Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

********* ******
Ganin ya juya zuwa dakin shi yasani fahintar fushin abinda nai mashi na rashin nuna mashi nai wanka da yadawo yayi.
Sai da na bata lokaci na sosai gurin gyaran jikina a gaban mirror na mike ina sake sake a raina na na kashe wutan dakin da A C nafito na nufi dakin nashi.
Na samu ya kwanta ya kashe wutan dakin a lokacin jin motsina bai sa shi koda dan motsawa ba a lokacin inda na tako zuwa bakin gadon na kwanta a hankali a bayan shi.
Bai motsa ba don jina saman gadon a tare da shi ganin ba zai motsaba nakwanta a hankali tare da dora hannuna a bayan shi.
A hankali na dan fara shafa mai bayan shi amma bai sashi motawa ba sai dai ya dan sauke ajiyan zuciya kawai da naji yayi.
Ban daina mai abinda nake yi ba sai ci gaba da nayi da mashi a lokacin ina kai gayi har na kai ga,tura hannu na acikin blanket din da yake rufe a jikin shi.
Inda na sauke hannu na a kan abin shi na fara dan amfani da hannuna ina dan shafan shi a hankali tun yana daure ma abinda nake mashi sai gashi ya gyara kwanciyan shi da kyau ta yadda zaiji dadin abin da nake mashi da kyau.
Ganin haka danayi yasa na ci gaba da mai yadda yake so sai kawai naji ya rugumoni shima ya shiga mayar min da martanin abinda nake mashi da farko.
Mun dauki lokaci mai tsawo muna farautawa junan mu rai a tsakanin ni dashi har sai da naga na kawar da fushin da akeyi dani da farko.
A hankali muke sauke numfashin mu don yadda muka aikatu da junan mu.
Hannun shi naji saman kaina a hankali yake kwantar min da gashin kaina da ya tarwatse a lokacin can ya sauke ajiyan zuciya yana fadin.
Fatima may yasa kika min abinda kikai min kika hanani more abinda Allah ya halasta min a kan ki.
Shiru nayi sai da ya kara maimata min tambayan nace a hankali yaya kayi hakkuri please ni da naji ba ka tambaye ni ba shi yasa na kyale ka
kawai don na dauko hutawa ne kawai kakeyi a ran ka.
Fatima hutu,?
Hutun may zan bukata a kan ki ke fa Allah ya kawo min ke daga cikin jin dadi na don may har kike bukatan wani huta na a hankan.
Yaya don Allah kayi hakkuri hakan ba zai sake faruwa ba insha Allahu.
Daga haka yai shiru tare kankamay ni a jikin shi sai dai naji ya furzo iska daga bakin shi kawai.
Washe gari nan na barshi kwance yana barci bayan sallah asuba da mukayi nima har koma na kwanta amma ganin yana barci yasa na dan zare jikina nafita daga dakin na gyara gida tare da doro muna breakfast.
Sallaman yaya Ahmed shiya sa na je na tayar dashi daga barcin da yakeyi.
Sai da ya dan dauki lokaci ya mike yafito falon yana saye da bakar jallabiya a jikin shi mai laushi.
Yaya Ahmed yana zaune sai bin falon yake da kallo ko ina yaya din yafito bayan har na kawo mai abin sha a gaban shi.
Yaya sadauki yace Normal kai ne yau gidan namu da safen nan haka ?
Yai murmushi tare da kurba drinks din shi yace na ce bari dai nazo tunda kai ba lokaci ke gare ka ba yanzun na mutane.
Yace kai haba kaine dai kawai bamu haduwa da kai amma ai muna haduwa da surfaco yana nufin Imiran.
Sai da suka dan kara gaisawa suka dan taba hira sai dan shiru ne ya biyo bayan kuma.
Fahintar da yayi yazo da magana ne kuma yana jin nauyin yin magana yake ce mai yaya dai akayi ne Normal ?
