Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

a taimaka mata.
Ya mike yana fafin kada ki manta please sai nagan ki ko ya ciro kudi ga aljihun shi yana mika mata yace ga kudin mota ko idan zakizo.
Sagir yace kada ka bata yaya wallahi wanan shegiyar maye zata sha dashi don dama shi take nema kaga ta lafa a gida tana neman na wanda zata ware dashi idan mai shi yai sakaci.
Yace ka barta dasu ai zata zo din kasan Nafisa akwai cika alkawari tace nagode babban yaya irinka muke so ko yaushe ba masu hana abamu ba.
Amira ce kawai a falon lokacin mama tana daga ciki na gaida ita tare da mata yaya kwana biyu.
Banza tayi dani kamar bata san ina gurin ba ma a lokacin sai wayan ta kawai take dakila a hankali a lokacin.
Nace anty har yanzu kina kallon film din queen of south ko kin daina ne don shirin yai nisa sosai.
Ke Bintu kikama kanki dani wallahi don idan kikai min tsiya yanzu na lahira zaifiki jin dadi wallahi ko.
Haba anty daga tambaya kuma shine laifi Allah ya baki hakkuri nacs mata sai ko ta dago da nufin kai min duka ji tayi daga kofa yace kada ki soma wallahi yanzu zan bata maki rai sosai wallahi.
Yar kice koko kaunan ki da duk lokacin da kikaga dama zaki dinga dukata son ranki.
Duka kuma dukan wa kuma wai ban fahinci may kuke magana ba akai wa ake duka ne wai ?
Bai fasa magana ba yace kin san ina da hayshin marin da kikai mata ranan yau kuma don samun guri zaki kara dukan ta to bisimillah gaki gata shege ka fasa.
Tambayan ku nake wa ake duka ne wai yace maji rabu da yar rainin wayo yarinyar nan ban san yaushe ta zama haka ba wallahi.
Har gidana fataje ta samu Fatima da mari ta tara shegun kawayen ta a gida suna juyata kamar ta samu yar aiki.
Bai isheta ba kuma yanzun daga tambaya shine wai zata duke ta again.
Duka shin Amira ko may dukan Fatima fa akace kinyi ko may ko kin fara shaye shaye ne kema bamu sani ba?
Bata fara komai sai rainin wayyo kawai ta ji na fada mata duk ta kara dora hannun ta akan matata ko zagi wallahi sai na bata marai Allah.
Nikan mikewa nayi na cire hijjab din dake a jikina na fara gyarawa mama falon ta da duk ya wani yamutse kaman bashi ba.
Na gama na koma can uwar dakin da dama nike gyarawa nai mashi kwal na kwaso shara gudan mai yawa.
Mama tace ki duba ki gani yadda muke zaune a cikin shara haka saboda shegen son jikin ki kin kasa gyara muna mazaunin mu sai fama da dakilan waya.
Nagama na dawo na zauna yace ke in kin gama tashi mu tafi akwai inda zamu biya in mun fita.
Tun muna hanya bayan mun baro gidan su mama nake jin marana yana murda min a hankali alaman period zai zo min ke nan.
A hankali na dan ya mutsa fuska na sai kawai naji yace ba tare da yakallo niba may nene kuma ya faru.
Sai da na sauke ajiyan zuciya nace ba komai yace shine kike yamutsan fuskan ki haka kawai.
Murmushi nayi nace bakoma mun tsaya wani shago naga yayi sayaya yafito aka sa mai a bayan motan shi.
Bamu tsaya ba sai gidan Inna mahaifiyar Bashar naji matukar dadin haka muka shiga a tare mun samay ta da yaran ta zaune suna hira suna ganin mu suka shiga murna.
Nan muka zube muna gaushe ta ta matsa sai mu tashi mu hau saman kujera bamu dade ba don yamma yayi a lokacin.
Mun isa gida duk nagaji ga marana yana min ciwo sosai a lokacin daurewa kawai nakeyi.
