Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

gaisuwa hankalinta ya daga don ta ga ban kiran ta da farar safiya irin haka.
Tace Fatima lafiya dai ko ?
Nace a hankali mama na haihu ne.
Cikin wani murya tace kinyi may fatima nace na haihu ne mama.
Sai naji ta kashe wayan maryam na nema tana barci wayana ya tayar da ita na fada mata na haihu sai Nafisa.
Koda na kira nafisa ina jin muryan mutanen gida a na yaya nasan zancen ne mama ta fada masu a lokacin.
Kafin wani lokaci naji kiran sadauki ya shigo yace batare da gaisuwa ba Fatima is that true o you are joking yanzu bashar ya kirani.
Kafin na bashi amsa yaron da nurse din ta daga ya dan yi kuka na kara mashi a waya yaji.
Yace it means yaron yana da rai har yanzu ke nan nace mai eh kawai sai aka turo kofa su mama ne da mummy da mama Asiya suka shigo dakin a rude.
Idon su akan nurse din dake shirya yaron za,a kaishi pediatric asaka a kwalba.
Gurin nurse din suka nufa suna kallon yaron dan karami dashi a cikin zani na da aka nade shi.
Muna kallo suka fita da yaron mummy da,su sagir suka bi bayan su harda mama Asiya.
Sai lokacin mama ta karaso inda nake zaune a bakin gado take cewa Fatima lafiya dai kike ko ?
Na kakaro murmushi don hankalina a tashe yake nake cewa lafiya kalau nake mama.
Tace to ki kwantar da hankalin ki idan yaron Allah yayi shi rayayye insha Allahu zai rayu.
Nakoma a hankali saman gado na kwanta na lumshe idanuwa na shigowan su maryam ne yasa na bude idanuwana a lokacin.
Maryam tana fadin tare da,waige waige ina yaron yake maji ?
Tace sun tafi dashi nan tafada masu komai basu tsaya ko a gaisa ba suma suka bi bayan su da sauri.
An saka shi a cikin wani dan karamin gado mai naurori tare da saka mai wani dan rigan sayi a ciki.
Kafin likita ya shigo dakin sun fada min zan tashi daga wanan dakin da muke na gany room zuwa maternity room.
Sai da,aka gyara komai suka mayar damu dakin lokacin yan uwa da,abokan arziki sun cika a dakin ko.
Sai hira ake yayin da niko zuciya na duk a cunkushe yake min ban majin farin ciki ko kadan ni.
Duk da kowa yazo fadin yake ai anyi arziki wata bakwaine insha Allahu zai iya rayuwa da yardan Allah.
Barci ne ya dauke ni a lokacin mai nauyi sai mama Asiya ne naji tana tayar dani wai na tashi na sha tea da aka hada min.
Na mike zaune ta miko min tea din yana wani irin tururi tace na kafa kai nasha shi hakanan.
Har na daure na kafa kai zafi ya konani nai saurin cire bakina daga cup din ga tea din gudan mai yawa dashi.
Lokaci daya suke ce min a,a a Fatima anya kuwa kafa kaifa zakiyi ki shanye shi duka yanzu.
Nace a dan marairaice mama duka fa wallahi akwai zafi mummy tace kin manta cikin ki akwai miki a cikin shi maza shanye shi don Allah kinji.
Haka na shanye tea din ina zufa take naji bakina ya dauki zafin kuna sai dai tea din yana shiga cikina naji wani irin dadi a jikina da nake jina yau kamar banawa ba.
Ban dade ba na koma barci mama Asiya da mummy sukace a dan rage a dakin don na samu barci.
Barci nayi sosai sai zuwa sha biyu da rabi na rana wata nurse tashigo dakin wai na tashi naje naba yaron nono.
Tare muka tafi da maryam da Nafisa da mummy a ka dauko shi na zauna na fara bashi nono sai dai bai iya kamawa.
Mummy ce ta gyara shi da dan kyau ya dan tsosa kadan ya koma barci don ba komai a nonon ma lokacin.
