Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

suka hadu kan a hada gadon daya bari a raba aba kowa nashi kowa ya kama gaban shi gashi ita yaran ta duk yan mata ne har su bakwai ras gare ta a gidan.
Nan akai kasafi basu yarda sun barta a cikin gidan su ba aka bata wani gida na Alhaji karami ita da yaran ta ranan sukace bazata kwana masu gida ba sai ta fice ta basu gurin su.
Da kyat aka lalashe su su bari a gyara gidan tafice masu daga gidan su.
Ban san Alhaji na da arziki haka ba sai wanan ranan nima na samu gida daga kason na na wanka da gona sai dai ba babba ga shanaye dana samu a ciki da kudi tare da sauran tarkace.
Iyayena suna ganin yadda aka kwashe da sabuwa suka roka abasu ni su tafi dani gida na karasa wanka a can amma aka hana.
Suka ce idan sun min hakana basu rike amanan da mahaufisu yabasu ba nawa ayi hakkuri kwana nawa in ga rai ga lafiya zan gama wanka na koma gida.
Mama Altine kwana arbain tai min ta barni cikin su banda wani matsala tare dasu sai na kewan Alhaji kawai wanda bani kadai ba har yaro karami dake gidan yana yi don halin shi na alheri ga iyalin shi.
Ban da rashin komai in ban da na maigidan don komai suna wadatar min dashi duk da an raba an ba kowa kason shi amma su yaya Hadi basu barina haka na cikin su.
A dadafe na gama wanka a gidan ranan da muka fita tun safe sai ga su Rukaiyya wai mama tace suzo su fara rage min kayana zuwa gida.
Mama hausatu ne tace haba sai kace zaman da akayi cikin bacin rai aiko zata koma a bari har a dan natsu sai ta koma gidan ko ?
Haka suka juya suka koma suna fada mata ta haufada wai ko ni nafi kowa son gidan miji yanzu ai dole na dawo gidan ubana tun da dadi ya kare anga guri anbaje ana cin dadi yanzu ko dole na dawowa turke na mai cabo yana nan yana jirana karya ya kare da sallon auren mai kudin gari gare ni.
Ban dawo gida ba sai da na cika sati biyu ranan mutuwan ta sake dawo muna sabo a gidan .
Ina kuka sunayi aka kwashe min kayana zuwa gidan mu su mama ne suka raka ni har gida da dare sai fadin alherina sukeyi suna fadin zasu sha kewa dai kan a gidan.
Yarinya karama amma bata san zafin jikin ta ba ko kyashi irin na yaran yau komai da zuciya daya zatai maka shi.
Mama jin su kawai take tana fadi a ranta ai dole kuce haka tunda kun samu boya to muma nan mun fiku bukatan ta ai yanzu.
Suka tafi suka barni ina kukan bakin cikin rabuwa dasu danayi na shige dakin Inna ta na kwanta a saman gadon ta na lafe.

****** ********* ******
Ban fito ba tunda na kwanta haka gari ya wayw min sai juyi nake ina tunane banyi barci ba mai dadi.
Sai bayan nayi sallah ne na samu barci ya dan dauke ni mai dadi har ban san inda nake ba a lokacin.
Can cikin barci naji muryan Inna ta tana tayar dani wai na tashi mama tana kira na a waje.
Nai mika tare da juyawa
na mike na sauko saman gadon tare da jan hijjab dina na saka a jikina.
Na nufi waje inda nake jin mama tana kwada min kira harshe sama na amsa da na,am mama .
Tace to kin shige daki kin mimike kafa wa kike jira ya debo maki ruwa da za, ai aiki da shi.
A hankali na dago kai na kalle ta nace ruwa mama ?
Tace eh ruwa ko kinfi karfin diban ruwan ne ke da bazaki ba kike nufi ko may , don ban san uban da kika aje da kike son yaje maki rijiya ba ai.
Ko har yanzu mulkin auren gidan mai kudin ne a saman kan ki muji ?
