Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ya dace duk uwa ta gari taiwa yarta.
Tace insha Allahu haka nake kokarin ganin nayi yo har ma may mutum zai cuta a wanan gurin kuma ?
Nan dai sukai ta zancen su har suka fado kan maganan sabuwa da irin hallin gallaza masu data dinga yi a zamanin ta a gidan.
Mama hausatu tace don yaran ai ayi hakkuri ta dawo dakin ta gashi kuma bazan so ace don wanan yarinyar tabar gidan nan ba.
Kada azo a shafa wa yar mutane labbo bata ci ba tasha akama zarginta ga banza kasan haln mutanen yanzu da dauka su dagwarawa kan su maganan da bata shafe su ba.
Dan nata yace hakan yana da kyau mama indai wanan mara mutuncin ne aiko ta dawo ba dainawa zatayi ba.
Gara dai tadawo dakin ta din zaifi don kaga yanzu idan tafice gidan nan nauyin diyan ta duk akaina zai dawo gasu ba tarbiya ke garesu ba.
Yadda mama hausatu tai shawara da danta haka akayi da yamma da Alhaji yadawo gida ta sanya shi a gaba tana bashi baki akan yayi hakkuri ya daure sabuwa ta dawo dakin ta hakana ko don yaranta.
Yace wai hausatu ke ce ke auren ta ko ni da zaki isheni naje nayo bikon ta ina indai sabuwa ce koke bata bari a gidan da tsufanki kuwa ?
Mama hausatu tace kadai yi hakkuri Alhaji kodan yaran ta ta dawo taci gaba da duba abinta.
Yace yara ai bada su tazo ba anan ta samay su kuma a gidan iban su suke ko ?
Ya ja tsaki ya dauki buta ya fice daga gidan.
Gaba daya yaran Sabuwa sun ishi matan gidan da rashin kunya idan ka cire shi Alhajin da basuyi a gaban shi don tsaye yake akan iyalin shi.
Don haka shi zaman su ma babu uwar su a gidan ko a kwallan shi bai taba damuwan shi ba don dan ficewan ta har ya samu natsuwa tare dashi.
Satin ta daya shiru babu labarin dawowan ta gidan har wanan lokacin ganin maganan wasa zai zama gaskiya yasa.
Mama hausatu samun wani dan uwan Alhaji kuma amin shi akan zancen sabuwa din don yaran sun ishesu ba hutu gareta.
Bayan sun gaisa ne tayi mashi bayanin komai akan matsalan da ake ciki tsakanin sabuwa da Alhajin.
Malam shehu yace a gaskiya ba yau ba Alhaji hakkuri yake da al, amarin sabuwa ke ma kin sani .
Don ko jiya muna tare nan dashi yake min bayanin komai don iyayyen ta da yan uwan ta sun damay ni da zariya agida.
Amma tunda kinzo ba komai insha Allahu anjima zan samay shi muyi magana idan ya dawo.
Mama tace don Allah malam a taimaka a sa baki ga alamarin a gyara tun bai baci ba kodon yara.
Daga haka sukai sallama ta tafi tana godiya don sun saba dashi sosai akan matsalar gidan su.
Duk yadda ya raya da Alhaji akan yai hakkuri Sabuwa ta dawo dakin ta yaki yarje mashi.
Don haka ya kyale shi malam shehu ya nemi wani amin shi da magariba suka shirya sai gidan wan sabuwa inda take zaune.
Lokacin da suka isa gidan sun samu wan nata baya gida dole suka dan jira shi don ba nisa ya tafi ba.
Bayan sun gaisa ne suke cewa da shi dama mun biyo bayan sabuwa ne don Allah ayi hakkuri ta koma dakin ta hakana.
Don sabani akasamu kuma yanzu kowa ya gane kuresa don ko tsakanin harshe da hakori ana samun sabani balle mutum da mutum don gaskiya iya hakkuri kukan ku kun sani Alhaji garbati yana iya hakkurin shi da sabuwa a gidan shi.
Yayan nata yace hakane amma naso ace shi Alhajin ne yazo nan da kan shi don na kara bashi hakkuri saboda nima dan zaman ta cikin iyalina nasan yana hakkuri sosai.
