Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

basu ganewa ai.
Shiru shiru suna,asibitin dashi muna gida da Iyya hankalin mi a tashe sosai a lokacin dashi.
Mama ce ta bugo waya tana fada min in kwantar da hankalina likitoci suna kan shi suna bincike yanzu haka.
A raina nace ina naga kwantar da hankali asirina zai tonu haka kuma daga taimako .
Sai guraren sha biyu da wani abu bashar ta dawo gidan yake fada min an bashi gado asibitin sunce wai canji ruwa ne ko kuma yaci wani abu a can wanda suke gani kamar bai dace da cikin shi ba.
Nan yake ce min mama tace yazo yaje dani yanzun don suna son zuwa gida suyi sallah su tinda yadan ji sauki .
Mun isa mun samay shi kwance yana barci har ya fada sosai bashar yake tambaya baiyi aman ba ko sukace yayi har sau biyu bayan tafiyan ka ai.
Ina tsaye kan ahi na kura mai ido ina kallon yadda ya koma a raina nake cewa wabda duk yai maka wanan asiri Allah ya saka maka.
Muryan mummy ne take fadin bari muje gida mu dawo sai azo maku da abinci nace ai da a barshi Iyya tana can tana hadawa ai.
Sun wuce aka barni da yaya bashar basu dade ba maryam suka iso da mahaifiyar yaya bashar din nan muka zauna atare dasu.
Sai dai mama tana bugo waya akai akai tana tambayan ko ya tashi a lokacin ko yana aman har yanzu ?
Nace bai kara yi ba yana dai barci ne tace Fatima kada ki yarda a cika dakinbda suruti kinji ku barshi ya huta please nace to mama.
Nan kuwa muka fara ganin yan uwa da abikan arziki harda ma wanda bamu sani ba suna shigowa gaidashi.
Mummy tagama shiryawa tace wa mama su fito su zo mama tace haba hajiya kubura kamar ban gode ma Allah ba ke nan ai.
Gaki ga matar shi da yan uwa a kan shi may kuma zan koma yi adduan mu yake bukata kuma ya samu ko?
Allah dai ya bashi lafiya sai kun dawo agaida su mummy taji dadin hakan sosai suka tafi tare da,Abdul.
Yadda yan uwa suka nuna mai yasa na gane cewa sadauki dan gatane sosai don sai ga yaya Imiran da matar shi tare da abincin sukazo muna.
Nan dai guri ya cika makil Nafisa da kawayen ta sun shigo su ma nan suke cewa yanzu Naffy ke fada muna mukace bamuga zama ba ai uwar dakin mu na cikin tashin hankali.
Kowa yai mamaki jin abinda suka fadi may ye hadina dasu kuma sai cewa Raiha tayi muna zuwa muna cika cikin mu ana muna,taron arziki ai dole ne mu zo gurin ki.
Wani likitane ta ke duba shi ko na kira P M O ne yazo da kan shi ya duba muna shine dai.
Kowa yasan zasu uya don sunyi kamari wuce pmo ma balle director gaba daya.
Yaya Ahmed suka shiigo da matar shi jamila a lokacin dressing din ta kawai ya isa mutum ya gane ko ita wacece.
Sai yatsune yatsune takewa mutane tana kallon shi tace au ashe shine ban ma taba ganin shi bani.
Sosai na mayar da hankalina gurin su Nafisa da kawayen ta muna hira maryam sai haushina suke ji da Amirah.
Suko yadda na ke tare da,su yai masu dadi sosai a ran su don sai jana suke da hira ina dan murmushi.
An cika duk yan gidan su ne gungun gungu a haraban gurin falkawa yayi da karfi yake kiran Fatima Fatima da sauri yaya bashar ya shiga dakin Abdul ne yakirani.
Na mike da sauri gabana yana faduwa idanuwa aka sako min caa da kyat nake tafiya a lokacin.
