Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ba suna dai ganin hakane tunda ya tafi har wani kasa yin wasa.
Sai gashi ta dawo gida ta samu zancen abokiyar aikin ta ashe gaskiya ne ke nan boyon kurwa yai masu dama.
Maji dai ta rakata da harara tana fadin muguwa aniyar ki tabiki dakin ki munafuka yar sheri, Allah ya shirye ki kawai.
Maji tace wa Amira gobe ina son a kwashe tsofin kayan nan akai wa mai masa gidan ta ita ma,ta canza.
Nan Bintu tafara murna tana godiya kafin hjy masa tazo tayi mai karfi da bakin ta.
Sai da yamma da Alhaji yadawo ya samu wanan labarin gurin mama Asiya da ta fara tsegunta mashi ciki tsigar gulma.
Yace masha Allahu kai amma ko naiwa maijidda murna haihuwa ta fara rana ke nan yau Allah ya amsa mata adduan ta .
Sai ga maji da nashi tsaraban shaddoji da su turare masu tsada ta zube mashi su a gefen kujeran da yake zaune.
Ya kalleta cikin murmushi yana fadin yanzu Asiya take fada min abin arzikin da ya samay ki ashe sadauki ya fara fitar da uwarshi.
Maji tai murmushi tace kai haba Alhaji kai kuma da kanka zakai min sheri kuma.
Suna cikin magana sai ga hjy Bintu dauke da tsaraban ta dana yaran ta tana ta faman washe baki tana fadin ga abin arzikin da mutanen ghana suka kawo muna.
Yace mata nima kinga ga nawa nan yanzu aka kawo min shi ko dubawa ban gama ba.
Mama Asiya mai girki tashigo ganin kayan hjy Kubura dana yaran ta yasa take kallo don taga sun fi yawa ga idon ta.
Nan take cewa hmm muma fa anbamu har yaran nan gaba dayan mu gidan.
Masha Allahu inji Alhajin ya fadi yana mai kai ruwa a bakin shi yace haka ake son samu idan ka samu kowa ma yasan kasamu cikin yan uwan ka.
Yana gama cin abinci ya nufi dakin Maji don yaga abinda ake ta faman zuzutawa,
Yako gani kuma yai murna da farin ciki sosai sai faman sawa dan shi albarka yakeyi.
Bayan fitan su Amira tace ikon Allah yau Baba ne da kan shi kewa yaya sadauki wanan adduan haka.
Amma da can an zuga shi a kan shi sai faman cin mutunci da tonon asiri yakewa mutane a tsakar gida.
Maji take ce mata wanan ai haka yake duk uwa mai haihuwa sai ta samu bacin ran mahaifi akan dan ta watarana.
Don duk abinda yayi mara kyau laifin uwa ne maikyaune na uba ni dai na godewa Allah daya takaita min wanan bakin cikin da wuri.
Maryam dake kunna tv take cewa amma ai basu daina kiran shi da sunan mashayi ko?
Don ko dazun naji Umma tana fadin wai tsaraban yan shaye shaye suka samu take fadawa yaya Imirana da ya shigo.
Ba sai ta dawo dashi ba tunda bata son kayan mashayi da aka bata maganan banza kawai.
Maji dai shiru tayi batace masu uffan ba har suka gaji sukai shiru.
Da safe ne sadauki yaba mahaifin shi check din kudi yace yana so ya fara noma dashi ko za,a samu anan ma din
Bayan Alhaji ya karbi kudin yaga yawan su yake cewa sadauki duk wanan kudin haka akan kwallone kawai ka samay su.
Ya dan dukar da kan shi a kasa yace Baba a nan na samay su don ma ban yarda bane da,har wasu club sun so su sayeni amma,nace masu a,a subarni cikin club dina kawai har gaba.
Ikon Allah ashe Alhaji Sani gaskiya yake fada min cewa idan nai hakkuri Allah yasa maka hannu watarana sai na dara akan kwallon ka.
Murmushi kawai sadauki yayi ba cewa mahaifin nashi komai ba yana fita hjy kubura tana shigowa suka gaisa dashi ya fita.
Alhaji ke ce mata kingani ikon Allah kudi sadauki ya kawo min wai na fara noma dashi.
