Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ke Bintu nifa ban san inda ake sayar da maganin su ba.
Nace a tambaya mana take cewa wai wa zata tambaya amsa nayi tare da daukan kudi ga post nafita.
Da tambaya,na gane gurin sai gani da maganin cike da leda nashigo dakin nan na mikawa nurse din dana samu tana gyara ruwan dake tafiya a jikin maji din nayi.
Shiko sadauki yana gama waya da Amirah mahaifin shi ya kira yake sheda mashi abinda ya faru da uwar su.
A gagauce Baba ke tambayan shi yanzu maijidda tana ina wai?
Yace tana asibiti an bata gado ita da wanan bakuwar yarinyar Fatima dake dakin ta.
Su su Amira fa suna inane da sauran mutanwn gidan da har za,a bar Fatima karamar yarinya takai ta asibiti da kanta duk an rasa wanda zai dubaran daukan ta zuwa asibiti sai Fatima karamar yarinya haka da ita.
Sadauki yace yanzu nakira su Amira ga,waya mazasu tafi asibitin suga halin da ake ciki don dai tace wai an daura mata ruwa a,jiki ko.
Allah ya sauwaka insha Allahu gobe zan dawo nazo naga abinda ke faruwa hakanan.
Suna kashe wayan sadauki ya dab furzo iska daga bakin shi kadan tare da dan gyara tsayin shi.
Agogon shi ya fara dubawa ya san idan yace zai taso daga anambara zuwa sokoto ba karamin tafiya bane don haka ya yanke shawaran samun jirgi zuwa abuja daga abuja koda da motane sai ya karaso.
Karfe, Biyun rana yana garin Abuja bai bata lokaci ba ya samu shatan mota sai sokoto,.
Suna zaune sai nice ke ta faman zirga zirga wai su yan gaye a hankali maji ta bude idanuwan ta da ta kusa yini tana barci.
A lokacin bani daki sai Amira ce zaune mun fita da maryam zuwa wani guri tace na,rakata.
Bayan ta bude ido tafara bin dakin da,kallo can tace, Fatima, Fatima, sai Amira ta mike tazo inda take kwance.
Maji kin tashi ne tace wa uwar ta, sai uwar ta ce mata eh ina Fatima ne ?, bata nan tabata amsa.
Sai ta mayar da idanuwan ta takara rufe su a hankali, kuma again.
Muna,shigowa take fada muna mama,ta,falka tana tambayan ki Bintu da sauri na isa gurin ina,fadin wani abin take so ne Anty tace batace komai ba sai ta koma barcin ta.
Ana maggariba ya iso garin a lokacin hajiya kubura ce kawai tazo duba mama sauran basu zo ba har lokacin.
Ban san da zuwan shi ba don natafi dauko kayan da za,a bukata a gida.
Ina dawowa daga gida na sauka mashi sai naji ana cewa ke pretty, Fatima,
Jin fatima yasani dan dakatawa na waiga inga mai kirana haka nan don ban sheda sunan mai shi ba.
Ya karaso gurina da murmushin shi yana wasa da key din motan shi a hannun shi.
Yace ai tun gida na,biyo bayan ki dama na dade ina son in samu time nai maki magana.
Kin gane ne wallahi kinyi min irin tsarin macen da nake son ke nan ba wani bata lokaci ki yarda dani kawai muji dadin juna dake zan maki komai wallahi koma may kike so idan kinyarda dani zan dinga saya maki anything, anything just kawai ki bani hadin kai mu more junan mu muji dadi idan gida akwai idon mutane zan sama muna wani scret place da zamu dinga hadu ehy kin gane ko.
Wani irin bakin ciki da taikacin shi suka rufe ni ban kai karshen tunane na ba,sai ji nayi yana fadi dibki don Allah wanan idan na samayki nagama neman mata wallahi.
Yana kokarin kai hannun shi ya taba min wuya ban son lokacin da nayar da pillow dake hannu na ba nakai mashi mari fayauuu,
Daga inda saudaki yake tsaye tun saukana a mashin da tareni dayayi duk akan idon shine da marin da na kaiwa yayan nashi.
