Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

koma gida ne yanzu.
Sai nace kana lafiya yaya yaya gajiyan hanya da taro sai da yai wani lunshe idon shi ya amsa da taro Alhamdullahi Fatima mun fara yau din nan.
Allah ya bada sa,a nace mashi ya amsa da amin fatima.
Yace kiyi tuki a hankali don nasan yanzu titi ya cika da motoci yamma yayi nace mai insha Allahu.
Yace nakiraki ne naji muryan ki don na kira ki da safe wayan ki baya shiga.
Nace ina class alokacin na rufe wayana ne ya sake cewa gashi na kasa barci sai naji muryan yar kauyen matata yaya zanyi da raina dole na kira ki naji ki don mu nan yanzu daryayi sosai .
Nace shine kaki bari da safe ka kirani yace abinda ya dace ke nan nayi don na kasa samun natsuwa rashin jinki .
Kwata kwata rashin jinki a tare dani ya hanani sukuni Fatima yaya zanyi dole ne na kiraki ai.
Take zuciyana ya narke sai naji kamar na shige cikin wayan na isa inda yake din naga kyakyawan suran mijina da nai missing.
Yaci gaba da cewa Fatima ina kewan bakar maganan ki ina kewan wanan fadan namu da muka kwana bamuyi shi ba.
Murmushi nayi yace kin dauka ina wasa ne ko sai idan kinga nadawo maki don kawai muyi shi zaki gane.
Nace a hankali ina murmushi haba yaya don fada kawai zaka dawo na rokeka kayi hamkuri ka zauna har kagama abi da yakai ka.
Har nakai gida muna waya dashi inda na ke ce mai na iso gida sai da zanyi sallah mukai sallama dashi yakashe wayan.
Wayan dake hannu na dan kalla na ce ikon Allah yau kuma mai ya samu yaya haka ne ya sauya min gaba daya.

****** ********* ******
Yau kwana yaya uku da,tafiya amma Amira shiru batazo ba tun ina saka rai da zuwan ta har nagaji na,fara fitar da rai ga zuwan ta gidan.
Yaya da yakirani ya tambaye ni Amira bata zo bane nake ce mai bata iso ba tukun.
Ranan Na dawo gida da yamma a gajiye neke a lokacin sai dai ina shigowa get din gidan na hango motan anty Amira a kofan gidan namu.
Nashigo gidan da yar fara,a na a fuskana don ganin ta tazo tana zaune saman kujera tayi daidai da ita sai waya take yi abin ta.
A sanyaye nai sallama ta dago kai ta kalleni a dan wullakace nace Anty sannu da zuwa.
Hannu kawai ta daga min ba tare da ta amsa min ba taci gaba da wayan ta da takeyi.
Ido nabi ga yadda ta kaca kaca da falon da yake a gyara tas kafin na wuce da safe.
Ganun bata da niyan gama waya yasani na nufi daki na don rage kayan dake ajikina a lokacin.
Sai d nai wanka nai sallah nafito falon har lokacin tana zaune a inda na samay ta da farko.
Ina batun na zauna take cewa ke ina key din daki na yake na bude naga a rufe yake.
Nace au yana gurina anty bari na dauko maki taja uban tsuki tana fadin don isa da sa.un guri zaki kulle ma mutane daki wai ke ga matar gida ko.
Nace fita zanyi ai shiyasa na kulle ko ina na gidan kuma ma ban san kina tafe ba yau ai.
Dalla Bintu ki dauko min key ni bani son yawan zuba haka kinji.
Kallon mamaki nake mata nace yau kuma nice mai zuba anty ki dai gyara maganan ki.
Au to abin har yakai kuma zaki min rashin kunyane Bintu ?
Wanan ba halina bane anty kinfikowa kuma sanin hakan don ban tabayiwa kowa rashin kunya ba.
Kai ta gyada tare da kutawa ta dauki jakar ta bayan na bata key din ta wuce zuwa ciki ran ta a bace.
