Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

har bashar ya fanhici yana da yar matsala a tare dashi sai dai bai san daga ina matsalar take mai ba.
Tunda zurfin ciki irin nashi bai bari ya fadawa kowa halin da yake ciki balle a bashi shawaran da ya dace dashi.
Zaune suke ga system ya aje a gaban shi amma ya kasa sauraren bayanin da bashar yake mashi a lokacin.
Shiru bashar yayi yana kallon shi can yake cewa wai may ke faruwa ne sadauki naga fa duk kwanan kana cikin dan damuwa.
Guntun tsuki yaja yace may ga nine wai lafiya kalau nake bashar ya hade hannayen shi biyu guri guda ya tagumi dasu ta kasan gemun shi yana kallon abokin nashi na tsawon dan lokaci.
Can yace tabbas akwai matsala a tare da dakai wanda nake gani kamar daga gida ne ko gurin kaunata Fatima?
Nace maka babu komai murmushi bashar yayi yace wallahi akwai komai kan don ni nagani kafada min may ye matsala please ?
Don nima shawarana da matsala bata wuce ka akan may kai zaka dinga boye min damuwan ka wanda a gaskiya banjin dadin hakan wallahi ko.
Kallon bashar yayi yasan abinda yafadi gaskitane har cikin ran shi ya dan ja tsuki ya mike tsaye tare da saka hannin shi a cikin aljihun shi ya nisa gurin window office din ya nufa yana kallon waje can ya nisa kadan ya juyo inda bashar yake zaune yace.
Bashar wallahi Fatima tana son jefani a cikin wani hali saboda dan dalilin ta mara amfani.
Ai tasan yadda nake ta amince ta aure ni amma kuma may zai sa yanzun sai da na yarda da ita zata bijiro min da,wasu akida nata na daban can.
Bashar ya ce tare da mikewa ya dan tako zuwa inda sadauki yake a tsaye yace ban fahinci tasan halinka ba ta yarda ta aure ka haka nan ?
Yace kai tsaye kwarai eh ai tasan koni waye tasan ina sha aiko ?
Bashar ya rintse idanuwan shi don takaici yace haba haba man kaida bakin ka har kake ikirari da sabon Allah haka why why please.
Lokaci yayi fa da zakaiwa kan fada kafin ai maka yau tun kuna kubiyu kaida Fatima inaga sai yaran sunzo an fara masu gori a makaranta akan shan ka.
Idon shi ya rutse yace kaga abinda yasa ban sha,awan auren ba hausa tun farko amma maji tanace akan wanan yarinyar sai nayi.
Ita Fatima har ta isa ta hanani abinda nakeyi ko nai niyar yi kamar ta who is she bad way ?
Itace ko wani abu don gashi saboda ita ka shiga bakon yanayi kana gani Fatima ba wata haske bace a rayuwan ka halan.
Ya dago ya kalli bashar ido da ido yace haske haske fa kace yace to haske may Fatima take a gare ni kuma?
Bashar yai yar dariya tare da dan buga kafadan sadauki yace ko wani irin haske nw a yanzu kafi ni sani wallahi.
Halan ka shawo har ta fahinta da hakan ko yace wai shine takewa fushi kwata kwata yanzu ta daina kulani har yar kwaliyan nan ma ta daina yin shi kullun tana daki a kumshe tana hadiyan bakin ciki.
Bashar yace da sauri kagani kagani zaka kashe yar mutane saboda mugun halin ka ko ?
Yace oh nima ma zan kasheta ba itace zata kashe ni ba ita da takasa bani hakkina dake a kanta.
Wallahi ta shiga hankalin ta don tasan idan yau nace zan cika uku a gida na zan iya wake da hasara ba ita ba.
Dariya bashar yayi yace wallahi da watan kunyan ka ya kama a garin nan don kafin ma ka gama zagaye dakin su ka dawo gareta gari yasan ko kaiwaye ko ?
Jeka auro mata uku yau kagani waye a matsa in ba kai ba zata kwabe mawa.