Jamila matar yaya Ahmed bata sanni ba sai ranan take fadi au matar tashi ke nan ashe ?
Ina shiga ya falka Bashar yana tsaye a kan shi lokacin na karasa gurin shi ya miko min hannun shi yana cewa zauna kija min hannu na da kafa please.
Mummy ma tashigo dakin don ganin ya falka a lokacin tana mashi sannu da jiki ya amsa mata da kyat da sauri ya dago yana son mikewa yace amai yake ji sosai da sauri na dauko roban da aka sayo don ya dinga yi a cikin shi.
Amai yayi sosai bakikirin dashi nan hankalin duk wanda ke gurin ya tashi sosai sai kawai ya rufe idon shi ya zama colarbs jiki ya sake mai da sauri na karasa ina kiran sunan shi bashar yace na fita dakin .
Don kuka yaci karfina a lokacin ganin na fito ina kuka yasa mutanen da sauri suka karaso jikin maryam na fada ina kuka tace may yafaru nace baya numfashi maryam da sauri mazan gidan su suka shiga gurin shi dakin
Ina nan naga bashar yafito da sauri ya nufi gurin likita duk wanda ke gurin hankalin shi a tashe yake sosai naji dadin su Nafisa da kawayen ta don sun nuna damuwan su sai akaina.
Likita yazo da sauri suka shiga dakin yana fadin suma yayi bayan ya duba shi ai hankalin kowa a tashe can sai ga baba da su umma sun zo.
Ikon Allah sai Nafisa ke fadin to baidai mutu ba balle aji dadi ba,azo ba sai yanzun da akaji ance baya da rai yana nan daram.
Taba wasu haushi musaman yan uwanta amma babu yadda suka iya da halinya dole aka saka mata ido uwayen dai sunji kunya sosai.
Yana falkowa yake fadin Fatima jamin hannuna da kafa please, sai da yaba kowa tausayi a dakin na koma dole dakin duk da ga iyayyen shi amma ina dan matsa mai hannayen shi da kafa a hankali.
Har dare muna tare da mummy don cewa tayi anan zata kwana amma sai yaya bashar yace duk mu tafi gida dashi da sagir da Abdul zasu kwana gurin shi.
Hakana na kwana a cikin zullumi tun da safe washegari ina asibitin gurin shi.
Ance mutum mai yawan bautar Allah yakan zama wani lokaci kamar waliyi ne saboda yawan ibadan shi.
Hakane ya faru da mama don tai sallah nafila tadan zauna tana tasbihi kafin a kira sallah asuba tayi sallah.
Nan tai mafalki ana ce mata kada ki damu taimakon shi Fatima tayi amma zai mike.
Ta falka firgigi da ita tana cewa subbahanallahi Fatima kuma haka yasa zuciyar ta zargin akwai wani abu a kasa amma koma may ye zata binciki Fatima din taji.
Sun shigo gaida shi da safe ne ta kirani gefe muka gaisai da ita can ta dafani tace ki kwantar da hankalinki insha Allahu zai samu lafiya kinji.
Can naji ta dafani sosai tace Fatima may kuka ba saudauki ya shane haka mai karfi don nagani a mafalki na yau.
Ras, ras gabana ya fadi uku uku lokaci daya nadaugo kai na da sauri na kalleta tace ba boyo tsakani na dake fada min nace cikin kuka mama yaya bai bar sha ba har yanzu.
Shine yaya bashar ganin muna yawan samun matsala ya koma gurin mutumin nan shida maryam suka anso wani wanda zai amaye abinda yasha gaba daya a jikin shi.
Ina fadin haka na dago kaina kalle ta murmushi naga tayi ta dafani tace Allah yai maku albarka Fatima kun karasa aikin dani ce ya dace nayi shi tun farko.
Kuma duk halin da kuke ciki na sani maryam ba ban sani bane amma tunda kikayi yadda nake so dake rufin asiri a tsakanin ku yasa na ja bakina nai shiru dashi.