Yaya Ahmed ya dan murmusa tare da gyara zaman shi yace wallahi abin ne duk ya jagule min UF kwata kwata yanzun harkan san,ana yana son tsaya min gaba daya.
Don dan abinda ke hannuna da nake juyawa yanzu sam kokari ma yake na koma ba komai a hannun nawa gaba daya.
Gashikasan irin matar da nake aure yanzu sai a hankali ba kirki ke ga jamila ba ko kadan.
Sadauki na sauraren shi sai murmushi yake yana dan kada kafan shi a hankali daya harde su guri guda.
Yace yanzun yaya kake so ne don ban fahince ka bane inda zancen ka ya nufa gaba daya.
Yace so nayi ka dan ranta min wasu yan kuli don na samu naci gaba da harkoki na dasu kada abin ya kwanta min.
Sadauki yace kaman nawa ke nan kake bukata yace koda miliyan daya da rabi ne koma dai dayan ne idan zan samu zanci gaba da juyasu hakanan.
Ok ba damuwa inji sadauki yanzu kabari idan na fita don tashi na ke nan daga barci amma nan zuwa two insha Allahu zakiraka kazo ka samay ni can site di na.
Zai fara godiya ke nan ya daga mai hannu yace no haba ka bari mana wanan ba komai bane ai zan kiraka anjima insha Allahu.
Yai mashi tayin ya tsaya su karya tare amna Ahmed yace sauri yakeyi ya fita da murnan samun nasara gurin dan uwan nashi.
Wanka yaya yashiga yafito cikin kanan kayan shi masu kyau yya zauna ya karya sai dai kiran wayan shi da ake tayi yasa shi barin gidan da wuri hakanan.
Zai fita ne nake cewa yaya dama nace don Allah mutanen nan naka ko zaka dan taimaka masu da dan wani abu don naga wata yai nisa kasan abu ga masu iyali.
Kallon mamaki yake min yana gyara wuyan rigan shi yace wasu mutane na ke nan fa ?
Nace cikin yar murya karama masu gadin ka tunda a karkashin ka suke da zama nagani.
Humm kawai yace min ban samu amsa ba sai ce min da yayi sai na dawo ke nan ni zan fita ki bar wanan girkin zan samo muna abinda zamuci har na dare.
Don naga kaman aiki yana son yai maki yawa zan wa maji magana ta samo maki wacce zata dan dinga taya ki aikin nan haka.
Kawai nafi bukatan ki kwanta ki huta sai dai kawai ki kula min da shimfidana da kuma na yara in Allah ya kawo su.
Nace kai yaya har ina wani aiki dagani sai kai kawai a gida in ma hakane don debe kewa kawai da a taimaka min na roko kaunata Aisha ta dawo guri na ko boko itama ta samu tayi.
Shima shiru yayi bai min magana ba sai cewan da yayi ni na fita sai na dawo ki kwanta ki huta please.
Yana fita na kammala komai da zanyi na koma dakina kaman ko yasan ina da gajiya a jikina sai barci.
Yana fita har ya tayar da motar shi abu de mai get zai fita daga gidan yaja ya tsaya da sauri musa ya iso gare shi ya sauke glass din motan yace .
Malam musa uwar dakin tace min kuna a cikin bukata na taimaka maku dashi sai dai ban da kudi mai yawa a hannuna amma ga ashirin ku raba har muga abinda zai biyo baya kuma.
Nan yaja mota ya barsu suna ta zabga mashi godiya suna muna fatan alheri.

****** ********* ******
Ban falka ba sai kusan uku na rana na tashi a gagauce ne sallah tare da watsa ruwa a jikina na fito falo ke nan ban dade da fitowa ba ya shigo gidan.
Da ledoji guda uku a hannu da sauri na mike na karbi ledojin dake hannun shi nan ya zube saman kujera yana ce wash duk nagaji wallahi.