Likita ya shigo yana cewa sannu madam ashe haka abin yazo muna kuma dai.
Allah ya raya muna,shi ga baban shi yace yau yana da ball da mungashi yazo.
Haka muka wuni yan uwa da abokan arziki sai zuwa suke gaishe ni allura akai min sai magani da,suke bani kawai.
Bayan shi ni banda wani matsala a tare danj gaskiya mama ta bugawa iyayyena waya ta sheda masu yadda haihuwan yazo min haka.
Sai dare aka rage a gurin mu inda aka barmu da Iyya sai mama Asiya da tace itama zata tsaya wai.
Nafisa bata bar gurin mu ba sai zuwa sha dayan dare wani yazo ya dauke ta tafi.

****** ********* ******
Bayan kwana biyu da haihuwa ne likita yace zasu iya sallamana na koma gida sai dai zasu bani time da zan dinga shigowa ina bawa yaron nono.
Karfe biyar na safe , tara na safe sha biyun rana karfe biyu na rana zuwa hudu sai shidda na yamma kuma zuwa takwas na dare idan da hali sai na dawo da,sha biyun dare ko sha daya da rabi.
Yaya bashar yace insha Allahu za,a kiyayye zan dinga zuwa ina bashi nono din.
Haka na dawo gidan don da aka bugawa sadauki waya cewa yayi na koma gidan shi kawai tunda ance lafiya na kalau.
Gwagona ta zauna dani tare da Iyya a gidan tana min wankan jego gadai jego ina yi haikan amma babu baby a gida.
Sai time yayi yaya bashar zaizo ya dauke ni ya kaini asibiti aba yaron dake karkashin kulawan likitoci nono ya sha.
Satin mu daya Alhamdullahi yaron yana ta kara murmurewa sosai don yana samun kulawa gashi ba,a barin kowa ya dauke shi sai ni idan zan bashi nono ko ganin shi ba,a bari yan uwa suyi yana ciki a rufe.
Kwanan mu goma da haihuwa yaya sadauki yashigo Nigeria da,tarin arzkin da yasamo a rayuwan shi sosai.
Don andage suna sai yaron yayi kwari sosai zaa saka lokacin yin suna bisa shawaran da likita ya bayar ayi.
Koda ya,shigo sokoto ya samu ina shiri ina jiran zuwan yaya,bashar don time din zuwan mu ba yaron nono yayi lokacin.
Ina saye cikin atamfa zani da riga don nafi jin dadin ba yaro nono hakanan.
Yana rataye da corth din shi a kafadan shi daganin shi a gajiye yake a lokacin.
Direct dakina ya nufo da ya,shigo ina zaune a bakin gado nayi kyau dani don jego ya karbi jikina sosai a lokacin..
Jin shigowan shi dakin ne yasani daga idona na kalle shi shima dai ido ne ya,tsura min a lokacin yana takowa zuwa inda nake zaune.
Sai da ya karaso inda nake nake ce mai sannu da zuwa yaya.
Yace aikece da,sannu Fatima ya kai zaune gap dani yana cewa yaya kike nace lafiya kalau yayana.
Yace yaya baby din yake kuma yanzu nace lafiya yake yanzun ma can zamu tafi bashi nono yaya nake jira yazo.
Yace to na tashi mu tafi tare dashi nace bazaka huta ba tukun yace ina zan huta banga baby na ba Fatima.
Tare muka tafi dashi da yaya bashar daya ja motan ranan an barsu sun shiga don shi.
Shiya fara daukan yaron da muka samu idon shi biyu a lokacin sai watsalniya yake da kafafuwan shi.
Ya dade da yaron dauke a hannun shi yana mashi addua ga sauran yara a gurin kwance suna barci zasu kai su biyar a lokacin.
Mun ba yaron lokaci sosai muna tare dashi muna kallon shi muka aje shi ba don mun so ba muka fito daga dakin.
Haka na dinga zuwa yaya ya na kaini har akai wata daya yaron ya dan yi wayau sosai a lokacin.
