Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

fara zargin ko dai yaya koma ruwa ne wai don yanayi yau da na gani akwai magana gaskiya.
Ganin shi zaune yana waya muryan shi kaman mai jin barci ko kasala haka ya kara tabbatar min da zargina akan shi.
Na nufi inda mama take zaune, cikin murmushi nace mama ashe alheri ya samay mune haka yau ?
Eh amma ai bai gama ba don banga ya nuna min naki ba duk cikin tsaraban.
Nace kai haba mama kullun fa ana bani don yau kawai ai ba komai bane kila ya manta da nine kawai.
Murmushin manya mama tayi tace ya manta dake Fatima, haba magana dai yana da dalilin yin hakan da yayi kawai.
Ya dago still cikin irin muryan farko da yake waya ba ko darr a ran shi ya ce, wai wanan yarinyar ban mata ba ban dai sayo mata bane ai na fada mata tun a cikin waya ba zan sayo mata komai ba.
O ko gadarare ya mike tsaye tare da gyara wandon shi da ya dan takure don zama yace eh maji.
Sai ya fice ko mama sai da tai mamakin wanan irin tsauri da yai mata yau ido da ido haka don ba halin shi bane bata ansa a tsatsaye.
Yana fita dakin shi ya shiga dakin duk a hargitse haka ya kwanta rubb da ciki don tun daren jiya yai mugun hadiye kwayoyi ko zai rags damuwan shi a ran shi.
Duk abinda nake hankalina yana ga yaya sadauki don haka nace wa mama zan shiga gurin gwagona don tana gari tana fama da ciwon kafa.
Tafe nake ina tunane abinyi sai wata zuciya tace min gwada dai ki gani ko zargin ki hakane ?
Ina tura kofan ga mamakina dakin da yake a rufe ko yaushe, sai na samau shi a bude, kamar na koma don na hango shi a kwance rubb da ciki kamar yana barci.
A hankali nake bin dakin da kallo har na hango wani farin roba saman dan stoll din dake dakin yana dagwara kaya akai,
Na jima gurin ina kallon roba don zargina ya zama gaskiya ko naga evidence da idona.
Zan juya naji yace Fatima,
Jikina ya dauki rawa kamar na ruga a guje don tsoro, ya ce may ya kawo ki dakina ?
Bance kallah ba nai shiru,
Yakara cewa uban wa yakawo ki dakina nace maki?
Ya dago daga kwancen dayake yana fuskan tana idon shi duk sunyi ja jajir dasu.
Bance kala ba sai karasa shigan danayi na taka har zuwa inda roban drugs din yake na dauka nace ga abinda ya kawo ni dama kuma nagani.
Komawa yayi ta,kwanta,lamo kamar ya koma,barci nikuma ina tsaye na kasa daga kafata nai bar mashi dakin shi.
Lokaci mai dan tsawo na zaci barci ya koma duk a tsorace nake a lokacin,
Nafara tafiya sai naji yai yar dariya da sauri naja na tsaya cikin tsoro da sauraren shi.
Ga tsoro ya kamani ban san gulman da ya kawo dakin shi ba don gani kwam kuma a part din samarin gidan gaba daya.
Hawaye ne na fara zubar wa daga idona a hankali ba tare da ya dago ba yace kuka kuma again cikin magana kamar rada ya fadi hakan?
Don Allah yaya kayi hakkuri dama zargi nake tun dazun dana gan ka a haka ?
Murmushi yayi tare da mikewa zaune yace, ashe bayan gulma har kin zama C I D ban sani ba ?
Haka kawai na tsinci kaina cikin karfin halin fadin gulman da nakeyi a inda ya dace nayi nakeyin shi ba hakana kai tsaye bs ga abinda ba damuwa na ba.
Fuska a daure yace, lalaima yarinyar nan ta raina ni wallahi sosai, zaki gane baki da wayo don gobe baki karawa wani bakin shishigin tsiya irin haka.
Wani irin naji cikina ya ansa kululu nace a raina yau ko na shiga uku nakawo kaina da kaina.
