biyasu kudin su.
Lokaci ne, komai mairai yana gani a wanan zaman da muke a cikin sa haka.
Da kudin sai ka zama sarkin dole saboda yanayin lokaci mai kudi yafi basarake daraja a idon al,umma.
Suma kansu sarakunan suna zubar da kimar su don kwadayi ga tallaka bawan su don kawai kwadayin kudi .
Sai da,Baba na ya,shanye tea,din tas sadauki ya,barshi yana,mashi sannu nan yake cewa matasan nan zasu iya,tafiya,gida su dawo .
A tare suka,fita,dashi ya nufi gurin likita inda ya samu bayanin matsalar dake damun Baba na dole sai an mashi, theater.
Bai muna bayani ba kada hankalin mu ya,tashi don haka yaja bakin shi yai shiru sai da gwago mai masa,tazo yai mata bayani abinda za,ayi kuma a gobe za ai mashi aikin,
Da farko gwago taso ta,rude amma yana daga,mata hannu yace dakata mai masa ban son abin tashin hankali shiyasa na kiraki don na,fada maki saboda zaki fi su kwanaciyan hankali ke.
Tace tau sadauki yanzu may ake ciki yace zamu tafi tare dakw ne ki saka hannu a matsayinki na yar uwar shi.
Tare suka tafi gwago na ta,saka hannu akan aikin da za,aiwa babana gobe da dare.
Washe gari naga shiga da ficen da yaya sadauki yake a kan Baba na yai yawa amma sai na dauka don halinshi ne taimakon yasa yake hakan.
Washegari ranan aikin ina sauri na tafi asibiti mama take ce min dakata, Fatima.
Sai gabana ya fadi ras,ras tace bari nazo mu tafi tare kuma ban son abin tayar da hankali idan mun tafi ki natsuna sosai banda shirmay.
Nace tau, tau,mama gaba na sai faduwa,yake ina ganin kaman wani abu ya samu babana boye min kawai akeyi.
Itako mama ta bawa sai hira take cikin daga murya ba abinda ya samay ta kamar wagara.
Mun samu har anyi mai theater an fito dashi ko sadauki da,yaran nan suna zaune a gaban shi cirko cirko.
Wani kallo cikin tashin hankali muke yiwa Baba dake kwance sharkaf saman gado kamar baida rai.
Da,sauri na isa gurin shi ina cewa baba may ya samu baba ina kokarin fasa kuka a lokaci guda.
Hannu ya daga min cikin daka,min tsawa yake cewa ke shout up please kada ki muna kuka anan please.
Aiki, akai mashi baya son damuwa Fatima mama take fada min haka daga gefena da take tsaye tana,kallon yadda yake sauke numfashin shi a hankali kamar zai shude,
Ranan a haka muka wuni cirko cirko tsaye cikin tashin hankali don ance irin aiki da akai mashi is hard aiki matsala,sosai ake samu idan ba,ayi a hankali ba don a marayan maza akai mashi aikin.
Gaskiya wanan jiyan banda abinda zance wa mutanen gidan mu (gidan maji) don ba karamin kokari sukai min ba kan ciwon dake damun babana ko aikin shi tsada gare shi sosai.
Kwana uku da yin aikin ya,samu sauki sosai don yanzu har zama yake yadan dauki lokaci a zaune.
Sai dai ya,wani irin ramaywa yai baki sosai sai ya koma,wani dogo dashi.
Da,sallama na,shigo dakin da,yake ban zaci cewa yaya sadauki yana dakin ba,a,wanan lokacin don bai faye shigowa da,rana haka ba.
Jin sallama yasa su juyowa su na kallo na har da baba na dake zaune ya dago kan shi da sauri ya dan saki murmushi yace Bintu ke tashi?
Na tambayi maman ki tace min ke kwanta kin samu barci.
Nace baba na dan kwanta barci ya dauke ni kaina ke ciwo shine na dan kwanta kadan.
Yaya dake zaune kusa da babana a bak8n gado ya bashi gassashen kifi yaji hadi yana ci a hankali .
Baba na Yace tai zuwa ki nemi paracetamol ki sha keji, kada ya kaiki kwance.
Nace tau baba yace ki tai gida ai na gode wallahi Alhaji karami yai min komai duniya da lahira, wadda sunkai min suma Allah yai masu.