Tace ban son jin zancen nan a bakin kowa daga Allah sai ku da kukayi don koshi kada ki yarda ya fahince ki don zai dauka wanan wahalan da yakeyi kashe shi kuke son yi ba taimakon shi ba .
Don haka ki rike wanan sirin a ranki ki boye sirin mijin ki danaki a kowa kinji Allah yai maku albarka nagode Fatima abinda nai hasashe ke nan tun farko akan ki.
Tare da mama muka dawo dakin yana zaune ya ramay ya fada sosai kamar bashine yadawo bulbul dashi ba.
Ya samu sauki don aman ya tsaya sunce har cikin dare sai da yayi aman sosai bakikirin dashi.
Yanzu sai barcine ya ke damun shi da ya dan falka sai ya koma yaci gaba da barcin shi.
A sibiti muka fara azumin wanan shekaran da wata ya kama na azumi amma ya samu sauki sosai.
Azumi uku mukayi a asibitin aka sallamashi ya dawo gida nan naci gaba da jinyan shi da kaina.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,


IDAN KUMA KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI DA ALLAH YAR UWA,,,


Ya ramay sosai sai dan wuya da ya aje a lokacin ga wani irin barci da ko ysushe yakeyi ni da iya ne kawai muke azumi don shi bai iyawa a lokacin.
Abinci ma sai da kyat nake samu ya dan tsakura yaci yasha magani.
Yau hudu ga watan azumi ya fito falo ya kwanta tun safe yake kwance a falon sai shige da fice masu zuwa dibiya sukeyi a gidan zuwa azahar bayan a watse ba kowa a gurin shi gurin da ya idar da sallah yake zaune.
Nafito zan shiga kitchen gurin da iya take a zaune ta na fere dankali na nufa sai ji nayi ya kira suna na a kasalance da Fatima.
Na amsa tare da juyowa gare shi kan shi na a,saman kujera baida lakka da gani a jikin shi.
Na karaso tare da zama a saman kujera da kanshi yake sama gyara kan nashi yayi tare da dora kan shi saman cinya na da kyau.
Yace wai may ake cikine ban ji kin ce min komai ba ba hannuna na dora saman kan nashi dake saman kafafuna na a hankali ina shafa mai kai dashi.
A hankali naji ya sauke ajiyan zuciya tare da lumshe idanuwan shi ya kara sako min nauyin shi a jikina.
Nima lumshe idanuwa nayi a lokacin nace yaya love kamar may fa ke nan ?
Yace may za,a ba mutane ne na azumi don na dawo da niyar na tambaye ki naji yaya za,ayi ne may ya dace aba mutane na azumi.
Na lumshe idanuwa again nace yaya bazaka bari kaji sauki ba sai ayi maganan ?
Murmushi naji yayi yace ai naji sauki mana ya kamata ayi wani abu don lokaci yana ja gashi ina son zuwa umurah cikin watan nan.
Nace to Allah ya kara baka lafiya yaya yanzu may kake ganin za,ayi ne ke nan ?
Naci gaba da cewa su baba ma nasan kaine mai tallafa mashi yanzu gashi kuma lalura yazo ya gifta akai.
No ki bar zancen na su baba da mutanen Rabah na riga nai masu tana din nasu ko yanzun dai ina son ki taimaka min ki yi list din mutanen da kika ga yadace aba wani abu sai na gani nace to bari na dauko pepper da biro sai na fara a gaban ka ko ?
Sai dana je gurin Iyya a kitchen na bata hakkuri taci gaba da aiki zan dan yi wani abu yanzun ne.
Tace haba hajiya dama dai aike ce baki zama amma komai da kuke bukata ai na iya yanzu wanda ban iya ba zan kiraki ki duba min .
Na dawo gurin shi ida na fara rubuta sunayen makwabtan su na can gidan baba.
Inayi ina lissafo mashi wa yanda nake rubutawa har na kawo gurin na ugun da muke zaune a yanzu shine ma yake kara tuna min da wasu gidajen idan na manta.
