Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yana,da nakasu ba ke nan tare dashi.
Tace kako san har mutanen gidan nan sun fara zargin wai kana shaye shaye ne,
Ya,dago kai da,sauri ya,dan kalle ta sai kuma ya dukar da kan shi yace maji nifa wa yan nan mutanen sun fara isa ta,sun fara saka min ido har da bina da,sheri haka?
Ni dai ka gyara halinka shine bukatana a,gare ka idan ka gyara babu wanda zai dora ma,sheri ai.
Ta juya tana cewa Allah ya kyauta kaji bukatana gareka don naga yanzu guduna ma kakeyi baka son shigowa nasan lafiyan ka kamar yadda kasaba yi a baya.
Bin bayan mahaifiyar shi yayi yana mamakin mutumin da,yafara gano likin shi a gidan don haka ya zama dole ya canza takon shi tun mahaifan shi basu tabbatar da,zargin su ba akan shi.
Don yasan in hakan ya tabbata ba karamin tashin hankali mahaifiyar shi zata shiga ba har ma mahaufin shi din dake nuna yanzu babu ruwan shi da shi yanzu.

****** ******* ******
Zaune take ta tula kudi a gaban ta,sai faman kidayawa take a hankali don gudin tai kure.
Sai da ta kirga su cif tajera a,faban ta tana kallo sannan ta,sauke ajiyan zuciyar ta.
Yanzu abin da ya rage min na hada kudin fridge din nan saura dubu goma don haka bari na kara kaimi naga sun hadu na,samu kafin azumi na dauko babban fridge wanda zai isheni sana,a yadda nake so.
Tashi tayi da sauri ta mayar da kudin inda ta ciro su ta boye, don gudun kada wani ya gani yasan inda ta,aje don tasan da,zaran maigidan ta ya kyala ido yaga kudin nan sunan ta sorry don yanzu zai mata dadin baki sai ya karbe su gaba daya su huta.
Abinda bata sani ba shine shi maigidan nata sam hankalin shi bai ga,abin hannun ta ko kadan don asali ma,shi bai bukatan wanan sana,an wahalan da yaga tana saka rayuwan ta a ciki yanzu.
Don da,ace yana,da,hali da iyalin shi sunji dadin rayuwa a gurin shi.
Amma ina talauci kamar ya yanke saka ne a kan shi don kullun bida yake amma kamar ba,ayi yake sai dai Allah bai hanashi dan abinda zasuci ba agidan daidai gwargwadon hali.
Mikewa tayi ta gyara dakin har zuwa tsakar gidan su don akwaita da,tsabta ko yaushe duk da,talaucin su zaka,samu gidan su tsab tsab dashi.
Yaran tane suka fara dawowa daga islamiya inda tun a,waje tasan da zuwan su din saboda hayaniyar su da taji tun daga waje.
Sannu da gida Umma suke cewa sai faman ce masu take kun dawo sannun ku da,dawowa ,
Yar karamar yar ta,take cewa mama yau a makaranta malam yai muna alwala mungani nima zan iya yadda yai muna nagani.
Nanyaran suka shiga bata labarin yadda malamin su ya koya musu yadda ake alwala har lokacin da mahaifin su yadawo daga kasuwa suka juya gurin shi yana,alwala suna bashi labari n abinda yafaru a islamiyar su yau.




ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,

A LOKACIN MU KE,,,,,,


Ya na fita daga waje ya,ci karo da,bucket din roban da mama ta,aje a tsakar gida shuri daya yayiwa bucket din din yai sama ya maku da,bango.
Ji kake pappp karan fashewan bucket din da ya maku da bangon dakin mama Asiya ji kake tayau,
Da sauri mama Asiya tafito daga dakin ta,tana ganin irin ta,asan da Umar yai mata tafara salati tana tafa hannayen ta cikin salalami da mamaki.
Maijjidda fito fito kiga,ta,asan da,danki yai min, dan iskan yaro kawai mara mutunci, kawai bucket yana aje may ya tare maka don kawai kana haushina zakai min wanan aika aikan haka,
Bari ubanka ya,dawo yau gidan nan akwai ta don sai an biyani kudin bucket dina a gidan nan.