Kitchen dama a rufe yake na dauki abincin dana aje zanci idan na dawo tunda safe na shige daki da abina nace can nafito nasawa gidan key na shige abina na kwanta.
Ban fito ba sai da safe na hada breakfast na bar gidan ko fitowa batayi ba tana dakin ta kwance.
Bayan fita data gaji da barcin ta tafito ta zauna taci abincin da ta samu na aje mata.
Inda taci anan tabar min kayan sai dana dawo na kwashe su na wanke na gyara gurin.
Ban fito na girka na dare ba don a gajiye nake nashige kawai abina nai kwanciya na kawai.
Amira tafito tasamu babu komai saman tabld din tai mamakin hakan ta nufi dakina lokacin ina bathroom ban maji tana buga kofan ba har tagaji ta,wuce.
Tunda safe ina kitchen sai gata ta shigo daga kofa taja ta tsaya tace ke Bintu wai may kike daukan kanki ne halan.
Nace namay kuma anty?
May ya hana jiya ki girka muna abinci da kika dawo ki ka barni da yunwa na kwana.
Nace kiyi hakkuri anty wallahi na gajine jiya sosai kuma ga yamma yayi dana dawo.
Eyye samun guri ke nan ke ashe har kinga gurin hutu ke nan to wallahi ki kama kanki da ni.
Murmushi nayi kawai naci gaba da aiki har ta fara tafiya ta juyo ki girka abinci dasu salma don sunce anan zasuyi breakfast yau.
Yadda tace haka nayi mata na sauri na fita yadda na dawo daga gajiya da yamma haka na samu gidan sai da raina ya baci.
Ban fito ba haka nabar falon sai da safe na tashi na shiga gyaran gidan sai da nai ko ina tas har bayin falo duk sun bata shi .
Sai na dora muna girkin rana ina tsaka da yine sai ga Anty tafito ta ce yau ma su salma sunce a nan zasu wuni kiyi girki dasu.
Ina gama muna girkin na koma dakina na kwanta can na fara jin hayanin yan su har da yan ihun su.
Nace yau kuma din nan wai may ke damun anty Amira haka tana son bata rayuwan ta.
Ki fito ki gaida su salma naji muryan Amira daga sama ina kwance na dago ina kallon ta kawai.
Kamar bazan fito ba sai dai na mike na fito da fara,ana a fuskana nake ce masu sannun ku da zuwa.
A lalace cikin kallon banza suka amsa min banji dadin haka ba amna na dake na dan samu guri daga gefe na zauna.
Sai naji dayar na cewa wai ashe musty ya auro wata gajar matace can yar kauye da ita.
Ke haba inji saura tace wallahi ko kada kiso ki ganta ga gida ga komai ya hada amma ina ba matar gwadawa tsara don bakauya ce wallahi.
Sai Amira tace anyi biyu ke nan muma ga.unan da irin matsalan ai a gidan mu kin san yan kauyen nan su iya bakin asiri su mallake miji.
Yanzu bari ki gani kwana biyu idan an aaruce shi zakiga ya fara wani bakin rawan kafa bai jin kunyan kowa akan ta.
Nagane maganan ta shagube ne amma sai na dake suna sako min magana ina jin su.
Bai mata ba sai cewa tayi ke Bintu kwashe kayan nan ki girka muna indomie kubura zataci tace.
Kallon mamaki nai mata may anty ta mayar danine yar aiki ko may wai ?
Ina gama kwashe kayan sai dana wanke su na,shiga daki in fito sai naga wace tace wa Kubura dauke da cup din tambulan yaya da nake mashi amfani dashi tana shan drinks a cikin.
Kamar na wuce sai na dawo nace anty da kun canza cups don wanan din na amdmfanin yaya ne shi.
What Bintu may kike nufi lalai ma Bintu kin kai wuyan ki ya isa yanka ashe ?
