Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Mikewa yayi ya ce kun daiji abinda na fada maku kowa ta kiyayyeni akan hakan.
Barin dakin yayi kamar wanda aka tsakara baiko juya ba yafice abinshi har lokacin yana jin hargowan Umma daga part din su.
Zancen bai kare ba don da maigidan yadawo an samay shi da zancen yana ji yace a kira mashi su Amira da maryam tun kan hajiya Umma tafita daga gurin shi har Nafisa din.
Bayan kowar su tashigo tare da uwarta harda mama Asiya da yaranta yan mata, yana cin abincin shi hankali kwance ga hajiya kubura dake girki daga gefen shi suna zuba soyayyan su a cikin style.
Alhaji kaifa kace a kiramu kuma kabar mu a zaune kana harkan gaban ka inji mama Asiya da kishi ya kumay a lokacin na irin yadda yakeyi da mummy.
Mummy tace ke hjy Asiya ko so kike kuma yabar cin abincin ya tsaya shirmen kishin ku na kullun da baku san angirma ba har yara sun fara irin shi.
Kada ki fara ki fada min maganan banza wallahi yanzu a jimu a gidan nan don ke baki da kunya kowa so kike yabi ki kamar yadda kika mayar dashi a gurin ki.
Alhaji wanda yagama wanke hannun shi da hjy kubura ke zuba mashi ruwa yace ta mayar dawa wai ni ko wa ?
Shiru tayi don tasan idan ta tanka yanzu zai iya watse ta a gaban kowa babu ruwan shi da yara na gurin.
Gurin Amira ya juya yana cewa mamana yanzu Umman ku ke fada min wai kun taru kunwa Nafisa duka yau a gidan.
Sai kuma ya juya gurin Maji yana fadin ina bakuwar yar ki ita bata zo bane don nasan ba,a dukan Nafisa bata sa hannun ta ba.
Nafisa tai but tace wallahi danaci uban ta ko murmushi yayi tare da duban Umma yace kin dai ji tarbiyan ki ko ?
Yace wa yar mama Asiya karama hauwa kira min yarinyar dake dakin maijidda tazo da sauri yarinyar ta mike zuwa kiran Bintu.
Ta na shiga bako sallama Bintu da ke zaune hankali a tashe ta kurawa tv ido sai dai hankalin ta ba,a kallon yake ba sai ji tayi ance ke yar kauye baba na kiran ki.
Tare da watsa mata harara tana yatsune fuska tare da bin dakin da kallon wulakanci ta juya da sauri bintu ta jawo hijjab din ta dake gefe har kasa tasaka.
Tare da bin bayan yarinyar don bata masan falon baban ba duk zaman ta gidan da tayi ba ruwan ta da sanin komai.
Saida tajawo kofan dakin Maji da zata fito tasaka key tabar dakin da key din a hannun ta.
Inda taga hauwa ta shiga nan ta shiga itama tare da sallama dauke a bakin ta.
Maji da hjy kubura sai Alhajin ne suka karba mata sallaman ta da tayi tare da samun guri ta tsugun na ta sunkuyar da kanta kasa tana fadin.
Ina wuni Baba, cikin lada bi tare da sunkuyar da kanta a kasa, yace tare da nuna ta da hannu kun gani,
Sannan ya karba mata gaisuwan nata yace ku diba ke Asiya da kika samay ni kan maijjidda ta dauko bakuwar yarinya takawo min gida.
Kinga abinda tabi ta jawo ta a jikin ta tarbiya natsuwa da sanin ya kamata ga yar kauyen yar makwabtan da kika ce.
Hajiya kubura dake gefd tace kai Allah dai ya sawaka idan kuma anyi magana ace wai wani ke hassada.
Ke kubura wai may kike so ma dashi ne ki fada min don kin san daidai nake da ke wallahi.
Ai kaji maganan ke nan yanzu ku dakata da wanan bashi nakiraku yi ba anan ina son nasan may yakai har ke Amira kuka taru kuka daki Nafisa yau a gidan nan.