Haka mama Asiya taita faman masifa inda take shiga ba nan take fita ba sai yan kore da suka fito kara zugata tana hawa.
Maji dai tana daki bakin ciki da takaici ya hana ta fita waje a lokacin.
Sai dai duk abinda suke fadi a kunnuwan ta yake irin yadda suke kara aibanta mata yaro duk da ran ta ya baci amma bata da bakin magana dan kuka maija wa uwar shi jifa.
Sadauki ya jawo mata wani sabon masifa don tasan yadda mama Asiya ta fadi sai an biya ta haka zancen yake sai an biyata din.
Don haka ta mike tsam zuwa kuryan dakin kwanan ta ta dauko kudi, a take ta dauko kudi taba Amira wai ta sayo mata bucket.
Haba maji don kawai tace sai anbiya ta basai taje gurin shi shida ya fasa mata taje gurin shi mana in ta isa, ya biyata abinta.
Maji tace,ban son rashin kunya Amira ki tashi ki tafi inda na aike ki kawai.
Bintu tace mama kawo naje yanzu zan dawo sai maji tace a,a Bintu yi zaman ki bari dai Amira din ta tafi.
Mama barshi kawai ni na tafi anty Amira ta huta kawai ta duka ta karbi kudin daga hannun Maji ta saka silifas din ta dake ta kofa tafita daga dakin.
Inda Amira ke zaune Maji ta dan kalla tace kin ga ikon Allah karamar yarinya haka da kaifin hankali,
Don tafahinci baki bukatan zuwa yasa ta karbi kudin ita ta tafi, da sauri Amira ta daga kai ta kalli maji tace bance banzuwa ba maji ,
Allah dai ya kyauta Amira ina tsoron kada ke ma kizo ki zama min irin dan uwan ki nan gaba wallahi.
Haba maji don Allah kibar fadin haka mana idan ranki ya baci kiyi hakkuri don Allah ta fadi a,dan marairaice,
Allah ya kyauta ta furta a fili a cikin zuciyar ta kuma fadi take ya Allah ka shirya min yaran nan shiri irin na addinin musulunci.
Wannan adduan ya zama kamar waka a bakin Maji don duk abinda take adduan ta akan zurian ta dana sauran yan uwa musulmai yake.
Exactly kalar roban da ya fasawa mama Asiya Bintu ta sayo don ma saida tai yawo kusan shago uku ta samu roban.
Gap da zata shiga gidan ne a daidai side din samarin gidan dake daga wajen haraban gidan ta hango shi zaune yai zaman kamar tsuguni saman dan dakalin dake gurin.
Kamar ance ya dago kai ya hango bakuwar yarinyar da yake yawan gani dakin mahaifiyar shi yanzu tafe da buket din roba kalar dayai shuri dashi a cikin gida kuma tun kan ya karasa fita daga gidan yaji bambamin mama Asiya akan wai ya fasa mata buket wanda ba ma fashewa yayi ba.
Daga hannun buket din ne ya balle hannu daya na bucket din ya balle daga jikin roban.
Sauri take ta shige gidan sai taji muryan shi kamar daga sama yace.
"Ke,
Cak taja ta tsaya don balain tsoron shi take ji don ko yaushe fuskan shi babu rahama cikin shi, don har takanyi mamakin ace wai wanan mai siffan bugai yafito daga mace saliha kamar Maji.
Zo nan yace mata inda ta dan taka a hankali kamar kwai ya fashe mata a ciki, har ta karasa gurin shi.
Waya aike ki sayan wanan robar ya tambaya cikin daga muryan shi.
Cikin dan in,in,niya take cewa, mamace tace na,sayo mata,
A gatsale ya tambayeta, waye mama ? Don ya tantance ko wa ya aike ta sayen robar.
Bintu tace mama ta dakin ku, kina nufin Maji ke nan, tace eh cikin daga kanta.