Maimakon yaji tayi murna yadda ya zata sai ji yayi tace Alhji adai binciki a gani wanan harkan amma abin yai yawa wallahi.
Ya juyo cikin mamaki yana kallonta yake cewa ban gane hausan ki ba fa kubura.
Tace ni gani nayi kamar wanan kudin sunyi yawa ace duk a saboda kwallo aka samo su haka gaskiya abincika dai aji.
Yace to kina ganin kamar da akwai wata a kasa ke nan ko ya tambaye ta don son jin may zatace.
Tace gaskiya kasan halin dan yau fa kada ya yaudare ku da,wasan kwallo ya fada wani harka na tir da Allah waddai.
Cikin mamakin jin abinda ta fadi yace assha kubura ban zaci jin wanan magana daga bakin kiba wallahi.
Sai lokacin ta tuna tayi barambarama fa don mahaifi mahaifine ai,da sauri ta gyara zancen tana cewa a,a ba wani abu nake nufi ba kasan halin dan yau ne shi yasa na ce a dai bincika kawai ba wani abu ba.
Nan dai taita kamay kamay ta tafita shi dai yana jin ta kawai baice mata komai.
Kwana biyu sai gashi zance na yawo a gari da unguwa wai ya samu kudi ba,a san inda yasamo ba sai facali yake iyayyen shi suna jin dadi.
Wasu suce wai ba kwallo aka dauke shi ba zuwa akayi dasu suka fita da kwaya kasan waje shine aka fake da kwallo kafa.
Maji dai da zancen yazo kunnen ta da farko ta so tayar da hankalin ta don sai da ta tsure sadauki a dakin ta take tambayan shi gaskiyan zancen abinda taji.
Murmushi shi na rabin fuska kawai yayi mata yace haba Maji idan wani ya fadi an yarda aike bai kamata ki yarda da wanan zancen ba don kin fi kowa sanin halina.
Ban son raini da wullakanci shiya sa na roki Allah yai min mafita na dogara da kaina.
Nan dai hankalin ta ya kwanta tace koma,waye yai muna wanan sherin mun barshi da Allah shikw nan.
Takara ja mashi kunne akan ya futar da ita da yan uwan shi daga kunyan duniya don mutane yanzu ake kiwo ba dabbobi ba.
Bata hakkura ba ranan da take da girki ma saida ta samu maigidan su da wanan zancen.
Yace au kema ashe zancen yazo kunnen ki amma ya kamata ace kin san halin abinda kika haifa.
Ni ban ji ko dar ba akan maganan nasan kawai hassada ne irin ta mutanen yanzu kawai.
Amma ai watarana gaskiya zatai halin ta don shi kwallo ba,sanar boye bace duniya tana sanin mutum a lokaci guda.
Ki dai yi mashi fada yai tanadi kada yaga kudi suna shigo mashi haka dayawa lokaci guda yace zai bullo da shashanci cikin rayuwan shi.
Haka yasa tattara zancen ta watsar tabar masu hassada akan danta suna zuba mashi taki.

****** ********* ******
Sadauki yana zaune a cikin falon Maji duk kannen shi sun tafi makaranta sai ita dake final exam din ta yanzu.
Wayan shi yake dakila ta hanyar yin game da ita,Bintu tafito daga cikin dakin kwanan su bata san da yana falon zaune ba a lokacin.
Tana saye da da dogon riga na atamfa a jikin ta, style din dinkin da akaiwa rigar yai matukar mata kyau a jikin ta.
Tunda ta sanyo kai falon ta gashin a zaune sai taji gaban ta ya fadi don a rayuwan ta ta tsani ta gan shi a falon zaune don yawan takuran da takeyi.
Jin motsin da yayi a zaton shi ko Maji ce tafito daga cikin dakin yasa shi daga kai ya kalleta.
Bintu ce ya gani tana kokarin komawa cikin dakin da tafito din,cikin sauri.
Yace cikin daure fuska ke zo nan kina abu kamar muna fuka dake, cak taja ta tsaya tare da juyowa inda yake zaune.
Yace ina Maji take ne ban ji motsinta ba ya tambaya cikin ci gaba da latsan wayar shi .
