Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

duk kin wani rude a kan shi don kawai kije abuja.
Baki tsaya kin tsarawa rayuwan ki abinda zai fishekiba mutum da iyali haka ke karama dake may zaki gane a gurin shi inba wahala ba.
Kai dakata ya isa haka na,rasa gane dalilin dayasa kake wanan abin haka
Yadago ya kalli uwar yace may nakeyi maji iyaka dai ina fadin gaskiyane ni kawai.
Duk abinda na hango mata kun kasa hangen shi sai faman rawan kai takeyi ita zatayi aure wawiya kawai doluwa.
A,a wai sadauki kana da hankali kuwa da may wanan abin yai kama hakane wai?
Mikewa nayi fuuu, nabar falon cikin fushi na shige ciki abina don ban iya tsayawa sauraren wanan shirmay na shi.
Tun ranan idan yaya sadauki ya shigo falon duk hiran da ake haka zan mike tsam na shige daki abina.
Ranan muna tahiran mu cikin dariya har maman tamu tana saka muna baki a hiran mu don hiran wasu samari da suka zo wai suna son maryam muke yi muna dariya.
Ya shigowa suna mashi ina wuni da jan shi da hira yana batun zama namikw tsaye tsam daga inda nake zaune, ina cewa.
Zan shiga na kwanta maryam tace wazai kwanta yanzu ke da baki barci koda rana shine yanzu da yamman nan zakice wai zaki kwanta.
Ya dago lumsarsun idanuwan shi masu nuna a gajiye yake a lokacin don tun safe yafita daga gida .
Ya dora su a kaina gaba daya yaga na canza mashi na koma wata fresh sosai dani don nima ban san may mama take yawan bamu ba muna ci muna,sha na gyara jiki kawai .
Ko kiftawa bayayi don mamakin sauyawa na a lokaci guda da yaga nayi mashi a lokaci guda.
Mama taga yadda yake kallona sai abin ya bata mamaki kwarai da gaske amma sai ta dauka wani sherin yake son fadi akaina kuma.
Don haka tai shiru tana sauraren taji abinda zai fadi a lokacin tai mashi tsiya.
Maryam dai tasan yar tsama muke duk kwanakin nan ta dai dubeni saboda ta san ba,kwanciyan zanyi ba ganin yaya ne kawai yasani barin falon nashige tana ce min atashi lafiya ko?
Nashige batare da na,kara,waiga inda yake ba ballw yace ga abinda nai mashi kuma.
A bangaren sadauki kuwa, fuska ya kara,daurewa batare da ya kara bi ta kaina ba don yasan mama tana jiran shi ne.
Maryam daga inda take tai mashi kuri da ido tana dariya cikin kyata tace ban san wanan fadan na yaya da Bintu ba wallahi.
Bai tanka mata ba sai tsukin da yaja ya dan dafe kan shi yana fadin rabu da,wawiyan banza kawai gaskiya ne bata so a fada mata.
Daga gurin da maji take cikin takaici tace gaskiyan may kada tai auren ko may ?
Yace ni fadan gaskiya nake mata saurin may take da,bazata iya tsayawa ta karasa makatantar taba ne wai, duk tsoho ya, hure mata kunne bata jin kiran yanzu sai
When it's too late to her zata gane kuren ta ai.
Allah dai ya tabbatar muna da abinda yafi zama alheri a gare ta.
Ina shiga daki kamar jira kabir yakw na shiga dakin sai ga kiran wayan shi ya shigo min.
Mama ta kwalla min kira wai nazo za ai program din da nake so wasan kwaikwayo a NTA sokoto wanda nake so ina kallo ina dariya don shirin irin namu ne na mutanen kauye.
Hakan bai hanani yin wayana ba don can na manne gefe guda yadda,ba mai jin abida nake fadi.
Kallo daya zakai min ka fahinci cewa ina cikin nishadi da wayan da nakeyi ga kuma kallon film din da nakeyi a tv duk a lokaci daya.
Muryan kabir ce ta ratso dodon kunne na yana cewa Fatima nayi rashin ki kwana biyu aiki ya hana nazo na gane ki.
Nayi murmushi tare da lunshe idanuwa na na gyara zama da kyau.
