Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ya katseta da cewa dakikazo gaban iyayyena kice masu may ?
Yace look Fatima da farko na so na karbi bukatanki gare ni amma yanzu hakan da kikai min duk kin jagula komai don haka idont think zan iyaci gaba da zama dake kuma again.
Ran Fatuma ya,sosu da jin maganan da sadauki yai mata sai dai dole yasa ta daure don tana son guy din.
Da sauri ta juyo gare shi tana cewa cikin hada hannayen ta biyu guri guda tare da marairaicewa tace don Allah U F kada kayi fushi dani.
Yin fushin ka akaina zai iya jefani cikin mawuyacin hali a rayuwana sosai wallahi don na mutu da son ka sosai wallahi.
Yayi wani guntun tsuki tare da kawar da kan shi gareta yana cewa don may zaki biyo ni har garin mu don baki da hankali.
Tace kayi hakkuri wallahi duk na,rude ne da ka fada min zakayi aure na,rasa may zanyi akai shiyasa nabiyo ka har nan.
Sadauki ya kara jan tsuki ya kalleta a wullakance yace na fada maki cewa anyi min mata a gida kuma bazan canza maganan iyayyena ba insha Allahu akaina.
Yace kuma ki sani na kyaleki ne yanzu don garin mu kikazo don haka yasa na kyale ki idan badon haka ba da na dauki mataki a kanki sosai.
Don bazan yarda ki hadani fada da iyayyena akan ki jamin wullakanci a gidan mu.
Ya farka mota da karfi cikin five star hotel da suka shiga da alama ran shi yakai kololuwar baci a lokacin.
Nan Fatima ta kifa kai tafara kukan tana rokon shi akan yayi hakkuri ya,aure ta zata zauna da wata su zama matan shi su biyu.
Tace na gane wanan far yarinyar dana gani itace proposer taka don naga tafaye shegen kyau.
Yanzu akan wanan karamar yarinyar kake min haka may zaka,gane a gurin yarinya karama haka ne please cikin kuka take magana.
Yace look Fatima na fada maki tun farkon haduwan mu ni ba mazina ci bane kuma ban iya,neman mata ba ina under control din iyayyena .
So kike akan ki na saba dasu ne for god sake don haka ki sauka na sama,maku masauki da safe ku kama hanya ku tafi.
And kuma na roke ki tun magana bata kaimu ga bacin rai ba kada ki kara,shiga harkata is over hakana.
Nan ya bude mota da zuman tafito su shiga ya kama mata masauki sai ma kunya da yake ji kada wasu su gan shi da mace azaci yazo yin wani masha,ane.
Cikin kuka tace no kabarshi zamu koma kaduna mu kwana gobe na koma Abuja.
Yace is better for you.
Nan tafito tashiga motan ta driver yajata tana kuka suka kama hanyan kaduna da yamma lis sosai.
Ya sauke numfashi duk da yaji tausayin ta yasan wanan shine kawai hanyan da zaibi yasamu kan shi daga shu,umancin ta akan shi.

A gida kuwa maji takai kololuwa da bacin rai sai jiran shi take ya dawo da yadawo yara yaba sokon maganin mama da kuma kaji da drinks da yasayo masu sanyi.
Yace ace yana massalaci zaiyi sallah mamatace koma may zaiyi ai zai shigo ya samay ni gidan nan.
Bai shigo ba sai da suka sallamay isha,i yashigo cikin gida kannen shi na gaida shi amma bai iya amsawa ba idon shi yana kan mahaifiyar su don jira yaji may tace mai yakeyi.
Ya zauna Amira tana fadin yayana kadawo ya bakuwar ta mu take, nan ma shiru yai mata baice mata uffan ba sai take cewa, a can ka barta ne ?.
Don Allah Amirah ki barni na huta haka na wanan tambayan ya isheni wallahi haba gaki kamar yar jarida.
Zama yayi ba,wanda yace kallah a cikin su sai zuwa can Maji ke fadi a da can baya idan ance min kana hurda da mata bazan taba yarda ba koma waye ya fada min.
Amma yanzu da yake ka fara rike kudin kanka gaskiya nai mamakin ganin wanan irin yarinyar ace wai da,su kake harka.
