Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

jefi jefi.
Kwalaben kayan shaye shayen ta ne ta zube su a kasan tana dan mixed din su a cikin wani drinks dake gaban ta.
Mahaifiyarta ce tashigo dakin unexpected taji muryan ta a bayan ta tana fadin,
Raihanatu ina kika shiga ne haka tun safe robon ki da gidan nan ne?
Daga sama taji muryan uwar nata a dakin shigowan uwar bai hanata yin abinda takeyi ba a lokacin.
Idon mahaifiyar kar akan kwalaben maganin da take juyewa daya bayan daya.
Wanan kuma may nene kike yi haka tambayan ta ya koma akan abinda taga Raiha din tanayi a zaune daga ita sai yar farar shimi dake jikin ta.
Raiha tace cikin rashin damuwa ko tsoro magani nake hadawa na dan sha kafin na kwanta.
Amma ai wanan maganin haka masu yawa kamar ba na ciwo bane?
Raiha ta juyo tana facing din uwar ta take cewa, ba wai na ciwo bane ko wani abu kawai dai don naji garau ne a raina.
Da mamaki mahaufiyarta ke kallon ta tace kiji garau da shan wanan uban kwalaben haka.
Raiha tai murmushi tana cewa kai haba mama wanan aiba komai bane kawai dai muna shan shi ne don ya karawa mutum lafiya da karfi.
Raiha, Raiha kodai shaye shayen da yan unguwa suke fadi a kan kinayi gaskiya ne.
Hmmm Umma kada ki dauki zancen hassadan su a gaskiya mana hassada ne kawai irin na mutune da zaran sunga kaci gaba.
Tana fadin haka ta dauki cup din da ta zuba drinks din a ciki ta kwankwade Umma na cewa ke, ke, ke
Yanzu Raiha wanan uban maganin zaki durawa cikin ki kina da hankali kuwa Raiha?
Haba Umma relax ba zai min komai ba don ba yau na fara shan shi ba ai.
Innalillahi wainna alaihim rajiun, Umma take fadi yaunzu Raiha irin rayuwan da kika zabawa kanki ke nan?
Mace da ke kike shaye shaye haka ko acikin shaye shayen kuma sai naga naki yafi ma wanda nakeji karfi.
Hmmm kawai Raiha tace tare da kokarin mikewa tsaye take wani jiri ya dauke ta takoma ta zauna.
Umma ta kara saka salati tare da tafa hannun ta biyu tana fadin na shiga uku ni Lami yanzu Raiha ashe da gaske kina shaye shaye,
Sai kuka tajuya tabar dakin cikin tashin hankali ta samu mijin ta dake daki zaune yana shan shayin data hada mashi.
Ganin matar shi ta shigo tana kuka yasa shi saurin cewa, may yafaru Lami,?
Gefen shi ta samu ta zauna tana cewa malam ashe, zancen nan da muke ji gaskiya ne akan wanan yarinyar Raiha.
Zancen may ye gaskiya Lami?
Ya tambaya cikin son jin ba,asin zancen da tazo mashi dashi wanda bai fahinta ba.
Tace zancen shaye shayen da Tanimu yazo maka dashi tana yi bamu bincika ba muka haushi da fada.
Yau sai gashi Allah ya nuna min nagani da idanuwa na ta fashe da,wani irin kuka cikin tashin hankali.
Malam bai san lokacin da ya cire hular kan shi ba ya fara fifita dashi a hankali.
Yana fadin Inna lillahi wa,inna alaihim rajiun, yanzu ita Raihan abinda take yi ke nan har a gidan nan.
Ya mike cikin sauri ya nufi dakin Raiha inda ya samay ta har syrup ya fara aikin shi a kanta tana kwance daga ita sai dan shimin dake jikin ta tai dadaya da ita.
Yace ke Raiha, Raiha fa dake nake magana ko bakijina ne wai?
Raiha ta dago kai cikun mayen da ya dauki caji a jikin ta tace haba Baba please ka barni barci nake ji .
Inna lillahi yake maimaitawa don ganin abinda idon shi yagane mashi kan yarsu Raihanatu dake buge lis a cikin maye.
Haka suka kwana cikin tashin hankali a wanan daren don sun kasa runtsawa.