Miko min bucket din kice mata na karba ya,fadin cikin dakewan fuska mika mashi tayi ta juya simi simi ta shige cikin gidan yabi bayan ta da harara yana fadin munafuka kawai.
Maji tana zaune Bintu tashigo gidan tana dan kiukiu da idanuwar ta alamar damuwa a fuskan ta.
A,a Bintu ba,a samu roban bane ko kudin shine baikai ba?
Kafi Bintu tai magana Amira tace a,a ya za,ace ba,a samu irin roban ba kodai baki san inda ake sayarwa bane ?
Harara Maji ta maka wa Amira da sauri taja bakin ta tai shiru tare da kawar da kan ta don tasan har yanzu Maji a kufule take da ita ke nan.
Bintu tace na,sayo amma ya karbi bucket din a gurina.
Shi wa ya karba ?
Shi wanan yayan namu da ya,fasa roban yace na bashi roban dana sayo din .
Sadauki ke nan ko ?
Eh shi yace na bashi nace ya karba.
Mikewa Maji tayi ta saka hijjab din ta ta nufi hanyan waje fuuu a cikin fushi da hasala.
Ya na kulle kofan dakin shi zai fita ne Maji ta karaso gurin tana fadin miko min roban mara mutunci kawai.
Wani kallo ya waigo yaiwa uwar sai kuma ya,dukar da kan shi kasa ya dan fara kokarin bude kofar dakin shi daya rufe.
Yafito da bucket din yana cewa wallahi matar nan yar rainin wayo ne naso ne ki barni da ita, tun da tace yau akwai balai akan bucket din roba a gidan nan.
Fisgan roban Maji tayi daga hannun shi ta watsa mai harara tana cewa.
Duk abinda tace waja min ida baka taba kayan ta ba ai bazatai wanan fitinan ba.
Ksi tayi sadauki tunda na fahinci kwanciyar hankalina ne baka bukatan gani a duniya.
Maji ni fa ba haka nake ba ki barni kawai na wuce gurin kwallo na in huta da wanan munafukan matan.
Anki a barka anan ma da kake yaya aka kare dakai balle ka sa kafa ka tafi wata duniyan da babu mai kwabon ka a can.
Indai zaka gyara halinka ka gyara don bakai kadai bane yaro a gidan nan da kullun a ce sadauki dai sadauki.
Ta juya zuwa cikin gida kamar yadda tafito a hasale daga gidan da farko.
Maji bata shiga daki ba,saida takaiwa mama Asiya bucket din dakin ta takuma bata hakkuri akan ta yi hakkuri da halin sadauki din .
Ba kunya mama Asiya takarbi bucket din tana zuba bakar magana tana cewa wallahi da ba,a,sayo min kayana ba da yau akwai magana a gidan nan.
Da maji ta shigo lokacin Bintu da su Amira suna zaune a falon ta, Amira ce tace bai bayar bane maji ?
Kamar yaya bazai bayar ba aiko ya sha giyar wake ne bai fara shi wallahi.
Sai Amira din take cewa to Maji ina shi tsohon bucke din ai naga bai wani fashe ba fa .
Amira ki fita idona don ni ba,sa,ar ki bace, don naga kina son raina ni.
Shiru Amira tayi tare da kokarin mikewa tabar falon don gudun fadan Maji a kan ta don yanzu tana sauke mata haushin dan uwan ta a kan ta in batai hankali ba.
Inda Bintu take Maji ta kalla tana cewa Fatima kinci abinci kuwa, cikin sauke ajiyan zuciya a hankali.
A cikin natsuwa Bintu tace ina jiran su anty Amira ne muci tare dasu.
Haba Bintu kada ki biyewa wa yan nan don su cin abinci a gurin su kamar shan zuma ne sai sunga dama suke ci.
Tashi kici abinci kada gwagon ki ta dawo ta samu kin ramay kan wa yan nan mara sa kai.
Haba mama aiko suna da kai adduan ku a gare mu shine takin mu akoda yaushe cikin murmushi da kwantar da murya Bintu tai maganan ta.