Allah yaceceni in ba kuma wani sabon rayuwan ne ka bulle min dashi ba aji dadin yin min sabon zagi a gidan nan.
Maryam na gaba ina bayan ta muka fito daga cikin daki mun samu mama tana mashi fada sosai kan wanan sabon halin da tagani a gare shi.
Maryam tai tsagal tana cewa ni dai kwata kwata,batai min ba mace haka yar bariki gata nan da ita sai wani iskanci take wai wayewa ke nan.
Maryam ba ga ku nan da irinta ba a gida ina yanzu Nafisa haka take shiga sai kaya ya matse ta sosai duk suran jikin ta a waje.
Amirah ke fadin haka wa maryam tace idan zagine kuma ai akwai shi a gidan ku.
Maji dai fada sosai take mashi akan mutum yayi hankali da duniya kafin ta kure mashi don duniya,ba matabbaci bace.
Baiyi magana ba sai chartting da yake da,wayar shi a zaton mu da bakuwar shi yake fira kafin ya fita zuwa gurin ta.
Amma har dare muna dakin zaune tare dashi sai hira yake da wayar shi kawai da amsa call.
Maji tace daka bar yar mutane acan may zataci sai a lokacin yai magana yace sun tafi maji.
Tace acikin daren nan suka tafi haka basu gudun dare yai masu a hanya.
Bai ce uffan ba yana zaune har dare goma da wani abu yamike yana fadin zai tafi ya kwanta sukai mai sai da safe kaina na duke ina karatu tun zaman shi ban yi magana ba a falon.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,,

A LOKACIN MU KE,,,,

Sun shirya tafiya zuwa lagos gurin Michael don haka Nafisa itama ta nace akan cewa dole sai tabisu.
Tare sukai tafiyan inda ya turo masu da kudin suka shiga jirgi sai lagos a gida kuma tace zata gidan wata kaunan mamanta ne ta,kwana biyu.
Ranan da takwana uku da tafiya Umma ta kira waya tana tambayanta cewa yaushe zata dawo ne don tace ga jiya zata dawo bata dawo ba kada Alhaji yasan bata gida fa.
Tace sai gobe nan uwar tai mata fada kan dole ta dawo ranan don gujin bacin ran su gaba daya.
Amma har dare Nafisa bata dawo ba haka yasa Umma ta tayar da wani wanta guda yabi bayanta gidan yar uwarta ya dauko ta.
Yaje gidan yar uwar maman nasu tace ai Nafisa batazo ba ma gidan ta kwata kwata.
Nan hankalin Umma ya tashi sosai gashi kuma ko sun kira wayan Nafisa basu samu a lokacin.
Tun tana boye damuwarta har uwar kwakwaf mama Asiya ta fara ganewa yan dakin na cikin wani tashin hankali amma da ta tambaya sanin hali sai Umma take cewa, bakomai bane dama.
Kwanan ta biyar suka dawo sokoto haja haja cikin kudi, nan uwar tasata daki da tambaya ido ya riga ya bude tace buki suka tafi na wata classmate din su gusau ta san ko tambaya Umma bazata bari ba shiyasa tai karya.
Imirana ranan kamar ya make ta yai mata fada sosai sai dai basu sani shiga yake yana fita inda ya shiga.
Don Nafisa tayi nisa ko batajin kira yanzu don kar take kallon su tasan abinda basu sani bako.
Nan uwar taga yadda take facali da kudi take tambayanta sai cewa tayi wani Alhaji ne dan canji ta hadu dashi a gusau shine yabata kyautan dollars kuma yace ma zai zo gida yaga iyayyenta.
Umma ta fara jin dadi har ta fara sake magana ita yanzu arzikin bana yaci uban na da don yarta tayo babban kamu sosai .
Wasu ko sai dai su zauna idan dan su ya tafi yayo fashi ya kawo masu kowa a gidan yasan Nafisa ta samu dan canji don sai facaka suke da kudi abinsu.
Uwar bata san cewa yarta ta wuce sanin ta ba yanzu da ita da iyamurai take hurda su ko suna son yaran hausawa don sunce sunfi iya making, love.