To baza ,a mayar ba sai kiyi abinda zakiyi don an dauki cups din yaya ko sannu mai yaya.
May kike gurin yaya din ke nace mata a daure mata mana mai miji kuwa.
O lalai naga alama tunda har kin fara bani ansa to baza a mayar ba din tunda daga gidan ku kikazo da shi.
Nace may yai zafi haka anty harda giri da zagin gidan mu kuma haka ?
An zaga ko zaki ramane ki nuna min wuyanki yai kauri yanzu.
Nace bazan rama ba amma koda banzo dashi daga gidan mu ba nawane dai ke ma sai ki jira naki.
Aiko sai saura sukacs iyye gorin aure kuma zaki mata Bintu don ke kin samu an maki auren hadi ko ?
Nace au haka ta fada maku ashe idan yin hadi banza ne wasu suje ai masu mana mugani.
Na bada amsa haka sai na juya zan wuce ji nayi an finciko ni ta baya sai kawai naji mari kyauuu.
Cikin mamaki na dafe kumcina da ta mara nace anty abin har da duka kuma sai sauran na fadi kyale ta please kada ta kulla maki shiri kin san su da sheri irin matan nan.
Banyi magana ba na juya kawai idona tab da hawaye na,shigd daki ina mamakin wanan irin cin zarafin da Amira tai min a gaban kawayen ta haka.
Kiran yaya sadauki ne yashigo min yake kirana na dauki wayan bayan na goge fuskana.
Na amsa mashi sallama da sauri naji yace Fatima may ya samay ki ko baki da lafiya ne.
Na daure nace may ka gani babu komai yace please nace may ke damun ki ne wai ba komai nace mashi.
Baiyarda ba sai dai kawai ya kyaleni tunda nace mai babu komai ina daga kwance nake tunane dole na dage na futar da kawaici na fara gwadawa Amira nima na iya.
Bayan kaman awa daya sai gata bazaki dafa abinda nace maki kubura tana so bane ko may ?
Ban bata ansa ba na kyale ta haka suka gaji da zaman su har suka bargidan.
Da safe ma washe gari haka na gyara gidan tea na hada nasha na koma na kwanta abina.
Can cikin barci naji takai min maka a baya da gigin barci na falka ina kallon ta.
Bazaki muna abin karyawa bane yau gashi har sha daya da,wani abu na rana.
Nace bazanyi ba .
Bazakiyi ba fa kika s tsuki nayi na koma na kwanta abina sai ji nayi ta nufo zata kara kai min maka na dago ido waje nace kada ki soma kara tabani don zan rama.
Ko dazun ma arziki kikayi a gaban kawayen kine kada ki matsayi yata na disgaki a gaban su shiyasa na barki.
Yadda taga na nuna tasan za,a samu matsala sai ta juya tana fada tafice daga dakin.
Tana fita wayan yaya sadauki takira tana fada mai wai na hana mata abinci taci.
Yace ina ganin bata jin dadin jikin ta nd don tun jiya nake jin ta hakana.
Tace shiyasa ban son zusa gidan nan wallahi sai yarinya tai batun raina maka wayon ,
Kashe wayan yayi yana mamakin iri wanan hali haka da ta sakd lokaci guda.
Tun daga wanan rana ban kara girka komai ba koma nayi iya cikina nake girkawa naci



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,


A LOKACIN MU KE,,,,


Tashin hankali a gidan su sadauki haka aka kai dare a cikin shi sai da kyat ya shiga dakin ya lalashi Nafisa dake ta faman hauka aka samu tai barci bayan irin tonon asirin da take zubawa umma da mama kawai tana kiran su da munafakai masu bin boka da malam.
Haka ya dawo gida ranan rashi a bace ina daki naji shigowan shi musalin takwas da aani abu na dare.
Nafito daga dakina saye cikin wasu kananan kayan da ya sawo min a cikin tsaraban daya zo min dashi.