Na shiga yin alwala naga har jini yazo min ko nan na dan daureye jikina na fito ina tunanen yadda zan fadawa yaya ina period yau.
Ban fito falo ba ina kwace rike da marana dake min ciwo yashigo dakin yasamay ni na kifa kai a filo sai nishi nakeyi.
Yake tambayan wai may ke damun kine haka kinki fada wa mutum ko so kike ki halaka kanki ne wai?.
Da kyat na iya cewa marana ne ke min ciwo tun dazun, yace shine baki iya fadi na sai maki magani tun a hanya.
Shiru nayi ba amsa yace ko period zakiyi ne wai a hankali na gyada mashi kai tare da cewa har ma yazo min ai.
Yace ashe ko da gaskiyan Bashar ni raggo ne tunda na kasa jefa kwallo a wana jan ragan naki.
Turo baki nayi yai murmushi tare da mikewa har yafara tafiya yace kwana nawa kike yi dashi ne wai ?
Nace sati daya da karfi naji yace what ?
Sati daya fa ko baki da lafiyane zaki dinga sati kina fitar da abu daya haka nan ?
Kara kife kaina nayi kawai batare da nai mashi magana ba naji da abinda ke damuna kawai.
Fita yayi zuwa can ya dawo min da magani da lemo mai bawa da sauran kayan fruits .
Sai da nasha maganin na samu ya dan lafa min na fito falo yana zaune yana kallon ball .
Guri na samu na zauna tare da gaishi shi ga kayan fruit da naman da yaci saman table a gaban shi.
Yace yaya jikin kuma nace yai min sauki sosai dana sha magani .
Zauna ki ci nama ga milk nan kuma kisha baida sanyi sosai nace na koshi yace kin koshi da kikaci may kuma ?
Banci komai ba na dai sha lemon da ka kawo min sai naji na koshi sosai.
Oya ki kara da,naman kisha milk din ko zakiji jikin ya kara sake maki ban yi musu ba na fara cin naman a hankali sai dai duk bakina ba dadi cikin shi ko kadan.
Yace kisha milk din mana ina kaiwa a baki naji kaman zanyi amai nan na cire cup din da sauri a bakina .
Na mayar da kaina baya saman kujera ina mayar da numfashi guda guda cikin wahala.
Ban san tasowan shi ba sai jin shi nayi a gaba na yace oya kwanta ki mike shi da kan shi ya gyara min kwanciya nan ya shiga dan tausa min ciki na a hankali.
Naji dadin hankan har na fara lumshe idanuwa na ban sani ba sai barci bai bari ba sai da yaga barci ya dauke ni sosai.
Sannan ya daina yadan kura min ido yaga yadda nake barcina a tsanake nan ya koma saman kujeran da ya taso kada ya tayar dani.
Mukai wani lokaci a falon yana kallon shi bai son ya tayar dani na falka daga barcin da na keyi.
Sai da dare yayi sosai ya tayar dani muka koma daki sai dai makale ni yayi haka muka kwana dashi.
Washe gari na gyara jikina nai wanka nashirya tsab nashiga kitchen hada muna breakfast, ina tsaka dayi ya dawo daga gurin motsa jikin shi.
Kitchen din ya shigo ya samay ni yana cewa har kin ji sauki ke nan ko idan bazaki iya ba ki barshi kawai sai a sayo muna muci nace zan iya ai har na kusa gamawa ko.
Yace yau fa kina da bakuwa don Nafisa zata shigo gidan nan don Allah idan tazo ba runki da ita don kin san yanzu ta burge sosai.
Sai misalin sha daya da rabi suka shigo gidan su uku ne da kawayen ta da ganin su tantiran yan duniya ne sauran don sun fita,wayewa sosai.
Da fara,a na fito daga dakina ina masu sannu da zuwa duk suka zubo min idanuwan su nan dai bayan mun gaisa na kawo masu abin sha suna godiya.
