Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

gefe a bango ina kallon kafan shi dake cikin socks.
Waya na yai ruri na dauka nace gani tafe ai yanzu don Allah.
Bata hanya mana ta wuce ko kuma wani sallon muguntane haka kace kuma ga abinda tai maka yanzu.
A dan tsorace da jin muryan mama ya ja baya kadan nazo na wuce shi har hijjab dina yana gugan jikin shi.
Nan na fita na barsu na samu Usman zaune a motan shi ya saka kida na gaishe shi tare da tambayan shi yaya aiki?
Yai murmushi yace aiki Alhamdullahi daga can nake nace bari na biyo na gan ki kafin na isa gida don idan na shiga gida yau da wuya na fito kuma again.
Na dan dariya har hakora na suka fito nace anty na itama zata nada nata kambun ke nan ko?
Shima dariya yayi yace ai Nabila matsalace wallahi an samu wanda ya kai mata gulman ina neman ki, kuma tace min wai daga gidan nan aka fada mata.
Nace ai ko sai ka bari kada ku samu matsala da matar ka yace akan ta zan daina son abinda nake so sai dai ta san nayi.
Ban san sun fito ba sai da naji yace ikon Allah dama U F a gidan nan yake ne shine har na dan juya naga suna fitowa daga cikin gida.
Nace mai eh ai yayana ne a gurin maman shi nake zaune.
Kafin su karaso har ya fito daga motan shi naga ya nufe su yana dariya ya mika masu hannu.
Sai dai shi gogan barka kawai yace mai ya zagaya ya shiga mota hakan bai ma Usman dadi ba harni din ma dake tsaye ina kallon su.
Ban san gulman da yakaini daga ido na kalleshi ba sai ganin shi nayi ya sha mur fuskan shi tamau yai min alama da zaki fadi da ido kawai.
Ko da Usman ya dawo yake ce min ashe ko abinda ake fadi akan dan uwanki da gaske ne kuwa ?
Ance ba ruwan shimana amma ni sai naga ya wani basar dani ko don yagan ni da kaunar shine yakawo hakan.
Nace ai ba ruwan shi kila dai akwai abindaya bata mashi rai ne kawai yace Allah yasa ba don ni bane dai ?
Yana nan har gap da magariba mukai sallama ya wuce abin shi ni kuma na ahiga gida ina tunanen halin yan gidan mu har wa ya gane gidan su Usman yaje ya fada wa matar shi magana.
Suna barin gurin batare da ya kallo Bashar ba yace waye wanan guy din , Bashar ?
Wa wai wanda ke tare da Fatima yace shi mana a ina yake ne ?
Dan nan garin ne mana ni nasan shi da dadewa ina ganin kaman aikin banki yakeyi ne ai.
Sai dai guy din dan karyane tun dana san shi bai aje kan shi kusa ba akwai shi da karya sosai wallahi.
Zai iya kashe wa mace kudi sosai don ta so shi amma yana da aure don gaskiya na san na taba sanin yai aure a baya.
Tsuki yaja yace, wanan yarinyar ko ina take kwaso maza haka kamar ita kafai ce budur wa a gidan nan?
Dariya Bashar yayi yace kaida may kake nufi ne wai wanan tsaleliyar budurwa haka wa zai ganta ya barta ko don ma dai tana da kamun kai bata da rawan kai ai da yanzu kofan gidan ku ya cika da samari.
Da sauri yace wallahi da naci uban ta kuwa Allah.
Dariya sisai Bashar yake mashi yace oho dai indai mutum yace girman kaine ai gurin zurfin cikin tsiya sai asha mutum a banza.
Kafito fili kawai kabada kai bori ya hau ka tsaya kana wa mutane kwanaye kwanayen banza haka.
Wallahi Bassh kana son ja min raini Allah ni irin kane da zan bayar da kaina ga karamar yarinya haka nagane a gurin wanan yarinyar karamar yar kauye ban da tarin kauyanci.
Fatima ce yarinya U F ?
