Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

maganin rashin jiki a gidan nan.
Yan tsun kafan nawa a take sukai wani irin jawur dasu bansan lokacin dana duka ina murzasu ba a hankali sai hawaye nake zubarwa shaaaa.
Can na mike cikin dan dan gyasawa nafara tafiya zuwa daki ina kuka raina a bace ina fadi a raina wanan ai cin zallun ne don kafi karfi sai ka cuce ni haka kawai.
Muryan mama maji tana fadin haba kana son wallahi in maka abin da bakai tsanmami ba kan yarinyar nan.
Yanzu mai taimaka da kai mata wanan cin amanan haka, ko kaima dai ka canza ne wai ban sani ba don ban sanka da wanan halin ba haka.
Ya ce kai maji munafukan yarinyace fa har may nai mata ne wai da zata sakawa mutane kuks haka don shagwaba kawai.
Uwarka kai mata nace,
Da sauri ya dago kai yana kallon maji don ya dade baiga ranta ya baci haka ba har tai mashi wanan kalman da fada.
Sai gashi yau akan Fatima ta zagi uwan shi, maimakon yayi fushi sai murmushi yayi yace dama haka take son ji ai munafukan banza kawai.
Fita min daga shiya mara kan gado kawai kasaka yar mutane gaba da kyashi da hassada kawai.
Maji Fatima ce zanyi kyashi kuma ?
Sai ya wani dan bushe da dariya don abin ma dariya ya bashi shi har may zai kyashe akan Fatima kuma.
Yana dariya yafita daga dakin don shi kalaman kyashin ma dariya yake bashi sosai wallahi.
Yana fita su Amira suka kwashe da dariya suna cewa kai maji wai kyashi yayane kuma zaiyi kyashin Bintu kamar wata hamshakiya can.
Ta juya gare su tana fadin in ba kyashi ba mai ya kawo haka don Allah kuma ?
Wallahi abin haushi da takaici yabani Allah kuwa haka kawai katon banza ka dannewa yarinyar mutane kafa da karfin Allah don cin amana.
Ina daga ciki naji muryan ta tana kirana da karfi na amsa da na,am nafito still dan gyasawa nakeyi har lokacin.
Tabi kafan nawa da kallo har na iso gareta tace wai may kikai mashi ne yai maki haka ?
Ina kuka ina mata bayanin yadda mukayi dashi tace bar macucin banza kawai ai zai dawo ya samay ni ne.
Something is fishing, something is fishing wooo, something is fishing somewhere,
Harara na maka mata Amira ma kallon mamaki ke kuma may ye haka dan Allah bari mana kinga ta sha,wuya tana kuka.

****** ********* ******
Wasa wasa sai ga kafa ya rure min ya dan hau ya kumbura da kyat nake iya taka shi sosai.
Take ya,saukar min da zazzabi da sanyi a lokaci guda haka ya jawo kwanciyan dole ban shirya ba.
Shiko yana fita ya shiga motan shi sai gurin da yake ginan shi yanzu har kayan gidan komai anzuba mashi a gida zakace ko an tare a cikin gidan ne.
Nan Bashar yazo ya samay shi don su fara lissafi, saboda zasu yo odan kaya kwanan nan.
Bashar na shigowa yabi ko ina da kallo a gidan ya dan nisa yace,kai gaskiya fa MAN ya kamata kai aure hakanan domin barin gida haka hatsari ne ko banza kuma a ragewa Maji consurming .
Sadauki yai dariya yace, ai sai naga kaima katon tazuru ne bani kadai ke cinye abin uwata ba.
Bashar ga zauna cikin yanayin nishadi da kuzari yana cewa Allah ba,wasa nakeyi ba ni da ka ganni nan na kusa zama family man insha Allahu.
Kai dalla jacan da zancen banzan ka kullun da bai karewa mutane saurare.
Yace ai ko zakace nace don kwanan zan baka mamaki ne sosai Allah kuwa.
Sadauki ya kwantar da kanshi a jikin kujera yace gashi ko kaji tsoho yace wai ya bamu wata uku ba.