Nace gashi ko yaya ya fita ya jiraki baki zo ba yace zai fita amma ba nisa zai tafi ba.
Kada ki damu ai zan jira shi ta bani amsa nace anty may zan dafa maku ne yanzu.
No ki barshi inji wace tafi haske daga cikin su nace ,a,a Allah bari na girka maku abinci mana kafin ku wuce.
Na juya nan na barsu a zaune suna bin gidan da kallo na shiga kitchen na fara hada abinci.
Basu dade sosai da zuwa ba yaya ya dawo gidan shi da Bashar ne wanan karon.
Suka gaisa dasu fuskan yaya a daure nagan sbi nafito muka gaisa da bashar nakoma ciki.
Yaya ce wa yan nan fa tace tie friends dina ke nan yaya wanan Raiha akace mata amma anakiran ta da Rayye ne ita kuma wanan Nura ance mata Nuriyya.
Yace ok sai dayan tace amma sai naga kamar na sanka da dadewa ko sai dai in ba kai bane amma nasan wanan fuskan gaskiya.
Nafisa tace ke banza shine fa U F da kike jin ana fadi dan kwallon wasan duniya.
Yadda tai maganan kamar a buge yasa kowa yin dariya a lokacin banda yaya daya daure fuskan shi.
Nakwao masu yaya ruwan sha da drinks na aje masu nakoma gurin girki na.
Yaya yace amma ba yanzu zaki wuce ba ko don kin san nace ina son ganin ki ko.
Tace ai shine nazo mana ko don nazo da kawaye nane baka samun ganin nawa.
Yace ashe kin gane nufi na nafito masu dauke da kulan abinci da plate na aje masu tare da masu bisimillah.
Can dayan tace na tuba inda na sanka yanzu muna haduwa da can baya gurin Brosha mai kayan harka ko?
Daure fuska yayi kamar badashi take magana ba Nuriya ta jawo kula ta bude abincin dana aje masu tace wowwo kamshi ke nan aiko mu gode wallahi dama yunwa nake ji sosai.
Sam basu da kunya atare dasu ko kadan sai wani girgiza suke yi adole sunga maza mata sa yaya yace muje na sauke ka gida Nafisa ki jirani fa kinji na fada maki.
Nan muka zauna dasu suna cin abinci muna hira jefi jefi dasu dayan take tambayan Nafisa ita kadai ce matar shi halan Nafisa taba amsa da eh.
raiha tace wai amma kan zakiyi fama da arnan yaki ga mijin ki matashi kuma mai lokaci ai akwai aiki.
Sai da sukaci abinci suka koshi yaidda nai masu sunji dadi haka sosai basu boye min ba don cewa sukayi da suka gama kai amma gaskiya munji dadin yadda kika tare mu ba kamar gidan wancan yayan naku ba da mukaje suna ce muna wai yan kwaya sun shigo gidan su.
Nace subbahanallahi ai ba wanda ya wuce jerabawan ubangiji don kuma ba haka kukaso ba a ran ku.
Shiru sukayi sai Nurace ke dai ganan min hanya yar uwa ina mamakin mutane wallahi mutum na da abin fadi amma sai ya takw nashi yaje fadin nawani.
Nace Allah Allah dai ya yayewa kowa wahala kuma Allah ya kawo maku mazajen aure ku huta duniya yanzu ba tausayi wallahi.
Raihane ta jefo min tambaya halan ke yar wace garice sister kafin na bata amsa Nafisa ta ce yar uwar muce fa agidan mu ta tashi ai.
Ai ko ban taba sanin taba gaskiya nai dariya nace niko nasan ku ai yakai sau uku muna hafuwa daku ai.
Allah sarki ban ko gane kiba wallahi, tace min suka mike suna cewa zamu tafi mungode kwarai da taron da kikai muna nace kai haba ba komai aiku yan uwa na ne.
