Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

saiga wayan kabir yana fada min suna lagos yanzun suka sauka da safe zai karasa gida.
Mundan jima muna fira sai na kwanta da farinciki a raina.
Mafarkin danayine yasa na tashi ina sallah kafin ai kiran sallah tare da rokon Allah sauki koma maye.
Da safe na dan makara nai sallah nai wanka a gaban mirro na kalli irin yadda nasha gyara na canza gaba daya kamar bani bace Bintu.
Wayan Kabir ne ya shigo yana fada min zasu wuce zuwa Abuja nai mashi Allah ya kai su lafiya nan ma sai da ya dan taba min yan maganganun soyayya sosai mukai sallama dashi.
Ga abin karyawa a gaba sai hira su Amirah keyi amma na kasaci a lokacin.
Mama tace badai auren ne ya saki tunane ba har kike kallon abinci haka a gaban ki.
Nai murmushi nace kai haba mama aure kuma bayan gaki ?
Tace gani ina gadai Kabir dinki ko ?
Amirah tace da ciwon kanki ba inji mama Sare da tace haka ranan.
Nace ni ai basu gabana Anty don duk fitanan matar shi bai taba daga min hankali ba ni.
Hajiya Kubura ta shigo da manyan ledoji guda uku nan muka shiga gaida ita.
Tace hjy maijidda ni dai ga dan nawa gudun mawar ba yawa sai ayi hakkuri dashi.
Kai hjy harda dawi niya haka takarba tana budewa ledan farko kuloline set har da flask din su sai dayan ledan turaren wutane masu kyau da kamshi sosai.
Dayan kuma kayan matane aka hada masu tsadan gaske a cikin wasu robobi masu kyau.
Godiya sosai mama tai mata su ka dan taba hira kan bukin tana cewa insha Allahu da ita za,a tafi kauyen mu gurin daurin aure.
Mama tai mata godiya tace kai haba ai shine zama tare din.
Wayasan inda zaici albarkacin yaro shima watarana Bintu ai mutum ce sosai wallahi.
Zata fita suka hade da saudauki dake shigowa a lokacin nan suka gausa dashi tafice daga falon.
Yai zaune ragwab saman kujera fuskan shi babu annuri acikin sa sai mama ke cewa may kuma yafaru nagan ka haka ?
Yace wallahi maji yanzun nake jin news wai Jirgi yai accident daga lagos zuwa Abuja da safen nan kuma akwai wani abokina da zai zo Abuja yau nasan yana cikin jirgin.
Da karfi nace Kabir,,,
Nace wayyo Allah na mama wallahi da Kabir a cikin jirgin nan dazun yai min waya gashi zai shiga jirgi zuwa Abuja.
Daga haka kuma ban san may yafaruba again ?
Ganin na tafii suuu, zan fadi yashi tsale daya yakamoni na fada a jikin shi suuu a somay.
Innalillahi don Allah ku taimaka min kubani ruwa mamatake fadin hakana a gigice cikin rudewa.
Su Amira duk sun rude suma tana cewa a bincika mana aji idan dashi a cikin jirgin ko ?
Ke debo muna ruwa a fridge don Allah kin tsaya kina surutun tsiya sadauki ke fadin haka cikin tsawa wa Amirah.
Ana yayyafa min ruwa nai ajiyanzuciya na bude idona da sauri na zabura daga jikin shi nace mama da gaske Kabir ko ?
Tace dagata a bincika inyana cikin jirgin dauko wayanta mu kira shi mugani?
Anyi kira wayan wai yana kashe.
Kara komawa nayi suuu na sumay a jikin shi yace kama nin ita ina zuwa don Allah.
Maji ta karbeni daga jikin shi tace kiramin hjy Kubura maryam.
Sai gasu tare a gigice tana fadin may ya faru maji take fada mata a takaice abinda ya faru.
Salati ta cika tace sai Allah idan bai ciki wallahi ku kunna Tv mugani don Allah.
Suna kunnawa ga jirgin annuno inda yafadi a wani daji ga yan ceto suna ta faman kawo agaji ga jirgin.
Sadauki ya shigo dakin yace bari mu kaita asibiti maji tace gaskiya kan.