Allah sarki Allah yai maki baiwa da kaifin basira karama dake Bintu amma kin san abinda ya kamata ko yaushe.
Tashi jeki ki debi abinci kici mai isar ki kin ji diyata Allah ya bar muna ku.
Bintu ta mike a hankali fon bin umurnin maji amma bafon ranta nason cin abincin ba ta shiga kitchen din su ta dan debo abinci dan kadan a cikin plate tare da ledan ruwan pure wata.
Maji tabi abincin da kallo tana cewa haba Fatima wanan dan abincin may zai maki ashe shiyasa baki kiba don baki son cin abinci sosai.
Ko har yanzun kina kewar gwagon ki ne kin ki sake jikin ki da mu.
Murmushi Bintu tayi kawai tare da cewa a kunyace a,a mama ai ban damu ba.
To dayafi maki don ko gwago ta dawo zance tabarki a nan don halaiyar ki ni dai yana min wallahi saboda yaran nan su dan kara daukan darasi a gurinki.
Don duk irin halaiyar yaran gidan nan shine diba,ar su a rayuwan su basu san halin rayuwan duniya ba.
Da,sauri Bintu ta dago kai tana kallon Maji sai kuma ta dukar da kanta tana dan juya abincin dake cikin plate a hankali ba tare da takai a bakin ta ba.
Yadda maji take jin sha,awan Bintu yasa take so da kaunar yarinyar har cikin ran ta ganin zata takura mata yasa maji ta dan mike tabar falon zuwa waje.
Bintu tana gamawa ta kwashe kayan zuwa inda suke wankewa ta wanke har ma da wanda tagani saura a gurin duk ta hada ta wanke su.
Daidai zata shigo da kayan, maji ta ganta take cewa Fatima baki hutawa duk aiki bai baki wahala ke.
Murmushi kawai tayi ta,shige da kayan ciki ta aje tana fitowa ta shiga wanka don magariba ya kawo jiki a lokacin.
Tsab Bintu tafito cikin wasu kayan da aka bata na Amira an gyara mata sun mata matukar kyau kamar don ta aka dinka kayan dama.
Maji dake zaune ta idar da sallah tana jan tasbaha takalle ta lokacin duk suna falo da yaran ta a zaune.
Duk suka bita da kallo a lokaci guda ta,zo har inda Maji take zaune tana cewa ina wuni mama.
Kai Maji dake lazumi ta kada mata tare da daga mata hannu Bintu ta mike zuwa bakin dayan kujeran ta zauna a kasa.
Maryam ta kalleta tana cewa may yasa ke baki son hawa saman kujera ne Bintu bata ce komai ba sai dan halinta watau murmushi.
Can suka fara jin dan hayaniya daga cikin gida yana tashi inda duk sukai shiru suna saurare don suji may ke faruwa ne wai.
Maji daga inda take tai murmushi tana cewa Alhaji ya dawo ke nan nasan an fada mashi.
Kai wanan matar batayi ba wallahi yanzu bayan an biya ta bucket din ta kuma,shine sai ta fadawa Baba zancen.
Maryam tace ai in bata fadi yayi masifa wa maji ba hankalin ta baya kwantawa.
Mikewa Maji tayi bayan ta shafa tafita daga dakin zuwa gaida Baba da dawowa daga kasuwa.
Ta samay shi shi da mama da uwargidan su a falon shi zaune tai mashi sannu da dawowa,da yaya kasuwa.
Ta juya zata wuce sai maigidan nasu ya ce maijidda yaya akayi dan ki ya fasawa Asiya roban ta da gangan?
Shaye shayen nashi har yakawo a,cikin gida cikin iyalina kuma?
Shiru maji tayi tana maijin kunan zancen baba a ran ta sai dai cikin dakiya yau karo na,farko tun da ya fara mata cin fuska a gaban kishiyoyin ta kan dan ta tace.
Da na ko dan mu Alhaji ina bani kadai na samu yaron ba tare da kaine kuma a tare mukai mashi ladabi a cikin gidan nan gaba dayan mi daku.