Tana dakin Baba tana gyarawa amma yanzun zata dawo,,,
Hannu ya daga mata yana fadin ban tambayeki ba bani abinci na naci yace cikin gadara da daure fuskan shi.
Haka ta karasa fitowa ta gaban shi ta wuce ba don taso ba inda yabi bayan ta da dan tsuki yana fadi a ranshi jita dan Allah kamar zata kare, mace haka ba kiba ko kadan.
Tafito da abincin cikin sabon kulan shi da ake saka mai abinci ta aje a gaban shi ta juya zata dauko ruwa ya kara binta da kallon haushi.
Yadan kara jan guntun tsuki wanda yai daidai da shigowan Maji falon, tace, a,a Baba na kai dawa kuma ke wanan tsuki haka kai kadai?
Yace kai tsaye ni da wanan yar kauyen mana tafito taganni shine kuma wai zata gudu anya maji yarinyar nan kuwa tana da gaskiya ya fadi tare da,dago kan shi yana kallon Maji.
Wani kallon da yaga tana mashi yasa shi shan jinin jikin shi ta,wuce zuwa ciki ta aje kayan dake hannunta.
Jima kadan tafito ta zauna tana fuskantar shi tace gaskiya banjin dadin irin yadda kakewa yarinyar nan,
Ko banza taci albarkaci na nida na ajeta a gurina bawai bata da gata bane a,a itama tana da gatan ta rayuwane kawai yasa ka ganta anan din.
Amma yarinya tana tsaye tana iya kokarinta a kan mu kai kuma,sai binta da hattara kakeyi da wani zataji na rashin iyayyenta kusa da ita ko kuwa da halinka zataji.
Ban son karatun yarinyar nan ya tsaya ne shiyasa kaga ana ajeta a gurina don itama watarana iyayyenta suyi alfahari da ita.
Ashe ba dadin ku bane yau ace a sanafin mu ta zama wani abu a duniya, ban rokeka komai don na tallafa mata ba.
Amma kasa yar mutane gaba haka da tsangwama tare da hattara ba yau ba ina lura balain tsoron ka fatima takeyi wallahi.
Wani kunci ne yaji ya rufe shi a ranshi ya mike ba tare da ya gama cin abincin da yake ci ba ya bar falon cikin fushi.
Maju da tabishi da kallo ta,tsuki tace sha sha kawai mara hankali mutane suna bakin cikin zaman ta anan kaikuma kace zaka tsiro min da naka kalar tsiyar a kanta.
Tsayin sati daya sadauki yana fushi a kan maganan gashi ya hana Bintu sakat a sashin nasu don da ya shigo ya kama hararan ta ke nan da kuma tsuki.
Allah Allah Bintu keyi ta gama exam tabi gwagonta kauyen su don dama zaman dole take a gidan.
Hankalinta yana gurin iyayyen ta da yan uwan ta don tunda tazo bataje gida ba,bata kuma ga kowa ba cikin su sai gwago dakan dan zo ta kwana biyu ta koma.
Allah ya taimaketa kafin su gama exam aka kirasu Abuja inda ya kwashi komatsen shi yanufi gurin kiran da akai masu.
Hakan ya,dan ba Bintu daman sake jikin ta har maji ta fahince ta tafi sake jikin ta idan baya nan ke nan.
Amma tana gama exam ta fito da zancen son zuwa gida don tagano yan uwanta.
Hankalin Maji yai matukar tashi a lokacin inda take tambayan ta cikin lalashi ko an mata wani abine take son zuwa gida.
Bintu tace cikin sanyi murya da,sauri a,a mama ba ai min komai ba ina dai son zuwa,nagan su ne tunda nazo banje gida ba shiyasa nake son zuwa nagano babana da yan uwana.
Maji ta sauke ajiyan zuciya tare da,tambayan idan kin tafi yaushe zaki dawo Fatima?
Don nasan ko kwana,nawa zakiyi acan saboda na tura a dauko ki in lokaci yayi.
Bintu tana,wasa da yan tsunta,da,harde su guri guda tana cewa mama sai na tafi tukun don ban san hukuncin da mahaifina zai yanke a kaina ba yanzu tunda na gama karatu na ko.