Idan kuma ta fita su da su Raiha sufita susha kayan mayen su suyi tatil dasu ta dawo taita barci.
Ranan Amira zata shigo taga su Raiha sun dawo da ita yanayin data gan su a ciki sai bai mata dadi ba tashigo maji na ciki take fada muna nace Anty kiyi shiru kada wani yajiki ace kina hassada da samunta tace wallahi hakane amma may zanwa hassada a wanan gurin haka.
Yanzu har takai sun fara neman junan su idan sun sha ko kafin su sha sai sunyi masha ansu a tsakanin su sannan su koma,suyi tatil dasu.
Idan abinta yai nisa ita Nafisa har kwalba take dagawa don zuwa lagos din da,sukayi saurayinta Johnson mashayi ne sosai a can takoya shan giya.
Gashi sai dare ya tsala zata dawo ba,wanda ya sani sai mahaifiyarta ce zasu bude mata gida ta shigo.
Amma har lokacin Umma hankalinta baikai ga cewa yarta ta samo sabon rayuwa ba ita gani take gajiyace dai take dawowa dashi.
Don Umma na da,wani hali indan ta,dawo aiki ta zube guri guda bata motsa jikin ta, dan damadama,idan ita ke da duty a gidan ranan zata danyi kiza kiza.
Hjy kubura ta fara jin zance Nafisa a gurin wata kawar aikinta, amma sai bayata yarda da zancen ba ta dauki maganan ba gaskiya ba tunda kawar tace har gari suke bari zuwa wani guri yawon banza kuma ita tana ganin Nafisa a gida.
Kuma abokanta su Raiha sun riga sun gagari iyayyen su babu maijin kwabo su, suji yanzu.
Ganin bata san labarin ba yasa kawarta cewa kai kila dai ba gaskiya bane kama daine suka gani suka ce itace.
Sai dai Umma ance laifi tudu ne, take naka ka hango na wani,
Zance ta shine sadauki yana can kasan waje ya zama tattacen dan iska, yana hurda da,turawa yana sayar da kwaya da fashi.
Inda Allah zai kashe mata bakinta ranan sai ga danta ya shigo da sauri yana cewa su Maji dasu mama Asiya ku kuna,tv tashan sport yau su sadauki zasuyi wasa.
Nan kuwa suka shiga kunnawa suka kai tashan wasan kwallo har falon Baban su, sai da ya kunna suna zaune aka fara fitar da yan wasa sai gashi saye da kayan wasan shi sun fito, yana saye da rigan shi an rubuta mai Umar sokoto, Nomba 9,,,
Haba take yaran gidan gaba daya suka dauki ihu suna,wallahi ga yaya sadauki ga yaya sadauki.
Nan aka fara wasa ranan duk gari ya dauki ihu sosai don ganin dangida kuma haifafen dan gari yaje fitar masu da sunan su.
Ba atashi wasan ba,saida yai masu ci biyu dada fa ihu ba kama hannun yaro wani haushi yakama Umma tace kai ku kashe min wanan shegen abin sai kace wani abin kwarai wai kwallo kafa kukewa wanan ihun haka.
Tasa aka kasshe mata TV ta baba daga dakin shi ya aiko mata su kunna Tv su ga Umar nan ana hira dashi a TV.
Rananta baiso ba amma dolen ta, ta kunnawa daidai Sadauki yana fadi cikin turanci da ba,wanda yasan cewa ya iya ta haka slays English irin na turawa yana fadin.
Yana mika gaisuwan shi da godiyan shi ga mutanen kasar shi Nigeria dakuma iyayyen shi da,sukai mai tsaye yakai ga wanan matsayin.
Haba gida ya kara daukan ihu da murna sai bugo waya mutane keyi suna cewa ku, kunna TV su gan dansu ana hira dashi a NTA sports.
Dakin Maji kan ranan ba a cewa komai don farin ciki da murna maji saida tai kwallan hamdala ga Allah.
Yayi kyau yai fari sosai hasken shi ya fito da kyau kana ganin shi kasan dadi da ni,ima ya sauka mashi.
