Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

nace ai ba duka maza bane basu da hali don ko matan ma,akwai marasa hali a cikin su sosai don sai kiga diya,mace yanzun tana abinda wani da namijin ma ba,zaiyi ba.
Har Baba yafito shi da su sadauki suka rakashi nan muka mike a inda muke zaune muna mashi a huta lafiya.
Sadauki dake tsaye ya bude motan ya dago kai ya kalli gurin da mu ke tsaye, yai muna inkiya da dakin da,maji ke ciki .
Nan take, na juya da sauri na nufi dakin suko sauran basu gane may yake nufi ba don haka suka tsaya jiran baba dake waya ya gama.
Ina shiga daki nasamu, maji ta farka daga barcin da ya dauke ta, na karasa gurin, da take ina mata ya jikin
Tace min ina yayan ku Fatima ya tafine ko yana cikin asibitin nace to na dai barsu waje da Baba zai tafi gida .
Kamar kira sai gashi ya turo kofan ganina tsaye a,bayan mama ina gyara mata filo yasa shi karasowa gurin da sauri yana cewa Maji kin falka,ashe ya jikin yanzu da sauki dai yanzu ko?
Likita ya shigo ganin ta a,zaune yake tambayan ta mama ya jikin naki da sauki ko
Ya dan dubata ya dago yana cewa abata abinci taci zuwa shidda na yamma za,azo ai mata allura.
Sadauki yace wani iri abinci ya kamata a,bata yanzu wanda zaifi mata, amfani.
Likita ya dago kai yana fadin tea mai kauri da fruit sai kuma anta da koda mai kyau ta dinga ci.
Sai kuma likitan yai shiru tare da kurama sadauki ido yace you look like U,F footballer yace cikin dakewa yes iam d one,
Nan suka fara shocking din hannun su suna gaisawa mutun yana faman dada wasan yaya,sadauki.
Likita baifi yan mintina da fita ba sai ga,wasu group din likitoci sun shigo lokacin yana gyarawa mahaifiyar shi kwanciya suke fadin lalai kuwa shine shine.
Nan suka cika dakin da surutu wa yannan group su shigo su fita wasu su shigo har abin ya fara isa ta don sun hana mama samun hutu.
Saida dare Baba ya,dawo tare da su Umma da mama Asiya ya,taso su gaba bayan ya gama masu fitina rashin zuwa duba yar uwar su dake kwance asibiti.
Inda yace na,tabbatar wallahi da dayan kune a,asibiti da maijidda sai inda karfin ta ya kare.
Nan dai yai masu tas yasa fito su zo tare su duba lafiyan ta .
Sun kai wani lokaci sai, suka mike zuwa gida, dama duk a matse suke kamar dole suka zo gaida ita.
Suna fita Mama tana kwance na mike na gyara ko ina tas a dakin tare da,kawar da,wasu kaya dake waje.
Sai ga,Sadauki ya,shigo dakin ya,aje ledan da ya,shigo dasu gurin flask ya nufa ya tsiyaya ruwan zafi tare da hada tea mai kauri sosai.
Yazo gabana ina zaune yake cewa gashi na,dube shi nace tasha tea ai kafin ta kwanta.
Fuskan shi a daure yake cewa ke zaki sha ba Maji ba, ya kara miko min yace karbi mana kisha idan kin gama ga nama a leda kici tunda wa yan nan sun tafi gida don lalaci.
Zanyi magana yace min shishsh bana son magana shaye shi kawai
Ban san ya akayi na fara kurban shayin ba saida naji na dan kai cup a bakina karo na farko.
Yace yaushe, likitan yace za,a kara mata allura ne wanda ya saura ai mata.
Nace ni ban ma tsaya tambayan shi ba,don ya ishi mutane da labarin kwallo kawai ya fita.
Ke kuma shine baki so zancen kwallo ko don kina jin haushi da hassada ko?
A kwallo ne mutum zaiyi bakin ciki ko kan may aiki wahala.
Kallona yake galala,har na, mike tsaye tare da dauko baredin na zauna a makure nasha ya dan kai kurbi hudu batare da bread ba.