Yace banji kin sa sunan mutanen ki ba mana suwa ke nan yaya na tabaya cikin sonji su ?
Yace masu gadin ki mana nace Allah sarki wallahi har na manta dasu nan rubuta sunayen su ciki.
Nace shike nan ko ina ga an gama ya dan dago kai yana kallo na, yace kin san ban san mutanen arzikin ki na can gida ba fa ?
Murmushi nayi nace har dasu yaya za ,a rubuta yace ki rubuta su mana su ma.
Mutum kusa goma na rubuta mai yan uwana dana mamana har da yayan mama tabawa ciki.
Yace motan da nai odan kayan sun shigo sukace don haka bashar zai zo sai a bashi list din kinga ga musa ya dawo sai yakai na mutanen ku shi da driver ko ?
Yadda ya fada haka akayi washegari nan gida ya kace may su yaya Sagir yaya Abdul da yaya Jibrin kannen shi sai yaya bashar da wasu ma,aikatan su ne sukai ta faman rabon wanan kayan shi yana daga ciki tare dani ina kula dashi sai dai duk wanda ke son ganin shi yaya Bashar ya hana a shiga gidan sai da shi da kannen sadauki kawai suke shigowa gidan.
Take labari yakai ko ina sai ga al,uma bayin Allah masu bukata sun yo caaa a gidan.
Nan yace ma bashar da ya shigo ya fada mai araba masu sauran sai a karo buhu hamsin a hada masu dashi.
Ba karamin mamaki nayi ba da irin wanan abin alherin da yaya sadauki yayi ba koda yake ba mamaki don yagaji alheri ga uwa da uba ne.
Ankai kayan azumi a gidan mu ida abin ya zama abin magana a gari ashe ya ba da buhu biyar na shimkafa yace a rabawa mutane gari kuma ban sani ba sai da musa ya dawo ne yake fada min.
Nai matukar mamaki duk da ba,a mamaki da ikon Allah wai a kwallon kafa ne yaya sadauki ya samu wanan kudin haka.
Ikon Allah ke nan yau sadauki ne da,wanan irin alheri ga al,umma haka ubangiji Allah ya kara albarka.
A kwana na shidda ne da azumi yace zai tashi da azumin naso yadan kara sha amma yace zai gwada ya gani.
Lafiya yakai azumin shi ranan haka yaci gaba da azumin shi kuma yanzun yana fita zuwa site din su ya dan duba su.
Ranan ya dawo da dare bayan mun gama buda bakine yake cewa ina fatan kin fara shirin tafiya ko ?
Nace zuwa ina yaya ?
Yace umurah mana daga can kuma zamu wuce chaina akwai wani aiki da zanyi don ina son bude kamfanin karfe anan sokoto insha Allahu.
Ban san lokacin dana fada jikin shi ba na ma manta da wata Iyya Rabi a gurin lokacin.
Shima rugumoni yayi yana murmshi yace cikin harshen turanci kin san dama fa bamuje honey moon din mu ba kin ga sai muyi shi acan tunda kuna hutu.
Dan jaye jikina nayi tare da cewa kai haba yaya wani honey kuma bayan wanda ka lashe a nan cikin gidan ka yace to bari kigani idan mun tafi ai.
Koda na farga ashe iyya dake zaune tana kallon sallah a kasar makka ta bar falon .
Nace lah ashe iyya bata falon nan ban ma san tashin taba wallahi kaga ka koreta ko yaya ga Iyya da son kallo wallahi.
Yace kin dai koreta ke bake ce kika rugumay ni a gaban ta ba ya kamata fa ace an saka tv a cikin dakunan nan don kallo kinga ko musa na lura idan ina falon nan kamar ina takura mashi shima.
Washe gari kuwa sai ga masu hada starlight sunzo gidan suka hada ako wani daki na gidan kowa da nashi receive din a dakin shi.