Ita da hjy kubura sukazo dani asibiti nan likita yace bari a dan min allura na samu barci a gani.
Hankalin kowa a tashe yake don har Alhaji yazo asibitin da wayana sukai amfani gurin kiran matanshi dana rubutawa yaya babba.
Wayan na rigin ba,a dauka ba sai gap da zai tsinke ne wani dan yaro ya dauka yana fadin.
Maman bata nan yanzu akazo aka kwashe wai baban mu yayi hatsarin jirgi sun mutu.
Salati suka saka daga inda yake yakai kallon shi gareni ina kwance sharkaf kamar gawa sai numfashin da nakeyi kawai a lokacin.
Sadauki ne ya fara ganin sunayen wa yanda ke cikin jirgin sunan Kabir ne na ashirin da biyar daga jerin sunayen list din wa yanda abin ya faru dasu.
Kuma babu wanda ya tsira daga jirgin duk wanda ke ciki ya mutu a jirgin.
Ban falka ba sai da la,asar na dan bude idona a hankali nake bin dakin da kallo sai dai ban fahinci inda nake ba sai muryan mama naji tana fadin.
Fatima kin tashi ne sai abinda ya faru ya fara dawo min arai a hankali wasu hawaye suka fara dan silalo min a hankali daga idona.
Dafani mama tayi tana fadin Fatima kiyi hakkuri kinji duk mairai mamaci duk wanda lokacin shi yayi tafiya zaiyi.
Allah baiyi Kabir mijin ki bane, sai kiyi hakkuri kibarwa Allah .
Allah da ya halicce shi yafi mu son shi ya karbi abinshi a lokacin da yaso.
Nace a hankali cikin wani murya mai ban tausayi ,mama Kabir ya mutu ko ?
Tace Fatima sai dai hakkuri Kabir yariga mu gidan gaskiya.
A hankali na fara rera kuka mama tana dan buga min baya tana fadin kiyi hakkuri kin ji Fatima.
Shi yanzu adduan mu yafiso da wanan kukan da kikeyi.
Kubarta tayi kukan don shine zai dan sa ta samu relief.
Nai kuka sosai na wani lokaci can na mike zaune da sauri suke fadin ina zaki kuma,?
Nace sallah zanyi mama naga kamar azahar tayi mamatace sai dai la,asar yanzu kan don har munyi sallah mu.
Bayan nayi sallah na zauna gurin ina addua sai kuma na barke da wani irin kuka gwanin ban tausayi dani.
Kiyi hakkuri suke ta fada min shigowan babane yana fadin ashe ta falka Fatima sannu kinji.
Kiyi hakkuri haka Allah ya nufa dake kada ki kara wanan rudewa ki zama musulma mai imani da duk irin kaddaran da Allah ya kawo maki a rayuwan ki.
Mama taso a sallamay ni amma sai Baba da sadauki sukace abarni harda safe aga yadda jikin nawa yake sai a sallamay ni.
Washegari ganin na samu sauki sosai sai dai ban magana da kowa don wani iri nake ji kamar zan shude.
Mun dawo gida inajin ana fadin wai ance a garinsu za ai sadakan ukun shi.
Baba ya shirya tafiya inda zamu ai sadakan uku damu inji Baba.
Haka yasa sadauki ya shiya don tafiyan yaso zuwa gurin mutuwan abokin shi duk daba musulmi bane amma saboda tafiyan mu yace sai an dawo ya wuce.
Motoci uku muka kama hanya dashi har da hajiya kubura da mama Asiya umma tace wai bata jin dadin jikin ta suka barta gida.
Muna isa tun daga nesa muka hango taron mutane a kofan gidan su Kabir, din haka ya kara sani sabon kuka sosai da kyat mama ta samu nai shiru suna min fadan na natsu na daina kuka.
Muna fitowa idanuwan mutane caaa akan mu nan aka fara fadin Allah sarki ga su Bintu nan sun iso
Nan kowa ya fara fadin Allahu akbar Allah bai nufi a zarga aure a tsakanin su ba haka ya kasance.
Sai gaisuwa ake muna nan muka shiga cikin gida a dakin mahaifiyan shi muka shiga.