Ban yi magana ba sai juyawan da nayi zuwa dakin mu na koma na zauna a bakin gadon dana tashi.
Inna dai tana jin mu batai magana ba sai aikin ta takeyi kawai a tsakar gida.
Can dai taji ni shiru ban fito ba ta kara kwala min kira karo na biyu daga dakin na leko kaina ina fadin mama ni ba zan fita ba gaskiya don kunya nake ji wallahi.
Eyya su kunya manya ke nan ke gaki matar Alhaji ko to Alhajin ma ina yake yau ko diyan shi da matan shi na kwarai sun kama kan su yanzu haka.
Balle ke da ba kowan kowa ba a gari kice wai ke kina jin kunya anganki a bakin rijiya.
Nace ciki ciki gaskiya mama ba zan je ba fa don wallahi ban san yadda zan kalli mutane ba da idona.
Eh lalai kuwa kin kai Rahama aure dadi idon ki ya bude don yanzu abinda na sani kin riga kin san shi shiya har nake fadi kina fadi ko ?
Nan ko ta hau fada ban san lokacin da wani kukan bakin ciki yazo min ba atake na shiga rera kuka.
Sai ga baba gidan kamar an jefoshi yayi mantuwa ya dawo gidan.
Tun daga kofan shigowa gidan yake jin muryan mama sai kuma sautin kukana dake fitowa daga cikin dakin mu.
Kai kai wai yaya hakane kuma may ke faruwa ne wai kuma yanzu fa na bar gidan nan na fita shine har zan dawo na samu gida ya rude may ke faruwa ne wai tambaya fa nakeyi ?
Tace isashiyar yar ka mana wai taje ta debo ruwa shine ba kunya wai har yarinyar nan ta kalli idona tace min ita bazata ba kunya take ji.
Baba yace haba lauratu wai har yaushe yarinyar nan ta dawo gidan nan da za, a fara jin ku da ita.
Yanzu koke ce kikaga ta dauki abin diban ruwa ai ki mata fada lauratu don haka bai dace ba gaskiya.
Tau ashe abin naku dama hadin bakine kukayi kun riga da kun shirya yar lele ta dawo gida ko ?
Baba yace kaji haukan ki ke nan ke wallahi yanzu don duniya su zage ni lauratu yarinyar nan jiya jiya da dawowan ta ace wai yau da safe har ta fara fita diban ruwa a rijiya.
Ki tuna fa mijin ta mutuwa yayi ba wai rabuwan dadin rai sukayi ba dashi da har haka zai kasance da ita.
Ya tako har kofan inna yana cew ke kama min bakinki ruwa dai ne nace bazaki diba ba su zauna haka ba ruwa in sai kin fita diban masu shi.
Maganan baba yasa na dan sasauta kukan da nakeyi tare da share hawaye na zuciyata yai min wani kololon bakin ciki dashi.
Mama tace aiko zaku ga tsiya a gidan nan don wallahi daga ita har uwarta ba yaron da zai debo min ruwa su taba shi.
Can bayan ta dan lafa fadan ta naji sallama a kofan dakin mu take na sheda muryan mai shi nace wa nake gani kamar habib.
Yace nice Anty naje can gidan shine akace min wai kin dawo nan yakarasa shigowa dakin yana zama tare da dan share hawayen shi dake zubo mai.
Nima kukan nake sai da mukayi mai isar mu wanda kowa da abinda ke damuwan zuciyar shi wanda idan mun hada damuwa guri daya zai dawo akan sanadin rashin Alhaji a tsakanin mu.
Nice na fara kawar da shirun da cewa yau habib ka tashi ka fita idan ka samu mai ruwa ka kira min na saya ina son nai wanka yace bari dai na debo maku anty.
Wanan randunan ne za, a cika ko na waje ?
Nace zaka iya kuwa Habib don rijiyan na da zurfi fa sosai yace zan iya mana anty ai kayan ba yawa ya dauki abin diban ruwa yafita daga gidan.