An saka mai sunan Baba watau Abubakar an yanka rago da shanu anyi sadaka da naman wa mabukata.
Likita ya bada shawara da yaron ya kai wata takwas akan zamu iya tafiya dashi gida a lokacin.
Ranan da muka dawo gida da yaron naga dan mutum sosai a gidan masu zuwa min barka aka saka suna sati mai kewayowa za,ai taron suna irin na al,ada hausawa musulmai.
Sai faman shirin suna akeyi Jamilan yaya Ahmed da ita ake komai a taron wanda mama ce ta saka ta yin haka dole.
Don su taushi zuciyar sadauki akan maganan gida dake aje a kasa ba,a tayar ba tukun don wanan al,amarin sunan dake gaban shi.
Ranan suna gidan ya cika makil da jamaa masu zuwa taron suna wanda na sani da ma,wanda ban sani ba yazo gurin taron sunan.
Anyi walima sosai tare da ciye ciye da lashe lashe yan uwana sun zo da yawa sosai gurin sunan.
Yan uwan mama ma sun zo da yawan su daga Niger state dasu akai sha,anin bukin sunan yaron wanda muke kira da Amir.
Yai wayo sosai amma gwago bata bari ana daukan shi kamar yadda mukeyi ranan suna duk wace tazo sai ta dauki yaron ta ganshi.
Likita ya hana haka yasa itama gwago ta hana a dauke shi yana gurinta a wani dakin da suke kwance a saman gado.
Duk wace tace ina yaro sai dai ace mata yana lafiya yana can gun kakan shi anyi rabon kayan buki masu armashi da tsada aka saka acikin ko wani jakkan da za,a ba mutum.
Zuwa yamma Nafisa suka shigo gidan da mutanen ta nan kallo ya koma kan su kuma sai gulma ke tashi a kan su.
Kuryan daki suka kutso anan muka zauna dasu wanda hakan yai masu dadi sosai don ni bani nuna masu kyama ko kadan.
Don nasan Allah ne ya jarabce su da yin hakan kuma muna rokon Allah ya yaye masu hakan a rayuwan su.
Basu dade da shigowa ba sai ga tawagan Rahama da kayen ta sun kai su goma suma dai sai a hankali wallahi.
Su ko suna ganin burgewa ne hakan suna jaye da troler har kuryan dakina inda nake suka kutso kai.
Sai dai suna shigowa ganin tawagar Nafisa tab a dakin yasa jikin su yai sanyi akan wulkancin da suka kullo suzo suyi a gidan.
Don sun san gaba da gaban ta wa yan nan yan daban da suka gani sun cuna masu gurin iskanci sau milayan albarka .
Don su basu tsoron ta kwana balle ta bare masu ko kadan sun saba da casa juna a daba ko.
Daya daga cikin su tace ga kayan yaron Rahama nan takawo mai aita saka mai har kala ashirin ba dai.
Daga cikin yan daban Nafisa daya ta cabe da cewa kai amma kuma ta makara don tasamu har uwar yaro da uban yaro sun saya mai kaya na kasan waje masu tsada ba yar sokoto central ba.
Sai ta koma da abinta ko ta samu cikin dangi a basu su suka don shi wanan yaro ko ta sunan shi mai tsadane balle suturan shi.
Ke kuma a suwa gayyan na anya waya gaiyato ki nan yar daba mai arna dubu.
Tace yanzu dani dake aga wanda aka gaiyato wanda ke tsaye ko wanda ke zaune kafin ai haka ashe Nafisa ta mike sai ji mukayi kawai ta kwashe Rahama dake gefe tsaye da mari kayau.
Abin nema ya samu kafin haka su Raiha da Nuriya har sun mike tare da sauran su sai ko daki ya rude da danbe in bakaci bani guri na sudade na bar dakin ina haki nagudu dakin dasu gwago suke zaune.
Take gida ya cika harda maza sunyiwa su Rahama kaca kaca da suturun su duk anyayaga masu shi.
Sadauki yana site din shi mummy takirashi a waya sai gasu gidan yazo a hasale tsawa daya yai masu kowa yaja ya tsaya.