Mutane sukayo caaa zuwa dakin don ganina ina saye da hijjab amma duk da haka mutum zai iya gani kwaliyan amarcin da akai min a jikina.
Mahaifiyan shi kamilar dattijuwa tana zaune da tasbaha a hannun ta mu kai mata gaisuwa ni dai ban iya magana ba don kukan da yaci karfina a lokacin.
Tace Fatima haka Allah ya nufa tsakanin ki da yaron nan Allah bai nufi akwai zaman aure a tsakanin ku ba.
Nan kuka na ya fito fili mutanen dakin suna fadin kiyi hakkuri kinji Allah yabaki wani wanda yafishi.
Sai naji an rikoni tabaya ana kuka Fatima Kabir ya tafi ya barmu Fatima.
Kabir ya tafi yana mutuwan son ki a ranshi kullun yana min nasiha akan narike ki amana idan kinshigo mu zauna lafiya amma Allah bai nufa ba Fatima.
Sai muka sa kuka nida ita duk da ban dago naga fuskanta ba.
Hakkuri aje tabamu ana muna nasiha sosai mai kashe jiki.
Nan mukejin ana fafin wai shi ko gawan shi ba,a gani ba sai alkur,anin shi da tasbaha da agogon hannun shi.
Nace Kabir Allah ubangiji ya karbi bakuncin ka.
Kowa ce Amin Bintu kiyi hakkuri kinji haka Allah ya nufa daku.
Can wata tace zoku gausa da dayar matar tashi gata can dayan dakin da yan uwanta.
Ni dasu mama muka shiga dakin mun samay ta tana waya muna gaida ita bata gaisa ba.
Sai mutanen dakin ne suka gaisa damu watake cewa wanan ce dama yarinyar da zai aura din ?
Wace ta rakomu dakin tace itace Wallahi, Allah baiyi aure a tsakani ba.
Mukan ai sheri aka kwaxo muna farar kafa yaja muna hasara.
Kai amma kuwa bakiyi ba wallahi gaki dai kamar mai ilimi saidai ashe baki da tauhidi?
Hajiya kubura ce taba ta amsa da hakan.
Tace banda tauhidi aiku kuna dashi aja muna tsiya ace kada mu fadi.
Kika dai jawa kanki ke da kishi har akan mamaci inji mama Asiya ta karbe.
Kamata yayi asamay ki cikin jimamay ba cikin kishi ba haka kamar ba wace tai rashi haka ba.
Ku tashi mutafi mu gausuwa mukazo maku ba tsiya yakawo mu ba nan.
Mun fita muna jin su suna zage zage nace a raina ai in sakwatawa kuke kun hadu da mama da hjya kubura a raina.
Bamu dadeba su baba sukace mu fito nan maji ke fadawa mahaifiyar shi cewa za a aiko da kayan lefen da yai min.
Ko yanzu don anzo gaisuwane yasa ba,a zo dashi ba.
Matan sukace haba haba habadai da zafi haka.
Sai mahaifiyar shi tace wanan ai kyautane tsakanin ta dashi tun yana da rai don haka mun yafe mata ba namu bane rabontane daga gare shi.
Allah ya bata miji nagari idan antashi auren ta a fada muna kada zumunci ya yanke.
Uwargidan Kabir da zamu tafi tayi kuka sosai muka rike juna tana min addua tace zata dinga bugo min waya.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,
.
YA ALLAH DUK WACE TA TURA MIN NOVEL GA,WANDA BAI BIYA BA ALLAH KAI MIN BAKAR ISA AKAN MAISHI YA ALLAH DAMU DA WANDA DUK YA KARANTA A SANADIN TA,,,,


A yammacin da aka,sallamo sadauki baba ya tara duk ilahirin iyalin shi a falon shi yana masu magana a cikin takaici da bakin ciki.
Ku san Nafisa ce ta karshen shigowa falon tana saye cikin wani dogon riga da yai matukar matse mata jikin ta sosai.
Baba ya bita da kallo na tsana da yakaici yace cikin bacin rai ke ina hijjab dinki zaki shigowa mutane kusan tsirara haka.