Take ya dafe wurin yana cewa ke ashe baki da kunya ashe ke yar iskan yarinya ce ban sani ba.
Har ya fara takowa daga inda yake zuwa gurin da muke don yana ganin kamar Imirana zai iya dukana.
Sai yaga na daga hannu ina fadin dan iska kawai mara mutunci masu gadon iskanci kaje ai kana da kauna Nafisa ka huta da ita ni ba karuwa bace .
Imirana yace wallahi sai kin gane baki da wayau don sai kin bargidan mu wallahi shegiya yar ci rani kawai.
Ke Fatima dauki kayan ki, kishige ciki kinji da sauri najuya don jin muryan wanda ban zata ba a lokacin duk kan mu kallon shi muke yi.
Imirana yace jimun wanan yar iskan yar kauyen fa waini zata raina wa hankali haka ji mun ita.
Hannu ya daga wa dan uwan shi yace please Imirana is OK naga komai tun saukanta mashi ina tsaye gaban ku ai.
Daga haka ya kama bina a,baya ina gaba yana biye dani har zuwa cikin female ward da aka kwantar da maji aciki.
Amirah na ganin na dawo take cewa yauwa Bintu dauki kayan can da akaci abinci ki wanke su.
Sai ganin yayan su tayi a bayana da sauri tace lah yayana ka iso ashe yace eh na tsaya yin sallah ne da na iso.
Ban zauna ba na kwashi kayan na,wanko su kamar yadda tace ina dawowa kuma duk suna tsaye suna magana Amira tace Bintu zoki sayo ruwa mu aje kada dare yayi ba ruwa a gurin.
Kai haba haba Amirah why komai Bintu, Bintu dai Bintu ku kuna may ye wai please.
Nace ina kudin yake na sayo yace ke maryam jeki ku sayo a tare da ita kuna zaune sai faman bada intruction kuke kamar wasu tsufi.
Maji da ta farka tace ai basauyi ba sai dai su bada odar yi don su sarakaine.
Sai yanzun yagane abinda yasa yarinyar ta,shiga ran maji sosai yarinyar bata da kiuyuya kuma bata fushi.
Yace ina son a sake mata daki yanzu zan tafi nai magana gurin nurse yatafi tai mashi bayanin yadda za,ayi.
Muna dawiwa muka samu har ya karbo takardan canza daki ko nan muka kwasa sai sabon dakin da aka canza mu.

****** ********* ******
Dakin kudi muka koma mu kadai ne a dakin yana da tsari sosai harda dan fridge da kayan kallo a cikin sa.
Maji har lokacin magani bai sake ta ba na kafe ta da idanu sai barci take gashi duk ta wani ramay sosai da ita.
Ban san lokacin da tausayin ta ya kamani ba sai jin hawaye nayi sun zubo a idanuwana sai sauka suke a kumatuna.
Ban san ya shigo ba yana tsaye yana kallo na may kikewa kuka haka duk suka juto gareni kuka kuma Bintu sai maryam itama ta fara kuka.
Tace Tun safe Bintu ke kukan nan idan ta kalli maji nai mata magana taki bari.
Likitane yashigo dakin saye da corth din shi baka duk muka gaishe shi yake cewa tare dan taba jikin ta har idanun ta.
Zata dan samu sauki idan ta farka amma yaya akayi kuna gari kuka bari har ciwo yaci ta haka a gida.
Gaskiya data kara awa a lokacin bata samu taimako ba da zamu iya rasata wallahi.
Ya juyo inda nake yana fadin idan ta farka sai ki hada mata tea mai zafi tasha sai ki bata wanan maganin da aka sayo amma don Allah kada kiyi mata wasa da maganin don ba abin wasa bane.
Yana fita dakin na mike tare da daukan cup na fita na dauraye shi na,dawo na,saka acikin wani leda baki.
Yace Amira waya zo daga gida cikin su Umma eh to Bintu tace ina barci wai mommy ta shigo bayan ita ba,wanda yazo kuma.
Muna zaune dakin kowa yai shiru a cikin mu duk kowa da abinda yakeyi sai ga hjy Kubura itace a gaba yaranta na bin ta a bayanta.