Malam sai fadi yake yanzu ashe kallon da mutanen shiya suke min ke nan ban sani ba suna min kallon mutumin da,ya,kasa tsare tarbiyan gidan shi.
Mutumin da baida kwabo ko tace ga iyalin shi suna,min kallon mahaifin yar maye a cikin shiya.
Lami tace nifa malam dama na dade ina,zargin wayewan yarinyar nan yai mata yawa wanan facali da take da kudi yadda,ranta ke so a ina take samun su haka.
Mijin yace bar wanan zancen Lami yanzu zancen shaye shayen nan zamuyi muji yaushe ne tafara shi har girma mata haka.
Washe gari Raiha bata tashi da wuri ba sai musalin karfe tara na safe tafito daga dakin ta don yuwan ne ya,tashe ta.
Dama shi kayan maye haka yake da zaran ya sake mutum sai ya ji cikn shi tankar babu ko hanji a cikin sa.
Sai neman abinda mutum zai zuba a cikin shi a haukace zai far ma duk abincin da ya samu yaci.
Brush tayi ta na kokarin shiga daki taji muryan mahaifinta yana kiran sunan ta alokacin.
Tai mamaki da taga har wanan lokacin baifita ba kamar yadda yasaba fita tun da farar safiya zuwa sana,an shi ta aski da yake wanzanci.
Nam Baba ta amsa mashi cikin nuna jin wani dar da kiran shi don bata san wai tayi laifi ba.
Tazo ta tsugun na gaban shi tana cewa gani Baba, wani irin kallo ya watsa mata amma ko ajikin ta.
Gani baba ta kara maimaita mashi cikin ko in kula da kallon da yake mata a lokacin.
Yanzu Raihanatu shaye shaye kikeyi a,rayuwan ki bamu sani ba ashe.
Kallon inda mahaufiyar take tayi cikin wani yanayi daya ba uwar tsoro sosai don bata san yarinyar takai haka ba ma sai yanzu ta hango a bubuwa da dama daga diyar tasu.
Baba bafa wani abu mai karfi sosai nake sha ba wanda kawai zai kara min karfi ne ta fada cikin nuna rashin jin tsoro a ranta.
Malam baisan lokacin da ya mike ba yafara kai mata duka amma Raiha ko gezau batayi ba.
Ganin haka yasa shi samun guri yazube sai wani zufa ya fara karyo mashi.
Raiha ta juya zuwa dakinta, babu ko damuwa da yanayin da taga uban ta ciki sai uwar ta ce take ta faman rusa kuka wiwi.

****** ********* ******
A Abuja an kira manyan yan kwallon da aka ga sun cancanci a kira su, daga various state din wanan kasan,
Inda sadauki ya samu daga sokoto aka sashi su uku suka wakilci jahar tasu ta sokoto state.
An kara,fahintar dasu wasu abubuwan kara wayar da kai inda anan kuma aka yaba wa su sadauki da suka halarci wasan da akayi a kasar ghana da suka tafi.
Ban wasu yan wasan suka,fara sanin su a lokacin inda akai masu bayani kan zasu dawo nan bada dadewa ba don fara wasan da zasu shiga kasashen duniya,yi.
Da zasu dawo gida anbasu kudade masu tarun yawa wanda zai amfane su a rayuwan su.
Daga haka suka,shirya dawowa gida a jike dasu ga mata sai wace mutum ya zaba amma shi sadauki duk basu a gaban shi saboda mace bata a cikin ran shi gaba daya bai ma,taba jin wai son wata mace ba,a,ranshi.
Kuma Allah ya kare shi daga cikin matasa masu sha,awa ko yaushe, shi kawai baida, wani guri sai kawai ta iyayyen shi da yan uwan shi.
Cikin dare suka sauka sokoto inda yai tashan mota ta kaishi har gida da ga shi sai, yar jakar shi kawai daya,rataya kamar kulun.
Yana isa gida cikin gida ya,shiga inda ya fara karo da Nafisa kaunar shi taci kwalliya zata fita,
Bata ce dashi kalla,ba,shima baice da itaba sai ganin da tayi bai da niyan kaucewa a hanya yasata dan jaye jikin ta ta bi bango har ya shige ciki ita kuma tafice daga gidan kawai.
Ba sabon abu bane wanan gare shi don in so goma zasu hade da Nafisa bazata taba tanka mashi ba ita.