Anyi magana kuma uwar ku ta daure maku harda ita ta shiga zancen, ana haka kuma mahaukacin wanku shima ya shigo ya saya ya zama nashi.
Nafisa ta tare zancen dacewa baba bakin cikine fa kawai don sunga ana zuwa gurina su ba,a zuwa kiran su kamar sauran yan mata.
Alhaji yace a gidan har ake haka banda labari Nafisat ?
Allah ya kyauta kawai yace tare da girgiza kan shi cikin takaici yana kada kafan shi irin na magidantan da abu ya daurewa kai.
Yace ke tare da kallon inda Bintu take zaune yace mayye sunan ki ne ma ?
Tace a hankali Bintu Baba, yai yar murmushin manya yace Fatima bintu ke nan ko?
Eh Baba ta bashi amsa yace ki fada min abinda kika sani akan fadan da akayi a gidan nan yau.
Shiru Bintu tayi na dan lokaci kamar ba zatai magana ba sai kuma can tace.
Baba muna daki bayan anty Amira ta shigo gida nan tafara bashi labarin abinda ta sani da irin kalamin da kowa ya fadi har marin da Maryam taiwa Nafisat din.
Amma maryam wallahi kin kyauta min inji hjy Kubuta tare da kallon gurin da maryam take zaune.
Eh zaki fadi haka mana tunda ba yarki akaiwa hakan ba a gidan.
Hjy Umma ce uwargidan su mahaifiyar Nafisa ta ke fadin haka din cikin bacin rai.
Batare da Alhaji ya kalli gurin da take ba yace kubura ban son na kara jin bakin ki a zancen nan.
Daga haka yai shiru bai kara cewa komai ba kuma again, ya juya gurin Umma yace to kinji ke maimuna zagin uwarsu tayi har dakin ta kuma tana zaune babu kunya don kawai an bata mata rai akan saurayin ta da yazo kiranta ba,a fada mata ba.
Alhaji kada ka juya zancen nan fa dukan min ya akayi kuma shi nazo fada maka din ka dauki mataki a kai.
Yace wani mataki zan dauka idan kece su Amira suka shiga gidan kike sukai maki haka a gaban ki wani mataki yaran ki dake gurin zasu daukan masu ?.
Shiru Umma tayi yace ba amsa ke nan sunyi daidai dai din ke nan ko ?
Tace yanzu mai kake son nace tunda na fahinci ka daure masu gindi akan abinda sukayi sunyi daidai.
Yace kin taba gani mai kai takaka yayi nasara gurin maida magana balle harda cin mutuncin uwa a ciki.
Ai ko ke ne suka kawo wa takaka akai masu hakan iya matakin da,zan iya dauka ke nan a kan su kinji na fada maki.
Ke kuma Nafisa wani yaro ne yake zuwa gurin ki gidan nan ban sani ba har kike iya tsayawa kiwa yan uwanki cin muntunci akan shi don ya aiko kiranki ba,a fada maki ba ranki ya baci kibi yarki har daki kina zagin ta don samun guri.
Shiru Amira tayi tare da dukar da kanta cikin tsawa ya daka mata tsawa yana fadin badake nake ba nace dan gidan uban waye ke zuwa gurin ki gidan nan har kofan gida na ?
Sai ga Nafisa tana hawaye don daga ita har uwarta basu zaci abin zai juye masu haka ba a lokaci guda.
Yace tunda aure kike so ba karatu ba sai ki turo min yaron yazo ai maganan aure dashi.
Ya juya gurin hajiya Umma yace maimuna yanzun saboda Allah kin san yarinyar nan tana tara min samari a kofan gida haka shine baki fada min ba saboda Allah da girmanki ?
Idan da da dan wani dakin ne yake haka dafa a gurin ki zan fara jin wanan labarin.
Yanzun dai nafahinci ka juye maganan ya zama laifi akan mu, shike nan nida diyana bamu da shakat kan yan mayen diyanka a gidan nan.