Kwana da kwanaki bakajin komai sai zance UF kawai ke tashi a gari nan sauran yaran gidan su, suka,shiga barazana da daukan kai a gari.
Baba ya kecewa su mama bayan ya tarasu yace yana son yaran nan suyi aure hakana don haka ai zancen zuwa gidan yan matan su ai magana.
Hjy kubura tace har da dana ke nan Baba yace aishi ma yakamata yai aure shida ke fita waje ya dade kinga sai ya dauki abinshi su tafi can su karata can.
Yace zaiga kanin shi Sani suyi magana kan Rahama don asan abinyi nan dai duk aka aje magana za,a aika gidajen matan su.
Sai dai may Baba yana zuwa gurin dan uwan shi kan zancen auren sadauki da yar shi da kowa ya dade dasani sai cewa kanin nashi yayi gaskiya shi sai sunyi shawara da matar,shi da yarsu tukun.
Baba yace ikon Allah sani akan auren yaran da,suke duk abu daya shine zakace sai kayi shawara da mace tukun kabani amsa.
Yace eh don akwai dan mahawara tun kwanaki akan zancen saboda haka abari ya kara tuntubar uwar yarinyar yaji.
Haka Baba ya bar gidan jiki ba karfi don yana da ,wuya ba,a samu matsala ba ke nan amma dai sai yabar zancen a ranshi.
Ita ko hajiya saude da mijinta yazo kan zance sai cewa tayi ita gaskiya bada ita bata daukan yar ta, taba mashayi yarinyar da kurciyar ta taje can takama hadiyan bakincikin da namiji ga banza.
Yaje can ya samu wata irin shi yar shaye shaye su daidaita tsakani su, amma bata ganin maciji da rana ta tura hannunta ramin shi da dare.
Yar ta tazo ta haifi yara lalattatu a rasa yadda za,ayi dasu yace amma dai kin san wanan magana zai iya kawo matsala tsakanina da dan uwana .
Tace zumuncin shi yadade bai baci ba ai akwai diyan dangi da yawa yaje mana ya nemay su can ba yarta ce kawai yar dangi ba ai.
Sai yaja bakin shi yai shiru don bai iya tunkaran dan uwan shi da wanan zancen gaskiya.
Shi mai daurawa sadauki aurene yau kuma ace shi da kanshi ya hana yarshi sai yaya ke nan
Maji ko da,sukai waya da saudaki tasa shi gaba kan lalai sai ya hado lefe daga can bai so ba amma don bin umurni ta ya hado kayan shi tundaga kasar Spain da sukaje wasan.
Sai murna take cewa dan ta ya kusa zama kamilin mutum tunda zai aje iyali,
Duk da dai ba son hada zuria takeyi da yar hjy Saudae ba don kansu guda da umma kuma yaran basu da kunys ko kadan.

Bayan kaman Sati uku ya shigo gari nan matasa su kai dandazo gurin zuwa taron shi da,dawowa zakace wani gwauna ne zai zo.
Mukan muna school bamusan wainan da ake toya ba a gidan don bamu san zai dawo ba a ranan.
Sai after six lis muka dawo duk a gajiye muke a lokacin, nice gaba maryam tana baya ta tsaya ba mai Napep kudin shi.
Tun a kofan shiga falon mu na fahinci akwai namiji a ciki don takalman maza danagani daga waje.
Ban kawo shi bane tunda nasan baya kasan a lokacin da yar sallamana na shigo falon.
Ina saye da,buje da rigan les da,akai min feeted dinkin ya karbi jikina pink color da,farin zare akai mai yan flowers kanani ajikin shi har bakin lace din banyi kitso ba don ciwo da kaina keyi sai dai na,wanke na daure da ribon kawai.
Na shigo ina fadin wai mamana yau kan duk nagaji, wallah,,,,
Ganin sa kawai nayi zaune ya kara haske yai kyau dashi yana saye cikin wasu kayan maza ko ba,a fadi ba kan san sukai kudin su ga wani irin uban kamshi daya hade muna falo tun daga waje zai tare ka.