Ban bashi amsa ba sai yar murmushin da nayi har yana jiyo ni a,wayan a lokacin .
Ya naji kina murmushi ko baki yarda na damu da nazo na ganki bane wai?
Na koma yin murmushi mai hade da sautin dariya wanda ya jawo hankalin kowa a kaina a lokacin.
Nace may zai hana na yarda duk da dai nasan akwai wasu a,tare da kai ba,wai wani damuwa zakayi sosai hakana ba ai.
Yace kowa daga cikin ku ina bashi hakkin shi ai nace ai nasan da hakan, yace da kyau da kika fahince ni.
Yace wai kin san wani abu kuwa nace a,a cikin dan girgiza kaina kamar yana gani na a fili.
Nace sai ka fada dai,
Yace wai ko Fatima kin san yadda nake jinki a cikin raina kuwa, ?
Wallahi da ina da iko ko kuda bazan yarda ya sauka a kanki ba.
Don ina ji a jikina ke wani abune da,Allah ya jefo min a cikin rayuwana mai muhinmanci a gareni.
Murmurshi nake irin mai kyalkyatawan nan nace kai amma kuwa nikan nayi sa,a,a,rayuwana wallahi.
Insha Allahu zanci gaba da kullan maka da kaina a duk inda nake .
Nace ni wallahi zancen kama har yasa na manta ban tabayeka lafiyan anty na ba da yara.
Yace duk suna nan lafiya yanzu tare muke da uwargida ta dan shiga shago tayi sayayyane.
A rude nace wai har na zaci ai a gaban ta kake waya dani haka wallahi.
Yace aiko a gaban ta sai nayi don ba ta damuwa tama fini matsuwa kizo gidan ai yanzu.
Na saki wata yar siririyar dariya nace kai ka taba ganin kishi har tafi ango damun akawo mata kishiya a duniya.
Yace baki san halin ta bane shiyasa amma ni nasan zanji dadin zaman ku a tare sosai wallahi.
Nace ni dai ka rufa min asiri kada dayar matarka tani tace zamu hade mata kai don muna shiya daya da ita.
Yace ai itama tasan cewa Haulatu na waya dake tai fada harta gaji tunda babu yadda zatayi.
Nace ni nasan dama idan ta sani sai anyi rikici don bata da dama,wallahi gurin kishi.
Maryam tace kai kai wanan matar dai tun ba,a shiga ba na hango ita ce matsalar ku ke da Kabir .
Dariya na kama tare da kashe ina cewa kai anty maryam watau kina jin hiran mu ashe?
Tace duk abinda kuke fadi inajin ku ai in ya damu ba sai yazo ya zauna ba yai ta kore maki kudan da baison yasauka a kanki.
Ya suke da hiran mu yakai geji yakawo iya wuya sai yaga fita dakin yafi mashi jin takaici kawai.
Ya mike yanace maji zan fita sai na dawo tace mai a dawo lafiya tare da ci gaba da kallon ta.
Yana fita Amira tace ke Bintu watarana sai yaya ya make bakin nan naki akan wanan wayan da baiso.
Mutum da mijin shi zai make ta idan yaji takaici yaje ya samo tashi matar mana shima inji maji takeba Amirah amsa.

Bai dauki lokaci ba sosai yakoma tafiyan shi don yanzu bai zama a gida shi sosai ga,wasan kwallo ga kuma business din daya fara gadan gadan na sayar da motoci da mashin mashin,
Haka yasa baida lokacin zama a gari yana fita business din shi da neman kudin shi.
Cikin dan lokaci guda sai ga sunan sadauki ya daga sosai a gari.
Abinda su mama suke gudun dai ya faru Allah ya nufi sai ya faru din don suna gani kuma suna jin yadda Allah yai ikon shi akan abinda suka so kada ya faru da dan kishiyan su.
Mama Asiya ce suna zaune suna hira take cewa, wallahi yaya wanan yoron shigen yaro ne kidiba fa,ba yan mu ba yanzu ko uban shi ya tsushe nisa ba kusa ba .
Umma tace ni wallahi ba inda na fara sanin haka zai iya faruwa damu sai wani rana da natafi dasu gurin buki.