Ina fitowa ya sako min mayan idanuwan shi har sai da naji kunyan hakan da yai min din.
Sannu da zuwa nai mashi idon shi na akaina ga damuwa karara a duskan shi.
Gefen hannun kujeran da yake zaune akai na zauna tare da cewa yayana may kuma ya faru ne naga kamar kana cikin damuwa.
Murmushi yayi a fili amma a zuciyar mamaki yake yadda nake saurin fahintar halin da yake ciki ko yaushe.
Yace ba komai Fatima dan matsalane kawai aka samu a gida da sauri nace subbahanallahi injin bada mama ba.
Yai murmushi ya jawoni zuwa jikin shi yana cewa don mamace kadai taki a gidan ko ?
Nace cikin murmushi ba hakana bane yaya ban dai son ace wani abu ya samu mama din ne kawai.
Yace yana sauke numfashi, Umma ce dai da Nafisa kawai ta dan shawo ne tazo gida tana hauka har ta jin ma umma din ciwo a kafan ta.
Nace innalillahi wa inna alaihim rajjiun Allah yai muna sauki wanan al,amarin kawai.
Oo ita anty Nafisa bata da ranan gyara rayuwan ta ne wai bata ganin cewa ita mace al,amarinta daban yake dana maza.
Ajiyan zuciya naji yayi yace zan samu lokaci ai na zauna da ita don na dan fahintar da ita ko Allah zaisa ta gyara halin ta amma gaskiya abin baiyi ba wallahi.
Allah ya kyauta nace tare da numfasawa na fara tunanen aanan halin rayuwan na shaye shaye gamu da acikin ta don ban sani ba ko wani hali shi mutumin nawa yake yanzu ko ya daina ko yana ciki tsunbul.
Jinayi yaja min hanci na shiyasa na sake sauke numfashi ji nayi yace kina tunanen naki mijin ko?
Murmushi nayi nace aini nawa mijin Allah ya,kawo mai sauki da sauyi a rayuwan shi Nafisa dai nake tausayawa kawai da sauran al,umma masu hali irin nata.
Idan kin gama tunanen ki nima sai ki taimaka min da dan ruwan wanka na watsa ko zanji dadin jikina.
Mikewa nayi sai naji ya kara jawoni na koma jikin nashi yake cewa amma fa zaki cika ladan ki don ke ce zaki min wankan don banjin lakkan yin da kaina ko kadan.
Da sauri na dan juyo ina kallon shi sai yake cewa eh haka na fadi ko baki ji ba nace amma yaya gaskiya sai kuma nai shiru yace to shike nan barni hakana na kwana da dauda.
Jin abinda ya fadi yasa jikina yai sanyi hakka na mike na nufi dakin nashi murmyshi ya sake tare da bin bayana da kallo kawai.
Sai da na hada ruwan wankan na aje brush din dana matsawa maclean da soso da sabulun wankan shi na fito daga bayin.
Yana zaune a ida na barshi a falon na ce a sanyaye na hada yaya yace ok sai naga ya miko min hannayen shi alaman na kama shi ya daga ke nan.
Murmushi nayi nace ni ina zan iya tayar da kato dan kwallo haka kulun cikin motsa jiki.
Dariya nabashi ya kara mika hannayen shi inda nima na kama hannayen nashi na mikar dashi din kamar yadda ya bukata din gare ni.
Amma kuma kamar ina daga dutse gashi na saka duk karfina na dago shi amma na kasa jawoni yayi na fada a jikin shi tsab ya mike tsaye dani a hannayen shi.
Bai dire dani ko ina ba sai tsakiyan dakin shi kawai ya tsaye kimkam yace sai ki fara aikin ko?
Kallon shi nayi yace uhumm bissimilah ki cire min kaya ko ?
Kallon shi nayi fuskan shi a daure dole na fara kokarin cire mashi rigan dake jikin shi.