Don haka sai makiyin Allah zaice ban ba sadauki ingantaccen tarbiya ba a cikin gidan nan.
Kawai dai Allah ne mai yin ikon shi akan duk wanda yaso ni kuma nasan bawai Allah yakini bane ya mayar da dan da yafito daga tsatso na haka a,rayuwa ba.
Ai bazata bari a,fadi ba don kaga har roban ta,sayo ta mayar ma Asiya da abinta wai don ta nuna ita ta haife ta.
Maji tace yaya Asiya ya kike son nayi kin face yau idan ba,a biya ki roban ki ba,akwai tsiya a gidan nan don babu mai rabaki da shrgiyar uwar shi sai Allah.
Alhaji ya juya yana cewa ke ko Asiya haka kika ce mata don maganan maji yadan sa jikin shi yin sanyi.
Ba dole ince haka ba tunda yana takamar shi dan iska ne har iskancin yakawo ga kayana tun yana dukan min yara yau kuma ya koma ga kaya na.
Idan ko haka kikace gaskiya baki kyauta ba don dai kinga maijidda ba itace ke tura shi wanan aika aikan ba.
Wai haka ma zakace Alhaji akan may zan zauna yaro kamar sadauki yana min cin fuska kala kala tsoron shi nake ji ko may da,zan kyale shi.
Yanzun dai idan har ya kara takalar wata a gidan nan don Allah na rokeku da kuyi hakkuri har lokacin da na dawo sai na dauki mataki da kaina.
Ke kuma Maijidda nasan kiyi hakane don kawar da fitinan don a zauna lafiya amma ba daidai bane ki biya Asiya roban ta don Sadauki ya fasa mata roba.
To ayi hakkuri in har ban kyauta ba amma ni bada wani manufa na biya roban ba.
Ai dan tane shi don haka ba zancen biya a tsakanin ku don dan wani yai wa,wani barna.
Mama Asiya tace wa ni sadauki ne dana Allah dai yai min katangar tsari wallahi da wanan bakar haihuwa a,rayuwana.
Ikon Allah Asiya a gabana kike wanan zancen haka ?
Ai gaskiya na fadi don bani fatan haihuwan dan majiciji a rayuwana na haife shi ya kasheni.
Allah ya kyauta inji Baba yafadi ciki kunar rai tare da mikewa yai shigewan shi daki kawai su ma mikewa sukayi suka watse daga dakin mama Asiya tana ta bakar magana.
Maji tadawo daki zuciyar ta na mata kuna ta samu su Amira suna ta hiran su Bintu tana gefe zaune a makure bata tanka masu a hiran nasu.
Suna ganin ta sun fahinci ranta a bace yake anyi ba dadi ke nan a can falon baba.
Amira tai tsuki tana fadin wallahi yaya sadauki dai yana jawo muna matsala a gidan nan.
Bintu tace sai ko mu bishi da addu,a don adfua makamin mumine ne tunda ba haka Allah ya halicce shi ba ai.
Dago kai Maji tayi ta dan tsura wa Bintu ido sai kuma ta kawar duk yadda taso ta danne hawayen ta kada su zubo saida suka zubo mata.
Hankalin yaran gaba daya ya tashi sai cewa Amira take halan mi sukace maki maji.
Bintu tace haba Anty Amira maganan manyane fa sai su kawai dai mama tayi hakkuri tabarwa Allah al,amarin shi, ian Allah mai karban adduan bayin shine idan Allah ya tashi canza shi sai kowa yai mamaki a gidan nan.
Hmmm Bintu ke nan baki san ko waye yaya sadauki ba ko a gidan nan ki barshi kawai kuyi yar nisa danisa dashi shine sauki wallahi.
A,a anty Amira insha Allahu wata rana sai kunyi mamakin shi Allah dai yasa wanan halin na iya kurciyane kawai.
Ikon Allah ke kin iya magana kamar tasbin kaka kamar wata babba van wallahi.
To Antu ai ba abinda yafi karfin ubangiji nagani don shine maitin komai a lokacin kuma da yaso wanan fa jerabawa ne akan su mama da baba sai dai muce Allah ya basu ikon cinyewa kawai.