Bashar ya mika hannun shi ga kafadan Sadauki yace na fada maka kayar da wanan daukan kan naka kawai bori ya hau idan baka iya fadawa Maji ni sai na fada mata.
Da sauri Sadauki ya dago kai ya dan kalleshi yace ka fada mata may kuma?
Cikin kashe ido Bashar yace zancen yarta mana Fatima tunda naga kai wanan shegen fadin ran naka bai bari ka fadi abinda ke cikin ranka.
Kai dai wallahi wani irin dabbane dan akuya kawai don banda kuya na rasa wace zan aura sai Fatima.
Illa ne auren Fatima din don dai kana so wallahi girman kaine kawai irin naka ke cutan ka.
Wai kasan Allah?
Bashar yace niko nasan Allah sosai wallahi ko.
Ce to ni wallahi daidai da rana daya ban taba jin digon son yarinyar nan a raina ba Allah ko.
May ma zan so ga jikin wanan maikama da takarda ne wai ?
Yanzun ma saida muka kwasa da Maji akan ta kaga na gudo nan don naga maji tahau sosai har uwana ta zaga yau akan yar kauyen nan nata.
Yace mai kawai Fatima din kuma kai ?
Nan yake bashi labarin abinda yafaru yakare da cewa kasan shagwababbane kuma muna fuka shine harda kuka da ihu don uwarta taji ta zageni.
U see aina fada maka wallahi son ta kakeyi amma kana wa mutane wani noke noke haka?
Yace ban fa son iskanci idan kuma na daina kulata ace ga batu ga zance kuma.
Wai yaya kuke son mutum yayine wai ?
Don Allah ni let's do what we here for.
Sun dauki lokaci a gidan suna lissafi yadda ya kamata tare da tsara abinda ya dace suyi a karshe.
Sai sadauki yace amma gaskiya wanan riban da muka samu ina son mu kasa shi uku bashar yace inajinka.
Yace ka kwashi kashi daya kashi daya mubawa iyayen mu dayan kuma mu samu wani abin tallafawa tallakawa dashi.
Wanan ma babban shawara ne amma nawa da kace gaskiya yayi yawa ni kadai.
Sadauki No kada muyi haka dakai please kaga kace zaka yi aure soon, to dole ne kuma kaima kafara dan wani abin dogaro da kanka hakana.
For me kaga ni banda matsala ina dai samu gwargwado gaskiya ga harkan ball din don haka bawai sai kabi ta nawa ba.
Ina fatan ka gamsu da magana ta dai ko?
Shiru Bashar yayi yarasa may zai cewa abokin nashi can yace man gaskiya ban yadda zan gode maka ba irin wanan kokarin da kake min.
Ksi don Allah just forget ni kafi min komai wallahi in har ma badon rayuwa ba ni ko abinda na mallaka ne zan iya baka duka.
Basu bar wajen basai gap da magariba suna gidan suna hiran duniya a tsakanin su.
Da zasu rabu sunyi cewa bayan sallah zaifito akwai inda zasu tafi ganin wani mutum.
Sukai sallama kowa yaja motan shi suka nufi gida maigadin gidan ya rufe kofan kuma.

****** ********* ******
Sai bayan an gama,sallah ishai ya shigo gida a gajiye yakw a lokacin maji tana falo zaune da tasbaha a hannun ta.
Sai da yake zaune yafara gaida ita da gida ta amsa mashi a dan darare ba sakin fuska.
Su maryam ma sun gaidashi tare da ci gaba da abinda sukeyi a lokacin.
Yana zaune shima waya yafara hsr tsawon wani lokaci kafin ya kashe wayan sai maryam take tambayanshi yaya abinci fa akawo ne?
Yace maryam banjin yunwa gaskiya amma ina yarinyat nan Fatima ne abinda nace ta hada min ta hada din ne ?
Eh ta hada tunda boyar kace,
Ka halaka yarinyar mutane kuma wai kazo kana tambaya tai maka aiki ne ?
Maji na halaka ta kuma dan taka kafan da nai mata wai shine matsala kuma dai ?