Ba yarinya bace tsohuwa ce ke nan ko ?
Sai ja tsuki tare da kawar da kan shi ga titi sai dai cikin zuciyar shi tunane yake yadda mazan yanzu basu jin kunyan hada halaka da yara kanana haka?
Wai to kai ban san yaya kake daukan kanka ba fa wanda ko 28 bai cika ba kana ta daukan kanka wani old man can.
A ganin ka ba ni kan ai nasan yanzu nakai yadda baka tsanmani don kagan ni ban girma ko ?
Dariya Bashar yai mashi yake ce mashi niko nafi kowa sanin yaya kake ai ka girmi duniya.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,


DUK WACE TA TURA MIN NOVEL GA WANDA BAI BIYA BA ALLAH YA SAKA MIN AKAN MAI SHI,,,,,



Fuskan ta a daure ta watso min harara tace shige ciki da wanan wasan banzan naku, simi simi nabi gefenta na shige cikin gida.
Binshi tayi da kallon mamaki shiko ko a jikin shi saima gyara hannun rigan shi yakeyi kawai.
Mama batai mashi magana ba sai kutawan da tayi ta shige ciki yace a fili i will dealing with you silly girl kawai.
Duk nabi na takura kaina sai jira nake mama tai min maganan amma shiru babu zancen haka yasa na sake gaba daya.
Rayuwa tana ci gaba yayin da takuran da sadauki ke min bai fasa ba don duk wani aikin shi nice zai saka komai wahalan aikin kuwa.
Zancen Maryam da Bashar har ya kawo gida yanzu don iyayyen shi sunzo gurin Baba.
Sadauki sai da ya dauki zafi sosai da Bashar har ya gaji ya sake don kan shi don Bashar din ya nuna mashi halin ko in kula ga yadda yake nuna mashi .
Halin zaman kishi na gidan su mama yana nan daram bai gushe ba don sai da suka samu mahaifiyan Bashar da cewa don may zata yarda ta hada zuria da wa yan nan mutane masu jinin tsiya fakirai masu gadon tsiya.
Inba yanzun ba da saudauki ya samu abakin may Hauwa,u take a gidan wace bata iya mayar da taro sisi zuciya ya mutu mata.
Amma dai yanzu ai Alhamdullahi ko don dama azziki ai gida biyu ne ko kai kayi ko danka yi ?
Mahaifiyar Bashar ce take tambayan su da hakan tace ai shi arzikin da yafi na iyayye dadi don zaka koma tankar basarake ne.
Baku jin ance bayan wuya sai dadi ba, dama cewa kukayi yarinyar bata da halin mutunci ne kila da sai na duba.
Amma Alhamdullahi, na zauna da yaran nasan halinsu don haka aure ne idan Allah yayi a tsakanin su nafi kowafarin cikin hada zuria da kamilan yara irin zurian maijidda a duniya.
Sai kuma suka fara cacan baki wai sun gane dama,kwadai ne kawai ya kai Bashar ga maryam don dan abinda yake samu ga,sadauki din.
Dama sun sani ai don haka ya raba shi da kowa nashi ya manne mashi kamar cingun.
Da,Bashar ya dawo ake fada mashi bai nuna bacin ranshi ba don yasan zasu iya hiya da hakan ma.
Amma yana barin gida direct kasuwa ya nufa gurin Baba ya fada mashi komai yace ai masu Umma iyaka dashi da uwanshi.
Ran Baba yai matukar baci sosai haka yasa shi dawowa gida a lokacin yai sa,a basu jima da dawowa daga gantalin su ba ke nan.
Ganin Baba gida ba lokacin dawowan shi ke nan ba yasa kowa mamakin ganin shi cikin wanan lokacin.
Gaba dayan su ya kirasu basuyi tsanmanin zancen bane sai da Baba ya tambaye su da cewa Atika ke da Asiya ina kuka tafi ne yau ?
Wana ta dubi waccan suka fara a tsakanin su sai umma ce yar gadara tace asibiti muka shi gaida Hanse yace abisa umurnin wa kuka tafi?