Malam shehu ya jinjina kan shi yace hakane amma da zuwan Alhajin da namu duk kusan guda ne don a madadin shi muka zo mu.
Koma may nene ai yanzu ta san ta fara kaishi bango don baka kallon babban mutum kamar Alhaji garba tsakiya iyalin shi tace mai munafuki.
Yayan nata yace don Allah akara bashi hakkuri kafin nazo har gidan na bashi.
Yayan yace kafin ku tafi bari na kirata taji da kan ta don ku kara ja mata kunne mace da girman ta kamar Sabuwa ace wai ta saura yaji don rashin hakkuri irin nata.
Bai jima ba suka fito a tare yana gaba tana bayan shi ta samu guri daga gefe ta tsugun na.
Yayan nata yace sabuwa ga malam shehu nan sunzo bikon auren ki a madadin maigidan ki.
Ta dukar da kai cikin kunya da nauyi zatayi magana malam shehu yace da ita.
Haba Sabuwa yanzu lokaci yayi da za, a san girma ya kama a daina wasu halaiya kuma.
Don Alhaji ya auro wanan yarinyar bai kamata ace daga gareki ne ba a samu zaman lafiya ba idan kin yi tunanen irin zaman da kukayi ke dashi har takai kina ci masa mutunci a tsakiyan sarakan shi hakana.
Don haka idan kin koma dakin ki da fatan komai zai sauya daga gareki yanzu shiga ki dauko kayan ki basai gobe ba mutafi na mayar dake dakin ki.
Zatai magana yayan nata dake zaune a gefe yace ya katseta cikin bacin rai da cewa .
Kin sani sarai bana son tashin tashin kije ki shiryo ku tafi.
Ba don taso ba ta tashi ta shiga ciki can sai gata tafito da lulubinta dauke da dan ledan kayan ta suka kama hanya.
Ko da suka iso gidan sun samu Alhaji a kofan gida shi da baba salla zaune suna hira.
Yacewa Sabuwa shiga gida ta shige simi simi ciki shi kuma ya tsaya wajen su Alhaji dake kallon shi a cikin mamaki.
Nan ya zauna ya dinga bashi baki akan yayi hakkuri ya taushi zuciyar shi akan iyalin shi.
Yace babu komai tunda taci albarkacin shi zai kula ya saka ido ga komai a gidan insha Allahu.
Muna zaune kofan mama gaba dayan mu gidan ga hasken farin wata ya haske ko ina anyi gungu gungu ana hira.
Sai ganin shigowan ta kawai mukayi gidan da kumshin kayan ta babu ko sallama.
Kowa ido ya saka mata wasu sun gane cewa itane musanman ma yara ta da suka hau ihu eh mama mama da murnan su.
Nan dai duk da batai sallama ba aka shiga gaida ita tana amsawa cikin basarwa ta shiga dakin ta.
Ganin akwai duhu a dakin sai gata tafito tana cewa mama yaya ara min fitilar ki na haska naga guri don Allah.
Mama tace a dauko mata ta amsa fuuuu ta juya zuwa dakin nata daya daga cikin sarakan mama tace bisimillahi Allah matsala ta dawo ke nan kuma.
Kowa nan suke fadin albarkacin bakin su akan dawowan nata kuskus kus daya bayan daya muka watse gurin kowa ya kama gaban shi.
Da daddare can sai gashi ya shigo gidan dakina ya nufo don nice da girki a ranan.
Ya samu kujeran da yake zama kafin ya kwanta ya zauna na gaida shi da dawowa yace.
Amarya kinga wanan fitinanan ta dawo gidan ko ?
Nace wa wai maman Suwaiba ?
Yace ita ,
Don haka abinda nake so dake kikama kan ki daga gareta daga ita har yaranta ba tarbiya ne dasu ba.
Nace insha Allahu zanyi kamar yadda kace Alhaji bazan shiga tsabagan taba ko na diyan ta a gidan nan.