Yace maynene haka wai please may kuke min haka a gidana ne wai wata mata tace muna aha,anin mu na lafiya wai ko yan kungiyar Rahama sukazo muna da fitana duka da zagi da habaici wai gida nasu ne sunzo ne kuma ba,wanda ya usa ya kore su a gidan.
Idon shi ya runtse yana maijin takaici yace ma Sagir dake bayan shi ya kira mai mobil police yace kuma a rufe gida ba inda zasu.
Take tan sanda suka shigo aka kwashe su sai police station aka rufe su kan tuhumar sunkai mai fada a gidan shi sun tayarwa mutane da hankali.
Baba Sani ranan kamar zaiyi hauka gashi ya kira wayan sadauki yafi a kirga amma wayan a kashe take wayoyin shi duk ya kashe su.
Yaje police station ance baza,a bada bellin su ba sai sadauki yazo da kan shi.
Har dare ba wanda yasan inda yake ashe yana can sabon gidan shi da yake ginawa gaba kadan da inda muke duk dai a unguwa daya ne da inda muke yanzu.
Baba Sani yaje gida duk da Baba baida lafiya amma haka yai ta yankar kauna da tashin hankali yana zagin Nafisa da kawayen ta.
Ranan munsha zagi don har dani sai da Baba Sani ya hada ya zage a cikin fadan shi da yakeyi.
Har yayi ya kare ba wani mataki da za,a dauka don ba,aga sadauki ba sai cikin dare lokacin mutane sun rage ya shigo gidan ya wuce dakin shi ya kwanta bayan ya fadawa masu gadi kada a bude wa kowa gidan.
Baba ya zo da wasu makwabtan shi amma masu gadi suka ki bude mai gida.
Haka ya hakkura ya koma da tarin takaici fam a zuciyar shi ba yadda zaiyi.
Asuban farko yazo gidan da masifa inda yake shiga ba nan yake fita ba yana fadin don sadauki na ganin yana da dan hali shine har yake gani zai iya taka kowa ya zauna lafiya.
Dama ba yau ba yasan cewa shi shedanin yaro ne shiyasa al,amarin shi bai mashi ba.
Duk hayaniyar da yakeyi bai san yanayin gidan bai bari a sani ba a banza yake ihun shi a,waje.
Na shirya a cikin wani dogon riga tare da daukan Amir a kafadana muka nufi dakin shi mu gaida shi.
Na samay shi a tsaye yana saka aninin dogon rigar shirt da ya saka a jikin shi jin shigowan mu yasa shi juyowa gare mu yana murmushi a fuskan shi.
Na karaso inda yake tsaye nace yaya na ina kwana yace maman Amir an tashi lafiya ko yaya gajiyan jama,a dai ?
Jama,a sunyi dadi sai dai abinda ba,a,rasa ba kawai da kaje ya dawo na halin taro.
Nace gaskiya yaya jiya banji dadi da kasa a rufe su Rahama ba kuma kai tafiyan ka Baba har dare yana zuwa gidan nan neman ka ba,a ganka ba.
Yace ko yanzu yana a,waje ya tafi can gida jiya ance yaiwa baba tas da mutanen gidan.
Amma kina nufin kinji dadin irin wullakancin da sukazo har cikin gida su sukai min ko ?
Nace ayi hakkuri son kane ya rufe mata ido har ta aikata hakan ba wani abuba.
Kuma aiko banza Rahama yar uwar kace yaya sai hhakkuri kawai wallahi amma basu kyauta ba gaskiya.
Nifa shigowan ta baidamuna sam don a tare na ganku gidan ku daya yar uwan kace Rahama ta jini.
Hannun shi ya mika yana son karban yaron sai bai iya ba don bai kan dauki yaro shi sam.
Zama yayi bakin gado yace min zoki gyara min shi please ban iya daukan yara ni.
Na zauna gap dashi ya tsurawa yaron dake barci nade a ciki a
showel a hannun shi.