Yace bama wanan ba don na riga na barku ga Allah kan fitan da kuke yi bada izini na ba a gidan nan.
May ya kaiku gidan marigayi salisu mai engine ?
Da mamaki mama ta dago tana kallon su sai hjy kubura ce tace gidan Alhaji salisu mai engine ai gidan su Bashar din da zai auri mayam ke nan mana.
Yace eh can din?
Shiru sukayi sai Umma tace da muka je ance maka munyi wani abin ne acan.
Yace mai zaihana kuyi tunda shi ya kaiku yace da farko da Sani ya fada min kuka soke zancen auren sadauki da Rahama ban yarda ba sai yau din nan nayar da da hakan don kaidin ku ya wuce yadda nake tsamanin ku.
Na dauka duk wani "da da ya fito daga tsatsona kamar kuma dan kune a gidan nan kuma.
Ya girgiza kai yace ashe nayi kuskuren yin wanan tunanen a kanku don ku din nan ba abokan zaman alheri bane a gareni tun da har kuka, iya wanke kafan ku kuka tafi soke auren yar yaruwan ku.
Salati suka saka suna fadin yaushe akai haka su sheri a ka kulla masu kawai daga sun tafi, gaida mahaifiyan shi kawai.
Yace to yanzun dai Bashar ya samayni ya roke ni nai maku kashedi akan gidan su da uwarshi don haka duk wacce ta kara shiga harkan shi duk abinda yai mata ita tajawa kan ta tunda daini bada izzina na kuke fita ba gidan nan.
Abin bakin ciki da rashin sanin ciwon kai ace kun fi son yaran nan suyi ta zama a gida suna shashanci kamar yadda diyan ku sakeyi suna bata min suna a gari.
Abinda Nafisa keyi a garin nan waye zai aure ta a haka da ita watsatsa yau itace wancan party gobe itace gidan mashaya gata kuma gata wai a kungiyan yan madigo a gari.
Da sauri Umma tace kan yar ka yar gwal kada ka kulkawa diyata sheri don da baifi daba a duniya.
Yace sheri kan Atika aike kika kulawa kanki ke da baki kaunan dan wani da karuwa kina ganin Allah zaibar naki yadda kike so ne ke ?
Ran Umma ya baci kan bankada asirin Nafisa da ya yi a gaban kishiyoyin ta nan ta hau sababi tana borin kunya.
Yace magana daya ya rage gareku yanzu shine daga mazan har matan duk kowa ta fito da miji tai aure su bar min gida na hakana na huta da fitina haka.
Ya girgiza kai cikin takaici jin borin kunyan da Umma ke tayi wai bai kaunan ta ita da diyan ta agidan dabakin shi yake kulla masu Sheri don ya gyara zuciyar masoyan shi.
Shidai yafita bayan yai masu warning da gargadi mai karfi kan duk wace ta kara fita bada izinin shi ba har yaji sai tabar mashi gidan shi.
Maji ta dawo dakin ta cike da mamakin wanan irin bakin jinin da mutanen nan suke gwada mata haka.
Nan take fadawa yaran abinda su Umma sukajeyi gidan su Bashar daga inda nake nace ai sun kai karshen gulma indai gidan su Bashar ne Inna ce ko Bashar din ai suna daidai da su.
Waya mama ta dauka takira Inna na ta kwashe duk yadda akayi ta fada mata mama tace Allah ya kyauta nabar su ga Allah.
Buki za,ayi a family house din su Baba haka yasa yanzu su mama basu zama a gida sosai don suna zuwa can gidan gurin aikin bukin da za,ayi.
Shima yaya sadauki baya zama a gida sosai don ina ga,akwai wani aiki da yasha mashi gaban shi don sai dare yake dawowa gida.
Yauma da dare ya shigo har lokacin su mama basu dawo gidan ba suna can cikin gari.
Daganin shi a gajiye yake sai dai kuma alama ya nuna min yana cikin halin shi don ya dan sha a lokacin.