Kana zaune kalau da matar ka kai mata abinda bata so ta dauki mataki maimakon ka bata hakkuri ka lalashi abinka tunda kaine baka da gaskiya amma wao kai shine har kake neman hanyan kuntata mata Allah ya baka sa an auro mata ka tara a gida tinda kana da kudin hakan .
Wallahi batin fada maka mata da kake gani suna da nasu ranan idan kace bazaka bari ba itama rana da hanyan rama cutar ta akan ka sai ka shiga hankalin ka.
Fatima dai ce ba yadda zakayi da ita don tai maka zara a zuciya kuma muddin bakane me shiri ba har mama taji naka ya samay ka kuma ji zarayi tunda inta gidana ta samu labarin halin da kuke ciki.
Dariya yayi yace ashe kaima kasan maryan magulmaciya ce ke na kyashan ta manne da sarki.
Yace to dakata don kawai tana gyara shine zakai mata mugun lakanin suna kawai wallahi yanzu zamu saba dakai akan maryam.
Kallon bashar yake yana dariya yace kai dai ka fadi da bakin ka bashar yace ai mantawa nayi a gaban makiyin mu nake.
Yace wallahi kaje kasan yadda zaka rarashi fatima ku fahinci juna idan ma kana fasa wanan shan yafi maka alheri don ko wata mace bazata ji dadin ace mijin ta ko dan ta yana sha ba ga mata da gorin tsiya wallahi.
Sun dauki lokaci suna musayan magana kan zancen karshe bashar yai mashi sallama akan zai tafi gidan Inna ya gaida ita bai samu zuwa da safe ba.

****** ********* ******
Yashigo gida fuskan shi a sake ya samay ta zaune a falo ta kunna tv sai kida da rawa na yan iska ake a wani tasha na kasar ghana.
Zama yayi a gaji saman kujera ta watso mashi harara tace kasamo kudin ne da ka dawo min gida haka?
Kallon mamaki yai mata yace cikin karfin hali wai Jamila may yasa baki son a zauna lafiya ne ke ?
Tace lafiya kudi kaima kasan idan ba kudi ni ba zaman lafiya gare ni don dasu nasaba.
Kasan wallahi inda ba kudi kai Ahmed baka isa ka aure ni ba don kasan da wa yanda nake hurda a baya.
Murmushi yayi yace Jamila ke dai in ba kudi sam babu zaman lafiya dake ni yanzu fa ban son abinda ya taba min rayuwan yar matata don ashirye nake akan duk bukatanki ko ina zan shiga na samo maki don kiji dadi kawai.
Hararan shi tayi tace in kana son kaji dadi na mike min su kawai inji dumus sai kaji dadin nawa.
Hannu ya tura a cikin aljihun shi yana fadin angama inda za a bar ni yau na shafi wanan body da ake min kwalelen ka dashi kwana biyu.
Kudi ya mika mata da sauri ta fisgi kudin tare da sake wani murmushi tace dama nasan kana dasu ai boyewa kawai kayi don kaji may zanyi.
Ajiyan zuciya ya sauke a ranshi yace don baki san zubar da kaina danayi na samo su bane don kwadayin ki da masifan ki kawai.
Yana matukar son jamila a ranshi do ba laifi yarinyar ta iya gado sosai gurin ma irin hakane suka hadu da ita har yaji ya kamata ya aure ta kawai yanuna mata karya ya auro ta din duk da mama asiya taso kawo cikas ga maganan amma yai sa,a ba ya yarda akayi abin.
Ranan kan yasan ya kawo kudi don tun wurin suka fara harkan ma,aurata a tsakanin su duk bashin da ke kan su na kewan junan su sai da suka biyawa kansu.
Don jamila irin matan da basu iya kwana biyu ba tare da namiji bane ya kusance ta.
Tun a gaban shi bayan sun huta tafara kashe kudin gurin sayen banza da wofi yana kallo ba yadda zai yi don son da yake mata.
Ranan da dare ma tare suka fita yawo da ita ya kara kashe mata dan canjin dake hannun shi kuma.