Wallahi yaya yazama mata zazzabi sosai tana dakima a kwance yau ta wuni don kafan ya kumbura sosai.
Kada ke nan dan wanan takin shine har da matsala haka kuma ?
Tana ina yanzu ya tambaya cikin damuwa da nuna kulawan shi akai, tana kwance mana tunda haka kake son ganin ta.
Shiru yayi na dan tsawon lokaci yana tunane shi har wani taki yai min da za,ace saboda shi an kwanta ciwo kuma.
Ai dama nace kaida ka halakata kai zaka sayo mata magani indan kadawo macuci kawai.
Murmushi yayi yace maryam kira min ita mugani yaya kafan yayi mata ne wai ni wanan cutar da maji ke kiramin.
Maryam ta mike tashiga kirana ina kwance na dunkule acikin blanket wani irin zazzabi ne ya kamani lokacin mai karfin gaske.
Ta kware bargon tana taba jikina tani yadda nake nishi yabata tsoro da sauri tafita daga dakin ta nufi falo tana fadin,.
Wallahi maji sosai ne fa jikin Bintu bakiji yadda jikin ta ya wani gashe ba sai nishi take da karfi ni har naji tsoro wallahi.
Zubur ya mike yana fadin wai tana inane ma tana dakin mu kwance tabashi amsa .
Dakin ya shiga ya samay ni a rufe yadda ta samayni da farko a hankali yadan tabani yana kiran sunana.
Ke Fatima fatima fa ?
Na amsa da kyat ,
Yace may ke damun kine wai nace a hankali zazzabi nake ji.
Da may kuma?
Da kyat nai dan mika tare da nisawa nace kafata ke min zugi sosai.
Oya taso kizo falo mugani.
Sai ya juya yafita daga dakin yadawo falo shiru shiru ban fito ba maji tace ina take ne wai?
Tana ciki nace tafito maga kafan nata ne ?
Ganin ban fito ba yasa mama mikewa da kanta tana tafiya tana bakar magana ita kadai zuwa dakin.
Yadda ta samay ni itama dai hankalin ta ya tashi da kyarta tashini in fito falon na sako kafana daga saman gado zuwa kasa sai naji wani irin zafi da nishi na karasa saukowa kan gadon.
Namike cikin karfin hali amma sai na kasa tafiya dafa bango nayi na fara bi ina daga kafa ta da kyat da kyat nakawo falon.
Bina yayi da kallo cikin tausaya min nakai saman kujeran dake kusa da kofan na dan zauna saman hannun kujera tare da dan kwantawa gurin.
Mama tace kagani ko sadauki kaga abinda kajawa yar mutane yanzu gurin mugun halin ka.
Wanan kakausar kafan naka daya saba buga ball zaka illata min ya dashi, kafan yabi da kallo yaga ya kumbura daga inda ya taka har yana walkiya.
Yace tashi muje asibiti a duba kafan nan kafin yafi haka.
Tsoron asibiti gare ni don ban son ace allura ko magani sam ban son su gaba daya.
Tashi ya kaiki asibiti kinji Fatima kada kafan ya kara hawa kuma yafi haka ko ya hanaki barci da dare.
Ke maryam dauko mata hijjab ku tafi tare da ita don Allah, mikew yayi
yana cewa ku samay ni a mota.
Yana zaune a motan shi muka fito daga cikin gida ni da maryam dana dan dafa kadan ta muna tafiya a tare.
Ido ya tsura muna har muka iso bakin motan maryam ta bude baya muka shiga yata da mota sai asibiti
Muna hanya Bashar ya kira shi yana tambayan shi yaya bai gan shi ba har yanzu ga dare yanayi?
Yace sorry wallahi ganin zamu tafi asibiti ne yanzun haka muna hanya ma.
Waye kuma baida lafiya Bashar ya tambaya ?
Yace Fatima ce kafan ta ya kumbura shine zamu tafi da ita aduba mata nan yai mashi kwatancen inda zamu tafi.
kusan a tare muka iso da Bashar gurin wani pravet asibiti ya kaimu gurin yana da matukar kyau dagani sabon guri ne don komai nasu gurin tsab yake.