Maryam waya take da,wata kawarta Amira tana kallon wani season film a tv bayan an gaisa dashi kowa ya juya gur8n harkokin shi.
Ni dake zaune da litrafi ina karantawa na mike sai gaban shi na ce mashi a hankali control yourself mr.
Da sauri ya dago jajaye idanuwan shi ya watso su a kai na gyada kai nace ka natsu kokabar falon nan tun mama bata shigo ba.
Mamaki takaici haushi ya kama shi a lokaci guda yace cikin tsawa ke kin raina ni ko dayawa ?
Easy mr behavour self da sauri maryam ta dago ta kalle mu nace akawo maka abincib ne.
Ban sani ba ya fadi a fusace sai ya mike cikin rangaji ya bar falon ran shi a bace wanan yarinyar kodai aljannace wai ita ?
Maryam na kallona na gyada mata kai alaman ya sha yau tace oh Allah wanan masifa da may yai kama.
Mikewa tayi tabi bayan shi, sai nima na biyo su yana tsaye ya dafa bangon dakin shi bai shiga ba yaji muryam maryam tana fadin haba yaya sadauki.
Da sauri ya juyo takaraso tana fadin kada kaga laifin Bintu gaskiya take fada maka tsawa ya daga mata lokacin nakaraso gurin.
Ya bini da wani mugun harara yace sai na karya ki a gidan nan wallahi yar iska mai balain sa idon tsiya kawai.
Sai kuma yai shiru tare da kyatafa kawai ya dafa bango kan shi ya dukar a kasa.
Nace yaya kayi hakkuri bani son mama ta fahince ka a hakane wata rana kaji may likita ya fadi a kanta.
A guji bata mata rai don dazara akai mistake watara zuciyan ya buga a lokaci guda za,a iya rasata gaba daya.
Yaya kana son sanadin ka ace mahaifiyan ka ta rasa ranta kan bacin ran ka ne ko yaya ?
Maimakon yai cikin mu da masifan daya fara yadda nai tsanmani sai naga ya dukar dakan shi a kasa.
Ikon Allah sai Allah yau gani mukayi yata sadauki yana kuka kuka kuma mai ban tausayi.
Yace maryam bani sha a ko ina sai ina garin nan i don't know why nakejin irin haka kawai a garin nan ?
Idan ina garin nan in basha ba bana jin dadi rayuwana sam wallahi sai na dinga jin kaman zan kama da,wutane.
Amma kudai tayani addua kawai Allah ya kawo min agaji ga halin nan.
Bana son ace sanadina uwata ta samu matsala a rayuwan ta ko kadan bani jin dadin hakan idan na tuna.
Kuka ne ya dan fi karfin shi maimakon mu bashi hakkuri sai nima nafara kukan abinda yasa Maryann itama kuka ke nan lokaci guda.
No no ku bar kuka please zanyi kokari naga cewa na daina hakan insha Allahu.
Nace yaya idan ka fara jin haka don Allah ka dinga nafila kana kai kukan ka ga Allah don ka samu sa,idan jin hakan da kake yi.
Ya dago ya kalle ni ina makure a bango kaman zaiyi magana sai kuma yai shiru, ya dade a haka yace ku shiga gida kada wani yazo ya samay ku anan.
Har na juya nace abinci fa yaya yace No kibar shi kawai I am OK.
Kuka sosai maryam tayi bayan shigan mu gida da kyat na samu na lalashe ta har tai shiru tana tausayawa halin da dan uwan ta yake ciki.
Bintu fada min yaya kike gane yaya yasha ne wai ?
Nai murmushi na ce da farko idan kinga ya shigo da glass a idon shi to yasha sosai ke nan.
Idan kuma kin gashi ya shigo ya zauna yai shiru kaman akwai abi dake damun shi to abin yadan fara sake shine hakanan bai son yawan magana sai kasala kawai yake ji.
Sai kuma da zaran kinga yana bukatan abinci a gagauce to abinda yasha ya fita kan shi ke nan sai kiga yana jin yunwa sosai.