Tace cikin wani bakon murya mai baiyyana wani sabon al,amari a gareta,
Baba,,, nifa ba tsi, tsira rarra nake ba don a saye nake da, da da riga a jikina.
Ido ya kura mata cikin nazarin ta yace Nafisa kanki daya kuwa yau din nan?
Warassss nake Baba may ka gani kafin yai magana Umma take cewa daga barci take fa take wanan ita shegen haka.
Yace maza jiki sako hijjab dinki na baki minti uku ki dawo nan mara mutunci kawai.
Ya juya gurin Umma yana fadin Atika ina son idan ina magana da yara na ki daina saka bakin ki daga yau.
Ki bari idan na sako sunan ki a ciki ki saka bakin ki, idan kuma kinga kamar fadi nayi kawai to kici gaba da hakan.
Yanzu saboda mugun halinki na yaro yayi laifi ki tsare ba ai mashi fada kinga abinda wanan fasikin dan naki ya jawo muna a gida.
Wai dana mane yau tunda yai laifi ko?
Au to ba danki bane dan waye a gurin nan , saunawa kina fadin ke kikai daukan cikin abinki don haka abar maki kayan ki.
Zaitai magana yace cikin daga hannu da daka tsawa ki min shiru don ban son jin kazamin kalamin ki yau a gurin nan.
Yace Imirah kai kuma abinda kai min a idon duniya banda abinda zance maka sai dai nace kaje duniya tana da fadi.
Don daga yau ina son ku sani na cire Imirah ga duk wani harkan kasuwancina.
Don ba a hada biyu a lokaci guda zina da neman arziki basu tafiya daidai.
Don haka tafi nima nema nayi Allah ya bani kaje ka nemi na kanka amma da kudi na ni Abubakar ba za,a dinga zina dashi ba.
Wanan kalamin na Alhaji ya tayarwa Umma da yaran ta hankali sosai don sun wani babban komawa baya ne ya samay su.
Yace daga yau duk wanda ya dauko min magana irin ta zubar da mutunci da kima a idon duniya wallahi ku sani na tsamay ko wanene daga cikin zuria ta.
Ni ba mazinaci bane kowa ya sani a garin nan don kaucewa zina yasa na aje iyayyen ku haka a gidan nan.
Duk wanda ya ganin a gurin mace to ka tabbatar aure ne yakaini ba yaudara ba.
Yanzu ina riba ga illanta wa mutane yarinya da kayi amma fa ka sani shi zina bashi ne karike ka aje hakan a ranka.
Haba Alhaji kada kai mashi baki mana mama Asiya ta fadi haka da sauri ta tare mashi numfashi.
Yace Asiya ki shiga hankalin ki duk kune barayin na,tsunta da baku iya kwabawa diyan ku kun bar yara sun zama ni alkakan kafa a gida na.
Sai yai shiru can yanisa yace Maijidda ke kuma kada ki ga kamar ban san komai ba da kikayi.
Nasani kuma nayi mamakin yadda kika boye, wanan mugu munafuki mazinaci akan mumunan laifin da ya aikata haka.
Dukar da kai mama tayi tare da dan nisawa Baba yace ina kwana ki akanki yaso sauke wanan iftila,in kan yar amanan da aka aje a gurin ki.
Idan da ita yaiwa hakan ashe boye shi zakiyi ke nan kici amanan iyayyen yarinyar da aka danka maki.
Gaskiya kin bani mamaki kuma kin bani kunya matuaka dana ji hakan a kan ki.
Sannan ke mai da mai hali ko ?
Kika saka danki a gaba sai da yazo ya fitar da,wanan fasikin dana so ai mashi daurin rai da rai ya karata can gidan yari inga yadda zai samu wata yar kuma ya lalata.
Cikin karfi hali maji tace Alhaji ni ba na boye shi bane don kada a hukun tashi kokuma wai ba mumunan laifi yayi ba.
Gani nayi a lokacin yadda mutane su kai dandazo suna neman shi zasu iya illanta shi.
Yace da tsawa shi da ya illanta yar wasu fa ?
Tace idan sun kashe shi ko sunyi mashi wani mugun abin a lokacin Alhaji sai abin yafi na farko muni.
Kai kuma ka hau sosai a lokacin ba shawara zaka ji ba don yadda ka hasala.