A,a Fatima idan hakane ki bari mu tafi tare sai mu kwana daya mu dawo, tare.
Da sauri Bintu ta dago kai tana fadin mama har gurin mahaifiyata nake son zuwa don mun dade bamu ga juna,ba da ita.
Eh to gaskiya hakan yana da kyau kuma ina ga,dai kila zakiyi sati biyu zuwa uku ke nan eh mama Bintu ta bata ansa da hakan wanda ta dai fadi ne don su rabu lafiya da maman nata sabuwa.
Amma yadda tajeji bata sa ran cewa zata dawo wanan gidan ba kuma da sunan zama duk da dai ba ai mata komai ba amma gidan ya fita ranta don tana gudun kada sanadin ta mama tai fada da dan ta daya shiryu yanzu.
Tsaraba sosai Maji ta hadawa Bintu na gidan mahaufinta da yan uwan ta daban wanda zata kaiwa mahaifiyarta daban.
Mota akai mata shata ita kadai Alhaji yabiya tare da bata kudi da zata rike don amfanin ta a can.
Kamar yadda akai alkawari da driver hakan yayi har kofan gida su Bintu ya kaita inda aka,ganta a bazata don ba wanda yasan da zuwan ta.
Irin kayan da,akaga a na,shigowa dashine yasa hankalin matar uban ta ya tashi, har ta kasa boyewa da zuwan Bintu din.
Nan dai kowa ya,wayance sai sannu da zuwa ake mata ana kallon yadda a lokaci daya ta canza kamanin ta gaba daya ta koma wata yar Birni da ita.
Kafin wani lokaci har zancen dawowanta ya zagaye dan kauyen nasu kowa na fadin Bintu ta dawo ta koma yar Birni da ita.
Saida dare ta samu ganawa da mahaifinta wanda ya dawo daga gona a lokacin ana gabanin magariba.
Nan suka kebe tana bashi labarin zaman ta a burni da kuma mutanen arzikin da gwagon ta,tabarta gurin su.
Takawo sakon da maji tabata na,tsaraba ta bashi yana ta murna da farin ciki.
Bintu ta sheda mai ta kare karatun ta har matar dake rikon ta tace zata ci gaba da karatun ta idan jerabawan ta ya fito.
Mahaifinta yai farin ciki da jin wanan albishir din da tai mashi sai dai kuma yasan abune mai wuya yadda ta girma haka yan uwan shi su barta taci gaba da karatu sai dai in Allah ya nufa zatayi din.
Washegari Bintu kamar yadda ta,saba zuwa daukan karatu a lokacin da take gida hakan ta shirya zuwa islamiyan su.
Sai dai ta samu yawanci yan matan da suke karatun tare sunyi aure a lokaci, dan kauye basu bari yarinya tagirma sosai suke mata aure.
Malamin nasu yai farin ciki daganin hazikan daliban shi ta dawo kuma bata watsar da karatun ta ba don taje birni.
Taso ta fara a inda ta,tsaya da karatu a gurin shi amma da,tafara biyawa sai yaji ta,wuce tsanmanin shi.
Don haka yace ta dauka a inda,take can birni haka yasa taci gaba don ta sauka bita take yanzu.
Ganin duk idon sauran dalibai yana kanta kuma suna sauraren yadda sabon sallon karatun ta yake fita.
Duk sai sha,awan ta ya kama su nan suke zuwa wai ta koya masu yadda take fitar da haruffa cikin kara harshe.
Nan fa samarin kauyen masu jin sun isa suka fara kawo kan su gareta da,sunan sun gani suna so.
Itako mama ta,bawa matar ubanta tunda ta kyala ido taga kayan maihaifiyan Bintu da maji ta bata ta sa a ranta su take so.
Bayan nata da,takawo mata da yaran ta duk sai da Maji ta ba kowan su tsaraban da zata basu in tazo.
Haka ta,bawa tasa Bintu da mahaifinta gaba da masifan kan lalai sai dai ta dauki turmin wajen ina da aka bata takai mata.
Har abin yaso yakawo sabani a tsakanin ta da mininta watau mahaifin Bintu.