Lokacin mama tana nan ta hake ruwan da aka debo mata mayawa uku tana jiran mu taba tai muna cin mutunci akan shi.
Don daren jiya bata bar komai ba a randunan Inna ta don tsaban mugunta dama gadan zare ne ta shirya muna.
Sai ganin Habib tayi yana cika muna kayan ruwan mu gashi da kwazo nan dana ya cika komai na kofan Inna ta da ruwa.
Naje nai wanka nafito na shirya naji shi muka fice zuwa gidan mama Altine don bazan iya zama gidan mu na wuni tare da Mama ba a gidan.
Tana ganina ta shiga nuna jin dadinta na ganina sai dai kallo daya tai min ta fahinci nayi kuka a ranan .
Take cewa haba yar nan yanzu har yau baki daina wanan kukan ba gaki da manyan idanuwa kada kijawa kanki illa fa.
Na kai zaune ina murmushi nake cewa mama ba kukan Alhaji nayi ba.
Nan dai na kwashe yadda mukayi da mama da safe na fada mata komai take cewa kai amma anyi mutumiyar banza wallahi.
Yanzu ita bata tausaya ma halin da kike ciki sai ma nina halin ko in kula zatayi ,
Da tasan ciwon kan ta da ta tausaya maki don itama ai uwace tunda tana da yaya mata mata zaune a daki.
Habib dake jin mu yace anty kada ki damu nai maki alkawari kullun safe da yamma zanzo na cika maku randunan ku na ruwa insha Allahu.
Mama tace kinga ma Allah ya kawo maku sauki ta wanan hanyan kuma ba.
Can muka ci muka sha sai lokacin zuwa makaranta yace min zai tafi sai ya dawo.
Ban shigo gidan mu ba sai da akai kiran magariba ashe wai mama takiba su Inna abincin rana a gida sai dan dabara mama tayi tabawa kanne na sukaci.
Kamar wace ke jiran shigowa na sai ta hau bakin ta tana cewa ni dama nasan ai asoye da mutum wanan mutuwar don gashi har an fara yawon zawaeci ko.
Bamu kulata ba muka shige daki sai da dare ya dan yi na kwanta abina na barsu nan suna harkokin su.
Washe gari ban shiga gidan mama ba sai da na hada kayan Innata dana kanne na na wanke su fes na shaya na bar gidan.
Ganin har kwana biyu mama ta hana ma inna ta abinci yasa na fito da kudi dake hannuna na aiki habib ya sayo muna kayan abinci a kasuwa.
Nai sa,a mama bata gida muka shige da abin mu daki muka boye nace wa inna ta daga yau basai kin tsaya jiran na gida ba ki girka abinki kuci ke da yara kada yunwa ya illanta ku.
Da yake mama bata da kunya da inna tai abincin ta ta kwashe bata tsaya tambayan na gida ba ranan.
Don gurin mama Inna ta take karban komai na girki kamar yadda wasu matan hausawa sukeyi komai sai dai mace ta karba a hannun uwar gida idan zatai girki.
Haka ranan mama ta hake mama tazo karban kayan girki tai mata wullakanci yadda ta saba yi mata.
Amma sai taji shiru bata zo ba kuma gashi tayi girki kamshi ya bure ta ko ina dama kuka ne da dadddawa sai magi take karba gurin mama din .
Amma yau mama kamshin lafiyayyen girki take ji tana mamakin haka ba dama kuma ta tambaya don tasan akwai magana jiran baba ya dawo takeyi.
Inna ta sa yaran ta daki tabasu abinci suka ci suka koshi tai masu wanka suka shige ciki.
Itako bata girka ba wai ala dole Inna ce da girkin gida itace zata girka masu suci ita da yaran ta takwas.
Shigowa na gida daga gidan mama Altine dana taya ta aikin kuli kulin ta yai daidai da dawowan babana daga kasuwa.