Wata mata irin matan nan masu ido a bude take ce wa daganin na shigo da yaran gidan lokacin suna kananan su.
Matar tace wai wai wai wake da wanan hamshakin yaron haka?
Wai akwai magana nan gaba a gurin nan yaro karami haka da,wanan baiwa irin haka.
Don Allah ku daina fita dashi don gudin idon makiya don wallahi wanan da kuke gani ba karamin mutum bane gurin nan aje.
Umma tace na dauka fa da yaron nan take (Imirana) sai naga ta kama hannun Sadauki kawai tana wani zuba mashi kirari har da dukawan ta.
Tace a lokacin na dauka ko shirmay su ne na yan bori ko neman kudi sai kuma nakarajin shi a gurin maigadin ma,aikatan mu ranan shi ma ya kawo min sako gida sai ga sadauki yafito naga yana kada kai yana fadi cabdi babban mutum Allah ya raya muna kai watarana,akwai magana gidan nan.
Wallahi Asiya tun ranan nasan in bamuyi hankali ba diyan mu na zama shara a gidan nan muna ji muna gani.
Hmmm ashe bani kadai nasan da haka ba tace ni wallahi a gurin baffa malami na fara jin haka.
Ranan da,suka rakani na gayar dashi duk cikin su ba,wanda ya cewa yazo inda yake zaune saman buzun shi wai sai sadauki.
Naji yana cewa manyan gobe Allah ya taya riko Asiya ki rike yaron nan don watarana shine gatan ku ke da yaran nan.
Wallahi baki yadda wani mashe ya sokeni ba sai da na dawo gida abin ya tsaya min arai sosai wallahi.
Nasan baffa kamar mai rafanne yake da,wuya yai magana ya zama karya wallahi.
Kinga wanan makiran nasan itama tasan komai shiyasa take wani wayayya,tana nuna ita tana kaunan shi fiye da kowa.
Shekaran jiya Adamu ke ce min wai motar da yasayo yana shiga yanzu takai miliyan goma.
Ke don Allah dai ki bari tace wallahi yace haka yaji ana fadi a gari wai ba kowa kedashi ba yanzu a kasar nan.
Hmmm lalai Hawau takai makiran mace amma baki ganin wani alaman facakan kudi atare da ita kuma kin dai san yana bata dai.
,A,a ba gashi yaron nan yana fada min ba,wai shi yayowa uban odan kayan da aka,shigo masu dashi wanan wata yace kuma kayan sun samu shiga sosai.
Ai harda noman da Alhaji keyi yanzu shine mai bada kudi anayi don dai ranan naji suna,waya dashi.
Dan banzan yaro maikama da dutsen tsakar ruwa , Asiya karkare mata da cewa, wai bai san tudu ana rana ba.
Yanzu don Allah wazaice dan banza zai iya irin wanan dabara duk kwaya ta halaka shege kullun gashi a bushe kaman kayan rani.
Sai suka sa dariyan keta har suna tafawa tace aiko yanzu in sun san wata ai basu san wata ba ko?
Da yammaci, ranan laraba sadauki ya shirya yafita zuwa masana,antar shi don yaga halin da,su Bashar ke ciki da sana,an tasu.
Ranan shirin musulunci yayi wanda da,wuya kagan shi saye da tufafi irin na,al,adan hausawa.
Shadda ce gezenah mai ruwan kasa,sai maiko takeyi, sai dai dinkin gajeren hannu ce,anyi ma,rigar aiki a gaba mai kyau da daukan ido.
Sai yar hular da ya dora akan shi mai tsada kalar kayan jikin shi,takalman shi bakake sai shining sukeyi sunci polish.
Ga kanshi na tashi kamar duk kwalban ya juye a jikin shi a lokaci guda.
Gurin maji yafara shigo ya sanar da ita zai fita don har yanzu kudi bai hana shi yiwa iyayyen shi biyayya ba.
Kuma baisa yace don yayi gina yabar gidan mahaifan shi ba yanan ciki tare dasu saidai ya gyara gurin shi sosai harda na yan uwan shi.
Ina zaune antu maryam tana min kitso sai faman masifa take min ita gashina yai yawa wahala kawai nake bata.
Azaune nake ba dama na gudu daga falon gashi fuskana yana facing din inda yake tsaye yana dauko wayan shi dake ruri daga Aljihun shi.