Suna fita nan Nafisa takife saman kujera sai barci koda yaya ya shigo ya samay ta tana barci sai baita da ita ba dakina yashiga ya samay ni zaune yace ita wanan barci tai muna anan.
Nace ina ruwan Anty Nafisa taci ta koshi sai barci abinci yace na bashi nabi bayan shi muka fita tare sai da ya zauna yake cewa ina ganin yau zanyi tafiya fa.
Amma sai dai yadda nagani amma iyakata Abuja zan tsaya kawai.

****** ********* ******
Bayan Nafisa ta tashi yana falon zaune ganin shi yasata mikewa zaune yace har kin gama barcin ke nan tace tana mikewa zaune wallahi fa yaya.
Yace haba Nafisa ya kamata ace yanzu kin wa kanki fada fa gaskiya baki kyauta wa iyayen mu musan man ma Umma da take mace tana zama dake a gida ko yaushe.
Shiru tayi tare da dukar da kan ta kasa yace lokaci yayi nafisa da zaki bar wanan harkan haka duk da nasan abune mai wuyan bari amma don Allah kiyi kokari ki dan rage wasu daga cikin halaiyar ki don Allah dai ba don niba Nafisa.
Abin mamaki sai gata kawai tana hawaye tace wallahi yaya nima kaina ban san may ke kaini sha ba ko naso na bari sai naji kwata kwata bazan iya ba.
Lokacin nafito falon ganin suna magana yasa na juya zan koma ciki sai yace No dawo ki zauna aikema maganan ya shafe ki tunda ya shafe ta.
Tace wallahi yaya ni ina ganin Alhakin kune da maji ne ya sauka aikaina dakin mu don irin mugun abinda Umma da mama suke shuka maku kullun tun ina karama nakejin irin tugun da suke kullawa akan maji da ku.
Dariya yayi yace kai haba Nafisa ai shi zama kishi ina ganin haka yake sai ta share hawayen tace yaya bazaka gane bane wallahi.
Amma nasan ko nayi rantsuwa ban kaffara don su Umma ne suka sa kayin shaye shaye a baya.
Na fadawa umma su bari kada Allah yajerabesu watara tundai ina suna zagin ka da mashayi dan maye mukan mata magana ni da yaya sagir amma umma bataji.
Munafukan ga mama bata bari umma tabar aikin ta yaya yaya kake ganin zan iya dainawa idan su basu daina sheri ba.
Tace umma tana sakaci da yawa tana yarda da mama asiya batan cewa muguwa bace ta karshe har yanzu bawai sun dai jifan ku bane fa.
Allah daine ke kare ku kawai amma kai kan ka da,wuya in ka daina sha yanzun haka?
Da sauri na dago kai ina kallon shi sai naga yai murmushi kawai yace Nafisa koma maynene ki sa a ranki cewa zaki daina sai kikaga kin daina din.
Ki samu miji kiyi aure koma may nene kike so ni nai maki alkawari zan sai maki duk lokacin da kika tashi aure.
Kai ta kifa tafara wani irin kuka take nima bansan lokacin da na fashe da kuka ba shima dai ina ganin kukan yakeyi a lokacin yadda na ga ya dukar da kan shi kasa.
Can ya mike ya shige dakin shi ya bar munan muna kuka tai matukar bani tausayi namike zuwa inda take na dafata.
Duk da nima kukan nakeyi amma sai na dafata ina bata hakkuri kawai sosai nake mata nasiha har nagama batace min kalla ba nace tazo tashiga tai wanka ko zataji dadin jikin ta.
Ta kalle ni da mamaki tace Bintu ke baki kyamanane yadda sauran yan gidan mu ke yi min yanzu nace kyama kuma anty akan may zan kyamace ki kina da cutane ko may.
Tace har fa ciwon aids mama Asiya da yaya Ahmad ke fadin ina dashi yanzun haka kallon mai cutar aids wasu mutane ke min.
Nikuma wallahi komai mayena ban bari mutum ya shige ni baida roba a jikin shi.