Ashe sabuwa tun shigowan shi gidan tana hankalece wai ita a zaton ta tunda ta dawo ranan a dakin ta zai kwana don haka takeyi wa sauran matan nashi a baya.
Tana ganin ya wuce zuwa dakina wani tukukin bakin ciki da kishi ya rufe mata zuciyar ta a lokaci daya.
Don haka tafito fuuu zuwa dakin mama hausatu tafada mata daki tana haki tace yaya kinga wanan mutumin baya son a zauna lafiya a gidan nan ko ?
Mama tace da akayi may kuma Sabuwa ?
Tace amma ai yasan na dawo amma ya iya wucewa ko dakina bai leko ba yana nufin cewa yarinyar nan itace zatai girki ko may ?
Ke sabuwa wai yaushe zakiyi hankali ne ke ki san jiya ba fa yau bane ?
Idan mu dacan kin samu kina muna yadda ran ki yaso yanzu baki tunanen cewa wata tazo gidan ne.
Gara ki rufawa kan ki asiri ki zauna dakin ki ki dubi yaran ki zai fi maki sauki wallahi .
Aiko da dakike muna hakan idan kin dawo kema kin san ba hakkin ki bane yin hakan don dai a zauna lafiya muke saka maki ido kawai.
Yanzu kuma wata tazo yarinya danya sharaf kice zaki tauye mata nata incin kinga haka zaiyuyu kuwa.
Gara ki kama kan ki da mutunci ki a gidan nan tun bakija wa kan ki raini ba ga yar diyar cikin ki da ko uwarta kin girma ga haihuwa.
Nan dai taga ba ci idan tace zata ja gashi da kyat ta samu tadawo dakin ta tun ba, a kwana ba kuma ace wani matsala ya taso a gareta haka ?
Ta juya cikin kwafa zuwa dakin ta tana faman mita da ace tasan zaman da muke da mijin nata da take ganin na anshe mata data bawa kanta lafiya.
Don idan tace taja wani fitina da daren nan wani sabon tonon asirin ta ne zai a bainan jama, a don yanzu maigidan nasu akan yar karamar yarinya baijin ass.
Don a dole banda yadda zanyi nake zaune gidan gashi har takai iyanzu na saba da komai ina zamana hankali a kwance tunda ba takura.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE NA FADA IDAN BAKI BIYA BA KIKA KARANTA MIN NOVEL NA BARKI GA ALLAH.

IDAN KIN BIYA KIKA TURA MIN NOVEL WANI GROUP KO KIKA BA WA WANDA BAI BIYA BA KE MA NA BARKI GA ALLAH DON KINCI AMANATA ALLAH ZAI SAKA MIN A KAN INSHA ALLAHU WACE TASAN BAZATA IYA RIKE AMANA BA DON ALLAH TAI MAGANA NA BATA KUDIN TA TAFITA MIN GROUP DON AMANA NAUYI GARE SHI ABINDA KA RAINA SAI YA HANAKA KETARE SIRADI GOBE KIYAMA ALLAH YA BAMU IKON RIKON AMANA A TSAKANIN MU.
DON NAGA NOVEL DINA A WANI GROUP KUMA NASAN WACE TA FITAR DON BATAI MAGANA BA NA BARTA GA ALLAH DON ALLAH SHEDA NE GA ALKAWARIN MU DA KU, ,


Ranan da na zana jerabawan karshe na na secondarya rana ce da ya kamata nai mafarin ciki a raina don kowa ka gani a cikin mu yana cikin farin ciki da jin dadi a ran shi.
Sai dai ni a gareni sabanin hakane don ya kasance min kamar rana na bakin ciki a gare ni.
Lokaci daya yanayi na ya sauya min naji duniya tai min kunci a raina komai ganin sa nake yai min baki a raina a dalilin tunawan da nayi wanan jin dadin rayuwan ya kusa yanke min.
Don wanan auren jarabtan da na tsinci rayuwana dashi na auren tsoho da mahaifina zai min a lokaci daya haka, batare da yai la, akari da irin rayuwan da zanje gidan miji na tarar.
Wanda yau baifi saura kwana goma ba naje gidan Alhaji garbati a matsayin matar auren shi nima a gidan.