Na aje tare da son na,rufe sauran sai yake cewa to ki jawo kazan kici don cikin ki ya kara,walwalewa da kyau.
Nace wanan ma,Alhamdullahi don nakoshi tace shiyasa bakya kiba har yanzu kamar a kallaki saboda baki son cin abinci.
Ya mike yaje bakin gadon mama ya dan tsaya can yake cewa ina ga shidda na safe zasuyi mata allura don gaka idan basu zo ba sai ki bisu.
Nace mashi tau ya kai kofa yake cewa idan ta farka kice mata na tafi sai da safe in Allah ya kaimu.
Yana fita naja kofan na rufe nan na, dako ledan naman na fara ci tare da karasa shan cup din tea dina.
Sai da nai nak na ture dama duk iya,shegena,a gaban mutane ne ban ita cin abinci saboda kawaicin da nakeyi kawai.
Zuwa dare maji ta,farka nan na mike ina mata sannu tare da tambayanta ko tana son cin wani abu.
Tace a,a tana tambayana su Amira nace yau a gida zasu kwana don likita yace mu dan rage yawa don ki samu hutu.
Tace hmmm kai Fatima boye su kuma,zakiyi bayan nasan halin abina sun dai tafi gida don su samu barci yau ko?
Banyi magana ba sai hira take min mai kama da nasiha tana ta bani labaran tun kafin nazo gidan su irin yadda su ke kwasa da kishiyoyin ta.
Nace mama Allah ya kyauta amma mutane kamar ba,a mutuwa sai a manta da ranan haduwa da Allah.
Sai kusan asuba,muka,samu barci sosai Allah ya taimaka na,farka da akazo yiwa mama Alluran karshe.
Ban koma barci ba na dauro alwala nahau sallaya na fara sallah har akai sallah asuba ina gurin a zaune abina.
Zaune nake inajan tasbi amma kuma zuciyata tana tunane akan hiran mu da maji daren jiya da irin wahalan da tasha a gidan miji amma tazauna tai hakkuri don yaranta.
Gashi kuma yau an wayi gari saboda dan tilon danta guda ciwo nason shigan ta.
Har na,soma gyangyadi a gurin sai jin muryan mutum nayi a akaina yana fadin ki kwanta mana ki dan huta hakana.
Yaya sadauki ne yana saye da kayan exercise na maza dogon wando da rigan shi mai dogon hannu dark blue.
Yanufi gadon mama yana duban ta sai ya juyo inda nake ina kallon su yake cewa, tasha maganin an kuma yi mata alluran kuwa?
Nace eh sunzo sunyi mata sun bata magani shiyasa mata ke barci haka don maganin barci yake sa mutum sosai.
Ya ce ba tare da ya juya ba ina ga daga wanan allura ya kare sai dai magani kawai.
Jin nai shiru yasa shi juyawa gyangyadi nake nai barci a gurin hakan ya nuna mai ina son hutu nima.
Kujera yaja zuwa gaban gadon mama yana mai kura mata ido cikin jin tausayin ta ta ramay tai baki duk ta canza kaman ta.
Yana nan zaune har wata nurse tashigo dakin take tayar da,maji zasu bata maganin safe. Shine dalilin farkawan mu ni da mama din
Sai da nurse din tagama ta tafine maji take tambayan dan nata sai yanzu yazo ne.
Yai murmushi yace maji na,tsaye nazo maki da,budurwana ta gaida ke sai na samu bata shirya ba .
Murmushi naji uwar tayi tana cewa kai kama isa kaida akaiwa mata tun kana karami kasan dai Alhaji ba zai canza maganan shi ba.
Sai yace wai wa kike nufi Maji Rahaman Baba Sani ko wa wai?
Tace itace mana ba itace matar taka ba da iyayyenku suka yima ko kw canza watace.
Yace maji ni may zanyi da Rahama yanzu ga mata yan gayu ko ina suna kawo min hari sai wace na zaba.
Dariya uwar tayi tace adaiyi sanni kada ruwan ido yai ma mutum yawa amma dai kasan zancen Rahama ba,tashi yayi ba har yanzu.
Wai maji da gaske kuke zancen Rahama har yanzu a da dawasa ne bayan ko wani shekara sai na hada toshin sallah ankai mata.