Don haka Bintu ta tsiri tafiya garin da mahaifiyarta take bashiri don tabawa sai fada takeyi wai bayan tagama wahala da ita yanzun anga dadi yazo shine zatace tasan uwar ta.
Bintu dai murmushi tayi kawai tana hada kayanta tare da tunanen yadda zata zauna gida da wanan masifanna matar mahaifin ta kulun.
Ta hada duk dan abinda tasan tana so tana bukata a cikin kayan ta tafito tare da,yi masu sallama ta tafi abinta badon ta tashi zuwa ba.
Ganin ta kawai mahaifiyarta tayi a bazata don rabin ta da ita tun tana aji hudu na primary bata sake zuwa ba don maigidan ta baida dadi ko kadan.
Bai son yaga Bintu tazo wajen uwarta ya shiga fitina da mitan shi baison zuwanta tana zuwa tana hure mata kunne don ta koma gidan mahaufinta.
Ta,samu mahaifiyarta da tsohon ciki a jikin ta kuma yana bata wahala don haka tun zuwan ta bata huta ba.
Da maigidan ta ya dawo daga Kasuwan kauye ya samu Bintu tazo ya dan fara daure fuskan shi.
Saida yaga abin arzikin da tazo masu dashi don har shima ya samu shadda yadi goma.
Shine har ya dan sake fuskan shi, yazo har dakin su fuska a sake yana cewa ,a,a Bintu harda tsaraba muka samu haka mai yawa.
Har yana tambaya ko taci abinci da tazo nan dai ya karaci surutin shi ita dai Bintu kai kawai ta gyada mashi har ya fita.
Washe gari tun da safe Bintu ta tashi ta gyara ko ina na gidan nan gidan yakoma wani fes dashi.
Sai zuwa rana ta fahinci ko abinci basu dashi a gidan nan ta saka katon hijjab din ta har kasa ta fita can sai gata da kayan cefanen ta niki niki mai mashin ya kawota gida.
Bata tsaya ba ta girka masu abinci suka zauna ita da yan kannen ta suka ci suka koshi harda mahaifiyarta dake auren wahala.
Maigidan sai zuwa rana ya dawo yana yan kamay kamay shi wai tunda ya fita ko sisu bai samu ba sai dan fura da akabashi da nono yace a dama,mashi,
Matarshi ta mike da kyat ta shiga daki sai gata dauke da kwanon abinci yana mamakin ina tasamu kudi har tai masu girki.
Bayan ta aje yake tambayan ta don ya zaci taciwo mashi bashine don diyarta tazo ta girka masu abinci.
Matar tace mashi yaringa ce ta sayo ta girka muna nan ya wani washe baki yana bude kwanon yai tozali da shimkafa da miya harda nama a ciki.
Yashiga ci yana sakawa Bintu Albarka tare dakai lomar abinci a bakin shi.
Bintu da ke daki tausayin mahaifiyarta ya kamata don tasan wanan susun mijin nata bai aje komai ba sai bakin shaye shayen da yakeyi kawai.
Abu tun bata da,wayo yake haka har yanzu data girma ta zo ta samay shi a hakana.
Dalilin da yasa ke nan take matukar tausayawa Maji akan shaye shayen da dan ta yakeyi don tasa mugun abune mawuyacin abune mutum ya daina shi a rayuwan shi.
Da yamma sai gashi da dan kunshin a leda yana wargale baki yana fadin ina,diyata ne gashi ba,sayo mata dan abin mu na kauye taci don nasan can birni basu samun shi.
Bintu najin haka tafito daga dakin tana gyara daurin dan kwalinta ta nacewa gani Baba.
Ya mika mata ledan ta,karba batare da,tasan abinda ke cikin ledan ba yana fadin ki gyara kici abin marmari ne gare ku.
Ta dauko kwanon ta bude ledan zogalane da rogo dafafe da zafin shi ya sayo mata harda kulikulin da zata gyara shi ya hado mata.
Bintu ta zauna ta gyara tasamo wani kwanon silver na miya ta zuba mashi azaton ta,bazai karba ba sai gashi ya karba har ya riga su cinyewa ko.