Suna dauke da kwandon da kuloli a cikin sa da flask din ruwan zafi sai ledojin da yaran suka riko na kayan fruit.
Tana ganin sadauki take cewa ,a,a sadauki ashe har ka iso yace cikin dagawa daga saman kujeran da yake zaune kusa da maji don ya bata guri na iso mummy.
Da sauri na mike na karbi kwandon dake hannun ta, nakao saman durowan dakin na asibiti na aje.
Tace ai natafi wancan dakin na farko sukace min kuna nan ancan guri.
Yace eh mummy gurin can bai min ba mutane sunyi tawa baza,a bar mara lafiya yayi barci ba da dadi.
Hakane gaskiya amma nan din kaga is ok zata samu hutawa sosai anan din.
Likitan ya shigo ko may yace kafin wata tai magana nace zazzabine wai typhod yai mata yawa suka ce ta ce wai da sauki ai nazaci suce ciwon zuciyan tane ke batin tashi.
Nace yama ce bata da ciwon zuciya wancan daya fadi haka bai san aikin shiba.
To Allah ya sauwaka muka amsa mata da Ameen mummy tace zamu koma don dare yayi sosai gani da yara bandawo da wuri ba shiyasa ban yi girki cikin lokaci ba.
Anwar yana lake jikin yayan shi tun shigowan su dakin yagan shi ya lake mashi sai hira suke dashi.
Tamike tare da muna sallama tabar dakin muka dan rakata zuwa kofa tace ku koma abinku zanga wata kawana dake duty acan ward din.
Tana wuce muka dawo ni da maryam nace yaya a zuba ma abincin kaci ne?
Yace No barshi banjin cin abinci yanzu Amira tace yayana bari a zuba maka kaci ko kadan ne don Allah.
Hakana jawo plate na,soma zuba mai abincin wanda dafa duka ne da kayan lanbu a cikin shi sai kifi da tai amfani dashi.
Sai dan ferfesun kifi danye da tayi daban ta zuba shi a wani dan kula karami.
Shina zuba mai don nasan bai shiri da dafa duka shi sai dai da miya ko tuwo.
Na koma gefe na zauna maryam tace zuba muna abincin muci mana kin kima zauna.
Nace sai dai na zuba maki ni ba yanzu zanci ba Amira tace kinbsan bafillatace sai kafa ya dauke taci.
Hmm aini Bintu tabani mamaki jifa yadda tai saurin boye ciwon maji wa mummy harda cewa ance wanda yace tana dashi bai san aikin shi ba.
Nace eh mana yanzu da anfadi gaskiya sun samu na fadi kena a unguwa cewa bakinciki ne zai kasheta ai likita yace kaza yace kaza.
Maryam tace wallahi kamar kina zaune kuwa don tana komawa zakiga muna fukancan sun tambayeta may ke damun ta kamar da gaske da an fada masu shike nan an samu na fafi ana canza magana.
Sadauki wanda yake zaune yana shan ferfesun shi hankali kwance bai ce muna kala ba.
Suna cin abincin duk kamshi ya bude dakin sai hira suke kasa kasa kan mummy a gidan su .
Yana gama wa yadago kai muka hada ido na daure fuska na yace kwashe kayan nan anan .
Sai da ya sha ruwa yace ke may yasa bazakici abincin ba ke nace sai anjima zanci yaya nadan sha lemo dazun.
Ya dan kalleni kamar mai nazari can yace su waye zasu kwana anan don dare ya soma sai nakai sauran gida.
Maryam tace sai dai abar anty Amira tunda itace babba ko da sauri tace a,a wallahi ban iya tsayawa ni kadai don tsoro nake ji.
Baki da hankali ne idan baki zauna ba wazai zauna dama ke dakike babba wallahi yayana ban iya zama ni kadai anan gaskiya.
Nace dama ka barsu yaya dama ni anan zan kwana ai tare da mama su tafi gida su huta su.
Yace don may za,a barki ke kadai dole dayan su ta tsaya tare dake a nan ya wuce da maryam mukuma muka zauna dakin nan zamu kwana da mama.