Kwanaki ma naji Alhaji na zancen yakamata wai kuyi aure ku uku tundai kai da kudi yake shigowa yanzu ko yaushe.
Yace ni gaskiya da za a bani zabi gaskiya Rahama batai min ba tayi min local da yawa gaskiya.
Murmushi uwar tayi tace kai har kana da zabi bayan ka bata tsallen ka ko?
Kuma Rahama yar uwarka ce ta jini zata zauna dakai tayi hakkuri ba,ajiku ba akan baren da kake son daukowa kan ka.
Nace ko kuma waye Rahama cikin yan uwasu oho koma wacece idan lokaci yayi ai mu ganta.
Banji ya kara magana ba sai ma motsin da yaji nayi yasa shi tuna cewa ina dakin lokacin nan ya dakai kallon shi gareni, nikan na kawar da kaina gefe ina cewa kaidai ka,sani.
Na kara hada kaina na da bango ina mai lumshe idanuwana ni adole ga mai jin barci.
A ranshi yace muna fuka kawai kamar bata jin may ake fadi wai tana gyangyadi.
Idona a rufe amma tunanen wacece Rahama ya hanani sukuni wanda ban san dalilin yin hakan ba gareni.
Tun ina barcin karya har na gaskiyan yazo ya kamani ban farka ba sai kusan karfe daya da wani abuna rana.
Duk ko da hayaniyar masu shigo gaida mama a lokacin nikan sai faman barcina nakeyi hankali kwance.
Dana farka sai naga Baba ne zaune a dakin yana ba mama abinci da hannun shi.
Naso na sulale na fita amma sai hakan baiyi ba don suna jin motsina baba ya juyo yana cewa a,a Fatima kin tashi sannu kinji.
Jeki wanke fuska kizo ki karya kinji sannu da kokari jiya mamanki tace ta hanaki barci ko?
Nai murmushi nace Baba ina kwana ya gajiyan tafiya yace Fatima aikece dagajiya ke mai jinya.
Bandakin dake dakin na shiga na,wanke fuskana tare da dauro alwala don lokacin sallah ya kusa.
Ina fitowa Baba yace oya maza zoki debi abinci ki zauna kici don mamaki tace baki son cin abinci.
Inbanda abinki Fatima ana jinya ba acin abinci ai sai ciwo ya kamaki ke ma.
Na dai daure na dan dibi kadan a plate Baba yace wanan abin fa kamar za,aba yaro dan goye kin dai ga ko ita mai jinyan taci abinci yau sosai.
Alaman sauki ya samu ke nan don haka kara kici kema kada ciwo yakama,min yar amana na.
Sallama akayi dakin gwagona ce tashigo tare da sadauki daya dauko ta daga gida don bata san guri ba.
Nan suka fara gaisuwa da Alhaji tana tambayan shi ya maijikin da kuma yadda ta kara ji.
Baba yace, ai hjy masa yar ki zamanta a gurin mu yai amfani nan ya shiga yaba kokarin da nake masu a gidan.
Gwago tace ai Bintu yatinyace maihankali saidai kuma gata abin tausayi don rashin jin dadin rayuwan da ta tashi ciki.
Sadauki yashigo dakin rugumay da wasu kayan bukatun da yasayo amma gwago sai faman ba su Alhaji labarin rayuwana da irin wahalan danasha a gurin uwar riko na har yakai Baba na da kan shi yace azo dani birni wurinta ko zan samu sassauci a rayuwana.
Mamakin gwagona dake ta zuba yake ta zage sai faman yabon wanan yar nata mara kunya take haka a gaban mutane.
Nan dai yake tambayan maji ya jikin nata shine ya katse gwagona yake cewa ko likitan ya shigo da rana dubani idan baizo ba sai ya shiga gurin su.
Mama tace ai shigowan shi biyu yau yana tambayan ka nace ka tafi gida.
Ya mike yana fadin bari na duba ko yana office din shi inda ya mike zuwa wurin likitan.
Ya samu likita a office din shi bayan sun gaisa yake fada mashi yadda maji ta samu sauki fiye da yadda suke tsanmani yace kuma gaskiya wanan yarinyar tana kokari sosai wallahi.