Amma afili nace duk abinda zakai min nasan akan kauna mama kai min don irin halarcin da take min a rayuwana komai zan iya yi akan farin cikin mama don bata nuna min banbanci ba a cikin ku.
Shiru mukayi dagani har shi ba wanda yai magana don kukan da yaci karfina a lokacin.
Ba tare da fargaba ba naci gaba da cewa why yaya why baka tausayin mahafiyan ka why please ?
Kai kadaine da namiji da Allah ya bata a rayuwan ta kaine take tunanen samun farin ciki a gurin ta.
Yan uwanka da ma mu dake a karkashin inuwan ku gare ka muke fatan samun budi a rayuwan mu,
Amma kai yaya baka tausaya mata baka jin kan ta baka tuna irin gorin da ake mata tsawon lokaci a gidan nan a kan ka why baka tausayawa kan ka da mahaifiyan ka ne please?
Kafi son ko da yaushe ka zama abin kyama ga al,umma da kuma abin kwatance a gari yaya kawai Allah kabar wanan harka ka dage da rokon Allah da bayar da sadaka akan Allah ya rabaka da wanan halin kodon goben ka.
Ina kaiwa nan na fara tafiya zanbar dakin yace Fatima, naja na tsaya tsaye cak guri guda.
Ido ya zuba min na dan lokaci yace wanan magana ta tsaya iya ni dake a nan.
Na girgiza kaina nace har abada bazan taba tona asirin dan uwana ba ga wani kai dai kadai tsoron Allah idan wani baigani ba ko yaji ai Allah daya hanamu shan maye yana kallon ka.
Murmushi yayi tare da mikewa tsaye daga zaunen daya ke ban tsan mani har ya kawo gareni ba sai ganin shi nayi a gaba na ido da ido muke kallon juna dashi.
Banyi wata alaman ta razana ko kadan kada ya gane a razane nake lokacin dashi.
Ya nuna ni da yar yatsan shi yace ban san koke wata irin shu,umar yarinya bace da baki da tsoro haka nima ina mamakin kaina da nake tausaya maki amma tafi babu komai zamu kara haduwa wata rana.
Nace kadai tausayawa mahaifiyar ka da kan ka kafin har mukai ga kara haduwan.
Kuma bani fatan haduwan ya kasance irin wanan zargin a kan ka sai da ya zama wani abin alheri can daban.
Roban kwayan na hannu na fita daga dakin tabi bayana da kallon mamakin irin karfin halin dake gareni haka.
Sam banda tsoro ko shayin wani a idona yadda ya hango cikin kwayan idona gaskiya ce sahihiyar ta na fada mashi kuma na fita.
Ina tafe ina sharan hawaye har nakai gidan gwagona sai da na samu gidan yana rufe tafita ke nan .
Na juyo na dawo gida tareda boye roban kwayan a jikina har sai da na kai part din mu ina shiga mama tace har kin dawo ne nace bata nan tafita.
Amma kuma ya fuskanki kamar kinyi kuka na dan yi yake nace kuka kuma mama?
Banyi kuka ba mama daga haka na shiga daga ciki sai kuma mama ta fara zargin ko dai tsaraban da sadauki bai kawo min bane ya bata min rai har nai kuka?
Ina kwance daki saman gadon mu kaina sama kafana suna zufe daga kasan gadon, na dan jingina jikina da kan gado.
Ban san shigowan ta dakin ba don nai zurfi ga tunanen da nakeyi a lokacin.
Fatima naji ta ambata abinda yasani saurin dago kaina ke nan ina kallon ta da sauri ina kokari gyara zamana da kyau.
Itama dai zama tayi daga gefe na kadan tare da kura min ido kamar mai nazarin wani abu a gare ni.
Abinda yaron nan yai maki ne yasa ki kuka ko?
Da sauri na girgiza kaina nace wallahi Allah ko daya mama ko kadan ban sa haka a raina ba.
To may yasamay ki kai kuka da fitan ki yanzu, don ba haka kifita ba a gidan nan.