Yake tambayana Rahama daga ina haka da wanan magariban nace ina gidan mama altine muna aikin kuli kuli da ita.
Yace hakan yana da kyau don zai rage maki kewa ai da zaman gidan da zakiyi na kwana biyu kafin Allah ya kawo maki mijin aure.
Muna nan zaune inna tana labarta min yadda mama take ta leken ta da take girki sai muryan baba mukaji yana kiranta ta kawo mai abinci.
Ba bata lokaci ta dauki tuwon masaran da tayi da miyan danyen karkashi ciki takai mai.
Ya zauna ke nan zai fara ci sai ga mama ta uso gurin tana zuwa ta jaye kwanukan abincin a gaban shi cikin hasala ya dago kai yana cewa yaya haka kuma ?
Tace ni za, a kawowa barkado a gida anshirya makirci ni na dama mutum na shanye indai gurin barkado ne.
Yace da akayi may tace wanan makiran matar taja bata girka tabamu ba duka gida shine kai zata girka ta baka daga kai sai diyan ta kawai iya bakin ku.
Mu may take nufi damu da bata bamu namu abincin da zamuci ba sai kai.
Kafin baba yai magana Inna ta take cewa kamar yadda kwana biyu kika hana min ni da yara na muci musha a gidan nan don kina bakin ciki da zaman mu cikin ku haka nima yau na girka na hana maki.
Lauratu may yai zafi haka da har zaki hana masu abinci a gidan nan ita da diyan ta.
Sai mama tace saboda ba yar aikin su nake ba nan ruwa a debi ka daurewa karya gindi wai Rahama bazata dibo ruwa ba waye dan aikin su.
Tsaki yaja yace amma anyi babban kwabo ke kan baki san girman ki ba wallahi ko .
Ashe ke kika fara an maki kuma kice kinji zafi tace zafin may abinci dai ne idan bamu ci baka cin shi kai ma indon ka akayi shi dama.
Inna tace idan kin hana mijin ki ci ki bani abinci na na mayar daki don kada ki fara ki ce zaki taba min abinci ko yanzu duk a rikice a gidan nan.
Tasan bata in ma Inna ta kuma tunda taji ta fadi akwai tsiya ke nan ranan don Inna ta hau.
Tace sai dai ki dauke shi amma bai cin shi Inna tace ai tunda yaci naki wanan ma kamar ya gama cin sa ai.
Ina daki ina sauraren draman su nace oh ni ko yaushe iyayyena zasu daina wanan kishin kauyen nasu haka ?
Gidan Alhaji da nai zama sabuwa ce kawai mai irin wanan matsalan a gidan ita kuma anfi karfinta bata samun yadda take so tayi a gidan.
Nan naji Inna ta tana cewa indai ni zan girka kuci keda diyan ki a gidan nan daga yau na kashe yi sai dai mu zauna da yuwan idan Allah ya bani abinda zamuci sai muci.
To, wooo yanzu nagane da kyau watau makiran diyar ki ta dawo gida irin mulkin da taje gidan Garbati ta kafa tasa aka raba talle shine tadawo muna dashi nan kuma yanzu ko.?.
Don kuji dadin cin karen ku ba babbaka ko ta baki isa ba wallahi Asiya.
Inna tace idan ma na usa ko ban usa ba ai yanzu ki gani na gaji da wulakancin ki gidan nan abu ba abu ba sai kice zaki horani da yara da yunwa to nagaji wallahi.
Baba yace ku dakata ni kan banda karfin raba maku tukunya nakawowa wanan nakaiwa waccan idan zaku gyara ku gyara yafi maku sauki.




ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, ,


IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH DON CIN AMANA NE YIN HAKA, , ,


Sanye take a cikin kayan sanyi irin na kasan turawa rigan yakai kusan gwiwan ta hakanne ga mijin nata kamar yadda tasaka kayan tare tsananin sanyin da akeyi a garin.