Na zauna ina cewa ai yanzu naga zaka fara dauka tunda dai Amir din badani yai kama ba.
Dawa yai kama ya tambayeni cikin dago kan shi yana mai kura min idon shi.
Ina dariya nace ai kaima kasani ni bai biyo ni ba,duk kaine ko yaya sagir ne ko yaya Ahmed oho ?.
Da sauri yace Ahmed kuma Fatima please ki bar hada min yaro na da,wanan mara mutuncin mutum wanda bai san Allah ba.
Nace hakkuri za,ayi yaya tunda ya riga da ya aikata yanzu baba ne abin tausayi wallahi don na san har gobe koda yake haka abin yana damun zuciyar shi.
Yace ai Monday zamu shiga kotu dama zancen ne na suna ya hanani sukuni don naga mutumin da yasai gidan baida mutunci ko kadan wallahi.
Yadda naso mu rabu dashi lafiya hakan baiyuyuwa sai anyi rashin mutunci dashi za,a wanye lafiya.
Don kamar ma da gaiyya ya,sai gidan don Sagir yace min wai yaji yana fadin zai saka a rushe gidan yayi maikatan shimkafa ne a gurin don idon gari gidan yake.
Nace ikon Allah kada Allah ya bashi ikon yin haka a,rayuaan shi da ya barwa mutane abin gori har tarihi.
Nace amma yaya yanzu mama Asiya tayi matukar sanyi sosai sai neman shiri takeyi da mutane.
Ko dana haihuma tare da ita fa muke kwana a,asibiti har aka sallamay ni.
Yace wanan dadin bakin sai tai maku kuda bakusan halinta ba ai kaikayine ya koma kan mashekiya.
Don ni suka so na lalace na aikata hakan uwana tashiga balai Allah ya karw ni.

Ya mike yana fadin barin fita zuwa wajen wa yancan marasa mutuncin inji yaya zamu kare da su.
Nace suwa ke nan fa ?
Yace Rahama da kungiyar ta na yan iska mana da tazo min da fitina gida.
Nace sai anyi hakkuri suma basu zaci cewa al,amarin zai kai haka ba ai, sunzo ne suyi son ransu suyi muna iskanci su tafi.
Sai Allah yafisu suka samu wa yanda suka fisu balai a gidan suka jamay dasu.
Wai ki fada min gaskiyan yadda abin ya faru don in san abin fadi a can.
Tsaba na mayar mashi da komai yadda akayi akai fadan yace ai bari zanyi maganin su don zan masu kashedin shigo min gida watarana ne wallahi.
Nace amaryan naka zakaiwa wanan furucin haka kasan fa itama nan gidan ta ne tana da ikon da zata shigo ko ina take so a gidan.
Harara ya watso min yace a,a kila dai kece zata aura bani ba dai kan don ni wallahi har gobe na tsani mutanen nan marasa mutunci.
Jiya wata matace ra rufe ido take fada min abindaya faru ne haka naso nagane ta amma ban gane taba.
Nace ai matar Atiku mai wanki ne mana matar da kullun take godiya kan taimakon da kaiwa dan ta a baya Aliyu mana.
Yace Allah sarki itace wallahi gar gobe ina son in taimaki yaron ya zama wani abu idan ya girma don na wanke mai wanan bakin tabon a rayuwan shi.
Allah ya nufa nace mashi yace sai ya dawo nai mashi Allah ys tsare yafice daga gidan.

Yana fita ya samu mutane cinjim a kofan gidan shi iyayen yaran da Rahama ta, gaiyyato su rako ta nan suka shiga bashi hakkuri akan ya jaye maganan don yan sanda sunce wai kotu za,a kaisu.
Sai ga Baba sani da motar shi ko kashe motar baiyi ba da kyau yafito cike da masifa babban riga yana jan kasa.
Yace ashe baka da mutunci haka sadauki ban sani ba kai har ka isa kasaka a kule muna yara su kwana a caji office.
Sadauki yai murmushi yace amma Baba kaji irin rashin mutuncin da,suka zo gidana sukayi ko?