Bude ledan nayi inda naga take away ne yayo muna hadaden fridrice ne sai drinks da kuma naman rago mai zafi sosai.
Ba mu ko je dining ba nan na dauko plate muka zauna, muka ci muka sha a tare sannan muka dan dauko hiran zancen abinda su Umma sukai wa mama Nafisa ta fada mata.
Shi ya kawo min zancen amma a karshe ni ya bari da magana don shi ba ma,abocin son magana mai tsawo bane sosai.
Muna nan zaune aka kirashi da waya yafita fitan shi bai dade ba da fita sai gasu nafisa da kawayen nan nata biyu sun shigo gidan.
Suke ce min wallahi yunwa suke ji shine sukazo su ci abinci ban tsaya ba namike zuwa kitchen na dora masu abinci dafa duka nai masu yaji kayan hadi sosai.
Sai da sukaci suka koshi muna ta hira dasu suna ban labarin wani mutum da yaso ya yaudare su duk sun tsorace dashi suka ce suna ganin kamar dai mutumin dan cult ne ma.
Nace Anty ubangiji dai Allah yakawo lokacin auren ku ku huta da wanan rayuwan haka na.
Kowan su tace min amin amin sai yamma lis suka bar gidan nai masu godiya suna jin dadi suka tafi abin su na koma ni kadai a gidan.
Har na kara komai da zanyi na shiga nai sallolin na nafito falo musalin takwasa da yan mintina a kai.
Nai kwaliya na don nasan duk inda yake bai nisa da dawowa gida a lokacin.
Shiru shiru bai dawo ba har goma ya shude nayi sa,a ina kallon wani action film daya dauke min hankalina a lokacin.
Ko da zan daga kaina na kalli a gogo har shadaya da wani abu na dare a lokaci don haka namike tare da kashe kayan kallon na koma dakina.
Ban dade da shiga ba naji horn din shi ya shigo gidan maigadi yana bude mashi get.
Shiru shiru banji motsin shi ba don nasan idan ya shigo sai ya fara leko dakina don nasan cewa ya dawo.
Jin shirun da nayi ne yasani fitowa daga daki na falon yana da dan duhu sai na nufi gurin kunna wutan falon.
Zaune na hango shi saman kujera shi kadai ya dafe kai yyai share share yana barci a zaune.
Karasowa nayi inda yake a kwance din take na fahinci yau hannun agogo ya koma min baya yayi halin nashi ke nan.
Gani haske wuta yasa shi dan bude idanuwan shi da suke mai a buge ya dan kalle ni a cikin mayen da yake.
Cikin karfin hali muryan shi kasa kasa yace min ke kashe min wutan nan please ?
Sai da na dan tsaya a kan shi na dan tsura mashi ido na wani dan lokaci na juya na kashe mai wutan na shige dakina na kwanta tare da fashewa da wani irin kuka mai tsuma rai.
Sai dai duk yadda nayi nai barci na kasa yi don hankali na yana gare shi don nasan zai iya kwana a haka idan na barshi a gurin.
Tashi nayi tare da share hawaye na na nufi falon har lokacin yana a yadda na barshi da farko a gurin.
Dan bugun kafadan shi nayi nace mai ya tashi ya shiga daga cikin daki yace ke wani daki kuma nan ma gadon ai yayi min.
Da kyata har da zagi na samu ya shiga daki ya kwanta na cire mai takalman dake kafan shi don har dasu ya haye gadon gaba daya ya kwanta dasu.
Na jawo mai kofa na wuce zuwa dakina nasaka key kawai amma barci yaki daukana sai tunane nakeyi tausayin kaina dashi ya kara kamani nan naci kukana ba mai bani hakkuri har zuwa dare sosai barci ya dauke ni.
Da asuba na tashi nai sallah na koma na kwanta don idona cike yake da barci kodana falka har naso makara zuwa school ranan.