Maji dake zaune a falon ta taji shigowan shi da sallama a bakin shi, cikin fara,a take cewa a,a kai kana hanya ne dama ashe?
Yai murmushi yake cewa, yanzun muka sauka ai bamu jima da isowa ba garin.
To yaya hanya ya kuma taro da,fatan komai ba matsala dai ko?.
Yace cikin aje jakar shi saman kujera komai Alhamdullahi Maji mun samay ku lafiya,dai ko ?
Lafiya kalau muke sai godiya ga Allah .
Jin shiru yake cewa ina,su wa yan nan suke ne naji gidan shiru mana maji ta,bashi amsa da cewa.
Amira bata dade da, shiga nan gidan su Aisha ba,wai zata karbo wasu takardu a gurin ta ita ko maryam tana ciki wai wanka zatayi.
Ya zauna da kyau saman kujeran yana fadin kai na dai kwaso gajiya,wallahi tun safe bamu zauna ba muna fitowa kuma na kamo hanya don ban iya kara kwana can kuma.
Shiru baiji ance ga abincin shi ba yake cewa wai ina ita wanan yarinyar ne tazo ta bani abunci naci yunwa nake ji Maji.
Yadan fadi cikin tsigar shagwaba da kuma langabe kan shi saman kujeran da yake zaune akai.
Maji tajuyu tana fadin wa Fatima kake nufi wai ko wa?.
Sunan ta ke nan wanan yarinyar dake nan dakin nake nufi dai.
Fatima kan ta koma gida tun gama exam din ta da tana nan kaima ai kasan da yanzu tafito gaida kai kuma ta baka abinci.
Amma wayan nan sakarkarun basu san wanan basu sai faman dakilar waya kawai suka iya su.
Ke Maryan, maryam fa baki jin yayan ku ya dawo ne fito ki bashi abinci don Allah.
Sai ga martam ta fito daga ciki da murnan ta tana fadin yaya sannu da,zuwa wallahi banji dawowan ka ba.
Nan suka gaisa da ita yana tambayan ta ya makaranta tabashi amsa da Alhamdullahi.
Ta juya zuwa kitchen don dauko mashi abincin maji tace baka bugo waya kana tafe ba,balle ai maka girkin kwarai Allah yasa dai ka iya cin jagwalgwalen nasu dai ma.
Taliya ce akai jeloup din shi da manja sai kifin da,suka,dan zuba cikin shi kadan.
Tun a ido yaga abincin bai mashi ba shi yanzu da,yasaba cin girki mai dadi a gida ko yaushe shine za,a bashi wanan busashen abincin yaci.
Yana, kai cibin farko a bakin shi yaji bai ma iya hadiye wa don salaf yake kamar ba komai a cikin shi.
Kai wa yai wanan mugun girkin haka kuma,ba test ba komai abu haka,busashe dashi?
Ai dama nasan bazaka iya ci ba,don wa yan nan komai basu iya ba ni ai tun tafiyan Fatima, wallahi duk komai ya jagule min.
Yanzu dubi falon nan kamar ba yan mata ke cikin sa ina ga,rabon shi da samun gyaran kwarai tun Fatima na garin nan,
Sai lokacin ya daga ido yabi falon da kallo yaga duk a hatgitse yake ba kamar yadda Bintu da take nan take gyara shiba.
Maji tace ina da kaman wa yan nan ba zan zauna ina masu girki da,gyaran daki su sau dai suci su mike kafa kawai.
Abu na farko da yazo mashi a,rai shine yanzu ya fara sanin advantage din zaman Bintu gurin Maji da take fadin zaman yarinyar yana da matukar amfani a,gare ta musanman yanzu daba lafiya gare taba sosai.
Ya juya gurin maryam yana fadin idan bakuyi
wa Maji abinda ya dace ba,sai wa zakuyi wa a haka zakuyi aure baku iya komai ba,a,rayuwan ku ?
Amira ta shigo tana mashi oyoyo ya,dakatar da ita,da,fada yana cewa dallah gafara mara wayo kawai yanzun ace kuna gidan nan amma zaku bar muna uwa da aiki dubi falon nan
Yanzu dubi girkin nan waye zai iya cin shi haka duba,fa ki gani abu haka,busashe dashi.
