Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

abinda ta,fadi yasa Amira fitowa daga dakin ta cikin sauri tana min sannu da zuwa cikin murna da jin dadi itama.
Maji tafito a hankali daga daki ganin yanayinta yasani saurin fahintar bata da,lafiya a jikin ta.
Inda,take na nufa da,sauri na,fada jikin ta sai ta rungumayni cikin jin dadi.
Ta,dago kai ta kalli gwagona tace mai masa nagode da,wanan karamcin da kikai min dawo min da Fatima,a kusa dani.
Kai amma dai Bintu badai a kauye kike ba dai ko gaba daya kin canza kin koma wata big girl dake haka.
Nan aka faea hiran yaushe rabo bayan nadan huta anmin tayin abinci nace na koshi.
Sai Maji tace naje na gaida Baba kafin ya,shige da sauran mutanen gidan gaba daya.
Ido na,runtse gami da,cewa ya Arhamanin Rahimin, ahankali na mike nafita,duk kallo suka,bini dashi.
Ina fita maryam tace maji gaba,daya, fa diyar ki ta,sake ta canza kyaunta ya,dada,fitowa a fili, jita kamar wata wace take zaune a abuja ba kauye ba.
A falon Baba na samu hjy kubura na shiga da sallama na itace tafara cewa wa nake gani haka kamar Bintun hajiya maijidda.
Na karasa inda suke gefe kadan na tsugunna ina gaishe su Baba ya nuna j8n dadin gani sosai tare da min ba,a naje gida na lake na manta da karatu a gabana.
Na dan kai lokaci a gurin Baba yana dan min tambayoyi a kan noman mutanen kauyen mu nai masu sallama nafita daga dakin.
Dakin Umma da nake jin haya niyar su na fara shiga duk sunyi mamakin gani na a wanan lokacin da kuma yanayin da suka ganni ba,wani fita hayacin da nayi banda kara kyau.
Nan dai duk na zagaya nagaida su na,dawo dakin mu nan aka zauna a ta hira inda maji da gwago suna can gefe suna,maganan su ta mayan wanda bamu san akan may sukeyin shi ba.
Sai dai yanayin Maji ya nuna min cewa tana a cikin damuwa sosai ko ba,a fadi ba.
Ban dade dasu ba na mike ina fadin zanyi sallah dake kaina.
Nan dai bayan na idar na mika,kukana ga Allah akan ya,kareni daga duk wani rintsi ko matsalar da zan fuskanta agidan mutane.
Ban fito ba na koma na kwanta amma kuma na kasa barci sai sunayen Allah maigirma nake kira ina neman agaji a gurin shi.
Tun dawowana kula,da lafiyan maji ya koma kaina ko yaushe ina daki tare da ita.
Banga Sadauki ba kuma,ban tambaya ko ina yake ba nasan dai kila baya garin ne.
A hankali natsuwa yazo min da zamana dasu don suna nuna min kulawa sam mutum bai gane cewa ba Maji ce ra haifeni ba a gidan.
Satina biyu a,sokoto nagane yanzu yanayin gidan ya kara canzawa sosai ba ruwan wani da wani a gidan har yanzu.
Amma,akwai ci gaban rayuwa,sosai da,suka,samu don yanzu budi ya kara sanuw masu sosai.
Hankalina yafara kwanciya sai dai kullun ina kewan iyayyena da yan uwana adan zaman da mukayi da,mamatabawa da sauko da,akidar nuna min tsana,a fili datakeyi.
Kuma wani abinda ya,tsaya min a,rai shine tunanen Kabir yadda zaiji idan yazo ya,samu banan nan nabar gari bada sanin shu ba.
A haka takardan makarantana ya fito wanda ban san baba yai min process ba saida yazo a hannuna.
Ranan nai murna da farinciki garda kuna don murna,saboda ban taba zaton zan samu ci gaba da karatuna ba.
Na fara zuwa makaranta tare da Anty maryam muke tafiya don makarantar daya da ita state university muke.

Wata rana mun taso daga makaranta ga hadari ta gauraye garin da kyat muka samu Napep din da zai kawo mu gida.
Ganin iska da kura ya,taso a lokaci guda nace wa mai Napep malam don Allah ka,samu dan guri ka Parker har iskan nan ya dan rage yawa don tafiyan mu a haka hatsari ne.