Gashi monday ne a guguje na shirya nafice daga gidan abina na samu masu aiki suna aiyukan su a waje nan suke gashe ni da min godiya jiya maigida yai masu alheri yace daga gare ni ne sakon.
Murmushi nayi kawai na masu sai na dawo na fice gidan zuciya tab da bacin rai da bakin cikin wanan irin rayuwan da na shiga.
Ina isa school na samu har lectura mu ya shiga ko na samu yabarni nashiga na zauna.
Bazan iya cewa ranan na fahinci abinda akayi ba a lokacin don irin yadda nai nisa ga tunane.

Sai sha daya saura ya falka ganin yadda lokaci yakai yasa shi mikewa da sauri ya fada bathroom yai wanka yazo yai sallah.
Inda ya idar da sallah ya zauna yana tunanen abubuwan da zai iya tunawa a lokacin .
Tabbas yasan nasan yasha ta juya ya kalli godon nan ya fahinci ban ma kwana a dakin ba ke nan.
Hakan yasa jin wani iri bai so shan komai ba ta yadda zan fahinci akwai abinda yasha amma sai yasha dozes da yawa yadda za,a fahinta yasha din.
Baiji dafin yadda yasha har na fahince shi ba sai yaji kunyan kan shi kawai ya kamashi da wani ido zai kalle ni yau.
Yuwan da yaji yasa ahi mikewa zuwa dining yaci abinci amma ya samu babu komai ya leka kitchen din yaga ba alaman ma na leka kitchen din yau.
Dakina ya nufa yaji shi a kulle sai lokacin ne ya tuna ai Monday ce nafita gidan ke nan zuwa school.
Koda muka futo daga class sallah nayi na koma cikin motana can na zauna nai kukana mai isa na maryam tana ta nana bata samay ni ba sai da tai dabaran zuwa gurin mota ta hangoni.
Ta kwankwasa min glass din da kyat na bude mata bayan na saita kaina .
Kallin mamaki take min motan ta shiga itama ta zauna tana min wani kallon zargi.
Can tace Bintu may ke faruwa ne wai?
Babu komai na bata amsa tai murmushi tace haba Bintu babu komai zaki shige mota ke kadai kina kuka haka?
May yafaru ki fada min nace ba komai anty tace da komai kan yaya ne ko ?
Shiru nayi saida takara cewa yaya ne ko ya tayar da halin nashi ke nan ko ?
Ban san lokacin dana fashe da kuka ba itama kukan ta fashe dashi tana cewa watau ashe yaya baibar halin nan nashi ba ke nan.
Nifa kwanaki yaya ke fada min cewa bai bari ba amma yasan zaki taimaka mai ya bari insha Allahu.
Nace ni anty yaya zanyi da wanan halin na yaya may yake son nai mai wanda ban mashi da zai min wanan sakauyan haka?
So yake idan na fita mutane su dinga nunani ga matar mashayin can ko may ?
Anty bazan iya ba gaskiya duk son da nakewa yaya dole na barshi yafi min sauki wallahi.
Tace haba Bintu inkiyi haka baki kyauta mashi ba dashi da maji dama mu yan uwan shi.
Baki ganin auren ki dashi ya kawo mai sauyin rayuwan shi da dama ya canza sosai kamar bashi ba.
Hakkuri zakiyi kawai ki jajir ce mashi ke ma kinuna mai yanzun kina da fawa akan shi kamar yadda take dashi akanki.
Tana saki yana hanaki kema din nuna mashi ke jaruma ce ba wai abin hannun shi kike so ke shi kike son ya gyaru ba wai abin alatun da yake kashe ki dashi ba.
Nan dai taita bani shawara take ce min kuma zata fadawa maji halin da yake ciki don itama ta tsawata mashi.
Da sauri nace kada ki fada mata anty ki bari na gwada nawa sa,an mugani idan bai bari ba sai mu sanar da ita.
Tace to shike nan amma gaskiya badon kince haka ba dana fada mata don ta san bai dena ba har yanzu.