Yamike tare da tsalake abincin zai fita zuwa dakin shi maji take cewa ai gashi nan in anyi magana kace Fatima yar kauye ce to ga ranan yar kauye yau don tafi yan bitmrnin iya komai.
Shi dai yafita zuwa dakin shi ya,sakey ya,bude saida ran shi ya,baci yadda yaga dakin nashi duk dashi ya barshi hakana da datti ya tafi.
Amma ai yaga da ko yana gari yakan dawo ya samu an gyara mashi shi tsaba ya shige cikin jin dadi da,shakan kamshi.
Haka ya daure yana abu tsanda tsanda tunda yanzu yafara zuwa birane yana ganin komai net sabanin yadda yakw da,can baya.

****** ********* ******
Tun zuwan Kabir gurin Bintu sukai musayan nomba dashi tun wanan lokacin bata da,shakat dashi daya koma abuja ko yaushe a cikin waya suke.
Tun bata saba ba tana,darrr dashi har ta,fara sake jiki tana,bashi amsa idan ya,bugo yana tambayan ta,abu.
Gashi da,tambaya kamar dan jarida yake bai minti biyu bai mata tambaya kan wani abuba ko wanda ya shafi rayuwan ta ko kuma,na kauyen su.
Taji dadin zaman ta da mahaifiyar ta don dan kudin da Baba ya,bata da,wanda maji tabata sai nata da tazo dashi da kuma kabir da zai tafi yabar mata su take gubtsurawa suna amfani dashi da uwarta.
Kauye ne ba,wani abin saye inba,abinci ba ita kuma dama yarinya ce da bata damu da kashi kudi ba ga banza da wofi.
Uwarta yanzu kan tai matukar kyau, don duk komadan nan da ciki yasa ta da,yunwa yanzu duk sun bace ta murje tayi kyau da ita.
Don yanzu tana ci tana sha sau uku ga yini sabani da can da,dakyat take samun koda sau daya a wuni.
Takan kira maji ko Anty Amira da maryam suyi waya dasu don su kadaine dama take da nomban su, sai wasu class mate din ta na can sokoto din.
Maji takan tambaye ta Fatima yaushe zaki dawo ne sai dai tayi dariya tace mama ai zan dawo idan mamana ta haihu.
Maji kance to Allah ya sauke ta lafiya ta ansa da Amin mama kawai sai dai a zuciyan ta takan ce wai sai dai Allah ni da,dawowa gidan nan kan.
Amira kuma takan kira ta suyi ta mata korafi don Allah ta dawo au fitinan yaya sadauki ya ishesu duk abinda sukayi basu iya,ba,sai fada da,zagi yake masu.
Bintu takanyi dariya tace halin yaya ai sai shi ni wallahi har gobe tsoron yaya nake ji gada ya,makeni.
Ke nan harda tsoron shi yasaki gudu Bintu ai bari ya,shigo sai na fadama shi abinda kikace,
Yanzu antu maryam ko kin fadi nai mashi nisa ina zai ganni ya,ma manta akwai wata yar kauye dama ya matsu na bar gidan nabar mashi amma yasani wallahi ban bar mashi mama ba,
Au haka kikace ai gashi zaune wallahi yana jinki duk abinda kike fadi tace ai gaskiya na fadi mama ce bai so na kwace mai ni da mama kuwa sai gani sai hage mutu karaba.
Ta kashe wayan dif tana dariya don tasan babu inda zaigan ta a yanzu sai dai a,waya kuma baida nomban ta ai.
Amira na kashe wayan tana dariya ita,kadai Maji take tambayan ta ita dawa haka,tana,dariya ita,kadai?
Nan take fadawa Maji yadda,sukayi da,Bintu da,amsar da,Bintu din ta,bayar akai.
Ai gaskiya,ta,fadi yayi dawani kuma ita,dai tayi gaba kuma,bai iya,rabani da,ita din.

Anyi dace lokacin da maman Bintu ta haihu mai masa tazo zagayen gidan su don haka,maji taba da sako na,barka,da haihuwa akawo wa,Bintu tabawa mahaifiyar ta.
Gwagi bata,kawo kayan ba,sai ta biya gurin mahaifin Bintu ta,gwada mashi abin arzikin da aka aiko albarkacin Bintun shi.