Duk abinda sukayi shine daidai mu bamuyi daidai ba indai duk wa yan nan marasa mutincin yaran Hauwa ne ka daurewa gidin ai suje suyi tayi.
Ba sabon al,amari bane gasu nan daga dan maye sai yan iska data tara muna a gida.
Ta mike fuuu, ta fita daga dakin inda shima yabi ta da kallon takaici mama Asiya ma mikewa tayi tana fita tana fadin babu dai adalci yanzu a gidan nan.
A dakin mutun kuma ace wai shine bai da gaskiya don samun guri da daurin gindi kawai.
Ya juya inda yaran suke ya kara masu fada akan baya son ya kara jin fitina daga gare su ko ya batawa mai shi rai suka mike suka mike suka bi bayan uwayen su rai a bace su ma.
Suna ganin ba ai sharian gaskiya ba a gurin don sune da gaskiya amma mahaifin su ya danne masu gaskiyan.
Bintu ma ganin yaran sun mike yasa ta mikewa tabi bayan su amma sai taji muryan Baba yana cewa ke Fatima sai ta koma ta tsuguna don taji may zai ce mata din.
Yace ban son naji ance kin saka kanki a harkan cikin gidan nan kamar yadda ban taba samun labarin banza ba a kanki fon haka ki kiyayye kin ji .
Ta amsa da to Baba nagode ta mike tabar dakin duk tsoro ya cika mata zuciyar ta ta samu su Amira suna jiran ta takawo masu key din kofan su data rufe masu.
Hauwa kici gaba da hakkuri don ance dan kuka mai jawa uwarshi jifa yau duk yaran ki bugu daya ake masu akan danki daya daya samu matsala,
Don haka saikin toshe kunnuwan ki don babba da yaro dashi zai zage ku duk wanda ya tashi a magana gudu zai fake ya harbe ki dashi.
Sai kuma ya jijiga kan shi a cikin takaici da jin zafin sadauki a ran shi yace Allah ya kauyata.
Sai lokacin hjy kubura tai magana tace rashin dai tunane ne ga mutane ai wanan matsalar ta shafi kowa a gidan nan don ba nata bane ita kadai.
Amma hakkuri da addua bai bar komai ba Allah ya sauwaka ya kiyayye gaba kawai za,ace.
Maji ta mike tare da cewa nagode Alhaji ranta babu dadi yabita da kallon tausayi kawai.
Har takai kofa hjy kubura tace gobe dai ba aiki don Allah ki ara min yarki ta tayani gyaran daki na.
Ta juyo tana cewa wai Fatima Alla ya kai gobe ai ita yaro ba kiuya ne bata jin nauyin jikin ta ko kadan.
A daki ta samu su Amira suna dariya Bintu wai ta rufe kofa da zata, fita daga dakin.
Tace ba dole ba don ni abin wallahi yanzu tsoro yake bani ma mutane haka ba tsoron Allah.

****** ********* ******
Sadauki yana fita jin shi yake kamar yana taka kaya don bacin rai, duk wanda ya yanzu ya tashi zagi akan shi akewa uwar shi gori.
Ya madai godewa Allah da jiya bai sha komai da da yai niyar sha yasan da yau gorin da Maji zata sha akan shi Allah kadai yadan irin sa.
Gashi saida ya zuba kwayan a bakin shi sai yaji kamar ance ya furzo su waje duk ya zube su a kasa suka narke yana kallon su.
Har ya usa filin kwallo zuciyar shi sai faman sake sake take mai kan abinda zaiyi wanda zai sa Maji ta danji sanyi akan shi.
Amma ya rasa mafita akan haka, haka ya samu guri ya zauna ranan yana kallon masu kwallo kawai ya kasa tsinanawa kan shi komai a lokacin.
Sai faman kulawa da warwarewa yake shi kadai a ran shi abin duniya duk ya damay shi.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,


Tun bayan dawowan Raiha daga tafiya gaba daya bata son fita zuwa ko ina ko yaushe tana gida sai faman barci takeyi kamar wace tai wani aiki.