Yana rike da ita a kafadan shi suke saukowa daga matakalar benen gidan nasu wayan shi ce dake aljihun shi ta ruri a lokacin yadan tura hannun shi cikin aljihun shi ya ciro ganin wacce ke kiran shi a layin yasa shi daukan wayan nata.
Sai da ya sauke wani irin ajiyan zuciya yake cewa yaya akayi ne zulfa ?
Jin sunan wacce ya ambata yasata zare jikin ta daga nashi a hankali, tafara tafiya tako biyu zuwa bakin dayan kujeran dake falon.
Ta zauna tare da tsura mai ido daga inda take a zaune daga jin yadda yake magana ta tsigan lalashi ta san fitina ne ake da shi ga wayan.
Can taga yayi dan murmushi a fuskan yana cewa ke ma ai uwarsu ce zulfa don haka kiyi yadda ya kamata dasu mana.
Kofa likita bamu samu gani ba tukun ki ke wanan zance haka idan mun gama ai zamu dawo ne ko.
Bataji may tace dashi ba sai dai murmushin da taga yayi a fuskan yake cewa wata rana kema ai zaki bar naki a gurin ta ko ?
Don haka ki yi hakkuri kifitar da komai a ranki ina diyana diyan ki ne kema koda ba, a gida kike ba.
Can taji yace kwarai da gaske zulfa aiko ita kun san dalilin zuwan namu wannan lokacin ko.
Shiru ya dan ratsa falon yana sauraren mai maganan ta waya har ta taji shi yana cewa ok shike nan sai mun yi waya anjima ke nan.
Ya kashe wayan tare da dago kai yana kallon inda take zaune, ya dan yi murmushi .
Ya zauna gap da ita yana cewa yaya tafi mana ko kin kuma zauna anan ?
Ta dago idanuwan ta fuskan shi a cikin damuwa take cewa dashi akan yaran take magana ko ?
Bai bata amsa ba don yasan ranta zai kara baci ne ga banza yace tashi mu tafi ko ?
Da kyat ta mike tsaye ga dan matashin cikin dake a jikin ta ya turo a cikin rigan dake jikin ta.
Rai bace take magana tana fadin kaga abinda nake gudu ke nan tun farko nace ka bari na kai su gurin hibba su zauna har mu dawo amma kace wai a barsu su zauna agida tunda akwai mutane.
Ya jawo hannun ta yana fadin ke ma dai kin san bazan lamunci ina da gida da iyalina a ciki kuma na dauki diya na zuwa wani gurin ba.
Tace idan baka yarda an kaisu wani wurin ba ai gashi kana shan korafi akai ni dai tsorona kada a cutawa yaran da basuci ba basu sha ba kan zancen mu.
Haba Sa,ade Zulfa ce zata cutawa yarana kuma kada ki manta fa a matsayin yar uwa take a gareni fa.
Tace a da ke nan yanzu kan ai a matsayin diyan kishiya take daukan diyan ka gare ta.
Kofa ya bude masu suka fito daga gidan wani sanyi ne ya daki fuskan ta amma ba yadda ta iya dole haka zasu fita duk da tsananin sanyin da akeyi a garin
Don fitan ya zama masu dole sai sunyi shine dole zai sata fita a hakan.
Bayan sun gama da asibiti ne suka wuce zuwa wani shago nan ta dan yo sayayan abubuwan da ya dace ta tsinta har da tufafin yaran ta dana yaran abokan zaman nata.
Ko da suka dawo gida a gajiye take don bata da kuzarin da zata dinga tafiya haka mai nisa a jikin ta.
Zama yayi kasa a daidai kafan ta ya dan fara matsa mata su a hankali tana jin dadi hakan har cikin ranta ta dan fara lumahe idanuwan ta a hankali.
Haka yasa ta samu saukin yadda take ji a ran ta a lokacin sai bata samu wani matsala komai ba ga yadda take zato.
Washe gari ta riga shi sauko wa kasa don ta karya saboda yace yana son ya dan kara barci.