Dukar da kaina nayi kasa nace a hankali ba komai mama,.
Yanzu har takai lokacin da zaki iya boye min wani magana a cikin ranki.
Da sauri na kara dago kai nace wallahi mama ban boye maki ba sai nai shiru.
Bazaki fada min ba ke nan ko?
Maimakon nai magana sai na sake kuka shiru tayi tare da kura min ido har tsawon lokaci can tace nace zancen tsaraban da ya rabane yai maki cin fuska kin ce a,a.
Wallahi Allah mama bashi bane kuma ba komai, ikon Allah inji maji ba komai kike wa kuka ba to may yakawo kukan?
Mama yaya ne sai kuma nai shiru don, na tuna da zancen alkawarin da nayi bazan fadawa kowa ba.
Hakali a tashe tace yaya yai maki may hankali a tashe take tambaya may yai maki Fatima ?
Fada min mana nace may sadauki yai maki ne wai,?
Taba ki yayi ko may ?
Nace da sauri a,a mama don nagane may take nufi da tambayana tabaki yayi.
To may yai maki nai shiru nace mama ba komai bane cewa yayi wai na faye yau shiyasa maza ke ganina .
Sai naji tai ajiyan zuciya tare da dafa ni tace kyaleshi ai munyi maga in don zancen Usman ne ya fada min yaron ba mai gaskiya bane.
Nace cikin kuka tau mama ta ce ki kwantar da hankali Allah zai kawo maki wani wanda yafi Kabir insha Allahu.
Tace karbi wanan kayan daga cikin kayan lefen da ya aje ne na debo maki kema a matsayin naki tsaraban.
Da sauri cikin girgiza kai nace mama a barshi wallahi ko kadan raina bai baci da rashin kawo min ba don ai yasaba kawo min.
Au kyautana ne kuma baki bukata ko may na girgiza kaina da sauri na sa hannu na karbi kayan dogayen riguna matsu kyau da masifan tsada har guda hudu.
Nace amma mama kaman kayan su yi yawa fa tace nifa na baki Fatima nace na gode mama.

****** ********* ******
Da yamma daya daga cikin rigunan nai kwaliya dashi kaman yadda suma su maryam shi suka saka sai dai nawa yafi nasu tsada da haduwa, nisa ba kusa ba.
Sam ban san yana cikin falon ba nafito cikin dogon rigan mai maroon clour sai tsakiya a bude yake an yi mai kwalliya da wani silk dark blue da duwatsu har kasa, hannun rigan manya manya ne shara shara dashi .
Kwaliyan yai matukar karbana fa kamshi turare na na white musk da ko yaushe shi nake shafawa a jikina da tufafina.
Haka kawai ganin shi zaune yasa kirjina bugawa a lokaci guda yana zaune cikin shiga ta kamilan mutane.
Masangalin kujera kawai na dafa nace ina wuni yaya ?
Kamar kullun wanan yaudararen idon nashi ya watso min ya na kallona a fakaice, da su.
Kai Bintu wanan hadaden rigan fa kuma maryam ke tambayana don bata san dashi ba.
Nace daga mai kauna na, a takaice.
Kan shi kawai ya girgiza don jin amsan dana ba maryam din a lokaci guda, wayancewa yayi don yasan inda magana ta dosa.
Na kalli maryam nace akwai wani tambaya ne kuma anty ?
Ai ni dama nasan da,wata a kasa tunda naga ba,a baki taki a fili ba nasan zance ya canza ke nan.
Nace wanan kuma zargin ki ne anty ni uwata mai kaunata tabani shi don tasan nina dace dasu.
Da sauri suka juya gurin Maji da idanuwan su suna mamaki wanan riga mai bala,in kyau yaya akayi tabani shi gasu.
Maji bata bada fuskan tambayan ba balle su san gaskiyan maganan don haka sai kowa ya share zancen.
Ganin yanayin shi duk a tsarge ya ke lokacin saboda yana ganin sai na fadawa mama zancen kwayoyin dana kwaso daga gurin shi.