Guri ya samu kamar tadda nace ya dan tsaya a gefen titi kamar ance na daga kai na hango Nafisa a cikin motan wani matashi.
Yanayin dana ganau yasa gabana faduwa da,sauri na juta gurin da Maryann take zaune sai naga hankalinta a,waya yake ita, don haka naja bakina nai shiru ban fada mata ba.
Can naji mai Napep na cewa bari mu lalaba don ga alamar ruwa nan tafe da sauri yake tuki sai gamu a unguwar mu har kofan gida yakaimu daidai ruwa yana fadowa da karfin Allah.
Take ruwa ya zubu ga iska sai kamshi yanayin garin ya canza launi alaman sabon damana yazo ke nan.
Haka muka sauka shiga gida ruwa,na kada mu yana daga muna mayafin jikin mu.
Yaya Imirana na hango can tsaye daga kofan part din shi tawani kura muna ido kamar tsohon maye.
Da,sauri muka nufi hanya shiga cikin gida duk habar kafan mu iska na dagawa yana fita a fili.
Daga inda yake naji muryan shi yana fadin kai ashe cikan nan tadawo ne tubarkallah dai kan komai tsab wallahi akwai kayan dadi a gurin nan.
Banzaci maryam taji shi ba saiji nayi tace dan iska a haka dai zaka kare gindin mata.
Mukan da,sauri muka karasa ciki muna kankamay kayan mu daya jike sharkaf da,ruwan da,akeyi.
Da karfi maryam ta rura kofan falon maji muka fada ciki a guje saukar da ajiyan zuciya nayi yain da naji ruwan bai dukan mu.
Ashe maji na,falon cikin damuwan rashin ganin mundawo kafin ruwa ya fado din sai ce muna take sannuku ku shiga ku cire wa yan nan kayan kafin sanyi yakara hawan ku.
Sam ban lura da mutum a zaune ba a lokacin sai ji da nayi Anty maryam ta,saji kara da karfi.
Da sauri na juya zan kona,waje da gudu sai naji tana fadin oyoyo yaya sadauki.
Najuya da sauri inda naga ta nufa yana zaune fuskan shi dauke da murmushi.
Yace jeki cire kayan sanyin nan kafin yai maki illa,
Cikin shagwaba tace yaya ni har na manta dasu ina murnan ganin ka ai.
Nikan ban tsaya ta kan su ba na,shige daki nafara rage kayan jikina tare da zuwa faban mirror dakinmu nayi wata futu, futu dani don jikewan danayi.
Na fada ban daki nawatsa ruwa tare da,dauro alwala nazo nai sallah.
Saida na,gama komai nafito falon ina,saye da,wata doguwar riga dark blue doguwa ce rigar har kasa hannun ta shara shara nazo na zauna falon har lokacin yana zaune suna hira da kannen shi.
Zamana yai daidai da kiran wayana da akayi na dauka ina mamakin wanda ya kirani a wanan lokacin haka.
Sai na,dan basar ban dauki wayan ba don ban san mai kiranaba alokacin.
Sai kuma ga,kiran ya kara shigowa again na dauka da,sallama ban damu da cewa wai na daga daga falon ba.
Don nasan daga inda suke babu wanda zai iya jin abinda nake fadi don tsabar kwantar da muryana da keyi.
Bayan na gaisa da may shi na nuna bangane mai magana ba.
Yace haba Fatima na zaci ko a mafarki kikaji muryana zaki sheda ai tau Kabir dinki ne wanda aka gudo akabari a kauye.
Maganan shi ce ta dab sani dariya sai duk suka juyo gareni hardashi suna min kallon mamaki.
Nan na,fara bashi hakkuri ina,fada mashi yadda tafiyan yazo min a bazata nadawo sokoto.
Amma yayi hakkuri dan banda nomba shine yasa ban fada mashi ba yakara complain kan cewa ban damu dashi badaine tasa hakan.
A hankali nace na tuba sake ba insha Allahu, abin mamaki sai naji ya kwashe da,dariya tana is alright hakan ma yafi min don yanzu zan dinga samun ki available,
Uhhm kawai nace cikin murmushi.