Juyawa nayi zuwa staff room don nai sallama da malam mutumin da yai tsaye a kaina har nakai wanan matsayin na yau a gare ni.
Malam yana ganina yace a, a Rahama an kanmala ko ?
Maimakon na nuna farin ciki na sai na kai durkushe a gaban shi na fara kuka yace subbahanallahi Rahama lafiya dai ko ?
Cikin kuka nafara cewa malam nazo ne nai maku godiya akan tsaya min da kukayi har na kai ga wanan ranan ga karatuna.
Sai dai kuma gashi guri na ba zai kai na zama likitan da nake son zama ba na taimakawa yan garin mu kamar yadda nake da gurin haka a rayuwana.
Mahaifina ya yanke min wanan gurin nawa ta bayar dani aure ga wanda yaso yau saura kwana goma ayi bikina akaini.
Subbahanallahi inji malam yace yaushe haka ya faru kuma Rahama waye kuma miji ?
Sai na dan kakaro murmushi a fuskana nakw cewa malam an kwana biyu da hakan ba kuma kowa bane mijin sai Alhaji Garbati dan bida na garin nan.
Shi da sauran malamai da suke saurare na cikin tausayi sukace garbati dai garbati wanan tsohon mutumin da muka sani ?
Nace shi malam ,
Malamai suka ce kai amma mahaifin ki ya cuce rayuwan ki Rahama ga wanan tsohonbzai bada ke dan kwadayi ko don may ?
A hankali nace nima ban sani ba malam na mike ina masu godiya na ke masu sallama na tafi,
Nan na barsu da mamaki kowa na fadin albarkacin bakin shi a kaina na nufi gida.
Na shiga gida da sallama na na gaida da su mama da na samu tana raba abinci a tsakar gida.
Nan na shige dakin inna na kwabe uniform din jikina fita nayi na debi ruwa don na watsa naji dadi jikina.
Mama ta bini da harara wai dan ruwan da zasuyi aiki dashine kuma zan kwashe nai wanka don ni nafi kowa tsabta ko may ?
Ina ban daki na fara watsa ruwa ne naji mama tana rafka salati haka yasa nasan ba lafiya ba ke nan.
Nai saurin watsa sauran ruwan a jikina na fito da sauri nan na samay su tsaye cirko cirko sai fada mama takeyi ita kadai Inna ta tana tsaye a bakin kofan ta itama fuskan ta a cikin damuwa yake.
Na karaso inda take ina fadin Inna lafiya ko may ya faru kuma ?
Kafin mama ta bani amsa take cewa dani wai angon ki ne ba lafiya gashi can an kwashe shi zuwa asibitin birni yanzu.
Gabana ne naji ya yanke ya fadi min ras ras nace shi Alhaji garbatin ne da kan shi baida lafiya ?
Mama tace idan bashi ba da uban ki ko bakiji may nace bane ni.
Allah ya sauwa nace na watsa ruwa a kafana dana rage a sauran roban da na fito dashi ban daki da nai wanka.
Nashige dakin mu kawai na fara sallah bayan na idar ina jin mama tana karasa aikin ta sai faman mita takeyi akan zancen ita kadai a tsakar gida.
Na juya inda inna take zaune cikin damuwa nace inna may ya samay shi ne ?
Take cewa dani yanzu nima nake jin zancen a gurin yaya wai ya kwana biyu yana irin wanan ciwon dama.
Allah ya sauwaka nace, naci gaba da kwalliya na ba abinda ya damu raina ko kadan.
Sai bayan dawowan babane muka samu labari wai ashe ya kwana biyu yana irin wanan lalurar .
Fitsari ne ke mai wahalan fita idan zaiyi sai kuma yanzu da suka tafi asibiti ake cewa harda hawan jini yana da shi.
Mama sai cewa tayi Allah ya cece mu ga farar kafa mu kan ?
Kamar yaya farar kafa kuma baba ya tambaye ta hakanan ?
Tace to yau saura sati a saka lalle haka ya kasance dashi ai sai ace yar mu ce zata shiga da farar kafa gidan shi .