Likatan yace dole sai an da jamin kafa sai ai min allura da magani don na daina jin zugin da yake min.
Wata sabuwa ai likitan yana fara taba kafan na yanka wani irin ihu da karfi duk yadda yaso yaja naki yarda don zafin da gurin ke min daidai dan karamin yatsan kafana sai walkiyan kunbura gurin keyi yana kyalli.
Bashar yace ki tsaya aja maki kafan kiji Fatima kada ya hanaki barci da dare.
Ban san yadda akayi ba sai ji nayi an rike ni ta baya nan likitan ya samu sa,an jan kafan da kyau nai wani irin juyawa wai kwace amma ina rikon da yaya yai min bai ma san inayi ba.
Duk rabin jikina yana cikin jikin shi ina gurji ina kiran wayyoni Allah na don girman Allah ku sake ni wallahi da zafi kwarai akwai ciwo sosai.
Don Allah yaya ka sakeni kada ya kasheni wayyo don giman Allah ku taimaka min kuji tausayina mana.
Kuka shabe shabe nake yi naba maryam matukar tausayi sosai, yadda nake ihun tasan zafi nake matukar ji sosai.
Suna gefe da Bashar take cewa kafan yai mata tsamine ko har zazzabi ya sakar mata.
Bashar yace idan ba,a ja ba zaifinan anjima ya hanata barci gara kawai a ja din shi yafi
Likitan ya dauko wani mai ya shafa min mai sanyi a kafan na noke kaina a jikin yaya ina kuka cikin ban tausayi.
Ya dan buga min baya yace is ok ya isa hakana please ai an gama jan kafan.
A hankali na zare jikina daga nashi ina share hawaye cikin wani irin dan kuka kasa kasa.
Haka gurin allura nace maryam ta rike ni amma ta kasa dole dai sai a jikin yaya akai min aka bani magani tare da muna bayanin yadda za, aiwa kafan.
Amma kuma cikin ikon Allah sai naji kafan yana rage ciwon da yake min da farko.
Mun fara fitowa muja barsu aciki dan anjima saiga su sun fito daga cikin asibitin
Yaya ke cewa baku shiga motan bane kuka tsaya a,waje ga sanyi na dauka ai a rufe motar take inji maryam
Bashar yacewa maryam jimana maryam sai ta dan tsaya ya samayta a gurin nikan na dan ja kafana zuwa bakin motan na tsaya magana sukayi a tsakanin su sai naga ta danyi murmushi tace taji.
Shima yaya Sadauki wani kallon mamakine naga yanawa bashar din na bangane ba fa?
Zan shiga baya yace wa maryam bari ta shiga gaba a nan na zauna ita tana baya zaune.
Mun fara tafiya maryam ke cewa wai Bintu ba dai raki ba kan anya ko kina iya haihuwa yadda nake ganin nan .
Ke wai wani irin jikine maki haka wai dan taki kadan shine kika rakwabe haka dake ?
Banyi magana ba sai dan jingina kaina da nayi ga glass din window motan kawai ina kallon titi.
Gurin wani mai gasa kaji saman hanya ya faka motar shi can dan nesa kadan yafita.
Sai gashi da ledoji har uku a hannun shi ya bude ya shiga ya zauna har ya zauna zai tayar da mota ya juyo inda nake zaune yace yaya jikin naki nace a hankali da sauki.
Sai bayan ya tayar da mota ya fara hanya sai naji kaman yace kiyi hakkuri kinji ban san haka zai zama maki ba.
Dan murmushin ciki nayi nace bakomai kaddarace haka Allah ya nufa dani.
Yace nagode.
Har muka kai gida ba wanda yai magana a cikin mu muna fita ya mikawa Maryam ledan karbi wanan kibata taci tasha fresh milk din sosai.
Muna shiga gida mun samu mama a cikin damuwa tace kun dawo na samu guri na zauna a dan takure.
Maryam tana shigowa tace wai maji yau munsha ihu wallahi, saida yaya ya danke ta tabari akaja kafan sosai.
Ya jikin naki yanzun Fatima?
Nace naji sauki mama.