Yace a ran shi kai may yasa wanan manyar yarinyar kowa dai yabonta yake ne haka yar kauye kawai.
Ya daiji dadin yadda likita tabashi bayanin kan mahaifiyar shi. Don ko ba komai yanzu hankalin shi ya dan kwanta ai.
Ya koma dakin har yanzu Baba yana ciki suna hira da gwagona sai Maji dakan dan jefa masu baki jefi jefi.
Bai so haka,ba don hutu akace Maji ta samu ba yawan surutu ba gashi gwago tana sata magana kuma.
Ga mamakin shi sai yaga Maji ma ta kara sakewa sosai akan baya don yinin da sukayi da gwago suna da surutu batai yawan kwanciyar da takeyi ba ranan.
Da,ya,dawo da yamma gwago take cewa ita anan zata zauna da Maji sai dai ni na koma gida.
Yasan idan na koma,akwai matsala don gwago jikinta ya yi nauyi bazata iya abinda nakeyi ba kamar ni.
Yace ai ba matsala kubarta a,nan don koda ana son yin wani abu sai tai maku.
Haka muka zauna tun ranan da gwagona dake kawar wa maji da damuwanta.
Sarai Maji ta samu lafiya sosai yanzu har ita da kanta take bukatan sallama amma sadauki ya hada,baki da likita a barta har zuwa lokacin da sukace sunan son su sallamay ta.
Bayan na,wanke yan kayan da muke amfani dasu a,sibitin ne sai na fito waje na zauna don nasha iska don zama ciki ya isheni.
A nan inda nake zaune ya samay ni yake tambayana barci sukeyi ne dana fito nace mashi eh shiyasa nafito don kada na tayar da su.
Nai mamaki danaga yasa hankici daga gefena ya zauna wayan shi tai ruri ya dauka.
Magana sukeyi da wani akan zasu fita kasan waje wasa amma yace bazai samu zuwa ba don yana jinyar mahaifiyar shi asibiti.
Mutumin yake ce mashi da ya daure su fita don akwai kudi da yawa a wanan wasan da zasufita yi yace gaskiya sai mamana taji sauki zan iya fita wani wasa sai yakashe wayan nashi baijira mai mutumin zai fadi ba.
Yana kashe wayan ya furzu da iska daga bakin shi tare da dukar da kanshi saman cinyar kafar shi kamar wanda damuwa ta dama.
Tausayi ya bani a lokacin saidai shi ba abin tausayi ba ne don duk wanan halin da mama take ciki shine sanadin hakan ai.
Ban san ya akayi ba sai ji nayi ina cewa yaya sadauki don Allah kayi hakkuri da abinda zan fada maka bawai nakai na fadi bane amma dole tasa zan fada ma koda bazakai amfani dashi ba.
Kan shi ya dago yana kallona cikin mamaki tare da kura min ido, nikuma banji tsoron shi ba naci gaba da cewa.
Ba tare da fargaba,ba nace why baka tausayin kan ka dana mahaifiyar ka?
Nace yaya wanan ciwon ban fadawa kowa ba,kaine silar haka ga mama sanadin irin rayuwan da kakeyi yasa mama cikin waban halin.
Idan dare yayi mama bata barci ko yaushe tana kai kukanta ga Allah akan al,amarinka.
Amma kuma,,,
Sainai shiru na kasa,karasa abinda zan fadi yace amma kuma may fa.
Nace a hankali yaya sai naga kamar baka sani ba kai don kullun ba batun dainawa kakeyi ba sai kara nausa,kanka kake a cikin wanan harkan ta,shaye shaye kishiyoyinta suna fada maganan banza wanda ke saka,zurciyar ta,kara,fadawa cikin halaka.
Shiru nayi kamar yadda shima,yai shiru nace yau abin bakin cikine ace duk yawan gidan nan kaine kawai nata kuma kaine mai jawo masu magana.
Kowa fa yana da nashi illar amma sun boye nasu saikai dake yi afili ake ganin naka.
Don Allah yaya idan ma,sha zakayi ka tafi can nesa da ita inda ba wanda ya sani kayi abinka.