Yana zaune ya rafka uban tagumi sai sauraren zancen, kanne shi yakeyi ba tare da yai magana da kowa ba sai kace wanda aka aiko ma wani sakon tashin hankali.
Daga inda mama take a zaune muka ji muryan ta tana cewa ku tashi ku bamu guri zanyi magana da yayan ku.
Hakan yasa muka mike daya bayan daya muka koma daga cikin dakin mu.
Shiko jin abinda mama ta fadi yasa shi saurin dago kan shi da sauri yasan ta faru takare kenan yanzu sai da munafukan yarinyar nan ta tseguntawa maji zancen nan aiko sai ball da yar iska gidan nan algunguma kowa ya huta.
Tace Baba na magana nake son yi da kai akan Fatima, yace shike nan yar iska tafadi ashe.
Ba karamin kokari yayi ba gurin gyara natsuwan shi tare da dan dagowa daga kujeran yana fuskantar uwar.
Mama tace ina son ka fada min gaskiya may ya hada ka da Fatima dazun da rana tashigo gidan nan tana kuka?
Yace maji ita may ta fada maki nayi mata da ta shigo?
Kai ma kasan halin Fatima da zurfin ciki da kyat na samu ta dan fada min wai kace tana kwaso samari kala kala a gidan nan.
Yanzu har wasu samari Fatima ke dasu ina bayan wancen da Allah baiyi auren su dashi ba sai wanan da kace baka amin ta dashi ba kuma ta daina nagani.
A jiyan zuciya ya sauke yace ta rufani ke nan ashe ai nazaci bata da,wayo ne ?
Tace tunda kai mata fada kuma taji banga abinda zaisa kuma ka kara matsa mata ba akan zancen.
Murmushi yayi yace maji ni fa duk abinda nake mata a saboda ke nake matashi don tana karkashinki ne.
Idan da a, wani dakin take mai zai kaini saka mata ido da daukan mataki a kan ta amma tunda bata son fada ai shike nan.
Maji tace dakata malam yarinyar nan fa amana take a gurina ka sani amma irin yadda naga ka dauko tsangwama mata bazan lamunci hakan ba gaskiya.
Yanzu irin cin fuskan da kai mata ka bawa kowa tsaraba a gidan nan amma ita ka hana mata kayi daidai ke nan Baba ?
Amatsayinta amma a guri na ina duk abinda kaga naiwa yan uwanka ita ma ya dace kai mata tunda ni bani banbanta tsakanin su.
Waya san ta hanyan da zata taimaka muna itama watarana shi mutum fa rana garw shi ta inda ba,ai tsanmani ba.
Yace maji yin haka bada wani manufa nai mata hakan ba kawai dai dama alkawari nai mata cewa idan bata gayar da mutum bazan mata tsaraba ba.
Tace wanan matsalar kace don ni na bude akwatin kayan lefen dake aje na zaba mata wanda ta dace da ita.
Ya dago kai kamar zaiyi magana sai kuma yai shiru can yace ai shike nan ko?
Idan kuma akwai abinda ya dace akara mata daga ciki sai abata suma su Amirah abasu man shafin da turare da sauran abubuwa suyi amfani dashi.
Tunda ba wani abin kuma za,ayi da kayan ba yanzu ai, ko ?
Kamar yaya ba wani abin za,ayi da kayan ba ka manta da maganan mahaufin ku ne da yace nan da wata daya ku fitar da matan da zaku aura.
Murmushi yayi yace maji ni ina zani na nemo mata nan da wata daya hakkuri dai Baba zai yi muna har lokacin yayi.
Mama tace wanan kuma maganan ku ne da mahaifin ku idan baka fitar va ai shi ya maka mata da kan shi.
Ya zaro ido yace haba maji kamana za,ace za aiwa mata kuma ai ni yanzu na wuce wanan ko.
Wancan ma da kukayi da farko ba,aji dadin shi ba balle yanzun ace za,a sake wani kuma again idan lokacin yi yayi ai za,ayi din ne maji.
Ina ruwana ina zaune ni a dakina matsalan ku ne da mahaifin ku ni banda na cewa ai.