Yace hello Bashar yaya akayine ?
Yanzu nake son fitowa tun dazu ina daki ina barci kasan wasan last week yabamu jiki sosai.
Saidai duk da waya yake idonbshi yana kan kitson da Maryam take min kur dashi gashi dole muna facing din juna dashi.
Yana kashe wayan ya mayar da shi cikin aljihun shi inda ya ciro ta da farko.
Yace maji fa?
Yanzun ta shiga ciki nasan zatafito tunda taji muryan ka ai inji maryam din.
Maryam tace yaya wanan wayan taka tayi wallahi ni dai taban sha,awa Bintu gashi kaman wanda mukaga Kabir dinki dashi ranan.
Da sauri yace ke maryam ban son iskanci wallahi ki daina hadani da wanan tsohon mai zarin tsiya.
Na muguda baki cikin tsiwa nace nikan banga tsoho ba wallahi.
Ban san ko tako nawa yayi ba,sai gashi gabana ya danko gashin kaina da karfi sai da na,sake wani irin kara,da sauri mama tafito tana fani kai kai yayane kuma wai ?
May haka dan Allah kasheta zakayine ko may ?
Wallahi maji yarinyar nan ta raina ni wallahi kan wani tsohon mijin ta can take son ta zage ni, ta zage ka tace maka may?
Maryam sai dariyan keta takw min idanuwana,sun kawo kwalla ko don har cikin raina naji dankan da,yai min.
Kadai zama babban kwabo wallahi ka ishi yarinya da sherin mijin ta tsoho ne basai ka,samo mata saurayi ba kowa ya huta.
Allah dai ya,sauwa wake son wanan bakauyan haka ko dressing ba ta iya ba balle gyara irin na mata.
Kyalkyalkyal maryam ke min dariya Amira da,tafito daga kitchen don jin karana take cewa, a,a yayana aiko wallahi yanzu ba may cewa Bintu bata iya dressing ba gaskiya.
Kallonta yayi yaja tsoki ya juta gurin maji yana fadin maji zan dan shiga gurin su bashar na,dawo yanzu.
Sai ka dawo tace mashi tare da samun guri ta zauna tana man fada na daina shiga harkan shi kada ya halakani ga banza.
Nace cikin dan kuka ina,share hawaye da bayan hannu na mama,wallahi duk anty maryam ce taja min.
Ban san may yakaita danganta,wayan shi dana Kabir ba,shine yake cewa wai za,a hada shi da tsoho kazami.
Dariya abin yaba mama tace ni dai na rasa wanan kiyayyan na sadauki da Kabir wallahi Allahbya sauwaka.
Amira tace jinin su ne bai hadu ba yace min wallahi haushin shi yake ji.
Wai babba dashi yazo zaiwa yarinya wayo itako sai shegen son maza duk ta mutu akan tsoho.
Dariya suka sa nace tunda yana jin haushin shi ba,sai ya kashe shiba in ya isa.
Har lokacin ina jin zafin dankan da yai min don har kaina naji yana sarawa wani iri.
Tafe yake cikin motan shi sai dai a hankali yake tukawa don akwai motoci da yawa saman titin a lokacin.
Wani iri yaji kamar ina cikin motan na,sake wanan razananen kara da na sake lokacin da yaja min kai.
Yace natural hair ne haka gare ta ashe nibna,dauka ko kari take ko yaushe ai.
Wawiya can zata karata dashi gurin dan tsohon ta babu ma gyara kila a karshe.
Yana faka motan daga inda ya tsaya yafito yasa remote ya kulle motar nan ya taka a hankali zuwa gurin da office din Bashar yake don yasan yana nan yaga motar shi a fake can ne sa.
Bashar na zaune yana cika wasu takardu sadauki ya shigo office din .
Bashar ya dago yana cewa kadai samu fitowa ke nan yanzu din na dauka sai ka tsaya ka cinyewa tsohuwa dan tallenta ka fito ai.
Murmushi yayi yana kaiwa zaune yace don wa ake dafa tallen dama ba don mu ba.
Gaskiya ya kamata ace kayi aure haka wallahi man, don Maji ta huta da katon gwauro haka kullun yana lashe mata talle.