Amma da zaka bari gaba daya shine alheri gareka dama kowa naka don nan gaba ba haka zaka zauna ba.
Kaima iyali zaka tara yau idan yaranka suka taso suka ganka cikin wanan halin ashe baka ganin tarihi zai iya maimaita kan shi gaba.
Za ai masu gori za aiwa matarka gori za aiwa yan uwan ka gorin hakan.
Shi wanan abin an san jarabta ne daga Allah amma kuma sai bawa yayi kokarin nisanta kan shi daga gareshi don gudun zama mujiya a cikin al,umma .
Baiwa arziki yaya duk Allah yai maka kamarya da kanka abin alfahari yadda ko wace uwa zataji dadin yin alfahari da zurian ta.
Nace amma,,,,,
Yace ke dakata haka ya isheni na kuma gode da kika kalli idona kika fada min gaskiyan abinda babu wani mahalukin da ya taba tarona ya fada min irin haka.
Nasan kinyi kokari yadda kika kalli idona yau kika fada min damuwarku akaina wanda yan uwana dangina abokaina ba wanda zai iya fada min shi.
Koke nasan saida kika shirya fada min don naga saida babu kowa a tare damu kikai min wanan magana ko haka na gode insha Allahu nima ina kokarin ganin na daina don bayanin da likita yai min a officer din shi nasan zancen da Umma taiwa majine last week ya hefata cikin wanan halin.
Da sauri nace ashe kaima ka sani yaya mikewa yayi yanackakabe wandon shi yace tundani ba mutum bane yaya zan sani.
Ya sakai ya wuce ya barni zaune a gurin take naji kamar ancire min wani dutse a zuciyana nace a raina koba komai dai na samu ya saurareni dole ne kuma daga cikin zance na yai amfani da wani yai mashi tasiri aran shi.
Ina gurin a zaune yafito hakan yasani sanin har lokacin barci sukeyi basu tashi ba.
Yana isowa inda nake yake cewa ni zan tafi idan sun farka ki fada masu cewa nazo sai na dawo anjima.
Yatafi abin shi nabi bayan shi da kallo ga mutum har mutum amma kuma babu shedun alheri tare dashi.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKK8N WASU PLEASE,,,,,,


A LOKACIN MU KE,,,,,,,,,,,


An sallamo mu daga asibiti bayan gwaje gwajen da akayi kan mama an tabbatar da ta samu lafiya yanzu sosai,
Sai dai likita ya kara jaddada muna cewa a guje bata mata rayuwanta, wanan kalamin na likita a gaban kowa akayi shi.
Duk yaran mama suna kusa haka yaya sadauki yakoso su zuwa gida motat tashi bata daukan mu duka don haka ni da maryam muka hawo Nepep zuwa gida da sauran kayan mu.
A kofan gida muna sauka na hango yaya Imirana da wata yarinya yar makwabtar mu ya rike mata hannu yana wasa da ita.
Kawar da kaina nayi tankatmr ban ganshi ba amma da yake baida zuciya muna kawowa kusa sai cewa yayi adon gari kun dawo.
Yaya mune kuma adon gari yau inji maryam yai dariya yace inbada abinki maryam ai yan mata adon gari ne ko?
Wanan yarinyar da Maji zata ban ita aida na more wallahi ta juya tana wa Bintu yace ita fa.
Ai babban adon garice wanan tun dai in ta samu guri zakiga ta baje ne kwana biyi lokacin caji ya fara daukan ta.
Nace ba adon gari ba adon dawa mara mutunci kawai, maryam tace ke Bintu yayan nawa kike zagi a gabana yanzu zamuyi fada kuwa.
Ban tsaya basu amsa ba na kwashi kaya zuwa cikin gida, ban san yana tsaye ba jikin motanshi sai da nazo shigewa na gan shi a tsaye ya sha bakin glass a idon shi.
Ni dai na,shige yabini da harara kawai, tun kan nashigo nake jin hayaniyan yan gidan ga kida na tashi dakin Umma.
Haka yasani sanin Nafisa tana gida a lokacin don idan tana na zakaji sauti yana tashi a dakin su.