Ban san lokacin da na runtse idona ba danaji abinda tace min ba kunya take fada min tana amfani da maza haka.
Dakina nakaita tai wanka na bata wani dogon riga na mai kyau tasaka muka dawo falo nan muka samu yaya yace tazo ya sauke ta gida don can zai tafi yanzu.
Tare sukafita da ita tana min godiya nace haba anty aiyiwa kaine tausayin ta yai matukar kamani sosai.
A hanya ma sosai yaya yaita mata nasiha ya na kwantar mata da hankali na ta natsu ta daina wanan harka baida amfani don babban illa da cikas yake kawowa mutum a rayuwan shi.
Sai yamma ya dawo yake ce min tafiyan shi yana nan yace ko bazan iya zama ni kadai bane yaiwa Inna magana maman su Bashar a turo min daya daga cikin yan matan ta nace a,a zan iya zama mana yaya.
Ai yanzun na saba da gidan ban jin tsoron komai kuma kamar baya yai min sallama bayan ya shirya ya wuce Abuja .



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,

IDAN KUMA KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA NA BARKI GA ALLAH YAR UWA,,,,

Zama muke na zaman kwari tsakanina da Amira don iyanzu takai ni inda bani son mukai tun farko da ita.
Ina zaune a dakina naui zugun ina tunanen irin wanan halin takuran da Amira take kawo min har a cikin gidana.
Sai hakkuri nake tayi ina hadiyewa don ban son mahaifiyar su su sami labarin halin da muke aciki.
Amma ranan da maryam tazo gurina ta fahinci akwai matsala a zaman mu da Amira.
Gaba maryam ta sakani sa tambaya iri nata har dai na warware mata duk irin zaman da mukeyi da kawayen ta da take kwaso wa su zo su dinga min abu isa isa a tsakar gidana.
Rayuwan maryam yai matukar baci tamike tana fadin wallahi sai tayiwa Amira magana
Amma na sha gaban ta na bata hakkuri tare da fadin idan Allah ya yarda ni da kaina zan dauki mataki a kan ta.
A kwana atashi ba wuya a gurin Allah sai ga shi yai har wata daya da kwana goma sha da tafiyan yaya sadauki.
Munan da Anty Amira muna ta kwamawa a cikin gidan don gaba daya yanzu na fitar da tsoron ta ko shakka da kawaicin ta da na ke ji da farko .
Karatuna nake don yanzu exam mukeyi hutu zamu fara next week banda wani lokaci sosai na kaina a gida gaba daya.

Tsaye yake idanuwan shi suna a lumshe dan murmushi ne ya sake don tuno da yanayin Fatima, da murmushin ta da take a boye tsiwanta da fushin ta da takeyi a lokaci daya ,
Sai dai kuma duk karancin shwkarun Fatima hangen nesa ta da kyakyawan zuciyan ta da manufan ta akan kowa haka halitta ne a gare ta.
Yana gyara tsayuwan shi yake cewa Fatima ke ba diyan masu hali ba amma kuma kina da,diyauci irin na masu halarci.
Su iso Lagos da yamma don ta nan jirgin su ya sauka Nigeria a gurin su basu dauki tafiya a bakin komai ba don haka ya tsaya yai clearing din kayan shi da ya shigo dasu.
A lokacin mun kammala exam na dawo gida satin nan ba fita duk wani motsi na da,wani taku na yana kan idon Amira da ta saka min ido a agidan.
A kullun tunanenta shine yadda zata kawo was Fatima cikas din rayuwa ta hanata jin da dadin rayuwa a gidan Sadauki.
Don ita Amira a watau ta sune yan uwanshi na jikin shi sune ya kamata suci arzikin shi fiye da,wata mace can da tashigo da sunan zaman auren sai su mamaye komai na miji ya zama na au suda yan uwan su kawai.