Sadauki yai murmushi tare da daukan wani takardan dake gaban shi yace aiko nai aure tallen maji ba zai huta dani ba.
Kana ma min zancen aure ga babban tazurai basuyi ba balle ni.
Da sauri cikin daga kai Bashar yace wa wai Imiranah kake nufi da Ahmad?
Yace su mana kai dan Allah rabu da wanan shashan yayan namu .
Cikin dare fuska sadauki yace ban son iskanci ba yayan nawa ne kuma sha sha.
Ce wallahi shi duk gari yanzu kowa yasan shi sai aukin bin yan yara masu tallah yana latsawa a kasuwa.
Kaifa dan iskane wallahi wanan kuma ai sheri ne nasan dai yana da shegen son mata amma ban san da wanan ba kan.
Yace aiku na gida baku sani kwanaki ma naji ana kudundumin yaiwa wata yarinya mai kai shikafa layin su ciki ko yaya case din ya kare.
Bashar yau dai da sheri ka tare ni ke nan dai don nazo gurin ka dana sani na zauna gida abina ko natafi stadium.
Wallahi ba sheri bane don ina ga Baba ma yasan da wanan case din ai .
Zai iya don kwanaki a gabana wallahi Fatima ta mare shi babu ko kunya wallahi.
Naso na lalatsata ai amma sai naga tana da gaskiya din taba tayi kasan bata da kunya itako ta kwashe shi da mari kayau.
Wata Fatima ke nan kuma?
Ya dan bata fuska yace wanan dayan sister tawa dake gurin maji mana da zama.
Au kace min pretty mana gaskiya mutumina yar8nyar nan ta hadu sosai wallahi ni dai tana min.
Dariya sadauki yayi mai kama da yake yace aiko dan tsohonta zaici ubanka wallahi.
Waye dan tsoho kuma babanta yace wanda zata aura dai wani guy ne mai mata biyu wai itace ta uku .
Zokaga shegiya yadda take rawan kai nace kici uban ki indai kince rawan kaine.
Kai kai amma gaskiya an kwabsa wallahi gurin nan .
Wai ma kai kana may har ka bari haka ya kasance ga ka har kabari akaba wani kuma can.
Wani kallon rainin hankali ya watso mashi gani sai ayi may kuma ?
Yace yar gida gida mai tuwona maina kawai musha buki mukan .
Kasan fa yarinyar wallahi matar manya ce sai ta samu gurima zakaga yadda zata baje sosai wallahi.
Kai don Allah ni bashi yakawoni ba wai how far ne akan kayan can da suka shigo.
Bashar yace baka son zancen ke nan dai mubarta anan kawai ko?
Yace zancen may kuma may zanyi da wanan mai zubin yan arab da ita.
Bashar yai wani dariyan keta yace kaidai sai naba Maji shawara tafara maka hayaki da rukiya wallahi.
Ya jawo wasu takardu daga drawer shi yana mikawa Sadauki yace duba nan ka gani kafin mu koma topic din mu don gaskiya ni iam serious wallahi.
Ko tayi miji ai ana iya tayar da zance don gida bai koshiba ba a kaiwa dawa.
Karanta takardan yake bai bashi amsa ba sai can ya dago kai yace ikon Allah so quick haka sun samu shiga da,wuri.
Yace yanzu haka ma munyi magana da SMG yace min kila zasu sa mukawo masu sabon sanfarin su din suna son su rabawa sarakuna shi.
Amma ko gaskiya in haka ya kasance da muyi sa,a sosai wallahi ko.
Nan dai suka kara dan tattaunawa akan business din su inda suka fito don dama suna da alkawrin zuwa wani guri da Bashar ya damu sadauki su tafi.
A hanya sadauki ya nisa yace amma gaskiya banji dadin labarin da ka bani ba na Imirana .
Yace kai kana ga zancen ne har yanzu yace ai wallahi duk ya zubar da mutuncin shi saikace ba Alhajin ku ya haisu ba.
Shifa Ahmad cewa akayi yana sanan kayan sata sai asato mota ko mashin ya saya .
Innalillahi da karfi sadauki ya furta tare da waigo inda Bashar yake zaune a gefen shi yace wallahi man .