****** ********* ******
Ina zaune a dakina kayana da aka wanke nake kokarin nikewa a lokacin don najera su a wardrobe dina.
Dakin ya shigo saye yake cikin kayan barcin shi sau daya na daga kaina na kalleshi na kawar da kaina tare da ci gaba da abinda nakeyi a lokacin
Karaso yayi bakin gadon da nake zaune yai tsaye akaina tare da kura min idon shi na wani dan lokaci.
Can naji muryan shi yana cewa kina ganin kamar wanan abin da kika zaba zai fishe mune Fatima.
Banyi magana ba illa mikewan da nayi tsaye na kwashi kayana zuwa cikin wardrobe dina dasu.
Ina ajewa na juyo ban san yana tsaye a bayana ba sai ji nayi ya rike ni kawai na dago idanuwa na da sukai ja don bacin rai nace may ye haka malam.
Oh tambaya ma kikeyi don na taba mata ta ko may ?
Zan wuce daga gefen shi sai naji ya kamoni yace ina zaki sai kin fada min may ye wai matsalar ki ne a gidan nan.
Nace cikin kukan da ya kubce min kai yaya kai kaiyaya sadauki kaine matsalata yaya.
Murmushi yayi ya jawo ni zuwa jikin shi duk kubce kubcen danakeyi sai saman gado na ya dire ne.
Nan ya shiga kokarin cire min kayan dake jikina har yai nasara rabani dakayana.
Nan ya shiga sarafani yadda yake so raina yai matukar baci tankar da dutse yake amfani a lokacin .
Har yagama abinda zaiyi ya koma gefe daya yana mayar da nufashi a hankali.
Kuka nake sosai don abinda ya aiwatar min a yanzu yai matukar bata min rai.
Nace cikin kuka abin yakai kuma har da fyede ka koma yi min kasani wallahi idan ka zalunce ni sai Allah ya isar min.
Dagowa yayi da mamaki don bai taba jin makamancin wanan kalman ba a gare shi yace.
Fatima nikike jawa Allah ya isa don na taba ki kawai ko may ?
Nace bayan na dan daga ina kallon shi da idanuwa da sukai ja nace kai bakaji kunyan tabani ba kana cikin rashin tsarki?
Nine banda tsarki Fatima nace ina kaga tsarki mutumin da ya mayar da sabon Allah abin yin shi.
Mutumin da bai tsoron haduwan shi da Allah cikin ko wani irin halin zai riske shi ko a maye ko a kalau.
Mutumin da baida mu da halinda na tare dashi suke ciki ba akan mugun halinda yasa wa kan shi don son zuciya.
Ni wallahi yanzun ko da ake cewa wai yimaka akayi kake halin nan ban yarda ba har da hali ma.
Ka cuce ni wallahi daka kusance ni a cikin rashin tsarkin zuciyan ka wama yasani ko ka shawo ne kazo min a haka tunda ba imani ke gare ku ba.
Idan kace wanan halin baza ka daina ba nima wallahi bazan iya zama da mashayi ba tubur na haifi diya ana masu gori na fita gidan buki ana zunde na nashiga mutane ana nunani.
Kuma wallahi,,,,
Ke ya ishe ki hakana nagaji da jin mugun kalamin ki a kaina haka na ko don kinga na damu dake ne zaki tsaya kina fada min magana son ranki.
Damuwa damuwa fakace yaya da kadamu dani dabakai haka ba wallahi dakaso abinda nake so maka a ranka.
Ni dana damu dakai aina fahinci abinda kake so da wanda baka so kuma na kiyayye su don azauna lafiya.
Yadda kake ganin an tursasa maka aurena wallahi nima haka aka tursasa min auren ka badon ina so ba.
Amma nai hakkuri na zauna ina maka addua a kullun na Allah ya shiryaka kamar yadda mahaifan ka suke maka a kullun.
Amma kassh kai yaya baka sawa ranka daina wanan halin mayen ba kaduba fa yadda kainan ka Nafisa maye ya mayar da rayuwan ta.