Gaba daya ta kashe wayan ta kuma ta hana kowa ganin ta tayi hakane don gujewa Nasir kawai.
Kusan sati biyu yana sintiri a kofan gidan su gashi tun dawowanta wayanta a kashe yake mata.
Ranan da ta bude wayan ta bayan kaman minti goma kiran unknown nomba ya shigo mata layin ta.
Da farko kyale kiran tayi har ya gaji ya tsunke don kan shi amma,sai gashi mai kiran bai hakkura ba ya kara kiranta again.
Cikin kasala ta dauki wayan sai taji murya cikin turanci a na cewa hey, baby,
It's me Michael, your friend from lagos, i hope you remember me now.
Cikin wata murya tace you mean, Michael Nasir friend ?
Yes it's me baby .
I called your nomber several time is switch up what happen with you baby?
Tsuki tayi tana fadin dan rainin wayo kawai har ma kana tambayana abinda ya samay ni ne wai?
Sam batai tsanmanin ya taba iya hausa ba sai taji yace don Allah kiyi hakkuri nasan bamuyi maki adalci ba shi yasa nakira layin ki na baki hakkuri don ban son abinda zai dawo a gare ni wata rana.
Maimakon tayo magana sai ta kama kuka dama gashi mahaifiyarta bata nan gida ta tafi makwabtan su .
Cikin rudewa michiel kece tayi hakkuri ta,saurare shi yana son magana da ita ne.
Da kyat ta dakatar da kukan ta yake cewa kina jina baby dama na dauki nomban ki ne batare da sanin abokina ba.
Don kawai nakiraki saboda ya bani labarin irin abinda yake maki wanda banji dadin shi ba kuma ranan ban san cewa two in one zamuyi maki ba don mun shirya dashi ne ni kadai zanyi amfani dake.
Wani abinda baki sani ba yanzun hakama yana nan yana planning din yadda zai fita dake waje, ne ya sayar dake ga turawa don ya tara kudi.
Bake ce ta farko da yai wa haka ba akwai yan mata biyu da ya kai waje daga garin ku.
Batan lokkacin da tace what da karfi ba cikin wani irin murya mai karfi.
Yace cool down my friend, kin bani tausayi ne don naga ke yarinya ce karama.
Kuma d way yadda naga kina kuka yasa kika bani tausayi, ba zan yarda ya yaudare ki ba shi yasa na kiraki na fada maki komai da fatan zaki rufeni bazaki bari yasan na fada maki komai ba.
Godiya take mai tana fadin tagode tagode yace ba komai, sai dai idan kina da account ki turo min zanturo maki da kudin ki.
Don shi ne ya hana na biya ki tun yana kuna nan yace free sex nayi dake ni kuma i can't dole ne na baki hakkin ki.
No kabarshi kawai ba komai, nagode, sai kawai ta kashe wayan.
Kifewa tayi saman dan katifan dakin ta ta,shiga gurzan kuka wi,wi tana cewa Nasir Allah ya isa tsakani na dakai wallahi.
Sai kuma tai shiru tafara tunane na, son, datakewa,Nasir ya haukatar da ita ta kasa fahintar irin son da Nasir yake mata.
Sai yanzu tafara tunanen lalai maganar Michael yana da kamshin gaskiya sosai don a wanan tafiyan ta fahinci wasu dabiun shi da bata sani ba.
Baida tausayi ko kadan son kan shi yai yawa bai damu da damurta ba ko kadan, shi kan shi kawai ya sani.
Gashi in ba dan sayayyan da yai mata ba bai bata komai ba haka ya barta tadawo gida sai dan dubu biyar dake a hannun ta.
Gashi kayan da,ta,sayo ta rasa yadda zata fitar tai amfani dashi a gani a gida, a tambaye ta ina ta samo shi.
Don har yanzun tana da sauran burbushin tsoron iyayyenta a ran ta.