Ina dago ido mukai arba da yaya sadauki da ya maka min wata uban harara na kawar da kaina tare da ci gaba da waya na.
Kabir yace min yanzu yana hanya zai tafi wani gurin aiki ne amma idan ya,dawo zai kirani.
Nace tau Allah yakaika lafiya Allah ya,tsare min kai.
Ina kara dago ido muka kara arba dashi dole nace mashi cikin yar murya sannu da zuwa yaya ya hanya.
A daure ya amsa min kamar wanda akasa shi amsawa dole.
Nikan namike zuwa daki sai Maji take cewa ina kuma zaki ba,aci abinci ba nace sai anjima zanci mama.
Kai Fatima kina dai wasa da cin abinci har yanzu mutum haka bai damu da cin abinci ba.
Nikan na shige abina daki ban tsaya ta kansuba don wanan mai mugun halin dake zaune a falon.
Ban dade da shiga ba naji ruwa yakara tsinkewa kamar da bakin kwarya.
A hankali na mike don na rufe window din dakin mu dake bude don feshin ruwan dake shigowa.
Karan mota naji za,a fita daga gidan mamaki ya kamani wake da karfin halin fita daga gida a,wanan lokacin da ake tsula ruwa haka masu yawa.
Mantawa nayi ina,son nasha ruwa sai na koma falin na dauka nan nasamu Maji na magana cikin takaici.
Tana cewa yanzu fita yayi cikin wanan ruwan haka ba ko ina zai tafi ba sai gurin shegen shaye shayen su.
A duke nake gaban fridge ban san lokacin da na dago ba nace mama yaya ya koma shane kuma ?
Cikin takaici tace min Fatima bari ke dai, Allah dai ya kawo min saukin wanan al,amarin kawai.
Abu sai yayi kamar ya sauki sai kiga yaron nan ya kuma koma ma halinshi lokaci guda.
Nace anya mama wanan abin ba ci gaba ake da tufka ana,wal,wala ba kuwa?
Amirah tace nima dai hakanace daki na koma hankalina a tashe da zancen danaji mara dadi.
Sai yanzu nagane abinda ya jawa maji ciwon zuciyan da akace yana barazanan kama ta.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,,


A LOKANCIN MU KE,,,,,


Da, tuna ne na kwanta barci bai dauke ni ba har tsawon wani lokaci ga ruwan da akeyi ba a dauke ba har cikin dare sai tsula ruwa ake kamar da bakin kwaraya.
Hasken wutan mota ce ta haska dakin da muke0 kwana a ciki nida Anty maryam don gyaran da akayi dan yi a gidan yanzu.
Part din Maji ne farkon shiga gidan don sauran suna daga ciki suna ganin sun shiga ciki kusa da part din maigidan.
A hankali na mike zaune na juya inda maryam ke ta barci ta yarda wayanta sai massage ke ta shigowa mata.
Window dakin na dan leka naga, mai shigowa a lokacin yaya sadauki na hango yana kokarin rufe motar shi.
Tafiya take a cikin rangaji irin nasu na yan maye kamar zai fadi ya dan dade a tsaye kafin ya bude kofan dakin shi ya shige.
Na koma bakin gado na zauna zuciyana naji ba dadi ko kadan tausayin Maji ne ya rufe min zuciya na.
Ina nan zaune naji motsinta hakan yasani sanin cewa batai barci ba idon ta biyu ke nan tana dakon dawowan dan ta tilo daya da masifa ta haushi na shaye shaye.
Haka na kwana ina matukar jin tausayin ta a raina har garin Allah ya waye muna.
Ranan bamu shiga school duk muna gida gaba dayan mu bayan na gama muna,abin karyawa don yanzu Maji ta raba muna aiki kowa da ranan girkin ta.
Na fito saye da wani buje da riga dinkin yan Niger, da hjy kubura ta sayo muna da suka je da Baba ta sayowa duk yan matan gidan hardani na samu shiga.
Ina zama nake cewa mama ina key din dakin yaya mu gyara mai, da sauri maryam take cewa nikan ba zan iya ba nagaji gaskiya yau hutu nake son yi.
Ina ganin ai yana ciki don banga ya shigo ba Amira tace naga fitan shi da safe da kayan wasa a jikin shi.