Nan tabawa ta shiga sake magana wau kura da,shan bugu gardi da kwasan kudi, yanzu ne da yarinya ta girma ta juya mata baya,bayan ta gama wahala da ita ta kama uwar ta.
Ita ko uwar ba kunya don taga gurin ci shine zata wani dinga haba haba da yar da ta watsar tun tana yar ficiciyar ta sai ita tasha,wahalanta yanzun kuma,an gujeta,
Gwago ce ta,bata amsa da cewa ke tabawa kiji tsoron Allah wallahi har wani wahala kikai wa Bintu gidan nan
Ko dai Bintu ta,wahala dake da,yaran ki tana,maku bauta dare da,rana,
Ai ke baki da ko bakin magana don kiri kiri kisa yarinyar nan takasa zama gidan uban ta don bakin matsin ki na tsiya.
O lalai dangin miji dangin tsiya dama ai nasan abinda kuke fadi ke nan har kukai muna,funcin da,sai da,kuka,dauke ta don kuga yadda,zanyi.
To da,kuka,dauketa don tana,min bautan da kukace na mutune ko kuwa wai.
Tabawa ban dai baki ko tsunke a cikin kayan nan wadda akace akawai ita din zan kaiwa abinta don ban iya cin amana ba ni.
Gwago ta tattara kayan suna sa,insa da,tabawa tabar gidan dasu zuwa kauyen da,Bintu take gurin uwar ta.
Ba maman Bintu har ma Bintu din kanta saida tai mamakin wanan kyauta na bajinta da Maji ta,aiko mata dashi.
Nan aka,shiga nunawa mutane kun san bakauye ba ya boye alheri komai kankantar shi .
Anyi suna lafiya don itakan mahaifiyar bintu sai tace shigan Bintu Birni alheri ne a gare ta.
Don wanan haihuwan da alheri yazo mata sabanin wanda takeyi a baya can busai busai sai kamay kamay kawai.
Don ko Muhammad Kabir da ya mutu son Bintu yanzu sai da ya aiko da nashi alherin duk da ma Bintun bata fada mai ba ji yayi gurin abokin shi na kauyen dayasa ya saka mai ido akan al,amarin Bintu din da bata masan yasaka a saka mata ido ba.

****** ********** ******
Bayan haihuwan mama da sati biyu na shirya komawa gida garin mahaifina tunda naga mama ta yi karfi yanzu,
Ba yadda batayi dani ba akan na tsaya na kara kwanaki amma naki, tsayawa.
Mama tace to idan Kabiru yadawo bai samay ki ba fa nace mama nifa ba,wai yana gabana bane mutum da mata uku yaya zanyi dashi gani da tsoron tsiya.
Asalima ni saboda,shi zanbar garin nan idan ya tambaya kice mai na koma sokoto gaba daya.
Tace kaiyya saikace ke ba diyar hausawa ba kuma musulmai zakice kina tsoron kishiyoyi.
A,a mama ba zan iya ba naga yadda mamana na sokoto take fama da,nata don haka abin tsoro yabani.
Gara na samu yaro bakauye dan uwana,a zarga min dashi yafi min ruwan idon sunan muna Abuja.
Dariya naba mamana take cewa kai yaro dai yaro ne ai abin sa,a ne ni yanzu da nake shan wahala a,nan kishiya gare ni?
Mama,naku daban ne nace ni dai zan tafi na kwashi komatsena sai yar karamar tashar garin amma,sai na rasa mota .
Akan kada,na kara kwana a garin yasa na tare wani mai mashin mukayi ciniki dashi la,asar sakaliya, sai gani garin mu har kofan dan gidan mu.
Tun daga kofa nafara jin harshen mama ta,bawa tana fada da,wata yar yan uwanta da,ta dauko riko.
Na,shiga gidan da sallama na inda na samu kafin na,shiga mama ta kewaya ban daki a lokacin.
Dakin da nake na nufa da kaya na nasamu dakin duk kashin awaki ya bata shi kuma,wai akwai mai kwana acikin sa hakana.
Ina ciki na fara gyarawa naji muryan ta tafito daga ban dakin take zuciya ta ta tsinke, don na san nadawo wa turke na mai cabo ke nan.
Na fito waje a tsorace nake da ita nafito ina cewa sannu da gida mama mun samay ku lafiya.