Nakai ga wandon shi ina kokarin cire ina kawar da kaina a gefe tsaya yake kimkam dashi sai murmushin abinda yaga ina yi na kawar da kaina gefe daya.
Ina na cire wandon na kara dukar da kaina kasa, ashe akwai wani gajeren wandon maza daga ciki jin bai motsa ba yasani dan dago kaina.
Kai ya gyada min tare da kashe min ido alaman saura wanda ya rage daga ciki din .
A hankali kaina a duke na karasa cire mai wandon sai naji ya sauke ajiyan zuciya da sauri na mike na nufi inda towel yake na dauko ina mika mashi tare da kawar da kaina gefe daya.
Hannu naji yariko da kyat na iya dago kai tare da juyowa na dan kalle shi kai ya gyada min alaman bai bukatan towel din yau.
Nashiga uku na furta a raina ashe har a fili na fadi hakan ban sani ba sai naji yace akan may kika shiga uku fatima ko rabi ban bari ki shiga balle har uku.
Muje kiyi min wanka please da sauri na shige gaba tana bina a bayana sai faman kawar da kai kawai nakeyi gefe daya don ban son dago kai na kalle shi, don wani irin mugun kunyan da nake ji a lokacin.
Zama yayi a cikin bahon ruwan inda na fara yi mashi brush sai na hau yi mashi wankan idona a rufe har muka gama muka fito.
Dan towel na dauka ina goge mai jiki dashi sai faman lumshe idanuwan shi kawai yakeyi a lokacin.
Kayan da zai saka na dauko mai wani dan riga daga cikin kayan barcin shi sai wando gajere don nasan ba zai fita zuwa ko ina ba kuma.
Falo muka dawo ya ci abincin shi da ya kare ya koma saman kujera two seater ya zauna ni kuma na kama kwashe kayan nagyara ko ina tsab.
Inda yake a zaune na dawo na zauna a dayan kujeran dake daga gefen shi waya yake amma sai ya yafito ni da hannu alaman na dawo gare shi.
Abin da ya buka ta nayi inda na dawo daga gaban shi na zauna a hankali ya fara kai hanayen shi saman jikina yana aiwatar da wasu abubuwa can na ma,aurata.
Tun ina lumshw idanuwana har nima na dan fara mayar mai da martanin abinda yake, min nan muka shagalar da junan mu a falon .
Lokaci mai tsawo muka dauka a hakan cikin wani irin yanayi mai shagalar da mutun a inda yake.
Sai da ya tabbatar da kowan mu ya gamsu da dan uwa sannan ya sarara min.
Dakina na koma nai wanka na gyara jikina tare da saka rigan barci na na nufi dakin shi don nasan dai duk wani abinda zaiyi a ranan yariga yayi shi a falo ko sai dai kawai mu kwanta kawai mu huta.
Shima dai na samu yayi wanka ya kwanta a hankali na hawo gadon ta bayan shi tare da rugoma shi daga bayan shi.
Murmushi naji yayi tare da juyowa gare ni yana jawoni jikin shi nai mamaki dana ji kan shi da bakin shi a saman kirjina again.
Sai da gabana ya fadi nan ya shagala a saman kirjina tun ina rutse idanuwana har yakai nima ina jin dadin abinda yake min.
Sosai muka tsotse junan mu a karshe ta shigeni yadda ranshi ke so sai barci mai nauyi yai gaba damu.
Washe gari bamu tashi da wuri ba sai after nine na safe don haka mukai sallah a makare .
Ya ce kada na girka komai na koma na kwanta idan mun tashi zaifita ya samo muna abin karyawa.
Nan muka koma barci sai to one muka tashi wanka kowan mu yayi lokacin duk muna bukatan abinci.
Nafito falo naji ana sallama na nufi kofa naga ko waye yaya Bashar ne tafe dauke basket dauke da abinci daga gurin maryam.