Idan badon Allah ya nufa mamatana tsaye da addua ba akan ka da yanzun ka fita lalacewa a hakan.
Nikan gaskiya ba zan zauna da dan maye ba don idan akwai abinda na tsana shine maye a rayuwana amma kuma ina kaddara ta riga fata yau gani Allah ya nufe da mai shaye shayen da baida ranan barin shi a rayuwan shi.
Yana sauraren maganan da nake fadi sai dai baiyi magana ba har lokacin karshe ji nayi barci ya dauke shi.
Har na mike na shiga bathroom nai wanka nafito nai nafila na zauna ina kara kai kukana ga Allah akan al,amarin nashi.
Nagaji na taso daga inda nake na kwanta daga gefen gadon nan nima barci ya dauke ni ban sani ba ina cikin tunane.
Da safe ko da na falka na samu yafita daga dakin bai kuma tadani ba don ganin da yayi ina barci a lokacin saboda yasan ban samu barci ba a daren jiya din.
Bayan na sallah na kimtsa jikina na shiga kitchen na hada abin karyawa na jera su atable na shige daki abina na kwanta.
Har ya gama abinda yake ba alama na a falon haka yasa shi leka dakin kwance nake rub da ciki kamar mai barci sai dai yasan ba barci nakeyi ba a lokacin.
Daga kofa yake ce min shi zai fita sai yadawo ban dago ba kuma banyi magana ba haka yasake labule yafice daga gidan.
Jin fitan shi yasani fitowa daga daki na gyara ko ina nagidan tsab na dora muna abincin rana again.
Bai shigo ba sai bayan la,asar naji shigowan shi ya shige dakin shi ina zaune ya shigo cikin shirin shi yana cewa ni zan tafi ga wanan ki rike a gannun ki sai badawo.
Da kyat na iya bude bakina nai mashi adawo lafiya yafita daga gidan ranan ban rakashi ba yadda na saba yi mai wanan abin ya kara bata mai rai.
Sai washe garine yaya Bashar suka zo gidan da maryam mun gaisa da su muna zaune tana min sheri wai na kore mata yaya a gari saboda halina.
Idona ya kawo kwalla nace cikin wata murya ta mai kararen zuciya haba anty don kawai baison a fada mashi gaskiya kawai.
Muryan bashar ne yake cewa Fatima kiyi hakkuri shi kan shi yasan bai kyauta maki ba kuma yaji nauyi da kunya da ya sani.
Hakan da kikai mai kin kyauta gara da kika rufe idon ki kikanuna mashi abinda yayi ba alheri bane.
Don idan mutum yana aikata barna a doron kasa bai samu wanda zai rufe ido ya fada mai gaskiya ba komai dacin shi sunan wanan mutum din tabbabe wallahi don baida ranan daina a rayuwan shi.
Amma kuma ke kuma kin tauye shi da yawa Fatima kin hana mashi hakkin shi bayan kin saba farauta mashi.
Kunyan maganan shi naji na saddada kaina akasa yace gaskiya kin hora min abokina wallahi.
Yace ko yar kwaliyan da kike mai da taro haba haba duk kin daina yi mashi su haba Fatima adai dan sasauta mashi mana.
Maryam tai tsagal tace akan may zatai mashi tunda shi baisan ciwon kan shi ba har yanzu ba gara ta kama kan ta ba.
Yace to gama dama ai yace shawaran ku daya da ita kece coordinater din ta.
Dariya mukayi nace babu ruwan anty kada yaga laifin ta a banza bataci batasha ba halin shi daine bai min ba yaya.
Yace to kiyi hakkuri Fatima tinda dashi Allah ya hada ki zama nifa ina ji ajikina insha Allahu zai daina nan gaba.
Tinda kinga yanzu yarage sosai inda dane ai abin ba dama wallahi don baku san irin halin da na shiga dashi bane a baya kafin ya aure ki.
Amma aikinyi sa,a ma yana shayin ki yana tsoron yayi ki gane ko ranan ina ganin akasi aka samu kawai.