Lokacin ya shigo mama tace haka kawai kajawo wa yarinya wahala haka.
Maryam tace ai ya bata hakkuri maji kuma tayi hakkuri shike nan ko?
Ke ban son shegan taka hakkuri may zai bata bayan ya cuce ta ko.
Kai maji wa yaya zai wa laifi ya bashi hakkuri inko ba Bintu ba yau.
Daga inda Amirah take tace ban taba ji ba gaskiya nima sai yau.
Shi dai baiyi magana ba guri ya samu ya zauna tare da kallon inda mama take zaune yace maji yanzun haka za saka ido ga hukuncin da Baba ta daukan wa yaya Imiranah a gidan nan.
Ni yanzu sadauki may kake so nace kasan halin mahaifin ku sarai idan ranshi ya baci sai ya ga dama don kan shi zai huce.
To amma ni naga barin shi a haka ba zaiyi ba gaskiya anyway zan ga baba din gobe a kasuwa na kara bashi hakkuri.
Amirah tace niko dai naga da kun kyaleshi wallahi, mutanen da basuki ace mune a cikin wanan irin matsalan ba.
Kamar ya akyaleshi Amirah dan uwankine fa ashe har ke zaki iya jin dadin ganin wani naki cikin damuwa ?.
Nikan naga suna hira sai na mike zan shiga na kwanta, don barci nakeji jikin still jikina da dan zazzabi har lokacin.
Kin sha maganin da aka bakine muryan yaua sadauki ne yake tambayana hakan.
Cak naja na tsaya na dan bata fuska nace ban sha .
Koma ki zauna kisha kafin ki kwanta yace min ba mussu na koma na zauna idan na daga .
Maryam tace ga maganin bazaki sha milki din ba kafin kisha don bakici komai ba ma.
Naman kaza da fresh milkin din takawo min kurba biyu nayi bakina ba dadi sai na aje kwalin don bazan iya sha ba zakin shi naji ya kara bata min baki.
Still magana sukeyi da mahaifiyar shi amma hankalin shi yana a gareni ganin ban ci komai ba yace maji kiwa yar ki magana ta ci tasha magani.
Fatima ko tea zakisha in baki iya shan wanan din don naga kaman yana da sanyine ko ?
Nace ,a,a mama nasha ai na dan kara kurbawa kadan na aje kwalin nan nakoma saman kujeran na zauna da kyau can kuma saina dunkule guri guda ashe barci ya dauke ni a hakan ban sani ba.
Sai da mama tai magana sukaji shiru shine suka fahinci nayi barci ne.
Maji tace gaskiya banji dadin yadda kaiwa yarinyar nan ba kadaina wanan halin karfin ku ba daya yake dasu ba.
Ko banza ita mace ce fa ysushe daga dan magana kadan zakai mata wanan horon haka ?
Shiru yayi baiyi magana ba don koshi yadda yaga ina wahala sai baiji dadin abinda yai min din ba.
Ga yanin yadda na kwanta yasa shicewa maryam ta da ita taje ta kwanta wanan kwancin sai kafan ya kara ciwo ai.
Bai wani jima ba yamike zuwa dakin shi don ya kwanta sai dai bai shiga dakin ba ya zauna daga waje gurin furanni kofan shi don ya sha iska.
Mamaki yayi dayaji har a lokacin jikin shi yana kamshin turare na na white musk danake amfani dashi ajikin shi.
Take ya tuna da yadda yaji lokacin da nake kuka a jikin shi da likita ke ja min kafa.
Tsukiyi dan ja daya tuna yadda likitan ya rike dan farin kafana wai yana shafa min magani a kafan nawa.
Haushin da yasa shi mikewa ke nan yabar gurin da yake zaune ya fada dakin shi cikin takaici.
To kai takaicin may kake ji da hakan yaba kan shi amsa a fili da oho, wanka yashiga yafito kusa da rigan da ya cire yasa kan shi.
Kamshin ne ya kara bugo hancin shi abinda ya sashi dan lumshe idon shi ke nan haka barci ya dauke shi.