Mikewa, nayi tsam na dauki kayan gyaran wuri na fice daga part din mu nasa key din hannuna dakin ya bude.
Bin dakin nake da kallo duk da dan sauyi da dakin ya samu an saka mai kayan zamani a cikin sa.
Kafin na fara gyara na fara aiwatar da nufina da yakaini dakin, daga nan daga can ina bude wani kwali dana gani saida naja baya da sauri don tsoron da naji.
Kwayoyi ne ciki irin masu tsada da,akai muna lecture a kasan makil a cikin kwalaye.
Gaba daya na kwashe su da,sauri nakai toilet din dakin na watsa ciki nai flushing din su suka wuce,
Haka nauwa sauran syrup din da nagani kai duk wani magani sai da na turashi a toilet din ya wuce.
San nan na,gyara mashi dakin tsab nafito da sauri kafin ya,dawo ina fitowa nazo na zauna ina jiran yadda zamu kwashe dashi.
Bayan wani lokaci muna zaune sai hira muke kwasa tsakanin mu ya fado dakin idanuwan shi sun kade sunyi ja dasu.
Yan uwan shi ke mashi sannu da zuwa amma ni ko kallo bai isheni ba don nama raina da,al,amarin shi gaba daya.
Magana suke mashi amma,bai iya,basu cikaken amsa sai cewa yayi Maji wa ya gyara min daki na.
Wani kallo ta,watsa mai kamar na tsana tace wakasan yake da,kokarin haka,ba Fatima ba.
Inda nake zaune da,waya ina game ya,kalla kamar zaiyi magana sai ya kuta kawai mikewa yayi har yakai kofa yace tare da kallon inda nake zaune.
Ke kawon min abin karyawa na daki zan watsa ruwa ne yanzu.
Maji tace bana son suna shiga dakin ku idan kuna gida bari mana ta mika mai maji Amira ta fadi hakan a lokacin har na mike ko tsaye don na,shiga kitchen.
Ance abu ga manya ashe uwar ta dan fahinci da,akwai wani abu don haka ta kyale mu.
Saida na dauki kayan zuwa dakin ta saka hijjab din ta tabiyo bayana batare da sanin kowa ba.
Ina shiga ban san yana tsaye daga kofa ba sai ji nayi an kai min shaka da karfi yana fadin Uban wa ya baki izinin shigowa dakina ki kwashe min kaya.
Ina kikai min pills dina yar iskan yarinya kawai mara mutunci.
Idanuwa na,sun futo sunyi ja don matsan da nasha jinake kamar zan shude.
Yakara cewa uban wa ya,aikoki ki kwashe min kayana?
Muryan maji mukaji daga bayan mu tana cewa, ubanka ya turo ta ta,kwashe mara mutunci kawai sake min yarinya kaji.
Ya sake ni da sauri sai da naji wani iska mai sanyi ya ratsani lokaci guda, ta juya tana kallona take cewa ina abinda kika kwashe mai din?
A hankali nace mata na,yi flushing din su a toilet sun wuce, tace kwayan ke nan ko nai shiru ban bata amsa ba.
Ta nuna min hanya tace zoki wuce kinji rabuda dan iska mara mutunci kawai, da,sauri na,fita zuwa part din mu a hirgice dani.
Azuciya ta ina cewa anya zan iya kuwa wanan irin shaka haka kamar zan shude lokaci guda.
Na zauna jiki ba karfi sai mazurai nake da idona can sai ga maji tashigo na zaci zatai min magana amma sai naji tayi shiru batace min uffan ba.
Ina nan zaune sai gashi ya shigo dakin cikin shigan shi na mutunci zaka dauka wani mutumin kirkine can idan ka gan shi a lokacin.
Magana yake wa Maji babu wanda yaji may yace mata sai dai mukaji tace Allah ya tsare kawai.
Ba irin yadda ta saba mai addua ba idan yace zai tafi wani gurin.
A,a yayana tafiya kuma zakayi yau bayan jiya kadawo?.
Yace ba dadewa zanyi ba kaduna zan tafi akwai wasan da zamuyi ancan yau da yamman nan gobe zan dawo.
Har kofa suka,rakashi cikin jin dadi a ran su suna tayi mashi adawo lafiya yana daga masu hannun shi.