Shiru dakin yayi suna nazarin zancen Bintu yarinya karama da babban magana kamar wata babba can.
Jin sunyi shiru Bintu tace da zamu dage ko mu iya dakin ga mu dinga aiwatar da ibada akan shi kawai ba,wai mu tsaya muna magana kamar sauran mutane ba muna kuma yin sadaka akai insha Allahu ba,dadewa zamuga saukin al,amarin da yardan Allah.
Don ni wallahi na yarda da addua takobin mumine sosai don da na roki Allah saiki ga an karba min.
Dariya,suka saka mata kai Bintu wanan cika baki haka kamar wata,shirihiya can.
Hmmm anty ke nan nifa tun ina karama Baba na ya kowaya min yin addua kin san ban tashi a gaban mahaifiyata ba.
Da sauri maji wacce sai yanzuta sa masu baki a zancen su tun shigowan ta tana hawaye tace.
Fatima ina mahaifiyar ki take Bintu tace tana can wani kauye tana aure sun rabu da Baba ance tun ana goyo na da ya auri kishiyar mamana.
Shine da aka yayeni iyayyen ta suka dawo dani gurin mahaifina wai bazasuyi wahalan banza ba .
Tayar dake shine suke gani wahalan banza Bintu tace cikin yar murya haka suke gani sai kawai ga kwallah ya zubo mata,
Bata daina magana ba don kwallan sai cewa tayi, mama nasha wuya a gurin mama hausi sosai don har tsakar gida na kwana ni kadai tun ina yarinya na.
Da kuma na girma abin ba,a cewa komai don ba irin wahalan da bata gwada min.
Amma sai gashi duk yaran ta ba wanda ya kaini don mazan su da matan su duk sun lalace mata sai nice ma nadawo tana dan jin sanyi a gurina.
Ina ganin ganin da Baba yayi aikin wahala zai kashe shine suka hada baki da,gwagona wai nazo nai mata hutun sati biyu na koma.
Sai daga baya gwago take fada min cewa wai Baba na yace na zauna gurin ta kada na koma garin mu.
Takarasa maganan cikin kuka tace ina kewan gida da yan uwana sosai da farko amma yanzu don rikon da gwago take min yasa na manta da komai gashi yanzu zama daku yakara sa hankali na ya kwanta sosai bisa ga zamana a can kauye don abubuwan da ban sani ba,a,rayuwa yanzu na,san su sosai.
Tun ina shekara sha hudu na haddace alkur,ani maigirma yanzu tulawa nake sai dai akwai banbancin karatun mu na can da naku na,nan birni sosai.
Kinga ashe na,dan san wani abu nima ga,addini ke nan don malamin mu yana gwada mu abubuwa siri sosai.
Allah sarki ashe mahaifiyar ki bata tare da mahaifinki gaskiya wasu mata akwai ha,inci a tare dasu sosai wallahi.
Shi yasa nake ta hakkuri tun farko da cin fuskan da ake min a gidan nan don yaran nan dake gabana don idan na fita na barsu cikin gidan nan wa kuke ganin zai rike min ku amma na cikin su, ina ciki ma yaya muka kare dasu balle na fita na barku.
Duk shiru sukayi suna nazarin maganan Maji don sun san gaskiya ta fadi ba mai iya rike su amma kamar yadda suke rike yaran su.
Kowan su tasan gaskiya Maji tafadi don ba mai iya rikon su amana suji dadi kamar yadda tace don haka sukaji tausayin uwar tasu ya kara shigan su sosai a gidan.

****** ********* ******
Salamu Alaikum wai ana sallama da Raiha sai mama dake duke a kitchen ta dago tana cewa kai waye da yamman nan ka ce bata nan.
Kai tsaya Raiha dake fitowa daga bandaki tace wa yaron je kace gani tafe kaji.
Raiha yanzu don baki da kunya zance zaki fita da rana haka kowa yana ganin ki kikau

Please Login or Register in order to submit comment