Mutum baka hada komai dashi ba zanan mutunci dai yai maka haka aiko ankai Allah dai ya kara daukaka da darajja.
Duk wanda ke gurin aka amsa da Ameen mamatabawa tace ai halin yarka na yya jja muna wanan alherin haka.
Shidai mikewa,yayi yafita,daga dakin har yakai kofa ya tsaya,batare da,ya juyo ba yake cewa make sure kin bashi maganin shi ida uku tayi.
Ya sa kai yafita can sai ga wani leburan asibiti ya turo kofa yace ga magani ance nakawo wa Fatima wai natane ta duba yadda aka,rubuta tasha.
Mamakin wanan sauyin rayuwa na yaya,sadauki ba ni kadai ba kowa na,mamaki ya koma wani salihi rashin yawan maganan shi ya karu mai.
Sai yana yawan aikin alheri sosai ga alumma mabukata da,rabon su ya ratsa ta,gurin shi ni dai zan iya cewa gaskiya alhamdullahi don rabon mu ya,ratsa aljihun shi tunda,mahaifina ya samu lafiya,a sanadin shi.
Don da akauye yakw sai yadda Allah yayi dashi kawai a can don ance mutum bai mutuwa,sai kwanan shi sunkare.
Sosai babana ya samu sauki gashi daga Alhaji har maji da yaranta zuwa mutanen gidan su sunzo duba ma mahaifina.
Wasu dai gulmane wasu kuma tsakani da Allah ne ya kawo su.
Kabir yazo nan asibiti ya samu baba tadan jima gurin tsaye shi bai zauna ba don girmamawa,
Yana batun wucewa,ne yaya,sadauki ya shigo dakin yana saye da, sworth farare masu kyau da tsada a jikin shi farare zakace ba dan hausawa bane kan shi yaji oil sai sheki yakeyi mai, kafan shi cikin bakaken cover shoes masu tsadan gaske ga agogon da,ya,daura mai matukar tsadan gaske.
Hannun shi yana,rike da dan key din motar shi yana juyawa a,hankali, yana shiga dakin yaga Kabir a zaune ya,sheda shi sosai ya gane shi.
Su mama tabawa aka,shi gaida Sadauki da yi mai barka da zuwa yana,wani amsawa cikin basarwa,yadda halinshi mai kama da kyankyami yake.
Kabir daga inda yake tsaye ya kurawa babana ido yana barci yajuyo gurin miskilin yana mai mika mai hannu don suyi musaba,a irin ta addinin musulunci.
Yace mai sallamu alaikum cikin mika mai hannun shi kamar mai jin kyamar hannu ya wa i basar tukun ga hannun kabir a mike can cikin sham kamshi ya dan mika mai hannu tare da,basar wa suka gaisa.
Duk da abin baiwa Kabir dadi ba ama sai ya shaye ya,dakw yana cewa sannun ku da kokari fa Allah ya,saka maku da,alherin sa.
Kamar bai jiba ya juya yana cewa ni zan tafi idan ya tashi ku kira likita yace a kirashi akwai abinda za,aimashi.
Daga haka ya fice dakin ni ina daga waje ban ma san yadda suka kwasa ba a cikin dakin.
An dan jima kadan Kabir yafito daga dakin nan na mike nazo ti mashi rakiya zuwa inda motar shi take.
Mun dan fara,tafiya,yana cewa,gaskiya jikin yai kyau don da,Alaman aikin anyi sa,a sosai gare shi.
Nace sai dai Baba ya ji jiki sosai wallahi ya dai samu gatane shine har yai saurin murmurewa haka.
Sunana naji yakira, murya a sanyaye yace Fatimatu don Allah may ke tsakanin ki da,wanan yayan naki na nan garin wanda ya shigo dazun ina ciki.
Nace wa ke nan don ban kula da,wanda ya shigo dakin ba ina can baya ni.
Yace wanan da,muka,taba gaisawa dashi acan gidan ku mana wani farin guy haka, mai dan tsawo kadan, mai karfi haka.
Nace,wai duk wanan kwatancen haka yaya sadauki ne mana dan mamana na,garin nan shi kadai ne danta namiji a duniya.
Kuma dan kwallo kila ma kana jin sunan shi don har kasan waje yake fita wasan kwallo sosai.
Nace ummumm wama suke kiran shi ne da,guy name din yan kwallo sai can na tuna nace U F sukekiranshi.