Wanan dalilin yasa nai hakan .
Amma da aka samu natsuwa ai an fahinci juna don kaddarace shima ai da yayi abin ya koma mashi ciki.
Sannan ita wanan yarinyar mutane sun sheda ta da haka take watsatsa ce ita dama.
Yace ai shi ya fita watsewa,
Maji tace na kira sadauki ne don yazo ya san yadda zaiyi akan al,amari don duk kan mu nan ai matsalar ta shafa don ba wanda bai shiga tashin hankali ba daga cikin mu.
Ke da danki ya shiga wani hali a gidan nan wa hankalin shi ya tashi ina a tsakar gida ake tsayawa ai maki gori dare da rana.
Wanan kuma ai ba komai bane don kowa ma uwace ai don dan sune suma.
Amma ni idan abinda nayi laifi ne don Allah ayi hakkuri a yafe min.
Sadauki ne yai magana yace Baba don, Allah ayi hakkuri tunda abin ya riga ya faru.
Kai dakata don Allah ai kaima zanzo gareka ne watau kai yanzu ga mai kudi ko ?
Shine zakai amfani da wanan dama gurin tallafa ma alfasha idan haka ya kasance daga daya daga cikin kannen ku yaya zakuji ne wai ?
Abinda nake son ku gane ke nan idan a cikin diyan mu akaiwa wanan keta haddi haka aka gurbata rayuwan su ashe taimakawa mai fyaden zakuyi a sake shi ?
Shiru falon yayi ba,wanda yai magana kowa na tunanen zuci daga cikin su.
Sadauki ne still ya kara yin karfin halin yin magana yace Baba don Allah ayi hakuri tun da iyayyen yarinyar sun hakkura.
Ido mahaifin shi ya watsa mashi cikin takaici yace eh maganan ta mutu ma na tunda kai mai kudi ka basu kudi ba.
Amma ni a gurina wallahi case din nan bai mutu ba dayan biyu ne ko na kai shi kotu ko kuma ya yarda cewa da zaran yarinyar nan ta kara dan tasawa zai aureta.
Da sauri kowa ya ke kallon baba cikin dago kawunan su.
Imiranah da,sauri ya dago yace haba Baba wanan yarinyar yar kauye yar talla ko boko fa batayi ba.
Au baka san haka take ba ne har ka turata daki ka kwamashe ta har ka kai ga halaka ta ?
Shiru kowa yayi ba wanda yace uffan Baba yace sannan kuma kaine zaka dinga dauka duk wani nauyi nata daga yau har zuwa lokacin da za ta tare a gidan ka.
Kuma ku sani wallahi ko bayan raina duk wanda ya tayar da wanan magana ban yafe ma maishi ba.
Daga haka ya mike zai shige ciki sadauki yace amma Baba don Allah ka barshi yaci gaba da sana,an shi da yakeyi.
Baba yace wani ai nagama magana ta yaje ya nemi tashi shima, don nima nema nayi ba gado nayi ba.
Ya shige abinshi yabar su nan a zaune kowa yai jigun jigun tsakanin su, hjy Kubura ta mike tana fadi yau dai ga irin ta nan.
Yanzu kowa na da abin fadi ke nan a gidan nan tab da tsuliya bamu kadai bane masu abin fadi ashe?
Ke tsohuwar kilakiya dama nasan a farin ciki kike don haka ya faru kuma nasan duk kece mai wanan shirin.
Iyakar ki ke nan zagin wasu naji ni dadewa nayi banyi aure har mijin ki yazo ya,aure ni gani kuma gidan zama daram ba inda zan tafi wallahi.
Ba kince lokacin da na,shigo kin bani wata uku ba dashi yau gani wata uku ya shude har da riba gasu nan min.
Sai da ki shirya don kilakiya tana nan dakin ki zaune ko kinzaci bamu san komai bane wai ?
Ni ba irin hajiya maijidda bace da kike wa yadda ranki yaso wai don takaici har da taimaka maku.
Nan da Sadauki ke dan shaye shaye a baya may nene bakuyi mata ba a gidan nan.