Azaton mu ya tafi ke nan can sai gashi ya dawo dauke da ledoji ya sayo muna su kayan shayi da kwalayen drinks sai naman kaza mai zafi ya kawo muna.
Yamika muna yana cewa kuci naman kubar wa maji idan ta farka kila ta danci
Amira ta jawo ledan gamu tana fadin oya muci Bintu nace fara ci ke, nan tafara yagan naman tana kaiwa bakin ta.
Zaune yake a saitina yana amfani da wayan shi data dauke mai hankali.
Yace wai may yasa ke bazakici komai bane wai, na dan tsuke fuskana san nan na ce haka kawai .
Yace amma badon kin ci wani abuba ko kin koshi ba ko?
Nace ban karya ba yaya ban dai iyacin komai ne saboda hankalina daya tashi.
Yaya na fada maka bar Bintu haka take ita bata damu da cin abinci ba fa ita.
Ya dubi Amira yace kina nufin zata iya kwana a haka bata ci komai ba?
Haka take ko agida sai maji tai mata fada take cin abu ita.
Yace tura mata naman da kwalin drink din tasha ban musa musuba na dauki yaka gudanakai abakina da kyat nake iya taunawa na dauki drinks din nakai abikina sai naji sanyin shi yai min yawa sosai.
Haka dai na danci naman nasha drinks din kamar wace za,a kama a lokacin
Wayana yai ruri da sauri na nufi side drower dana aje wayan akai.
Ina kokarin duba maikirana a wanan lokacin don dai nasan ba Kabir bane don a lokacin yana cikin iyalinshi.
Sadauki ya kafe ni da ido don jin waya kirani a wanan lokacin kuma ko zanyi fitsaran dana saba na waya agaban mutane dayace inayi.
Na daga tare da sallama sai naji muryan gwagona tana tambayana jikin maji nace gamunan ma asibiti da ita an bata gado.
Nan take ce min insha Allahu gobe tun da safe zata shigo gari don yanzu tafi gane ma ta dinga kai kaya gari gari.
Ina kashe wayan maji tana,farkawa duk mukayi kanta gaba dayan mu muna mata sannu da jikin ta.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA,BA
KA DA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,


A LOKACIN MU KE,,,,,,,



Kudi yabashi har dubu daya,yace yaje yasaya duk abinda yake so dashi yaron bai san girman kudin ba yadai san ko nawane don yaka,yaje ya fara sayen abinda ke ran shi.
Kayan zaki sai kayan sanyi su ya,kwasa ya sha har yafara kyautawa,abokan shi.
Ya dawo dauke da roban shi dakin sisko nan suka zauna ya sa masu wasan turawa suna kallo daga,shi sai shi a daki.
Can sai ya sauya tasha inda ake wani wasan shedana zallah.
Yaron sai ya,fara kawar da kan shi gefe sisko ya ja mai kafa yana fadi ji dan nema kaida wata rana zaka zama boss da wanan harkan kake kawar da fuska ai gara ka fara koyo tun yanzu.
Nan dai har yaron Aliyu yadan fara tsayawa yana kallo ta gefen idon shi ajima kadan yake cewa zai tafi gida sisko yace kai tun yanzu yace lokacin zuwan shi makaranta yayi ne.
Jawo shi yayi kamar wandaya,samu budurwa yana dan wani wasani dashi sai da yaji dai,dai ya sake shi da zai tafi sai da ya,kara mai dan kudi saboda jan ra,ayi gobe.
Ruwan sai makaranta,wasu, almajirai yakai yace inji wani mutum yace na bayar sadaka anan.
Shi kuma ya kama hanyan gida yana murna da farinciki ya isa gida ya mika wa uwar shi kudin ta,saura ya samu guri ya boye.
Kamshi turare taji a jikin shi tace kai kai kai ina,kasamu wanan turaren haka mai kamshi.
Nan ya shafto karya yana fadi wani yaro ya ysunci kwallaban turare shine muka dan sawa jikin mu.