Sai yamma na shigo gidan na shiga dakina nai sallah nan ma kuka na zauna nayi sosai a gurin sai da naji yunwa namike don neman abinda zanci tea nasha don hanjina ya dan warwale a lokacin.
Sai da nai sallah magariba ne na zauna ina tasbihi har akai kiran sallah na mike na gabatar da ishai.
Wanka na kara yi na koma kan gado na na kwanta sai ga kiran anty maryam ya shigo min muna cikin magana da ita ya shigo dakin.
Ban ta da kai na kalle shi ba na ci gaba da wayana kawai shima bai fita ba tana tsaye ya kura min ido kawai.
Sai da mukai sallama da ita ne yake cewa kin dawo ashe ?
Umm kawai na bashi amsa dashi batare da nai magana ba na juya ina saka wayana a caji kawai.
Ganin ba zan juyo gare shi ba yasa shi cewa abinci fa naga banga komai ba a table.
Ban yi ba na bashi amsa a takaice kawai.
Bakiyi bafa kikace nace mashi eh kawai.
Ya dan tsura min ido take ya gane cewa nasha kuka yadda idanuwa na suka koma luhu luhu dasu.
To may zaki ci dabaki girka ba nace ban jin yunwa ni daga haka na mike ma nashige bathroom don ban ko son ganin shi wallahi.
Ganin nashi bathroom yasa shi juyawa ya fita daga dakin fita yayi daga gidan zuwa sayo muna abinda zamuci da daren.
Jin yafice yasani fitowa na sawa daki na key kawai na koma na kwanta abina can bai wani dade sosai ba ya dawo gidan.
Murda kofan tayi yaji shi a kulle ya kwankwasa ban bude ba ya kira wayana jin kiran shi na kashe wayan gaba daya na kwanta abina.
Ganin bafa zan fito ba yasa shi ya zauna yadanci abinda yasayo muna duk da ba dadin ci yake ji ba a lokacin.
Haka yamike yaje ya kwanta cike da tunane kala kala ta yadda zai bullowa al,amarin namu.
Yasan baida gaskiya amma haka zai daure ya dakatar da abinda nake shirin haifarwa a lokacin nan.
Don shi yana ganin don may zan so takurawa rayuwan shi kawai ina ruwana da bukatan shi may ya rageni dashi na rayuwa da zance zan hanashi nashi kalar rayuwan.
Har barci ya dauke shi bai gama tunanen abinda ya dace ya aiwatar a kaina ba hakanan.
Washe gari ma kafin ya dawo motsa jiki har na bar gidan ko na fita yai mamakin hakan shi da kan shi ya nemawa kan shi abin karyawan da zaici.
Da wuri na dawo nai girki na aje mai saman table nashige ciki abina ban kara fitowa ba.
Yana shigowa a lokacin idon shi akan table yaga abinci a gurin yakai kallon shi ga kofana yana saye yasan dai ina ciki a lokacin tunda babu inda nake zuwa.
Dakin shi ya shiga yai sa,a yau ma na gyara dakin bakamar jiya ba da na hau sosai.
Murmushi yayi kawai ya shiga wanka a lokacin yafito yasaka kayan shan iska don zafi akeyi sosai lokacin.
Dakina ya nufa don ganin har lokacin ban fito falo ba ina dakina a kwance nake kasa saman ties idanuwa na a rufe ina bin kira,an dake tashi a wayana a hankali.
Ya dan dade tsaye sai jin nauyin mutum ya shigo dakin danayi yasa ni bude idanuwa na da suke min a rufe.
Yana tsaye a kaina ya saka hanayen shi a cikin aljihun wandon shi tare da kura min idanuwan shi.
Ganin shi tsaye a kaina bai sa na bude idanuwan nawa ba sai kara lumshesu danayi kawai.
Dan tsugunowa yayi tare da rage tsawon shi ya tabo kaina da sauri na bude idona na watsa mai wani irin kallon tsana da ban masan lokacin da nai mashi shi ba.