Wai kai kana nufin duk wanan zancen baka san dasu bane ko yaya?
Yace ina zan sani tunda ba shiga gati nake ba yawo iyakata idan ina gari ina gida ko nan gurin ka,sai ko can site din da nake gina na kawai.
Lalai na yarda baka gari gama,wanan sister din naku kwanaki saida yan hizba suka kamasu wai ance sun hada party suna abin banzan ga da mata keyi tsakanin su.
Da karfi ya taka burki yace Nafisa ko?
Yace ita wallahi naji kunyan wanan abin sosai wallahi ance ai shaye shaye takeyi sosai yanzu kowa yasani ma agari.
Subbahanallahi ya,furta yace how comes abubuwa suke zo muna haka agidan mu kaman mu kadaine a gari.
Kadai Allah ya,sauwaka kawai amma ai abin ba dadi wallahi.
Can suk shiga kasan gari gurin ginan shi irin na mutanen dana daganin gurin mutum zai gane cewa tsohon gari ne gurin.
Da,kwatancen da Bashar ke mashi suka isa gidan da suke son zuwa,
Daganin gidan basai anfadawa mutum ba gidan wani masani ne na alkur,ani maigirma don ga alluna nan na almajirai daga waje birjit dasu.
Nan suka,tura ai masu iso da,maigidan sai ga,yaron ya,dawo yace ance su shigo daga cikin zauren gidan.
Wani tsohone ya tsufa sosai yana zaune saman shimfida irin ta mutanen da can baya masu fada aji.
Bayan sun gaisa da tsohon ne Bashar ke cewa malam ka gan mu sai yau muka samu zuwa ko yace tau harkokin ku na mutanen yanzu yawa gare shi.
Nan dai suka kara gaisawa Bashar yace malam kaman yadda na,fara maka bayani ne akan al,amarin wanan abokin nawa dai.
Yau gashi nazo dashi malamin yai shiru can ya dan mike zaune tare da kallon su da kyau yace.
Karbi wanan yana mai mika mashi tasbahan hannun shi dayake ja, yace ka zabi guda ko wanine ma daga ciki.
Ya dauki wanda ke kusa da farko sai, tsohon yai dan murmushi yace ai abin yazo da sauki tunda naga baka da zari.
Don da,wanine na tsaka zai dauka yana ganin yafi mai killla yawa.
Ya dinga karatu mus,mus mus dabaki can yace umm,umm Allahu akabar to Allah ya sauwaka.
Su dai suna zaune suna kallon shi can yanisa yace Alhamdullahi Bashar don al,amarin abikin ka ba acewa komai don yanzu ma kuka fara insha Allahu,
Sai dai gaskiya akwai dan matsa dana gani yanzu dai tunda bashi yakawo ku ba harkankuce ta sana,a takawo ku bati muyi abindake nan.
Nan dai yai masu wasu bayanai yakuma basu yan abubuwa tun ana gaban shi yace su sha.
Sadauki da cukin kyankyami yake ya matsu subar gurin don shi bai son irin harkokin nan gaba daya a rayuwan shi.
Bashar ne ma ya matsa mashi kan lalai sai suzo don yanzu duniya ba,a shigan ta haka kai tsaye don A LOKACI MU KE.
Sukai mai godiya tare da mikewa zasu fita bayan sun bashi, dan abincin goro don yace bai karban komai nasu don abokin kakan Bashar din ne sosai.
Sadauki dake gaba ya dafa zauren na kasa zai fita sai tsohon yace ji mana idan kaje gida kacewa mahaifiyar ka kada ta manta da zancen baya da tai alkawari kai ka gurin da aka bukaci ta kai ka a baya.
Don idan bata maida hankali ba hannun agogo kullun zai dinga koma mata bayane.
Da mamaki sadauki ya kalli tsohon sai dan tsohon yai murmushi cikin kada kan shi yace abinda nace zaka fada mata ni dai bata sanni ba ban san ta ba.
Yace cikin mamaki toshike nan malam zan fada mata insha Allahu kaman yadda kace na fada mata yace Allah bada sa,a suka ce amin suka fita daga zauren.
Duk zukatan su fam yake da tunanen

Please Login or Register in order to submit comment