****** ********* ******
Washegari kodana tashi na danji saukin kafan nawa sai dai yana da dan sauran kunburi still.
Ban fito ba sai zuwa 9,30 nafito don na karya nai wanka na saka dogon riga baka abuga farin mutum sai rigan ya haskani.
A falo yana zaune da abinci a gaban shi yana ci yana waya fitowa na ina dan dan gyasawa yashi bina da ido.
Ina kwana nai mashi Amirah tace kin tashi ashe Bintu nace eh anty tace to yay jikin naki ?
Da sauki anty na zauna yana kashe wayan yace zonan naga kafan nan ko yai sauki ?
Idan baiyi a koma a kara jamaki shi da safen nan da sauri nace a,a wallahi naji sauki yaya.
Dariya suka saka min yace no ki bari akara ja maki for second time mana zaifi sakewa.
Wallahi yai sauki sosai yaya abarshi kawai ki karya kisha maganin ki kada fever ya dawo maki.
Na amsa da to nabar gurin shi zan shiga kitchen sai ga maryam dauke da wayana dake ringing da sauri na dauka.
Bashar ne a layin yake min yajiki yace yanzu yace maryam tabadhi layina yakirani.
Na koma na zauna don ba zan iya tsawon tsayi a tsaye ba ina amsa wayan nashi.
Ya dain bani hakkuri nace wallahi ba komai nagode ai ina taka kafan yanzu nace ka gaidasu mama.
Ina kashe wayan yana watso min wani irin mugun kallon dayasani shan jinin jikina lokaci guda.
Sai na tuna ya saka min idon kancewa ina waya da maza a gaban kowa haka yasa lokacin da marigayi Kabir keda rai na daina waya a falo gaban su.
Daga inda maryam take tsaye gaban tv tace yayanane yakira ki halan nace eh shine.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BA KI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,


YA ALLAH DUK WACE TA TURA MIN NOVEL GA WANDA BAI BIYA BA ALLAH KA ISAR MIN AKAN MAI SHI,,,,


Suna zaune sai hayaniya suke a tsakanin maryam da Amira suna hiran wai sun kalli wani film din biri jiya da,dare shine suke hira a tsakanin su.
Ina zaune a kan kujera na jingine jikina saman makarin kujeran nai shiru ina sauraren hiran su.
Sai dai anihi na sha jinin jikina sosai daga irin kallon tsana da yaya sadauki yake min daga gefen da yake zaune.
Na fahinci wayan da nayi ne yanzu ya jawo min wanan tsanar haka to amma ai saboda shine ,aka gaisa dani din.
Hannun shi saman goshin shi ya dan dafe kai yakai bayan shi a makarin kujera yai kwanciyar balance saman kujera ta hanyar mike kafafuwan shi.
Ganin haka nima na murde nawa fuska babu wallawala acikin sa ko kadan.
Ganin yaki ya bar falon yasani mikewa ina tafiya cikin dan dan gyasawa na nufi kofan shiga daga ciki.
Yabi bayana da kallo a hankali yana duban yadda nake taka kafana still a cikin wahala.
Yace ke zo nan kawo kafan nan nan na kara ganin yadda yayi sai a shafa magani .
Kamar na wuce don yadda yake magana cikin nuna isa, da gadara kamar dan wani sarki shi mutum ne muskilin karshe kilama shiya sa yake cin kwallo don in ya kama sai ya kai gola kamar abin tsafi sai yaci kwallo.
Shigowan Maji falon ne, shi ya katse min zancen zucin da nakayi tsaye .
Sai maryam ke fadi lah Bintu ba dai wai tsoro kike ji ba haka tun dazun yaya yace ki kai kafan ya duba ya gani, ko sai an koma asibitin ne ?
Nace cikin daurewa ni kafata normal take don banjin komai yanzu,
Yadda nai magnan tare da dan murguda baki kadan yasashi cewa cikin takaici wanan yariyar typical yar kauye ce wallahi.
Shigowan mama yasa take kallon mamaki da son tambayan ko lafiya yace cikin rashin nuna tsoro ko damuwa.
Wanan local yarinyace

Please Login or Register in order to submit comment