Yace au shine dama UF dan kwallon jahar nan tamu lalai ina jin sunan shi ko sosai wallahi a lailai guy din dollars sun zauna don yana kawo wuta sosai ga kasan nan anaji dashi.
Nace lalai ma ni ban damu da harkan kwallo ba balle nasan wani abu acikin sa sosai.
Sai tambayan da ya jefo min ta bazata na a kunnuwa na yana fadin to may ke tsakanin ki da shi Fatima.
Da,sauri na juyo tare da,dakatawa,da,tafiyan da nakeyi nai may tambayan hausawa tambaya cikin tambaya.
Nace washi yaya sadauki din yace sunan shi kuma ke nan ko nace eh UMAR FARUQ yake shine ma,anan UF din ai yace ok.
Nace sai ban fahinci tambayan da kai min ba nacewa may ke tsakani na dashi nace yayana ne mana, dakin mu guda dashi ai dan fa mamane na fada maka tun farko.
Yace nasani kin fada min, shima yaja ya tsaya wuri daya tare da fuskanta na da,kyau.
Fuskan shi ta nuna min damuwa acikin ta karara nace ba wani abu a tsakani da shi sai yan uwan taka kawai, amatsayin yaya yake gare ni.
Sai naga yai murmushi mai ma,ana da magana can ya nisa yace badon na fadi wani magana ai fushi dani ba dana fadi abinda nagani a zuciyar shi.
Nace kaga yana matukar jin haushi na ko wallahi haka yake mugu ne tun da nazo gidan su zama yani gaba da hattara da tsangwama.
Shi kullun yar kauye da munafuka yakw ce min don kawai yaga mama tana so na.
Fatima nace na,am sai yayai shiru can yadan harde hannayen shi gaban kirjin shi tare da kallo na ido da ido yace .
Wanan yayan naki sadauki yana son ki na hango kishin ki karara a kwayar idon shi wanda ba kowa ne zai fahinci hakan ba sai wanda ya kwantar da hankalin shi sosai zai gane hakan.
Wani kallo nai mashi na amma baka san komai ba nace, haba yaya kabir har may ya rufe maka ido yasa ka fada min wanan magana haka.
Mutumin da ko kashe ni yana iya yi don haushi da takaici na da yake ji zakace wai yana so na.
Ni may ma zanyi da wanan may bakar zuciyar kamar arnakun farko.
Wai tsaya ko don kaga ya taimakawa mahaifina ne yasa ka fadi wanan maganan?
Nasan ba,shi yai niyar hakan ba uwarshi ce ta sakashi yai taimaka muna don tasan yana taimakon mara shi a gari.
Yace to is OK tunda baki yarda ba amma watarana zakice nace nidai don Allah ki rike min amanan kanki don wallahi ina tsoro don zantafi zuciyana yana min kwankwanto ga abinda na gani.
Take naji raina ya baci nace ni wallahi yaya Kabir har ka bata min rai ko na rasa miji may zanyi da wanan mugun mara imani.
Dariya yayi yace shike nan tun da naji haka ga bakin ki da zaran an sallami baba zan turo da kaya a kawo wa mama kamar yadda nace don komai an hada kawowa kawai ya rage.
Nace ni dai yaya Kabir da dai zakayi hakkuri har na kare karatuna da zaifi sauki wallahi.
Yace wa ni ance abari ya huce shi ke kawo rabon wani don haka akarashi a gidana na san na kama abina a hannu kafin ai min sakiyar da ba ruwa.
Yabude motan shi ya shiga har ya zauna sai kuma yafito yace wallahi ina ji kamar kada na wuce nabarki da wannan mayen dana hango nai dariya nace kai zuciya mai nashe nashe wallahi.
Ni ai wanan da kakw gani yafi karfin aure na don shi ba kalana bane ka bar wanan zancen kawai don Allah.
Yace to tunda kince hakana na gamsu yanzu sosai sai mun yi waya ke nan idan na isa gida nace Allah ya tsare idan kaje a gayar min da su Antyna da yaran.
Yace zasu ji insha Allahu yatayar da mota tare da yi min horn na daga mai hannu yafice daga harabar asibitin, saida naga security sun daga mai kofa fita daga get din na juya zuwa ciki.

****** ********* ******
Kwana biyu bayan haka aka sallami babana daga asibiti sai dai

Please Login or Register in order to submit comment