Zakiga yana shiru shiru sometimes to yana cikin dan maye ne zai dinga zama kaman wani salihi can dashi.
Bintu baki ganin kaman asirin da akace su Umma sunyi mashi a cikin gidan nan yake kuma kilama a dakin shine ko makamancin haka ?
Nace sanin gaibu sai lillahi anty amma hakan kuma fa magana ce sosai.
Tace in hakane yabar gidan nan ya koma gidan shi mana da zama zai fi mashi sauki nake gani.
Anty yaya zaibar gida baiyi aure ba?
Ke kinga alaman aure a gaban shine yanzu Bintu ?
Nace ai irin su mata basu gaban su anty duk matar da zai aura matsayin baibar wanan rayuwan ba sai tayi hakkuri wallahi.
Don bata gaban shi idan yasha kuma sai dai yai ta tabara yana zubar da kiman shi a idon ta da jama,an da suke tare.
Wai ke ina kika san wanan halaiyar tasu ne haka Bintu ?
Murmushin takaici nayi nace a gurin mijin mahaifiyata mashayine shima amma shi irin shan nan na yan kauye yakeyi mara fasali.
Nan nai ta bata labari na yadda mamana take hakkuri tana kuma nema mashi maganin hakan ?
Nisawa tayi tace shiyasa lokacin da su Baba Sani suka hana yarsu daga baya banji haushin su ba wallahi.
Don yau babu wanda zaiso ace nashi na cikin fitina ko tashin hankali haka ai ?

****** ********* ******
Washegari Mama ta tilsata mu kan sai mun tafi gurin buki don ayi kamun amare damu tana fada take cewa, ban san may yasa baku son yin zumunci ba wallahi.
Zumunci da kuke gani ba abin wasa bane wallahi don igiyace mai kai mutum aljanna idan Allah yaso.
Amma rashi sanin darajan shi yasa kuke sakaci da shi alhalin gaku Allah ya baku yan uwa bila,adadin a gari babu gidan wanda kuke zuwa kullun kuna kulle a gida kaman kayan wanki.
Ba don mun so ba muka fara shiri bayan sallah azuhar zuwa gurin sa lalain yan uwan su da za,ayi a family house din su na diyan kannen baban su.
Ga ba dayan mu dogayen riguna muka saka muka daura dan kwalaiyan su akawunan mu.
Shigar tai matukar karban mu sai dai matsala motar da zata kaimu ce babu a lokacin haka yasa yaya sadauki yace mu bari ya kaimu da Amirah tai mashi magana.
Amirah ce agaba tare dashi mu muna baya a zaune sai dai ban san yaya akayi na zauna a setin mirror shi ba na gaba.
Maryam ke fadi wai yau kan sai mun sha surutu a gurin mutane yaushe rabon da naje gidan nan ni.
Amirah tace ni wallahi ba,son zuwa ne banyi ba yadda ake damun mutum yaushe zaiyi aure yake damuna.
Daga inda nake zaune nace kai mutane akwaisu da daukan wa rai shifa aure kamar rayuwa yake idan ya tashi koba shiri sai anyi shi haka ma rabuwan shi idan yazo ko bashiri sai anyi shi.
Dago kan da zanyi naci gaba da magana muka hada ido dashi ta glass din motan yadda naga idanuwan shi sai naji gaba na ya fadi daga haka naja bakina nai shiru ban kara magana ba don duk na dago kai dashi nake arba sai ma na daina daga kan nawa kawai.
Tun a kwanan gidan muka fara ganin dandazon motacin mutane da sukazo gurin kamun.
Wata mata tazo da motar ta shige gaban mu maryam tace shegiya mu akewa kurin mota mima watarana insha Allahu ki gan mu da namu.
Nace kai anty kin rage mata kaya bata masan kinayi ba ita, Allah Bintu inason naganni da mota ina ja wallahi.
Nace in Allah ya nufi ki ja sai ki gan ki dashi kuwa ai tace wai da su Umma sun mutu ranan.