Shiko miji da dangin shi sai yadda akayi dasu kawai a gidan sun zama yan bi ke nan a dinga juya su yadda rai yaso,
Hakan ke matukar bankan ta mata rai ita bata kaunan ace dan uwanta sai wata ta bata doka akan shi Amira na cikin irin jinsin mutanen dake adawa da matan yan uwan su maza a duniya.
So take sai yadda tayi da shi da matar shi sai dai ta dinga bada commad ana bi kawai shine zaman lafiyan kowa da ita don bakin ran ta da yai yawa.
Takan ce dan uwa dai dan uwan tane babu mai raba shi da ita don a tare aka gan su don haka sai dai mace ta kare kutin gwilar ta tabar da dan uwan ta saboda babu wanda zai kawo wani shamaki a tsakanin su.
Haka mukai ta zama da ita a cikin fitina da gori habaici bakar magan cika baki sai dai wanda ba bu shi don duk nagani ga Amira lokaci guda.
Gashi kuma yadda take samun, gashin kanta yanzu a gidan namu tayi kiba tai fari ta kara dan girma da ita.

****** ********* ******
Suna zaune falo da kawayen tabar gazan ta wai su wayayyu su salma kubura da Fauziya sai jin motsin turo kofan shigowa falon gidan sukaji.
Idanuwan su na kan kofan don suga mai shigowa falon a lokacin don yanzu sha daya saura na safe muke ciki.
Cikin mamaki Amira tace yayana dama yau zaka dawo ashe bai amsa mata ba sai bin falon yake da kallo cikin mamaki bayan ya gama kallon fuskoki wa yanda ke zaune a falon lokacin.
Daya bayan daya yake kallon su har ya kai karshe Fatima bata falon.
Hakan yasa shi wuce wa direct dakina yagani don sai yaji zuciyar shi tana mashi wani irin kuna a lokaci guda.
Yana bude kofan zaune nake na sallamay sallah walha, ina dan jan tasbaha bayana yana jingine da fadon dakin
Jin an turo min kofa yasani saurin dago kai ina kallon kofan dakin wanda nagani a tsaye ya harde hannayen shi guri guda yana min murmushi yasani saurin dan sakin murmushi tare da yunkurawa in tashi.
Na nufoshi a a cikin fara,a ina cewa sannu da zuwa yaya yaya hanya ya can ?
Murmushi yayi tare da,ware hannayen shi na sheko da dan gudu na na shige ciki ya mayar da hannayen shi ya rufe ni dasu .
Sai da muka dan dauki lokaci a haka muna shan dumin junan namu ne yake cewa cikin wata irin shakkakiyar murya su waye nagani a falo kuma a ina suka fito hakane da au kuma ?
Nai dan murmushi tare da dan dago kaina daga jikin shi nace ban san da ga ina suke ma amma kullun dasu muke wuni a gidan nan sai dai na girka na basu idan kuma sun gama na kwashe na gyara gida idan da duk ya baci.
Yace a bisa ga umurnin wa hakan ke faruwa min a gida ban sani ba nace umurnin second command ne Anty Amira don haka sai ka tambaye ta bayanin komai.
Ina rike a hannun shi yaja hannuna zuwa falon muna shiga suna ganin mu suka sauri dawo da hankalin su a gare mu irin yadda suka gan mu a tafe ne ya kara daure masu kan su.
Zama mukayi a saman kujera daya nidashi ya dago fuskan shi dake a daure yana fadin wa yan nan kuma fa daga ina suke ne haka ?
Shiru babu wanda ya amsa ya dago kan ahi yana kallon inda nake yake yana cewa nace su wayen haka kuma don ban san su ba.
Nace ka tambayi anty Amira don tare na gan su dasu kuma ta fada min sunfini daraja a gidan nan kaga ni dole sai dai na bisu don yan uwankane na ji aiko.
Sai dana fadi haka ya dago kai ya kalli inda Amira take zaune wani irin haushin ta ne da kiyayyan ta ya darsu

Please Login or Register in order to submit comment