Ki kadai fadi yanzu inji baba lalurar da kowa yasan ashe yana dashi dama shine zaki fadi haka ?
Tace ai idan ni ban fada ba iyalinshi su fada tunda koda yake dashi duniya basu sani ba sai yanzu .
Lauratu wai may yasa baki son a zauna lafiya ne ke duk abinda zai kawo fitina a tsakani kin san yadda zaki jawo shi.
Idan da yar cikin ki ce za, a kai gidan ai baza, ki fadi haka ba akan ta.
Allah ma ya tsare ya ta da wanan rayuwan gaskiya ne baka son a fadi kuma in ni ban fada ba duniya zasu fada ai.
Baba yace yanzu na gane may kike nufi akan yarinyar nan mutane suna fada min ban yarda ba amma yau na yarda da hakan.
Nan dai suka fara halin nasu na sa in sa a tsakanin su wanda ba mai shiga don ko mutum ya shiga sai yai kunya don ajima kadan zakaga sun shirya ne.
Bayan an sallamo Alhaji garbati ne daga asibiti ya turo kiran babana yana son magana dashi.
Baba baiyi nauyin kafa ba ya tafi amsa kiran da Alhaji Garbati yake mai a kofan gidan shi inda akai mai shimfida mutane suna zuwa gaida shi da jiki baba ya samay shi.
Bayan sun gaisa yai mashi yaya jikin shi da sauran iyalin shi ?
Ya bukaci da sauran mutanen dake gurin yana son ganawa da babana akan wani magana sun san alakal dake a tsakanin su don haka suka basu guri.
Alhaji garbati ya sake gaida babana yake cewa ya aika a kira shi ne don su yi magana akan zancen auren shi dani.
Yace bai san ko don matsalan da ya samay shi za, a iya daga bukin har zuwa lokacin da Allah zai bashi lafiya sai ayi.
Baba yace haba Alhaji ai kowa yasan lalurar ciwo inda yin ba zai zama matsala ba sai ayi din a wuce gurin.
Alhaji yace amma duk da haka da a shawarci yarinyar da uwarta aji ta bakin su don kada azo ayi daga baya kuma a zo a samu matsala ya biyo baya.
Baba yace hakan ma shawara ne zai je yayi shawara da ni da uwata yaji ra, ayin mu ga hakan.
Nan dai sukai sallama baba yai mai fatan samun lafiya ya tafi ya barshi a gurin da ya samay shi a zaune.
Baba ya dawo ya samay ni da inna ta a daki muna hiran mu cikin jin dadi tai muna sallama ya shigo daga ciki.
Nan ya samu guri ya zauna ya na mike zan bar dakin yake cewa dawo ki zauna magana zamuyi daku.
Na koma na zauna cikin natsuwa a inda nake yace dama akan zancen auren Rahamane yanzu Alhaju garbati ya kira ni gidan sa mukai magana.
Jin abinda ya fadi yasa muka natsu daga ni har inna ta muna sauraren shi muji may zai fada muna.
Kaf yadda sukayi da Alhajin ya fada muna tare da tambayan mu may ye ra,ayin mu akai mu ?
Inna tace to malam ko dai an daga bukin nan ai ba fasawa za, ayi ba ko ?
Don may ba, a ayi a haka ba kowa ya huta da kace nace akai asan ayi an gama ta zaunu a dakin ta.
Baba yace ke Rahama may kika ce shiru nayi ni may zance tunda bani ce da ikon kaina ba.
Baba ya sake maimaita tambayan shi a gare ni a hankali nace baba abinda Inna ta fada gaskiya ne ayi kowa ya huta kawai.
Baba yace to madalla Rahama Allah yai maki albarka yasa haka shine alheri a gare ki.
Sai kiyi ta hakkuri da halin rayuwan da zaki tsunci kanki a gidan don kin san manyan mata zaki sama a gidan.
Idan kin je masu da taushi yadda na san ki sai kiji dadin zama dasu har iyalin su.
Amma idan kince zaki nuna masu halinku na diyan yau sai ki samu matsala dasu har iyalin su.