A darara ta amsa min da yauwa anga dama andawo ni dai nasan ai ba gurin zuwa sai gona.
Na juya zuwa cikin dakin naci gaba da gyarawa kamar yadda,na fara da farko kafin wani lokaci dakin yai neat duk da dakin hakine da,daben kasa a,kasan shi.
Na idar da,sallah magariba naji shigowan mahaifina nan nafita zuwa yi mashi sannu da,zuwa.
A bazata yaganeni yace a,a Bintu andawo ke nan yaya,su wajen maman naki nace duk suna lafiya suna gaishe ku.
Na mike na koma dakin mu tare da kunna dan chager daki mai aiki da battery.
Daga cikin dakin namu ina jin mama tabawa tana,wa Baba na mita wai gashi na,dawo wurin ta, na kasa zama da uwar nawa.
Naji Baba yai gyaran murya yana cewa tabawa ina son ki sani nan gidan uban Bintu ne bata da gidan dayafi mata wanan don haka tana da incin duk lokacin da taga dama ta shigo ta zauna iya adadin kwanakin da take son yi.
Jin firinan su zauyi nisa yasa na jawo wayana na kunna kira,a ta yadda ma,ba zanjiyo hayaniyar su ba.
Ban fita ba daga dakin sai washe gari tun da safe nafito na fara gyaran tsakar gidan mu dama har ta,wajen gidan.
Dama aikinane da nake gari da ban nan kuma ba mai yi kowa baida lokacin yin shi.
Na tara wanke wanke nafara saiga mama tafito tana wani yatsune fuska wai ita a lokacin ta,tashi daga barci.
Muryan ta naji daga bayana tana fadin kada kuma mahaifinki da yan uwanku su gani suce ina sakaki aikin bauta.
Bance komai ba,sai cewan danayi mama ina kwana.
Ta amsa,a,wulakance tana aikin girkin dumamay tana minti kan fadan su da Baba akaina jiya da dare sai fadi take dadin abindai nima na haifa a gidan don haka na wuce gori ga kowa balle ace min ni juya ce.
Ina kallo suka cinye dumay mayn su ita da,yaran ta ban damu ba na,shige daki sai zuwa rana dana yunwa zai kashe ni nafito zuwa bakin wani shago na,dan sayo garin kwaki yakai mudu biyu da,dan sugar na na,saka a hijjab dina na,shige dashi bata gani ba.
Ina zaune ina sha idona yana kawo hawaye sai ga,wanan yarinyar da mama ke riko ta dan zo gabana tanayi tana leken kofan mama tace don Allah ki san min nasha nima basu bani dumamay ba wai ba yawa su Lawal taba suka cinye da ita sai cewa tayi na kankare kanzo naci.
Kuma kanzon ba gishiri ba,komai wai haka zanci shi dan kadan ne bai isheni ba.
Gaba daya na tura mata kofin garin nace yi sauri ki shanye kafin ta fito tagan ki tace zan koya maki munafunci.
Tas yarinyar ta,shaye garin gaba daya tafita da,sauri take tabani tausayi.
Tun ranan duk dan abinda naci tare muke ci da ita, komai rashin yawan shi kuwa don a daki guda,muke kwana da ita.
A haka dai nai ta,zaman hakkuri a gidan mu da matar mahaifina watarana tabani abinci watarana kuma tace bayawa ancinye.
A haka kwanaki suka shude min zuwa satittika har wata ina gidan mu zaune kamar wata bare can.
Wata rana ina zaune na gama duk abinda nakeyi na gida kamar kullun sai ga wani yaro ya shigo yana cewa wai ana sallama da Bintu.
Kafin in magana mama ta karbe da fadin wanene kuma wanan da yamman nan.
Yaron da aka aiko yace yace nace mata wai kabir ne kafin mama tai wani magana na mike kawai na fada daki sai gani tayi na fito saye da hijjab dina har kasa cikin wanda Maji ta dinka min lokacin ina gurin ta.
Nace mama zan fita na gan shi daga garin su mamana yazo, ban tsaya jin may zata ce ba na,sakai na fita zuwa waje.
A jingine yake gabab motar shi kirar hilux irin ta,shiga kauye, ya,sanya wata koriyar shadda da akaiwa dinkin Jamfa harda hular ta

Please Login or Register in order to submit comment