Nai sauri na karba ina gaishe shi tare da bashi hanya ya shigo ciki lokacin sadauki ya fito daga daki shar dashi kayan da yasa sunyi matukar yi mashi kyau sosai.
Nan suka zauna suna hira na nufi dining da kayan na fara had gurin yadda ya kamata bayan na bude ne naga tuwo semo ne da miyan yauki.
Nace mai ga abincin can na hada mashi, a dining yace ok bari na dan ci abinci bassh.
Yace bari dai naje gida nima jirana ake muci nafito zuwa gurin ka kasan maryam yanzun ba ita kadai bace.
Ita da waye ya tambaye shi yace a anfada maka ni irin kane raggo sai iya jefa kwallo fa raga kawai amma ba ka iya jefa shi inda ya dace a jefashi ya shige.
Dariya yayi tare da kaimai nashi ya gwauce mashi yana fadin baka da kunya,wallahi wai ka manta cewa ni surukin ka ne.
Har zai fita yace kuna ko da labarin Umma bata da lafiya idan kaje ka fada mata please.
May kuma ya samay ya tambaya cikin son ji hankalin shi a tashe ya bata fuskan shi yace kawai dai dan matsalane ita da Nafisa shine ta gwauce kafan ta.
Yace mashayiyar ta shawo ke nan tazo tana hauka a gida ko yace raban ma acan na gane ta ta bugu a hanya duk dan taxes din ta tsare sai yaki tsayawa ni na daukota zuwa gida tana min tanbele a hanya.
Yafita yana maijin haushin halin rayuwa irin na Nafisa da ta jefa kan ta a ciki yanzu.
Sai wani dukar da kaina keyi don balain nauyin shi da kuyan shi nakeji yau din sam ban iya hada idona dashi.
Can yace ke na ce naam yace dago idon ki ki dube ni nan da kyat na iya daga kaina kalleshi sai nai saurin dukar da kaina kasa kawai.
Murmushi yayi yace wai wanan kunyan na may ye kuma haka ko abin bai sheki bane na kara maimata maki fiye dana jiyan ko?
Da sauri nace don Allah dai yaya kayi hakkuri kawai dai ban san yadda zan kalle ka bane dai.
Ok yanzu zan kawar da kunyan nan ai daga yau bazaki kara jin shi ba aiko da gudu na kwasa sai cikin dakina harda saka key na rufe daga ciki.

****** ********* ******
Kaya irin na marasa lafiya muka saye sai gidan su mama kwana biyu ke nan da faruwan abin amma kafan ya hau yai sundum dashi.
Tana ganin mu duk da nishin da takeyi amma bai hanata daure fuskan ta ba a lokacin.
Mun gaida ita tare da mata yaya jiki cikin daure fuska ta amsa muna Allah ya sauwaka nai mata tare da mika kayan gaisuwan da muka zo mata dashi.
Na mike na fita na barshi a dakin nasu dakin mummy na shiga na gaida ita na fito zuwa dakin mu.
Ina fita a dakin umma yaya sadauki yace ina Nafisa take ne wai ?
Umma bata amsa mashi ba sai sagir ne yace mahaukaciya tana ciki mana yar iska kawai.
Kira min ita yace wa sagir din nan ya mike ya shiga har dakin Nafisa yace tazo yaya sadauki na magana da ita.
Tafito jikin ta babu ko riga tace cikin wani yamuste fuska yaya sadauki ina wuni ya amsa mata cikin girgiza kai tare da tausaya mata.
Yace Nafisa ina son ganin ki don Allah gobe a gida na idan babu damuwa.
Tace ina ne gidan naka nema wai ?
Yai mamaki da wai batasan ma gidan shi ba yace sagir zai kawo ki idan kin tashi goben.
Tace kai tsaye niba zan shiga mota dashi ba ya illanta ni ga banza kawai mugune kagan shi nan wallahi yaya .
Tausayi tabashi don abin ya fara taba ta sosai dole ne

Please Login or Register in order to submit comment