Duk wanda yai mai asiri bai fasa ba mai shi yana kan yi har yanzu don dai suga ya lalace kawai a rayuwan shi.
Maryam tace ina fa suka fasa kwanaki da nafisa tai shaye shayen ta ai ta fadi amma aka mayar da abin haukan tane kawai yatashi take fadin hakan.
Bashar yace ai zan koma gur8n mutumin nan da muka taba zuwa don wallahi Alokacin ya daina kwatakwata dawowa abin yayi.
Kuma zan fada maki wani sirin shi idan yana son sha zagiga idon shi sun rine sunyi ja jajir dasu yana dafe kan shi yana dan murzawa to yana sin yasha ke nan.
Kuma ko a gidan yana da kayan maye har na shayin su da yake sa kina dafa mashi da hannunki amma ke baki sani ba.
Nazaro ido nace wallahi ko duk dare yaya sai na dafa mashi bakin shayi mara sugar da madara yasha.
Yace to sune yake sha yanzun dai kafin ya dawo insha Allahu zan koma kauyen nan naji may ke ciki akan al,amarin don idan akwai wanda zaki bashi yaci batare da yasani ba sai ki hada mai.
Nace nagode kwarai yaya yace kiyi hakkuri kinji ban son mama taji wanan zancen ko kadan don kada ciwon ta ya tashi.
Nace nima shine wallahi amma badon mama ba ranan wallahi dana gudu gidan nan yaya.
Yace no no don Allah kada kije ko ina kefa haske ne a gare shi Fatima.
Zamaki tare da Sadauki wani falala ne ga kowa ga masu gadinku suna fada min irin alherin da yake masu akan ki.
Idan kinyi haka mama bazata ji dadi ba masu hassada akan auren ku kuma zasuyi farin ciki sosai.
Maryam tace ai bata ma zuwa ko ina mutu ka raba ita da yaya sadauki sai dai yan bakin ciki su mutu.
Mun kai wani lokaci dasu suna bani shawaran yadda zan kara bullowa al,amarin.
Sukace zasu tafi don zasu shiga gaida Inna gidan ta a lokacin nai masu rakiya har waje suka tafi yaya bashar yace yace akawo maki kayan abinci sai gobe za,a shigo dasu don ina ganin zai dade a can ne.
Har ya shiga mota yake cewa kin ko kirashi kinji saukan shi na dukar da kaina ina dariya yace don Allah ki kirashi nace mashi to kawai .
Amma bazan kiraba nace a cikin zuciyata indan yadamu yakirani in kuma bai kira ba ajira har ranan da ya dawo din.
Jin za,a kawo min wasu kayan abinci na shiga kitchen na auna shinkafa da taliya don tun na garan mu sunanan ba ai komai dasu ba na kira malam Atiku na bashi kowan su leda guda guda da dubu uku uku na cefane akan Allah ya yaye mai wanan lurar tashi.
Suna ta godiya suka fice kowa yakai nashi gida don dama a bukace suke a lokacin don abin sai shukaran kawai.
Na idar da sallah la,asar naji anata kwada sallama daga kofa nafito ina karba sallah ma.
Na so sheda matar amma na manta ida na san ta a baya muka gaisa da ita cikin sakin fuska take ce min baki gane ni ba ko hajiya ?
Nace na dai so na gane ki tace Allah sarki yanzu maji tai min waya wai nazo na zauna dake don maigidan bayanan kuma tace ma zata bugo maki waya ai.
Nine Rabin dan musa uwar goyon sadauki a baya nace cikin sakin fuska Allah sarki wallahi mama ban gane ki ba saudaya na taba ganin ki ranan da kika zo gaida mama ina gida lokacin.
Na mike tare da amsan ledan bakon dake a hannun ta na shiga mata dashi dayan dakin da anty Amira ke sauka a cikin shi.
Nace mata ga daki nan inda zaki zauna mama tana washe baki tace ai da ko nan kika barni ma yayi min wallahi ko.