Nan naita faman koyawa iyya yadda zata dinga kamo tashan da take so a dakin ta ita kadai.
Ashe tafiyan har su babane da su mama za,ayi shi sai da tafiyan ya matsone saura kwana biyu mu tafi naga ya shigo da passport din masu tafiya.
Daga iyya sai Musa na muka bari a gidan na fada mata don Allah kada a manta da masu gadi gurin girka abinci idan sunyi.
Naje gidan gurin su mama na samay su suna shiri gaba dayan su ban fita ba sai da na gyara mata kayan ta da daki da yake wuni zan dayi masu a gidan take ce min ai gwagona ce zata zo ta zauna mata daki da Amira don bata tafiya ta barta ita kadai a gida hakana.
Anty Amira sama sama muke don haushina da take ji babu abinda ya canza a ciki sai ma ince ya karu ne kawai yanzu.
Sai bayan la,asar na bar gidan zuwa gidan anty maryam can muka lalace da ita wanda hiran namu akan mazajen mu ne mukayi shi.
Na dawo gida na samu Iyya ta gyara ko ina ta gama komai yadda ya kamata sai bayan sallah magariba ya shigo gidan.
Muna falo gaba dayan mu sai mashi sannu da shan ruwa mukeyi a kasalance ya zauna don har yanzu ba wai karfin jikin nashi yake ji ba sosai.
Nan muka shiga jera mai kayan buda baki a gaban shi bai ci wani abu ba sai kayan fruits din da ya sha kawai ya kai kwance fuskan shi yana kallon tv ana sallah asham a saudiya tv.
Yace iyya Rabi gobene fa tafiyan mu insha Allahu zamu tafi mu barki da Musa sarkin son yawo kingan shi kada ki bari ya wuce takwas bai shigo gida ba kun rufe don tsaro.
Tace insha Allahu nawaje na za,ayi yadda kace yace kai kuma kaji may nace ko?
Musa yace naji yaya ai ba inda zan tafi ga tv nan muna kallo ai da rana ne kawai nakan dan fita can bakin shagon.
Daga haka yai shiru idanuwan shi suna a lumshe sai da akai kiran sallah suka fita tare da MUSA.

****** ********* ******
Washe gari da azahar muka bar garin sokoto zuwa sadauya mun sauka da dare inda akai muna screening motan da ke jiran mu muka shiga sai wani hotel nan muka kwana a jidda sai da safe muka wuce zuwa madina.
Ibada sosai mukeyi ba kama hannun yaro har su umma da mama sun bani mamaki sosai yadda naga suna ibadan su sai dai bawai sun bar halinsu bane ko acan.
Adduoina sun fi yawa ne akan Allah ya shirya min yaya sadauki da samun zuria masu albarka dam yan uwa musulmai da suka fada cikin irin wanan halin .
Sai dai a can ni da mummy muka zama kamar kawaye sai mama da muke tare da ita wani lokaci don mama bata da time din wasa ko kadan ko yaushe cikin ibada take .
Mun bar madina mun nufi makka a can mukai kwana goma muka fara shirin dawowan su gida mu anan zamuyi sallah two days after sallah zamu wuce chaina din.
Ana gobe zasu tafine ina makale da mama da mummy da wani iri shakuwa ya shiga tsakanin mu yanzun da ita.
A can nice mama take sakawa na zaba masu abubuwa ni da mummy wanda kusan sayayan na Amira ne da naji ance wai zatai aure bada dadewa ba.
Har gado nice yaya yasa a gaba na zabi gadaje har guda biyar masu kyau.
Da,safe mukai masu rakiya suka tafi muna tsaye muna kallon su ba yadda zan yi ban san lokacin da hawaye ya zubo min ba.
Muna motane yai dan murmushi tare da rungumoni zuwa jikin shi na langabe kaina ina share hawaye a hankali yace baki son rabuwa da mama ko?