Yace ki taso muci abinci nace akoshe nake ya mike tsaye yana cewa to sai kizo ki zuba min ai.
Nace ai banice mai zuba maka kwayan ka ba idan zaka sha don haka sai kaje mai baka kayan mayen ka ta baka amma bani Fatima ba.
Da mamaki ya kalleni yace ke kada ki soma kice zakiyi min rashin kunya wallahi.
Nace da ke nan da nake daukan ka a mutum ba yanzun da ka zube min ba.
Ke ni kike fadawa haka watau kin raina ni ko don kin ga kamar ke kin isa ko may wai.
Nace aini ban isa ba kuma ba kowa nake ba don haka kowa tashi tafishe shi kawai.
Kaman zai yi magana sai kuma ya juya yafita daga dakin ran shi a bace yana ci yana kallon kofa na ko zan fito daga dakin amma shiru har ya gama babu alamana a falon.
Gaba daya taji gidan ba dadi ban fito ba sai ma da naga tara da rabi na dare kawai na kulle kofana na kwanta kawai.
Goma da rabi ya kashe kayan kallon da komai na falon ya shiga daki sai da yasa kayan barcin shi har ya kwanta ya mike zuwa dakina ya murda a rufe kofan yake a lokacin haka ya juya ya koma don yasan bazan bude ba.
Bai taba tsanmanin cewa akwai shakuwa haka a tsakanin mu ba kuma ba zai iya daure rashi na ba a yanzu sai da yaga yai rabin kwana yana lalaban gefen da nake kwantawa bai jini ba.
Nima a nawa bangaren kusan hakane na kwana da kewan shi duk da haushin shi da nake matukar ji a lokacin.
Kowan mu da tunanen dan uwan shi ya kwana a ran shi cikin damuwa muke .
Tun da safe ina kitchen ina hada abinci yazo bakin kitchen din nai matukar mamaki da bai fita motsa jikin shi ba yau.
Kamar ban san yana gurin ba na share shi ya tako har zuwa cikin kitchen din inda nake tsaye ina motsa dankalin dake saman gas.
Ganin da yayi bazan mai magana ba yasa shi cewa kin tashi lafiya ?
Nabashi amsa da lafiya kawai.
May yasa kike rufe min kofan ki kwanan newai Fatima ?
Dagowa nayi muka hada ido kawai sai na kawar da kaina naci gaba da abinda nake yi ina tunanen watau bai masan abinda yayi ba ke nan koko tsaban rainin wayyo ne hakan ?
Ke nake tambaya ya maimata min .
Kaina na girgiza mai nace ina kwashe dankalina a tunkuya a hankali.
Nace ban da amfanin komai a gare ka don shaye shayen ka yafini daraja a gare ka nagani.
Don haka kaje kayi abinka kabarni na yarda na zama ma yar aiki kawai a gida don shine ya dace dani.
Murmushi yayi ganin zan wuce ya dan ja dabaya ya bani hanya yana fadin wanan kuma maganar kice amma ni shana baida alaka da kusantar ki a gare ni.
A ganin ka ba amma ni bazan taba mu,amula da mutumin dake a cikin sabon Allah insha Allahu.
Ido ya zuba min don jin abinda nace ya fahinci a shirye nake na zuba mai bakaken maganganun dake a bakina a lokacin.
Shiru yayi ya dan dade tsaye a gurin yana kallon yadda nake aikina a cikin tsabta da gwanewa sai ya juya kawai yabar kitchen din zuwa falo ya zauna cikin damuwa.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,


A LOKACIN MU KE,,,,


Gaba daya na daina kwaliya a gidan na daina fitowa falo yadda na saba na zauna a tare dashi, gashi wasa wasa mun fi sati daya haka sai zaman yar tsama mukeyi a tsakanin mu.
Shi kan shi

Please Login or Register in order to submit comment