Maji batai min magana ba sai da rana na idar da sallah ta kwala min kira nazo da sauri ina fadin gani mama.
Samu wuri ki zauna tace min ida na na kai zaune a kasan ties din dakin nata.
Fatima fada min komai kada ki boye min don naga ke kina da hankali kinfi sauran tunane.
Nafara magana,saiga Amira tashigo hakan bai hanani fasa maganan da zan fada mata ba.
Nace tun fitan shi cikin dare jiya ana ruwa nagan shi ta,window dakin mu har ya dawo a cikin maye banyi barci ba.
Naga kuma yashigo da leda yana tangadi haka yasani sanin cewa da kayan mayen ne ya dawo a hannun shi.
Shiyasa da,safe nace zan gyara dakin nashiga ba fara neman su sai gasu na gani nan na nuna mata hoton su dana dauka a,wayana dakuma yadda nai flushing din su.
Allah yai maki albarka Fatima, da yanzu duk wanan abin shaye su zaiyi a cikin shi tayaya wanan bazai wa mutum illa ba wai.
Nan take fadawa Amira tun da yazo rai a bace yana tambayan wa ya gyara mai daki nasan akwai magana shiya da yace takai mai abinci don ban taba jin yace haka ba nasan akwai wata a,kasa.
Bin su nayi na,samu ya shaketa wai sai tafito mashi da kayan shi sai gani.
Amira tajuyo inda nake race kai Bintu akwaiki da karfin hali wallahi ai danice sai kawai na,suma.
Nace niko muddi ina gidan nan anty naga yayi abin shan sa na dauki alkawari sai nai mai magana.
Baki, gani zai kashe muna uwa da bakin cikin shine anty?
Murmushi Maji tayi sai ta kara jin Bintu ta,shiga mata a,rai sosai fiye dama baya yanzun saboda ita tai wanan kasadan haka.
Amma a fili cewa Maji tayi kiyi a hankali Bintu kin san karfin ku ba daya,ba dashi badon Allah ya kawoni ba da Allah kadai yasan irin dukan da zai maki kan kayan mayen shi.

****** ********* ******
Tuki yake amma zuciyar shi sai faman tukuki takw mai yana kitayatta idan ya samu sa,an Bintu irin dukan da zai mata watarana.
Haka ya isa ya kira maji tana kallon kiran shi amma taki daukan wayan nan ya gane har yanzu fushi take dashi ke nan.
Da yamma ma bayan sun gama,ball yakira sai Bintu dake falon ta dauki wayan tasan shine amma sai cewa tayi mai wayan bata kusa ta kashe wayan kit.
Haushi da takaicin yarinyar suka rufe shi a lokaci guda yace a fili, I will deal with dis girl.
Bari na dawo zata sha mamakina don naga akwai raini a kanta.
Ance kowani mahaluki danasa irin baiwan sai dai wanda ya,rena nasa kawai amma kowa da irin wanda,Allah yai mai.
Hakane ga,sadauki don yanzu yana cikin matasan da kasa ke alfahari dasu a fagen kwallon kafa.
Don idan yana a cikin kwallo Allah na bashi sa,an jefa kwallo ga raga, yaci duk tsananin wasa idan ya kama sai yakai gola.
Suna gama wasa washe gari ya kamo hanyan sokoto bai iso garin ba sai zuwa yamma sosai ya iso gida.
A lokacin muna,gyaran falon Maji duk da,ba aikina,bane amma ina tsaye ina,taya anty maryam mofing din kasa.
Sallaman shi yasa gaba daya suka juyo kan shi suna,mashi sannu da zuwa.
Amma banda ni da na zage ina,aikina hankali a,kwance.
Sadauki ya samu kujera ya zauna akan daya daga cikin kujerun falon nan suke ta tambayan shi ya hanya ya wasan su na can.
Naso na share shi don ina cike da takaicin makuran da yai min jiya kafin ya tafi tafiyan dayayi.
Sai nai tunanen bari dai nagaida shi kodon mahaifiyar su dake zaune din bata,rage ni da komai ba na rayuwa.
Don yan magana,sunce ko lahira wani tana cin albarkacin wani, na dan waiga gurin da yake zaune ya wani lumshe idanuwan shi nace.
Sannu da dawowa ?