Kai har ina gidan yake da kakewa mutane wanan wulakancin haka kan shi akan wanan yar matsiyantar matar taka kake son wullakanta muna yara kamar wata mai asalin kwarai can.
Baba maganan ya tsaya iya ni daku kada ka hada da yar mutane please ?
Ko nima zaka saka a kulleni ne idan na zageta din ?
Bai mai magana ba don yasan dalili yake nema kawai ya shiga motar shi ya nufi police station din inda ya samu su Rahama sun ji jiki sosai dan kwana dayan da sukayi a rufe.
Nan yasaka akai masu warning akan kada su kara shiga mai gida gaba dayan su idan ba haka ba zai yi karan su again a kulle su kuma.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,


IDAN KIN BIYA KIKA,TURAWA WANDA BAI BIYA BA DAKE DA ALLAH,,,

Munyi arbain yaro yayi matukar kyau dashi gashi sai kara murjewa yakeyi yana kara haske da kiba sosai.
Ga sadauki yanzu sai ahari,a akan gidan su sukeyi da dan masani wanda yaja sosai a kan zancen.
Anyi nasaran kama yaya Ahmed an kulle shi a cewar Baba ma kada a sake shi a rufe shi don matsayin shi daya da barawo a gare shi.
Tunda gidan shi ya shigo mai ta dakin shi ta baya ya fasa ya shiga ya kwashe mai duk wani abin kwarai nashi a lokacin.
Don haka sata yazo yai mai a gida kuma ya kwashe mai takardu da ga baya yazo ya kwace mai gida.
Hankalin mama Asiya yai matukar tashi sosai jin irin hukuncin da baba yace a yankewa yaya Ahamed.
Sai gata a gidan mu tunda farar safiya ta sallama muna lokacin na gama shiri na tsab nayi kwalliya Iyya tayi wa Amir wanka takawo shi ya sha nono.
Don shan nono kawai ke kawo Amir gurina da ya gama kuma zata goya shi sai idan ya falka ko tana daki su kwanta tare.
Haka nake fita na barsu zuwa school don ina semester karshe yanzu ga karatuna.
Sallaman mama yasa mu fitowa daga dakina ina rike da yaro a hannu ina bashi nono muka fito falon.
Mama Asiya ce zaune saman kujera ta rafka uban tagumi cikin damuwa take.
Nace a,a mama sannu da zuwa ashe kece mama shine kika zauna a falo baki shigo ba.
Tace Fatima ba zama nazo ba mijinki na zo gani Allah dai yasa yana gida bai fita ba ?
Nace yana nan mama tace yi min magana dashi don Allah Fatima kice gurin shi nazo.
Na nufi dakin tabini da kallon yadda na koma wata fresh dani sosai kamar ba Bintu ba can.
Yana kwance ya kifa ciki yana barci na,shigo dakin na samay shi a hakan .
Sai da na zauna bakin gado na dan fara taba shi a hankali ya bude idon shi ya dago kai yana kallo na.
Ina zaune ina kallon shi ina gyara yaron a nono nace ina kwana ina dare da fatan an tashi lafiya ?
Ya dan goga kan shi a filo ya gyara mirginowa yana kallon mu yace my friend har ja tashi kai wanka ni ina kwance ko ?
Nace tuni mukai wanka kaima ka tashi kai wanka sai ka karya sai dai mama tana falo tana jiran ka.
Yace mama tare da kallon agogon bangon dakin shi da ido yace wata maman ke nan ke jira na kuma ?
Nace mama Asiya ce mana Asiya kuma may kuma ya kawo ta nan gidan ko dama takanzo ne wai ?
Nace gaskiya bata taba zuwa haka ba babu wani dalili sai yau kawai tazo ya ja tsaki ya mike zaune da kyau sai da ya shiga bandaki yai brush yafito daga dakin.
Ya karbi Amir a hannu na ya fice da shi ina bayan ta jin motsin fitowar mu daga dakin ta dan gyara zama da kyau tana cewa kafitu Sadauki

Please Login or Register in order to submit comment