Haka kawai ganin shi yasa na makale magana ta sai gabana da naji ya fadi yaushe rabon dana dan matsala a gidan mu kusan wata shidda da yan kai ke nan,
Tun tafiyan shi don ko suna vedio call dasu Amirah bani zuwa kusa ni balle nagan shi.
A hankali nakai zaune saman masangalin kujeran dake daga kofan falon ina fadin sannu da dawowa yaya.
Cikin dan basarwa ya amsa min yace kuna lafiya,
A taikace na bashi amsa da kalau na mike zan shiga sai ga Maryam tana ganin shi tasaka wani irin uban ihu tai kanshi.
Yace ke ke kinfa girma yanzu kinga yadda kuka koma,wasu big ladies da ku kuwa,?
Ta wani shake murya tace kai yaya yanzune ma fa zan cika twity cif fa.
Itako Bintu she is just 18 da yan kai yanzu kaga mu yarane har yanzu don dai ka dade baka ganmu bane kawai.
Yace baki ganin tana ganin ta girma yanzu harda bani amsa any how.
Ni kaina na san amsar dana bashi bata dace ba amma yadda ya hade fuska shi ya dace dashi ai,
Maryam tace kasan aure zatayi shiyasa ta fara daga kai.
Yace aure kuma tare da kallon maji yace badai da wanan tsohon ba dana taba gani.
Kai yaya Kabir ne tsoho wallahi dai ba tsoho bane don dai tana da mata ne kawai
Yace da karfi cikin tabaya da what?
Mata bako guda ba fa ke nan maryam tace ai Bintu babbace itace ta uku a gidan.
Yace fir god sake Maji may zaku aurar wanan wajen don Allah kuma wai mai mata har biyu ita ta ukun su,
Nace tau bisimillahi matsala ya sauka na,shige abina ciki kan shi kawai ya girgiza yace ok lalai ma yarinya ta girma kan.
Har nashiga nai sallah kada lokaci ya karasa shigewa suna falo sai zuba suke shi dai bakajin bakin shi.
Nafito dauke da abinci a dan plate na koma can nesa dasu na zauna na fara ci a hankali.
Kamar kullun fuskan shi a daure yake ba dariya amma kuma wanan yaudararen dariyan tashi da baikai cikiba yana nan shi amsa da yake ba kannen shi kawai.
Inacin abinci na jin sunana da maryam ta kira yadani dago kai shima idanu ya,watso wanda tun ina yarinya nasan da wanan kallon wanda nake dauka kallon tsana.
Tace wai Bintu don Allah ba har part mukace zamuyi mashi ba amma maji ta hana mu.
Nace kunfi kusa anty maryam ba magana na bane wanan na mike zuwa cikin kitchen din dake attache da falon mu na aje plate na shige don lokacin magariba yayi shima naji muryan shi yana ce masu zai fita yai sallah ya dawo.
Bayan na idar na samu mama a falo nace mama dama antanadarwa yaya da abinci ne tace waya fadawa zai dawo yau.
Barshi kawai kinji tunda yazo nai mashi magana yace min wai yaci a government house can yafara sauka wai.
Nace ,a,a ashe abin nayi ne ke nan abu har gidan gwauna kuma tace bari kedai mutane sun dauki kwallo yanzu kamar wani bauta can.
Amira tace ku may kuka gani mudake gida mu mukasha kallo yau kinga yadda aka rako yayan mu kuwa a gidan nan.
Motoci mashin mashin kala kala mungan su yau wai duk yaya aka rako gidan nan.
Nan dai mukasha hira har muka lakace dare yayi bamu sani ba shikuma ba dawo gidan ba har lokacin.
Halinshine idan ya,dawo bai zuwa da,tsara ba sai bayan kwana biyu su iso garin.
Wanan karon ma hakanw ta faru don sai bayan kwana uku da,dawowan shi kayan shi suka iso.
A gaskiya mun sha,tsaraba sosai don bai nuna,min yan ubanci ba a nawa ganin Amma mama sai naji mama na mashi fada wai bata son haka don may kayan su Amirah yafi nawa kyau.
Amira tace Maji haba duk abinda yaya,yaiwa Bintu sai kice ya,nuna mata banbanci mana.