Nace kai haba dai nan a waje mama tace ina wajen yake nan na je na kawo mata abincin mai yawa taci sai da ta koshi tana godiya.
Mun dayi hira sai da magariba ya gabato muka shiga daki don yin alwala da sallah.
Da dare ma mun dan taba hira da ita take ta bani labarin irin zaman da akayi a baya a gidan su sadauki yadda maji tasha wuyan su Umma da mama a baya.
Sai zuwa goma mukaiwa juna sai da safe kowa yanufi dakin shi ya kwanta.
Washegari kafin duk ince nafito na samu ta gyara gidan tas ta goge ko ina tai wanke wanke nace bayan mun gaisa haba mama baki huta ba kuma wanan aikin haka tace min haba to may yakawo ni gurin ki ba don na taimaka maki ba na zauna kuma ina kallon ki haka uwar dakina.
Tun ranan itace mai gyara gida iyakata nai muna girki kawai wanda zamuci ko girkin ma tace bata iya ba da abinda mukeyi sai da icce amma in koya mata don watarana.
Shine dalin idan zanyi girki muke shiga kitchen da ita tana kallon yadda nake aiyuka na.
Yau satin shi daya da tafiya baikirani ba ban kirashi ba muna zaune a falo da Iya take ce min wai ke yar nan ni banji kuna waya da maigidan ba mana.
Sai da na kakaro murmushi a fuskana don tambayan nata yazo min a bazata lokacin .
Narasa may zance mata sai nace cikin murmushi lah iya ai shi sai tsakandare yake bugo waya kin san lokacin mu ba daya bane dasu can namuna rana sukuma suna dare ne.
Tace Allah sarki ni kan dai ince yaran yanzu baku wasa da waya da mazajen ku shiyasa na tambaya ai.
Takara cewa ba dai dan nawa yana lafiya ba dai ko nace lafiya yake yana ma yawan tambayan ki na ce mai kalau ki ke.
Tun da na fadawa Iya Rabi haka shikenan bata sake tambayana komai a kan shi ba kuma.
Abu kamar wasa yau satin sadauki biyu rabon shi da gida amma ba waya daga gare shi da farko abin bai damuna amma daga baya sai abin ya fara ci min rai kuma.
Mun shiga daki kenan munyi sallama da iya Rabi sai naji wayana yana ringing da sauri na isa furin don na dauka murja ce wata course mate dina da muka dan shaku da ita.
Nobar kasar waje ne daga US na dauka da sallama a bakina naji ya amsa sallaman nawa cikin wani murya.
Sai kuma mukai shiru gaba dayan mu can yake cewa Fatima yanzun kan na sheda dole akai maki a kaina don yadda kika nuna baki damu ba dani.
Nace dole dai akai muna da juna aikama kasan kabar mai gadi gidan ka baka damu dani ba.
Hmm naji yace yace wanan kuma mafanan ki na rasa ke wata irin yarinyace haka mai taurin kai dake.
Kina nufin idan munzuba ni dake waye zai sha wuya a cikin mu ne wai kefa mace ce ba kowa ba.
Nace oh don ina mace shine akace ban san right dina ba ko komay ?
Idan kina ganin halin da kika dauko yi min zai sa na daina abinda kike ganin zan daina sai ki matsayi ai gafili ga mai doki.
Nace ban ma son ka bari don ni ai nafison kabari don Allah da iyayyen ka da zurian ka masu zuwa.
Yace oh ashe kin sani kik matsawa wa kanki nace ni ban matsawa kaina da komai ba sai dai kawai ina tsoron mu,amulane da wanda baida tsoron Allah kawai.
Yace na gode nima haka nabashi amsa sai naji ya furzo iska yake cewa ance Rabin dan musa na gurin ki ko ?
Nace oh iyaba tananan yanzun ma ta kwanta don muna tare yace ok ina son ki kula da ita sosai don tana da mutunci sosai nace insha Allahu zanyi yadda kace.
Bashar ta kawo maki kayan abinci nace eh amma

Please Login or Register in order to submit comment