Tace yaci abinci yace sai ya dawo ba yanzu don haka tace yai niya yafita koshi da kyat tasamu ya fita don ya kwata jikin shi yana mai ciwo ga kuna kayan sanyin da ya cika cikin shi dashi fam.
Amma ita da yake son kudi ya rufe mata idon ta sam bata hango illa ga rashin cin abincin da yaron baiyi a kwanakin nan ba.
Yaro idan ya,fara talla ko yarinya komai zama kamilin yaro kwana kadan da,fara tallan yaro idon shi zai bushe.
Idan sau daya kakewa yaro tsawa ya bar abu yanzu sai kayi uku masu karfi kfin ya bat abinda ka hanne shi.
Yaro idan ya fara talla baijin naiyi ko kunya fada wa babba magana yadda yaso sai dai kai babba kaji kunya.
Yanzu duk irin haka ke faruwa,da,Aliyu amma uwar bata da fahinta ita bukatar ta kawai ya kawo mata kudi a rayuwan ta.
Mahaifin yaron ya ga matukar canji akan dan shi sai dai ya danganta halin yaron sai ya dangata shi da girma yasa shi canzawa a baki daya.
Tun wanan ranan kullun sai Aliyu ya,tafi gurin sisko saboda dan kudin da yake samu gare shi.
Gashi uwar ba ido take sakawa akan yaron ba ita gurinta kawai shine, taga ya kawo mata kudin da yawa.

****** ********* ******
Tun wanan ranan da suka hadu suka zama abokai tsakanin su da Nafisa.
Ance abokin barawo barawo ne don Nafisa bata san ya akayi tafara shan abubuwan dasu Raiha ke shaba saidai kawai ta tsunci kanta a cikin shaye shaye dumu dumu da ita.
Ga uwar ta,Umma a kullun zancen ta sai zagin sadauki da yiwa uwarshi dariya bata san na dakin ta yafi illa,ba ma.
Sai dai tana kokarin ganin kowa a gidan su kada ya,san zancen har a,kyamce ta ita da uwarta kamar yadda akewa Maji da diyan ta gaba daya da abin bai shafa bama.
Yanzun takai har fitan da,su Raiha keyi zuwa wani gari tare da Nafisa suke yin shi, don sai ta,shirya karya cewa za su wani gurin yan uwan su ko gidan kawarta sai kawai su fita garin suyi kwanakin da zasuyi ba ta gidan.
Gashi ir8n na fitsara ba komai bane a gurin ta don wayewan ta tana ganin yakai haka ita.

Al,amarin ciwon maji yasa Alhaji baro aikin shi ya dawo gida don ganin yadda jikin naya yake saboda hankslin shi yaki kwantawa da jin da yayi an bata gado.
Yana isowa ya wuce asibiti direct Don ganin jikin nata, ya samu Tana zaune ina tsaye agaban ta ina we, mata lemun tana Dan sha a hankali.
Baba yashigo dakin da,sallaman shi Nan muka shiga gaishe shi dadawo daga tafiyan da yayi.
Idanuwan shi kyar akan ruwan da ke kafe daga gefen mama ya Kara juyo kallon shi a gareta Yana mata sannu da jiki.
Ganin shi yasa mu kokarin Fara barin dakin don mu kauce masu daga dakin.
Yake cewa ku tsaya abinku Fatima ance kece Kika kawo ta asibitin har aka baku gado to Yaya likitan yace yanzu .
Nace cikin dukar dakai likitan yaiwa Yaya sadauki bayani dazun da safe Kuna ya Kara rubuto wasu maganin da za,a saye.
Yace zasu kwantar da it's na sati biyu anan don ta samu Hutu sosai a jikin ta tare da treatment din ta.
Ok hakan na dakyau ai said dai ku dinga barinta tana samun barci sosai zaifi Kara mata lafiya .
Bai dade dashigowa ba sai ga sadauki ya shigo dakin ya sayo maganin da likitan ya rubuta mai yana fadin da kyait muka samu maganin babu shi nan cikin asibiti.
Yaiwa mahaifin shi sannu da dawowa tare da tambayan shi Yaya aiki a can inda ya fito.