Maji tace ban son hakanane nafu idan zai saya maku abu ya saya maku iri daya koda kala zai banbanta.
Shi dai shiru yayi kawai baice komai ba yasan al,amarin maji da,wanan yarinyar sai Allah kawai.
Wai ma ko yaya akayi har maji tagane hakan da sauri amma ita,wawiyar sai wasan baki take tana godiya.
Gaba daya gidan an sheda sadauki ya dawo don har kudi sai da yabawa mutanen gidan.
Sai cikin dare ya shigo yace wa Amira ta kira mu tazo mu kwaso kaya a motan shi.
Tirka sa don set din akwatina ne har uku mukai ta,kwaso bamu iya daukan manyan dole shi ya kwaso sai da,muka huta muka shiga duba kayan.
Ni har tsoro kayan suka,bani abu sai kace diba akaitayi ba kudi akasa aka saya ba don yawan su.
Mun gama Amira ta nisa tace wai yaya munga kaya har bamu iya dubawa don yawan su.
Murmushi na kullun yayi yace sunyi maku ke nan dai ko da,sauri mukace sosai ma yace yana mikewa maji idan akwai abinda babu aciki sai a,saya anan.
Ban san lokacin da nace kai haba sai kace riya wanan kaya haka aiko gidan sarki za,a kai sai haka.
Maryam tace, ke Bintu akwai abin dariya wallahi baki taba ganin lefe bane haka nace nikan sai yau gaskiya Allah dai yasawa aure albarka sukace amin gaba daya dakin
Muka kwasa sai cikin dakin muka mayar dasu can kuryan maji muka,kawo zannuwa muka rufe ba,wanda yasan anyi a gidan balle afara yadawa.
Shafa,i da,wuturi nayi nice farkon zuwa na kwanta zuciyata sai tunanen wanan irin kayan da yaya hado na laife nace a fili Allah ya kara shirya wa maji dan ta.
Na sauke wani ir8n ajiyan zuciya tare da cewa Allah gamu gare ka mai kudi yaji dadin shi gaskiya.
Wankan da nayi kafin nai sallah yasani jindadin kwanciya sai barci sai dai kuma zuwa dare ban san may ya,farkar dani ba.
Amma sai naji dirin mota an dawo da daren nan nace a,raina Allah dai yasa ba yaya bane a cikin daren nan.
Sai kawai na tsunci kaina da tashi na leka shi din ne yana rataye da corth din shi kawai sai na zarge shi.
Da sauri nai istigifar don zato zubi ne koda ya zama gaskiya da sauri na koma makwanci na.
Sai dai barci ya buwaye ni don haka na mike na fara gabatar da nafila har tsawon wani lokaci na koma na kwanta.
Sai barci da,safe ban shiga school ko maryam yau bazata dadeba can da,wuri zata dawo.
Sai na,dan kara,kwantawa sai zuwa goma nafito don na kama,ma Anty Amira aiki don zata fita yau.
Ina fitowa mukayi kicibis dashi kallo daya nai mashi na gane yasha daren jiya.
Ban kula shi ba don wani irin tsanan shi naji a,raina ya kare zuben min a idona ko lokacin mama tana ciki tana shiryawa haka ma Amira tana kitchen tana aiki.
Ke dauko min abin karyawana yace cikin wata murya na dan kalleshi nai saurin kara dauke idona.
Ya zauna yana wani lumshe idanuwan shi nasan abin bai sake shi ba har lokacin.
A hankali na,tako inda yake dauke da,kayan karyawan shi na duka saitin shi kamar zan aje kayan .
Cikin wata yar karamar murya nace mashi ka,saita kanka kafin mama ta,fahinci halinda kake ciki hankalinka ya tashi.
Don nasan kasha daren jiya kadai jin tsoron haduwan ka da Allah ka tausayawa mahaifiyar ka.
Na mike da,sauri na,barshi daidai ya mike yana gyara saita kan shi daidai don yai mamakin yadda duk yakamay amma wanan manyar yarinyar wai ta fahinci yasha jiya da dare.
Da kyat don mamaki

Please Login or Register in order to submit comment