Na samu su mama da gwagona zaune a falo nan na zube kayan suna min kun iso nace eh.
Nazauna ina cewa wai Allah mun gode ma, jiki dan tafiyan nan kikewa wai inji Amirah.
Kafin nai magana cikin muryan mara lafiya mama tace tunda baki san kwana rayen da takeyi akaina ba ai zaki fada mata hakan.
Amirah tace cikin make murya maji tare fa muke kwana da Bintu don dai na daina kwana biyu kawai.
Kudai kuka sani ace uwar mutum na asibiti amma ku har kunji dadin kwana a gida.
Ashe badon Allah ya kawomin wanan yarinyar ba sai dai na karata can ni kadai.
Gwagona tace a,a haba hjy ai bazasuyi haka don dai sunga ita din tana masu kara ne kada su raina mata shiyasa.
Mai masa bari yaran nan ban san irin su ba kodan sunga su kadaine min suke min wanan halin ban sani ba.
Amirah ta tashi tashige daki tai fushi da maganan mama, nice ma na tashi nabi bayan ta har zan shiga gwagona ke cewa dawo mana ki kwashe kayan zuwa ciki kada a barsu nan watse.
Maji tace ai kinga abinda nake fadi din waya fara dawowa cikin su ba ita ba amma batai azancin ta kwashe ba.
Suna ganin abinda sauran yaran gidan keyi sun zaci alheri ne basu san cewa suma gidan wani zasuba.
Idan kaje gidan mutane kace kai baka iya motsa jikinka kai komai sai dai ai maka aiko akwai aiki babba.
Da sannu za,a koya masu tunda basu saba da hakan ba tun farko amma ai zasuyi insha Allahu .
Allah dai ya kyauta mai masa yaran nan halin su sai su wallahi basu san ciwon kan su ba.
Koma irin yadda ake min a gidan su baya damun su dawasu ne ai basai an fada masu abinda zasuyi ba wanda ya dace.
Kiyi hakkuri hajiya kowa da ir8n halin shi amma bari zasuyi idan ana lurar dasu.
Na samu Amira a daki tana, waya nashigo dakin , tabini da kallo tace yanzu duk kokarin da nake wai maji bata gani.
Nace Anty uwa uwace duk abinda suka,fada muna gyara ne a garemu mu godewa Allah da ya barmu dasu a raye.
Wanda baida uwa fa a duniya bai kuma damai kwabamashi fa.
For god sake may ye banyi a gidan nan ne wai amma kulun maji tace banyi daidai ba.
Fadan iyayye fa takine gare mu anty tun da tace haka yanzu da ta dawo gida sai ki matsa ki kula da ita yadda zata ji dadin ki.
Kallo na tayi kamar zatai magana sai kuma tai shiru kawai nikan na koma dakin mu na,shiga wanka don duk warin asibiti nake jin ina yi a jikina.
Bayan nafito ne na tara duk kayan da mukai amfani dashi asibiti na wanke su tas sannan nadawo falo na zauna sai naga Amirah tafito.
Taje gurin mama tace a kawo maki abinci ki dan ci ko da kadan ne maji don rana yayi lokacin shan maganin ki ya kusa.
Uwar taji dadin haka sosai don ta kasa boye farincikin ta tace tau akawo min Amirah.
Ta hado ta kawo mata har gaban ta tare da ruwa da maganin gaba daya.
Maji tace mata na gode Allah yai maku albarka da haka kuke min wa zaiji mu daku.
Gwagona tace tau gashi dai uwata ta gyara yanzu ai shiya fadan yake da dadi ga yaro don ya gyara kuskuren shi.
Tajuya inda nake tana cewa ke kuma Bintu wallahi ki bar yi wa maji komai daga yau kibarni ni zan mata.
Maryam tace wallahi saidai a raba amma ban yarda nima ai ina son albarkan .
Nan dai aka wasance zance ana dariya tajuyo tana daga min gira alaman godiya nima hannu na daga mata alaman komai ya wuce.

****** ********* ******
Kabir yazo duban jikin maji da ya shigo kauyen su kamar

Please Login or Register in order to submit comment