Tankar a mafarki ya tsinkayi zakkakan muryan na ina,gaidashi.
Da sauri ya,wani bude idanuwan shi, yana kallo na na zaci ba zai karba sai naji yace yauwa.
Ban kara bin ta kan shi ba naci gaba da,abinda nakeyi a lokacin, ganin da nayi bai bar cikin falon ba yasa na aje mopan ina cewa anty maryam ki karasa sauran zan shiga ciki.
Dakin mu na nufa duk da magariba ne amma sai na,fada kan gado in tunanen ashe kuwa zan iya taimakawa Maji kuwa.
Shigowan Anty maryam din daki yasa ni dakatar da,shawaran da nakeyi a lokacin.
Tace lalai ma Bintu watau gudowa kikayi kikaki karasa,min aikin ko?
To tashi yaya yace ince ki hado mai abin sha yasha kafin ya tafi sallah.
Nace anty ke mai zai hana ki hada mashi nifa ban iya masifan shi wallahi.
Mutum ko yaushe a murtuke kamar mugu sai faman bakin rai da hararan mutane.
To naki yake so ai yana ganina,baice na,hado mashi ba,sai ke, yake son ya,wahalal.
Ta fadi hakan cikin yanayin zolaya tare da yin dariyar keta a fili tana ta darawa.
Nace wallahi anty badon mama ta haife shi ba,sai nace yayi gadon mugun ta,sosai.
Maryam ta juya tana fadin lalala haka,kikace mashi bari naje na,fadawa Maji kince yayi gadon mugun ta a,gurin ta don haka,baki hado mashi.
Da sauri na mike na,sha gaban ta ina cewa don Allah anty yi hakkuri kada ki hadani da mama barin fito na kawo mashi.
Dariya tasa min tace koke fa aikw ce da shegen rashin ji kike taba mai kayan shi.
Na,jera ruwa a jug da,cup cikin dan tiren su na,roba nafito mashi dashi falon .
Yana zaune a,falon har wanan lokacin ya,dauki kafan shi daya,ya,dora,a,dayan yana,kallon news din da ake a,tashan NTA.
Na kai turen gaban shi na aje da zuman na bar gurin.
Yace waye zai zuba ruwan da kika girke kamar wata,bakauya haka dake sai shegen sa ido.
A ya,tsine nace ai dama yar kauye ce ni.
Yace ke baki da kunya fa don naga kina,son raina ni a gidan nan don kin samu guri.
Nace a hankali badai a,guri ka,na,samu gurin ba ai, da hanzari na,mike na,shige ciki kafin ya,furta,wani abu.
Nan na barshi baki bude yana mamakin da,alajabina sai ya kuta,
Yana kutawa daidai Maji tana,fitowa da,alwalan ta,do ita,saidai ta jira kiran sallah kullun haka dabian ta yake.
Ta bishi da harara tana cewa kada ka,soma taba min yarinya wallahi za,ajimu dakai a gidan nan.

Da,dare muna,zaune abinci kowa ke ci sai gashi ya shigo falon wanan karon ya canza kayan jikin shi zuwa wasu kanan kaya masu matukar kyau na maza.
Ya zauna ba,wanda tai azancin mikewa ta bashi abinci nima da nake taimakon shi ina,bashi sai na,share shi kawai don yanzu ban ganin kimar shi kaman da can baya.
Waya na dake gefe yai kara don haka nakai hannuna da sauri na dauka don ganin kowaye mai kira,na.
Kabir ne, yake kirana da,sauri na dauka don kada kiran ya tsunke a lokacin.
Da murmushi a,fuskana nake cewa Assalamu alaikum sahibi rayuwa,
Ya,amsa da cewa haba Fatima kishin ruwan rashin jinki da,ganin ki yana,son illantani amma,ke ko a jikin ki baki damu daki kirani ba.
Na dan langabe kaina kamar yana,kusa dani nace, cikin yanayin tausayawa.
Nace wayyo Muhammad Kabir dina,wallahi ba,haka,na,bane kasan yanayin karatun dana,fara ne ba hutu yanzu, amma nima na damu da na gan ka ai.
Ya ce hummm saika ce dagaske Fatima keda har yanzu baki iya,sakewa dani idan ina

Please Login or Register in order to submit comment