Ban yi magana ba sai ajiyan zuciyar da nayi kawai muka kai masaukin mu wanka mukayi muka nufi masallaci gurin sallah sai dare sosai muka dan huta kwana biyu duk a cikin masallaci mukayi shi.
Ranan sallah na saka wani dogon rigan mai tsananin tsada da ya sayo min a wani katon shago na kayan mata.
Rigan da gani ta matan manya ce irin tasu sai wace ta isa take sayanta
Na yafa mayafin rigan take na koma kamar irin matan manyan larabawan da muke gani ko kuma matar wani kusa a kasan mu.
Ga zubbunan gold da na saka guda biyu a yatsuna wuyana kuma Diamond ne kiran Dubai sai takalma mai tudu da yar karamar jakan takalma dana rika a hannu na sai wani kamshin turaren larabawa ke tashi a jikina.
Yana falo zaune na fito a cikin shirina wani irin mugun kishina ne ya darsu a zuciyar shi.
Na karaso inda yake zaune shima kayan maza yasa na larabawa masu tsada na karaso inda yake zaune cikin wani takon da ban san inayin shi ba.
Wani kamshi ne ya daki hancin shi har ya saukan mai da kasala a lokaci daya.
Ya sake idon shi yana kallona har na karaso gare shi tare da,dan fadawa jikin shi ina cewa yayana barka da sallah.
Yace Fatima anya kuwa kece haka ko dai an canza min matane nace bari ka tabbatar da ni dince to na dan kai mai wani guntun cizo a kunnen shi ya dan saki wani dan kara yace muguwa.
Na mike ina dariya yace Fatima kinyi kyau kinyi kyau sosai wallahi ban san may yasa duk dogon rigar da zaki saka sai naga tai matukar karban ki kaman don ke aka dinkata ba ?
Gaskiya kafin mu bar garin nan sai na kara saya maki irin dogayen rigunan nan da yawa koda mun koma gida ki dinga min kwaliya haka dasu.
Nace kai haba yaya kaface da tsada ka,sayo su fa ai biyun nan ma sun isa haka please.
Yace Fatima shigan ki a cikin suturun alfarma shine mutunci na ga idon idon jama,a shigar ki shine zai nunawa duniya ni Umar ina sauke hakkina akan iyalina.
Ya jawoni da hannu daya na fada a jikin shi yace bakin san ko waye mijin ki ba ko bakin U F ba ko Fatima ?
Nai dariya tare da dan shafo fuskan shi da hannu daya yai murmushi nace niko nasan waye mijina don ni nasan kayana.
Yace to ki godewa Allah daya baki Umar a matsayin mijin auren ki uban diyan ki nan gaba kuma.
Yace Fatima mijin ki mai tsada ne mai daraja kuma a idon jama,a sai dai a idon mutum biyu zuwa uku ne kawai yake mai rauni.
Dariya nayi nace idona dana mama ke nan na ukun ne ban sani ba yace na ukun shi ne baba.
Kai yaya kada kaiwa baba haka wallahi tun haihuwan ka har yau baba baida wani da dayake ji dashi kamar ka a duniyan nan.
Iyya fa ta fada min irin son da baba ke maka tun haihuwan ka har ya kai su Umma suna kishin ka tun kana karami har yanzu.
Murmushi yayi tare da jawoni jikin shi yana sinsina na kamar ya samu handkici mai kamshi yacs nasani Fatima nima nasani wallahi.
Iyya Rabi batai karya ba son da baba ke min yasa su imma suka sakani a gaba da horo tun ina karami ga mamanki da shegen hakkuri duk abinda akai min kona fada mata bata cewa komai sai dai tace min inyi hakkuri kawai.
Ya kara motsoni a jikin shi yace kin san may fatima nace ,a,a yayana yace watarana har nakan zargi su Umma a raina akan da hannun su a cikin lalacewa na a baya.
Sai dai zato zunubine koda ya zama

Please Login or Register in order to submit comment