Mama da taji muryan baba a dakin mu ta kasa zaune ra kasa tsaye akan tana son jin may akeyi a dakin wanda ba, a son ta sani.
Sai ta hau fadin tsuntsun da yaja ruwa shi ruwa ka doka ai wanda yaci shi ka biya don dai nasan bai wuce ance garbati yace a mayar mai da komai nasa ba ya fasa.
Wanan rufa rufan wa za aiwa shi wa zai kwashi mai farar kafa ya jefa a cikin iyalin shi .
Baba dai ya fito bai kula ta ya fita da dare ya koma ya fadawa garbati yadda sukayi da iyalin shi.
Shiru yayi yana nazari maganan baba na irin halarcin da sukai mai don shi a rayuwan shi yana son kasancewa da wanan yarinyar a rayuwan shi.
Don haka ba, a fasa komai na shirin buki ba akaci gaba da gudanar da shirin da za, ayi.
Mama a zaton ta an fasa ne ne sai da taga yan uwan Inna suna shige da fice ta fahinci akwai zancen bukin ke nan.
Nan kuma hankalinta ya tashi ta sulale har gidan garbati taje a cikin dare ta gana da matan shi take fada masu mugun kalamai na batanci akaina da uwata.

****** ********* ******
Ranan kamu aka saka ni a lalle kamar yadda akewa ko wace budurwa kamu.
Duk wanda ya ganni ko inna ta yasan bamu a cikin walwala ana dai sha, ani ne kawai na bukin ba cikin dadin rai ba.
Gidan mama altine nake zaune da kawayena don a gidan mu babu fili ga magan ganun mama da basu da dadin ji.
Ya kasance washe gari daurin aure nan mama ta dora a tsakar gida ga dakin Inna tab da yan uwan ta sai cewa mama take ita bata gane ba fa.
Ace har yanzu ba, a fito da kayan amarya ba aje zuwa jere ko sai mutane sun watse ne za, a tafi jeren kamar marasa gaskiya.
Wata daga cikin yan uwan Inna ta fito tana bata amsa da cewa in ma mutane sun watse ai ko wasuwasun mu zamu iya gyara dakin yar mu.
Ballanta na rana muke jira yai sanyi mu tafi don bamu fada gidan mutane da rana tsaka ba kamar mun gaji da yar ta mu.
Dole mama taja bakin ta tai shiru ta kyale su dai gani ai duk abin da akewa taratara din ake boyo yau rana ce da bata karya sai dai uwar diya tai kunya.
Sai zuwa karfe biyar mutane suka fara shiga gidan mama Altine suna kwaso kayan da aka saya min na aure.
Wata daga cikin kawayen mama da ta gaiyyata suzo saka ido ta shigo tana cewa mama.
Ke laure wai kayan da naga ana fitowa dasu gidan mai kuli na waye ba dai kayan yar taki bace haka?
Ni duk garin nan ban taba ganin yarinyar da akaiwa kaya haka ba ?
Kinko ga kayan kamar ma na kamfani ne fa don a cikin ledan su ma suke, ga wasu irin manyan zannuwan gado da na fani kamar na makka dasu didin didin dasu.
Gaban mama ya fadi tace ke haule wai da gaskiya kike ko ba, a baki ga komai nakai gida ba tace idan karya nake fita ki ganewa idon ki ai.
Mama bata saya ba taja wani raggan zani dake shaye a igiya ta nufi kofan gida da saurin ta.
Aiko tana lekawa tai tozali da kujerun da ake fitowa dasu tace kan uban nan ni za, aiwa munafunci ke nan.
Watau malam yana da kudin yin wanan kayan haka wa yar shi.
Shine ya barni da yara a zunbule a daki sun kai sun kawo ga girma kuma ba manema suka rasa ba.
Da kyat kawayen ta suka samu ta natsu suka jata zuwa cikin gida dakin ta suna tausan ta akan idan tai haka taba da kan ta.
Nan dai aka shiga shirin buki ba wanda ya tsaya kula mama da haukan ta da takeyi ta kasa boye hassadan ta

Please Login or Register in order to submit comment