Yau gashi ita da dan da kike mata gori kullun sun taimake ku ai da kun gane kuren ku wallahi da ankamashi fasikin banza kawai.
Nan fada ya kici may masu hjy kubura tai masu tas ta fita maji dai tana ganin su sarke tabar falon zuwa part din ta.

****** ********* ******
Ina zaune a falo ni kadai don ban tafi gurin kiran da Baba yai wa iyalin shi ba don nasan magana ce da yashafi sirin iyalin shi.
Sadauki ne ya fara shigowa falon su maryam na bayan shi, nan ya samu kujera ya zauna tare da furzo iska daga bakin shi.
Daga inda nake zaune cikin yar siririyar muryana nace sannu yaya.
Sai da ya nisa yace yauwa sannu Fatima ke ma.
Maryam tace Fatima dauko muna salad din mu, mu sha kinji.
Namike na nufi kitchen na dauko salad fruit din dana gyara mu a a cikin wani roba mai fadi da cups din da zan zuba muna aciki.
Shina fara zubawa fruit din idon shi suna a lumshe na aje mai a gaban shi nace yaya ga naka nan na juya zan wuce.
Kamar mai rada yace ki zo ki dauki kayanki inba zaki juri bani hannu da hannu ba kuma ki tsaya nasha naji ko may nene?
Wani din nayi kamar na wuce sai kuma nai wani tunane tare da dukawa na dauko cup din na mika mai,
Bai ce min kala ba ya karbi cup din daga hannu na, zan juya na wuce yace amma kinji abinda nace maki ko?
Dan guntun tsuki naja wanda ban san zai fito fili ba yace, ai da ma na barki ki tafi din yau kiga abinda zan ma shegen kunnen nan da baijin magana.
Babu shiri na dawo daga gefen shi na dan tsaya tsaye.
Yace ya haka kuma kamar wata soja can ko bodyguide, zama nayi daga kujeran gefen shi ina cewa Anty maryam ki zuba naku kada yai sanyi har nazo.
Bai ce min kala ba ya fara kurban salad din da cibin dake cikin cup din a hankali.
Ya kai cibi uku ya dago kadan yace me sunan wanan abin kuma ne wai ?
A hankali nace fruits salad ne.
Ya dan mayar da hankali ga sha can yace waya hada shi haka ?
Nace nice nayi shi dazun da safe.
Ya nuna cup din yace ina son kullun da safe da yamma idan ina gari ki dinga hada min shi.
Zan so na sha shi kafin nasha komai da safe haka da yamma kafin na kwanta.
Kaina na gyada mashi kawai.
Yace baki ji may nace bane ?
Da sauri nace tau yaya.
Maryam tace Bintu zo dauki naki mana kafin yai sanyi ki sha.
Na yunkura zan mike sai naji tasa kafan shi ya take min kafa, wani mugun zafi naji ban san lokacin da na sake wani dan kara ba da karfi.
Da sauri na daga kai na dubeshi sai naga shi sai shan salad din shi yake hankali a kwance.
Da sauri su Amira suka dago kai amma basu ga abinda nakewa ihu ba hakanan.
Gashi shi kuma yaki daga kafanshi daya danne min nawa dashi idan na dan motsa kafana wani irin mugun zafi nake ji sosai.
Kuma yaki koda kallon inda nake balle yasa alaman cirewa.
Take idanuwana suka fara kawo hawaye, mama ce tafito daga dakinta don jin karan da nayi tana tambayan maye haka kuma kikewa mutane ihu haka Fatim?
Ban ce komai ba sai dan kukan dana kara da sauri takai kallonta ga ketan da yake min.
Tace kai amma ko anyi babban banza anan wallahi yanzu mai tai maka kake mata wanan cin amanan haka sadauki ?
Kamar badashi mama take magana ba tace bazaka cire mata wanan kauren kafan naka ba da yasha buga ball.
Sai lokavcin su Amira suka gane wani keta yake min duk tsawon wanan lokacin su dai sunga kawai ina kuka ne.
Mama ta kara cewa wai bada kai nakeyi bane sadauki ?
Jin haka yasa shi daga kafan shi a kan nawa yana yamike tsaye yana fadin, ai na fada maki sai nai

Please Login or Register in order to submit comment