Duk hiran da suke da uwan hankalin shi yana akan zancsn abinda ya faru da rana tsakani na dashi.
Mama ta kwala muna kira tace ku fito tun dan uwan ku bai fita ku kara mashi godiya ya baku kayan kwaliyan dake cikin akwatinan shi gaba daya wai ku raba ku uku.
Godiya mukai mashi sai dai yana kokarin ganin idona danake boyewa a bayan Amirah.
Mikewa yayi don wayan da akai mashi yafita lokacin naji dadin sakewa sosai a falon.

****** ********* ******
Sannu sannu na dan sake jikina na koma normal na bar zancen komai a raina sadai kallon mai bisa ruwa nakewa sadauki doni na tsinke da lamarin shi yanzu.
Maryam tafito tana tambayana na bata wani handout din muna chemistry na 200 level nace ta duba a cikin jakad litattafaina yana ciki don ina kitchen ina aiki.
Zaro takardan da zatayi sai ganin roban wanan drugs din dana dauko a dakin yaya tayi.
Saman gado ta zauna tana kallon maganin tare da karanta shi a fili ta furta drugs kuma a jakkan Bintu.
Hankalin ta ya tashi sosai a kitchen ta samay ni tace Bintu zo nan ganin hankalin ta a tashe yake yasa ni bin bayan ta zuwa dakin mu.
Sai da muka kai zaune ta zaro roban daga inda ta boye fuska a daure take ce min Bintu may ne ne wanan nagani a kayan ki?
Cikin kura min ido bata ko kiftawa don son jin bayani daga gare ni cikin damuwa.
Nace ba nawa bane anty nima dauko shi nayi a wani guri na boye shi a nan da kika gan shi.
Bintu fada min gaskiya a ina kika dauko wanan roban in ba naki bane ?
Na nisa nace wallahi anty ba nawa bane nagi maki kama da mai wanan halin daidai da rana daya ne ?
Tace shi ya bani mamaki ai nake son sanin nawaye ?
Nace na dauki alkawarin boye zancen anty don Allah kiyi hakkuri amma,wallahi ba nawa bane Allah.
Sai naji tace na yaya sadauki ne ko ?
Da sauri na kalle ta nace ni ban ce ba anty.
Amma kin san zaman su haka a gurin ki hatsari ne babba kuwa a gare ki ?
Yanzu dabanice nagan su akayan ki ba kuma nasan halinki may kike ganin zai faru ?
Nace nayi kuskuren barin su a tare dani amma na aje su don sheda kawai.
Tashi kiyi flushing din su yadda kikayi a ranan tun wani bai gani ba hankalin maji ya tashi.
Yadda tace din haka nayi na zubar dasu a cikin toilet suka bi ruwa suka wuce.
Nan na barta zaune tayi shiru tana tunanen dalilin da yasa na boye mata tasan cewa na yayan sune duk yadda akayi.
Da dare da Bashar yazo ta samay shi yadda ya fahinci bata cikin hayacin ta ya sa shi matsa mata da tambaya may yake damun ta hakane wai ?
Tace matsalan yayan mune yayana ina ganin kamar bai daina shaye shaye ba har yanzu.
Da sauri yace, kai may kika gani ban tsan mani yana sha ba kuma har yanzu gaskiya.
Tace koma may nene Bintu ta san komai sai dai tana boyewa ne, nan ta bashi labarin yadda mukayi da ita da rana.
Ya nisa bayan yaji maganan ta yace tabsa tunda kikaga taki fadi akwai magana gaskiya amma yaya akayi ta samu wanan abin a gurin ta in ma nashi ne.
Tace nima shi nake ta tunane nasan tayi hakane don farin cikin maji don kada hankalin ta ya kara tashi kuma ?
Tace nima abinda na fhinta ke nan hakan take boyewa don kada aji hankalin shi ya tashi amma ba matsala gobe da safe zanzo na kaiku makaranta anan zan fito mata da zancen muji.