Maganan Michael yai matukar tsaya mata a rai sosai don duk da bata ga Nasir ba amma matukar tsoron shi take ji a ranta.
Ko da Raiha tafara fita bata yarda ta hadu dashi ba sai guje mashi takeyi duk inda tasan zasu hadu bata yarda su hade dashi.
Wata rana tana tsaye tana jiran taxi taga wata far mota ta tsaya a gaban ta.
Bata tsaya kallon kan motar ba, sai kokarin tare mota take yi hankalin ta yana kan titi.
Ya fito daga cikin motar yana saye da shedda kalar kakin soja tai matukar yi mashi kyau sosai da haka yake yaudaran yan matan gari.
Don Allah yai mashi matukar kyau don duk shigan da yayi zai mashi kyau sosai ya karbe shi.
Baby ya karaso yana fadi kamar bata ji shi ba tayi ta kawar da kanta tana kokarin shiga motan da ta tare.
Da sauri ya karaso gaban ta yana cewa haba baby wai may ke damun ki ne don Allah na fa rasa gane kan ki.
Wani kallon tai mashi kamar bata san shi ba ta na kokarin zaunawa a motan da zata shiga.
Hannun ta ya riko da karfi yana fadin sunan for d first time sabanin baby da yake ce mata da, Ke Raiha wai may ke faruwa ne please ?
Sake min hannu tace cikin wani zafafan muryan tare da kokarin kwace hannun ta daga rikon da yai mata din.
Mamaki sosai abin yaba Nasir din don dai shi yasan lafiya suka dawo da ita daga tafiya.
Look baby Raiha ki fada min idan wani abu ya faru ne please don ban san laifin da nai maki ba ni.
Kawai ra,ayina ne hakan na nisan ta kaina dake don bakai min ba ni, maganar ta yasa shi murmushi yace to ni kin min ai.
Ko ba shike nan ba ki tsaya please muyi magana mu fahinci juna kada ki tara min mutane please.
Da,wasa ya dauki zancen amma sai yaga finfirin Raiha ta shige mota ta tafi abinta tabar shi nan tsaye.
Gurin Brosha ta tafi don dama kayan aikinta sun kare gashi kuma tana son jinta a network sosai don kwana biyun da tayi bata sha ba duk wani kala take jin kanta.
Shiko Nasir nan ta tafi tabar shi da mamaki don ya kasa fahintar abinda yai mata, saidai tunanen shi ya tsaya ne kodai yadda yai mata a lagos ne yasa tai hating din shi.
Wanan yatinyar may take nufi sai da tafiya tai nisa take son ta bata min show dina wallahi bata isa ba.
Don na riga da na fara shirin fita da ita waje gashi shegiya nasan ba karamin kudi zan samu a kanta ba don shegen dadi ke gareta.
Koni don dai son kudine kawai da ya rufe min ido aida bazan iya rabuwa da ita ba.
Gidan mahaifan shi ya nufa inda yan kannen shi suna ganin shi suka taso da murna suna mashi sannu da zuwa.
Duk cikin subabu sa,an Raiha don suna girmay mata da shekara biyar ko hudu.
Bayan ya gama gaisawa dasu ne yake tambayan
Gaban hajiyan shi dake zaune saman kushin ya zauna yana mata ina kwana.
Ta amsa cikin dakewa tana ce mashi lafiya yakara da tambayan ta ya gida da sauran al,amuran gidan, nan ma ta bashi amsa da Alhamdullahi.
Sai dan shiru, can uwar tace ashe kadawo ban sani ba yace eh inna ai yau kwanana biyu da dawowa.
Wani kallo tai mashi tace bayan Abdul yau kusan kwana biyar ke nan da yace min kun hadu dashi, zakace wai kwanan ka biyu da dawowa.
Nasir ko kana son mayar da kanka mutumin kwarai kuwa ?
Ka saki matar ka kakuma ki aure sai yawon kwasan yan mata kake a mota baka nan baka can dasu.