Har sai bayan ta gama ne sai gashi yau sauko kasan a lokacin har yai wanka yana saye a cikin kananan kaya a jikin shi.
Sau daya ta daga kai ta kalleshi taci gaba da duban wayan ta da takeyi tana murmushi a fuskan ta.
Da alama hiran da takeyi yana mata dadi a ran ta lokacin ya iso inda take yana cewa madam yaya jikin naki ?
Ta dan dago kan ta a hankali ta dube shi tana cewa Alhamdullahi ya kokari bai amsa mata ba sai da yakai zaune yace kokarin yiwa kaine ai nidai gurina naga Alllah ya rabaki da wanan cikin na jikin ki lafiya.
Sai lokacin tabar abinda take a wayan ta ta dago kan ta ta dube shi inda ya zauna sai suka hada ido dashi tayi saurin kawar da idon ta cikin nasa .
Yace No no no kada ki soma yi min wanan kukan naki dake tayar min da hankalina please ?
Yace cikin kamo hannun ta zuwa na shi cikin girgiza mata kai yake fadin ki dinga sakawa zuciyar ki dangana Allah daya baki ciki a cikin wanan halin da kike yasan dalilin yin haka a gare ki.
Don haka ki zamo cikin bayi masu rugumar kaddaran ubangijin su ako da yaushe.
Wanan tayar da hankalin da kikeyi zai iya kara jefa ki a cikin wani sabon tashin hankali kuma har mu dake tare dake abin ya shafi zukatan mu.
Ajiyan zuciya ta sauke tace dole na daga hankalina idan na tuna da lalurar dake tare dani sai ga shi kuma wanan cikin yazo ya shiga again.
Murmushi yayi tare da jawo ta ajikin shi yana dan shafa bayan ta yake cewa lafiya lau zaki haihu insha Allah ai ciwo ba mutuwa bane.
A hankali tace dashi abin ne ke bani tsoro sosai sai yake hanani sukuni a raina.
Ya girgiza mata kai yace ai abin bada ga nan bane heartbeat ke dai Allah ya kawo muna sauki ga al,amarin.
Sai da ya tabbatar ta kwantar da hankalin ta ya mike yana cewa zai dan fita amma ba zai dade ba indan ya fita.
Nan ya fice ya barta zaune zuciyan ta cike da tunanen yan diyan ta biyu dake gida Nigeria gurin kishiyan ta.
Tun ba akai ko ina ba gashi ta fara jin Zulfa din ta bugo waya tana korafi akan rikon yaran nata gashi zasu iya share wata uku basu koma gida ba.
Shine dalilin da tun farko taso zuwa da yaran ta ko tabar su gurin yar uwarta amma sai ya nuna mata rashin yardan shi ga hakan .
Don shi mutum ne mai matukar son iyalin shi a kusa dashi akoda yaushe haka ne yasa akwai shakuwa sosai tsakanin shi da italin shi don yana fitarwa kowa da hakkin shi yadda ya dace.
Wanan zuwan da sukayi dashi ba itace ya dace tabiyo shi ba amma saboda dalilin rashin lafiyan ta yazo da ita din.
Wanda kafin su zo saida akakai ruwa rana da sauran kishiyoyin nata akan basu yarda da hakan ba don acewa su yafi nuna kulawan shi akan Sa,ade da yaran ta bisa gasu.
Don har kara suka kai shi gurin iyayyen su kan abinda yake shirin yi masu.
Ita bata da ko labari sai dai ta fahinci ya dauki zafi da sauran matan nashi a lokacin.
Ita da ake abin akan ta sai daga baya ta fahinci rigiman akan tafiyan su ne akeyin sa.
Haka ne ya dan haifar mata da rashin natsuwa a tare da ita don haka ta bukaci da ajaye tafiya sai taga likitan ta na nan gida Nigeria.
Amma amma mijin tana yaki janye zancen ba irin rokon da bata mashi ba kan ya barta amma sai yaki

Please Login or Register in order to submit comment