Nace su kuma ai zaman su ke nan hassada wallahi basu ko tsoron haduwan su da Allah.
Allah suka sani aida basuje gidan su Bashar suke auren maryam ba inji Amirah.
Da sauri ya juya gareta yace kamar yaya wai har muka isa inda zamu sauka tana mashi bayani haka yasa bamu fito daga motan ba sai da tagama mai bayanin komai yadda akayi.
Mutanen dake tsatsaye daga waje sun matsu sugs ko suwaye a wanan haddadiyar motatar haka ga shi na cikin motan basu fito ba.
Sai da suka gama magana ya bude muna tare da tambayan mu karfe nawa zai dawo ya dauke mu Amirah tace shidda daudai yaya.
Nice na fara sako farin kafa na a waje daga gefen da nake zauna sai wata tace dama nasan wasu special ne daganin wanan uban motan haka sai gidan gwauna, muna fitowa ashe su Rahaman shi ce a tsatsaye nan shima ya hango su,
Kiran mu yayi muka dawo gare shi daya bayan daya yake muna magana kowace tana juyowa da dariya ganin ya gama magana da kannen shi yasa nima na juya zan wuce nabisu sai yace Fatima nace naam yaya yace zo nan na karasa gaban shi.
Yace don Allah kada kiyi masu kayanci agurin nan kiga dai duk ido akanku yake.
Maganan shi ce tasani dariya a lokaci guda wanda mutanen dake gurin suna zaton ko wani maganan soyayyane yake fada min hakanan.
Yana fadin haka yaja mota yana murmushi duk suka bishi da idanuwan su caaaa kowa na son ace itace ta mallaki aana haddaden guy din mai kyaun dan maci ji.
Abokan Rahama da yan uwanta ke ce mata kai amma gaskiya kinyi hasaran miji ko dai wanan yarinyance zai aura ne?
Tace a kufule kamar
yaya zai aureta anfada maku anfasa zancen namu dashi ne halan .
Nan suka shiga gaisawa da mutane yan uwa da abokan arziki ana ta masu sheri don yau bukin gidan su ne yasa su fitowa.
Buki yayi buki duk guri ya kicimay da kida don an fito da amare su hudu ne gaba dayan su a filin.
Muna tsaye gefe sai kallon amaren muke gwananin ban sha,awa nace anty Allah ya nuna muna naku muzo musha bidiri muma.
Ameen ke dai Bintu inji maryam itako Amirah cewa tayi nifa duk wanan abubuwan basu damay ni ba fa.
Nace nima nafison in zanyi aure aimin walima haddade wallahi duk yafi wana gwatsale gwatselen da mata da yara keyi.
Ji mukayi wai ana kiran dagin amaryam su Amirah su fito suyi rawa a fili basu so fita ba kuma banyi tsanmanin zasu jani tare dasu ba sai ji nayi maryam ta jawo hannu mun shiga fili tare ban iya rawa ba don ban ma,taba yi ba don haka takawa kawai nake yi a hankali.
Kaina a duke naga su maryam su falle jakkan suna min liki take guri ya hau ihu da sowa sai tambaya mutane keyi wacece ita da suke mata likin kudi haka?
Komai namu a gurin a natse muke abin mu cikin nuna sanin ciwon kai da kuma tarbiya.
Muna gefe mu kaji guri ya kaure da sowa maryam ke tambayan ko su waye wata tace wai ance wasu mashaya ne yan uwan su amaryan yan mata suka zowa kawarsu kara.
Innalillahi wacece kuma maryam taja min hannu Anty Amirah na gaba muka leka Nafisa ce da kawayen ta suke wani irin rawa gasu sunyi shega zakace akwatawan ghana ne su guri ya rude da sowa masu tir da Allah waddai suka shiga bakin su.
Daganin su a buge suke don rawan ba rawan kai sake bane har gaban samarin da suka shigo suke shigewa.
Kiran wayan da sadauki yaiwa Amirah yasa mu saurin barin gurin muka fice a filin

Please Login or Register in order to submit comment