Wallahi kayi hattara da cutan zamani don yawa gare su ko ba wanan akwai wancan.
Dukar da kai yayi kamar wani mutumin kirki yana cewa Inna ai zanyi bandai samu wadda namu yazo daya bane har yanzu.
Don ina gudun kada akara maimaita irin na wancan karon aza kuma ba,a dace ba.
Kai din ma ai ba halin kwarai ke gare ka ba tunda baka iya zama kurum.
Ga shaye shayen da ka sawa kanka don ban tsan manin ka daina yi yanzu.
Girma dai ya kama ka in kanawa kan ka,fada kayi wallahi ni zan fitane kada kazo ka tare ni da surutun banza.
Yace Inna ina zaki sai na sauke ki dayani tunda gani na shigo.
Tace da sauri wa aganni da kai ace may ace har alfahari nake da irin halinka ina shiga mota da kai darana cikin gari.
Murmushi kawai nasir din yayi duk da,zancen mahaifiyar tashi ya soshi zuciyar shi.
Ya mike yana mata a dawo lafiya yafita inda kannen shi suke ya basu dubu goma wai su raba don yasan ko yaba inna ba karba zatayi ba don tace kudin da yake sayar da kwaya ne ita bata ci.
Duk yadda yaso ya fada mata matar shi da suka rabu kazafi take mashi amma inna taki yarda da ba gaskiya bane.
Abu daya tasan yana masu shine biyan kudin wuta da na ruwan fanfon gidan nasu tun bayan da mahaifin shi ya rasu.

****** ********* ******
Ranan da matan gidan suka samu labarin tafiyan da sadauki zaiyi zuwa kasan waje sunyi ta zuba bakar magana kamar tashin hankali.
Inda suke cewa lalai maji bata san ciwon kan ta ba da har zata yarda ta barshi yafita zuwa wani guri wai ma kwallin kafa.
Itako mama Asiya cewa tayi sai dai a kare da hakan a lalace wai wasan kwallo don tambadewa kawai.
Umma sai da ta samu maigidan su da zancen tana cewa wai da gaske ne zancen da taji yara suna fadin sadauki zaifita waje wasan ball.
Yace da gaske ne mana akwai illa ne ga hakan ko yaya ?
Tace haba Alhaji yanzu kamarka da kimar ka da darajan ka,za,ace wai danka ne ke wanan abin.
Shi kwallon kafan kuma yanzu mugun abune, da na barshi nan zaune gida yana tambadewa ai gara na san ya kama wani abun.
Tace amma gaskiya Alhaji,,, ke yafa isa haka Rakiya don nasan abinda nakeyi sarai wallahi don haka na fada maki da yardana zai tafi.
Cabdi ashe akwaita gidan nan ke nan don sunan ka bai lalace ba yanzun ne ake shirin yin ta.
Ta fito fuuu, daga dakin tana zuba bakaken maganganu itakadai har zuwa dakin ta.
Ba su hakkura ba sai washegari kuma suka kara,tayar da zancen.
Lokacin haniya kubura tana kusa sai cewa tayi maye cikin wasan kuma ai wanan idan Allah yasa mashi hannu sai kiga an take akai.
A sawan kwallon ko a shaye shaye wanan dai kawai an kara turashi ne yaje ya kara yin cos kan shaye,shayen shi kawai.
Nikan wallahi idan ya dawo naga yakara haukacewa sai dai na bar ma su gidan shida uwar shi kawai don dama haka sukd so.
Allah dai ya shirya muna shi amma ai ba kai wa dan wani mugun fatan mugun abu ya samay shi.
Daya samay shi da farko ni nai mashi fata ko may kada fa mace ta daure ni da raina.
Ni yanzun ma gani nake kamar ya koma ga shaye shayen shi ne don ko yaushe yana gida kwance kamar wani malalaci sai aukin barci kawai.
Duk a kunnen maryam dake zaune a

Please Login or Register in order to submit comment