Muna waje zaune saiga Yaya Imiran yazo don sunyi waya da baba yace sure hadu a Nan asibiti dashi.
Zan iya cewa tunda mukazo asibiti bai shigo gurin Maji ba don ya Dubai lafiyan ta Amma salmanu Dan wurin mama Asiya zuwan shi biyu Kuma harda fruit yakawo Muna.
Ya na isowa ya gan mu, zaune mu uku nan Suka fara gai da shi cikin ladabi, Banda ni dake zaune ina mashi wani kallon raini kawai.
Tambaya yayi ko baba Yana ciki suka bashi da amsa da eh Yana Nan cikin dakin.
Yana kokarin shigewa naja wani tsuki da karfi Yana ji sai dai bai juyo ba ya shige ciki kawai abinshi.
Muryan anty maryam ce naji tana cewa ke may ya hana kiki gaida yayan mu Bintu?
Nace bai isa na gaida shi bane kila don da nagaida shi inda mutumin kirki ne.
Fitowan shi yasa su yin shiru suna mashi sai anjima, bintu tace haka dai za,a kare .
Wai ke Bintu harda yaya Imiran da ba,ruwan shi da kowa, amma sai k8n tsula mashi halinki na tsiya?
Maryam tace a,a anty Amira tunda kikaga haka akwai dai koni ranan mun dawo school bakiji, abinda yake fadawa Bintu bane,
Nace aini Anty Amira idan mutum bai shiga gonata ba ni bani shiga nashi don haka kibarni kawai dashi dan iska kawai.
Haba Bintu haka,kawai ki dinga zagan muna dan uwa a gaban mu haka gaskiya zamu saka wando kafa guda dake a gidan nan.
Nace maida yukanki kube anty Amira ai ni ba haka nake ba da ace da yai min ban dauki mataki ba,ai da ko yanzu bata kare muna,ba,wallahi.
Ke dai yanzu kin zama disturb wallah kamar ba Bintu Maji ba wallahi nace lokaci ne idan baka baki sai a shaka a,banza.
Wai don Allah may ya,hadaki da yaya Imirana kodai laifin maganan ranan ne har yanzu kike kule dashi.
Nace a,a ai anan cikin asibitin muka yi case din mu dashi ban ma,san yaya sadauki na gurin ba,sai da naji ya daka mai tsawa yace mai ya sake min hannu na.
Tace ashe kin kuru, ne harda yaya,sadauki a gurin lalaima Bintu kinyi nisa sosai wallahi.
Nace marin shi fa kawai nayi saudaya shine wani abu wallahi har yanzu a kule nake dashi a raina .
Da sauri sukace mari da,gaske mari Bintu nace don ma banda karfi aida abinda zan mai sai yafi mari wallahi.
Yadda yake dan iska haka yake ganin kowa dan iskane shine harda daukan kazamin hannun shi wai zai shafa min jiki niko nakai mai mari sosai Allah yaban sa,a na samay shi da kyau.
Da sauri Amira tace don Allah da gaske marin shi kikayi nace wallahi Allah kuwa nan na,basu labarin abinda ya faru a tsakanin mu dashi har takai na mare shi.
Maryam tace dan iskan mutum kawai mara mutunci yau da wani ne da uwar shi ta samu abin kasawa a,ture tana baradawa a gari.
"Dan kowa ,dan banza ne, nata ne diyan kwarai a duniya, nace wallahi ni ko gobe yai min maganan iskanci sai na,dauki mataki ko a gaban waye.
Maryam tace ya ganki haka ya zaci irin yan matan shi da ya saba yaudara ne.
Nace shi dai jarabar shi ce ta motsa kawai har idon shi ya rufe, irin yan iskan ga ai su kowa bi suke basu da zabi mace da mai aure da mara aure in sun, samu, duk so sukeyi.
Nace Allah ya kyauta Allah dai ya,shirye mu, don wanan shima ba karamin masifa bane wallahi.
Don ai zina ya mafi komai muni a rayuwan mutum da ban kyama, ga al,umma.
Nifa ban yarda da maza don a mayaudara nake daukan su baki daya inji Amira

Please Login or Register in order to submit comment