Yadda suka tsara haka din ne kuwa da safe sai ga Bashar mun gani a jenction din gidan mu yana jiran mu.
Muna shiga muka gaida shi yafara hanya sai dai tuki yake a hankali, sai naji yace malama Binta ya garin dai nace lafiya kalau yaya Bashar.
Ya ce ranan sai mutumina ke fada mai ta,asan da kikai mashi da kayan shi ?
Da sauri na dago kai na kalli maryam sai na dukar da kaina nai shiru bance mashi uffan ba.
Yace Binta yaya akayi kika kwaso abubuwanan a gurin shi shiru nayi babu amsa.
Yace look Binta ba boyo ki fada min komai nai maki alkawarin bazan fada mashi komai ba akai don hanyan da zamu ceto rayuwan shi nake son mu bida a cikin sauki.
Nace shi may ya fada maka don nasan na daukan mashi alkawari bazan fadawa kowa ba wanan magana.
Sai Bashar ya nisa tare da buvun sitiyarin motar shi yace ina ganin baki fahince mu bane kawai.
Nace yaya Bashar kadai gane cewa nashine ne ko to abar maganan don Allah, kyau alkawari cikawa.
To shike nan na fahince ki yanzu, amma don Allah yadda Allah ya hore maki gane irin halin rayuwan da yake shiga ina son muyi amfani da wanan daman naki guri gano abinda ke saka shi a irin wanan halaiyar.
Sai yai kaman ya bari sai kuma ya koma ciki tsunbul dashi al,amari gaskiya akwai daure kai a cikin sa sosai.
Nace nima na fahinci haka amma gaskiya ban tsan mani zan iya ci gaba da wanan aikin ba saboda yai min warning sosai akan mashi shishigi ga al,amarin shi.
Zaki ya mana inji Bashar abinda nake so dake shine kamae yadda baki tsoron fada mashi gaskiya haka zaki daure ki ci gaba da fada mai a kai tsaye.
Murmushi nayi nace anya yaya zan iya hakan kuwa yace kwarai kuwa Binta ai zaki fitar da tsoro ne ga komai ki kama aikin ki,amma fa kuma kin san aikin nason jan mutum a jiki sosai.
Nace da sauri yaya zanhi in ja yaya sadauki a jiki mutumin da kullun yake cikin hattarana da tsangwama.
Yai murmushi kafin yace wanan kuma,wani haline nashi nan dai ya fara fada min ga yadda zanyi akai nace to ba matsala zan gwada nagani amma idan naga da,wahala gaskiya bazan yi ba.
Yace zakima iya tunda kina da hakkuri kawai ki dan sake dashi shine farko.
Muna kaiwa school ya sauke mu tare da min fatan alheri nace Allah yasa muyi nasara dai.

****** ********* ******
Yana tsaye ya bada baya waya yakeyi kuma a handfree yasaka wayan nashi a lokacin.
Magana yake da wata mace sai dai magan tankar fada sukeyi yake cewa na fada maki ni mace bata a gaba na yanzu.
Don haka ki daina yaudaran kaki don baxan aure ki ba koma zanyi aure yanzu akwai qualities din abubuwan da nake so ga matar da zan aura ke kuma baki da ko daya daga cikin su so kima daina yaudaran kanki a kaina.
Ban san may yarinyar tace ba sai ji nayi tace wanan kuma matsalar kine ni da kika gannin ban taba zina ba a rayuwa ta kuma akanko ba zan fara ba.
Da sauri na juya don nashige ciki sai nai karo da dutse ina batun faduwa naji ya riko ni bai bar wayan ba kuma bai sake ni ba.
Nace a kakausan murya sake min hannuna kaji malam, wani kallo ta watso min na ki shiga taitayinki kinji ko.
Sai da ya gama wayan ya juyo gare ni yace ashe kuma banda sa ido harkin fara lebe ne kuma ?
Cikin tsiwa nace, akan may zanyi labe Allah ha rabani da annaminan ci ni fita zanyi nagan ka kuma zan koma.
Murmushi

Please Login or Register in order to submit comment