Sai faman santi yake zubawa sosai taji dadin ganyen don ta dade bataci ganye ba haka mai yawa.
Kamar yadda tai masu girkin rana haka ta girka mazu na dare inda tai tuwon garin masara data sayo da miyar kuka yaji daddawa da kayan yaji sai kamshi ke tashi ciki.
Haka ta zauna gidan mahaufiyan ta don yafi mata dadin zama gidan mahaifinta da matar uban ta ke sakata gaba da fitina kyashi kishi da hassafa duk ta dagwara mata shi.
Satin ta biyu a kauyen bata fita ko ina kulun tana gida da yan kannen ta suna hira ko tana koya masu karatu.
Ranan dai mahaifiyarta ta matsa mata akan tafita taje gidan yan uwan ta,su gaisa.
Ba don Bintu taso ba ta shirya tare da yan kannen ta mata biyu suka fita zuwa gidajen dangin su.
Suna gap da zasu dawone suka hadu da,wani matashi daganin shi kasan bako ne a garin ko kuma dai yazo ne ba,a nan yake zama ba.
Saboda yanayin shigar shi jikin shi da suturun shi ya banbanta da na mutanen da yake tare dasu a gurin.
Tun da su Bintu suka tunkaro idon mutimin yake kanta duk da katon hijjab din dake jikinta bai hanashi kallon ta ba.
Sun kawo daidai inda suke Bintu tai masu ina wuni gaba daya suka amsa cikin washe baki, a hankali mutumin ya tambayi wanda suke tare wanan a garin nan take ne ?
Har zasu wuce sai dayan mutumin yace wa dayar kaunan Bintu a,a Dije bakuwa kukayine yarinyar ta tsaya tana cewa eh yayan mu dage Birni ne tazo.
Su dai suka wuce zuwa gidajen da Inna ta tsara masu sutafi sukai Bintu ta gaida su.
Agajiye suka dawo gida lokacin yanma tayi ko gashi batai sallah la,asar ba don haka ta shuri buta ta nufi gurin alwala don kada lokaci ya shige.
Inda ta idar da sallah tana zaune mahaifiyarta take tambayan ta kawo mata abincine tace sun koshi tasha fura a gidan kakanta.
Sai ga,yaro yana sallama yace wai ance ana sallama da bakuwar gidan nan.
Bintu dake daki a ran ta tace ai kaji matsalar wallahi shiyasa ban son fita ko ina wallahi.
Bata so fita ba amma mahaifiyarta ta takura mata akan sai tafita badon taso ba haka ta shirya tafita cikin katon hijjab din ta kamar kullun.
Wanan mutumin da tagani a cikin gari dazun shine tsaye a kofan gidan nasu ya jingina jikin shi da motar shi baka henixe,
Yana dan kada makulin motar dake hannun shi a hankali, yana ganin fitowan ta ya dan fadada murmushin shi.
Yana cewa barka da fitowa gimbiya sai kika gannin kwasan kofan gidan ku babu tsanmani kuma ko?
Murmushi tayi tana fadin ina wuni yace shaf kinga na manta bamu ko gaisa ba ko ya kuke ya garin kuma?
Ta amsa da Alhamdullahi,
Yace ko da yake nasan ke bakuwa ce a wanan garin don ban sanki ba a garin namu.
To nidai sunana Mohammed Kabir kuma ni haifafen wanan garin ne ina aiki a abuja ne ina da mata biyu da yara biyar.
Jin haka Bintu ta dago kai tadan saci kallon shi yace yes kwari kina mamaki ko nayi yaro da,tara iyali haka ko?
Gashi kuma nagani ina son karawa ta uku ke nan insha Allahu idan an yardan min.
Mahaifina shine hakimin wanan garin nine kuma dana uku a gidan mu don yan uwana da kowa nawa suna garin nan da zama nine kawai Allah yakaini wani nahiyar zama.
Ina aiki a Federal houses ne a can da fatan kin gamsu da bayani na.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,

A LOKACIN MU KE,,,,,,,

Zau ne take a tsakar dakin da ta gyara da sunan ta wanda babu mai shiga daga ita sai kawayen ta dakan shigo gidan

Please Login or Register in order to submit comment