Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ragowa.
Uban yaro yafara rusa kuka yana ya shiga uku ina zai shiga ya samo wanan kudin haka masu yawa.
Dole aka fara neman inda za,a samu kudi don a taimakawa yaron dake cikin wahala.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,


A LOKACIN MU KE,,,,,,,


Tun bayan fitan yaya Sadauki a falon dakin shi ya nufa kai tsaye ya fada a kan katifan shi ya kwanta yai lamo tankar wanda yake barci, sai dai ba barcin yake ba.
Damuwa ce tayi masa yawa a ran shi a hankali wasu yan siraran hawaye suka rika silalowa daga idanuwan shi.
Ya dade a haka ya mirgina gefe daya yana fadi a fili, wayyo rayuwata may yasa nake yawan tsintar kaina a cikin mawuyacin halin komai na tashin hankali akaina yake faruwa ni kadai a gidan nan.
Allah ya jarabci rayuwana da masifa saka uwata a tashin hankali ko da yaushe .
A yadda ya lura maji ta dauki son duniya ta kwallafa mashi shi kuma gashi ya kasa bata farin cikin rayuwa.
Ya kai zaune daga kwancen da yake yana cewa ya Allah kada kasa na zamo sanadin jefa uwata a masifan rayunwata.
Gashi tunda ya tafi waje bai mai da hankali ga sha ba amma yana dawowa gida sai ji yake zuciyar shi tana azzalzalar shi sai da yaje yasha ya samu natsuwa a zuciyar shi.
Ba don wanan yar kauyen yarinyar mai saka ido ba da ta taimake shi da bai san yadda zai yi ba idan maji tafito ranan ta fahinci a buge yake.
Can kuma ya tuna zancen baffan shi wai ba zai ba mashayi yar shi ba shi dama Rahama bata gaban shi abudai ne in Allah ya nufe ka dashi ba yadda zakayi.
Tuna siffan Rahama yayi bai san lokacin da ya sake wani tsuki ba akan wanan abin har za,ai masu wulakanci shi da uwar shi a cikin gidan su.
Yana da,budurwa da ta lake mai yar adamawace amma saboda zancen Rahama da maji ta nace shiyasa ya,fita zancen ta kuma yarinyar irin masu son abin duniya din nan ne ko yaushe cikin bani bani take shiyasa bai son al,amarinta.
Sai dai abinda ya daure mashi kai shine kishiyoyin mahaifiyan shi da bai san may tare masu ba haka a rayuwa.
A,sanin shi dai komai yana masu wanda ya dace in ma ba yanzun da yaga tsana tayi yawa a tsakanin su dashi ba yake nisanta kan shi da al,amarin su.
Kiran wayan shi akayi bai tsaya duban ko waye mai kiran nashi ba ya daga wayan tare da karata a kunnen sa yace hello.
Muryan Fatiman adamawa ce tace sweety na baka kirana sai dai ni na kiraka ko?
Dan guntun murmushi ya sake iya bakin shi, yace Fatima ya akayi ne, ?
Tace my life nayi missing dinka sosai, tunda ka tafi gida baka kirani ba banji daga gare ka,ba.
May yasa kake min hakane, baka damu dani ba sai nice ke yawan nuna damuwata a kan ka,
Yai yar guntun murmushi yace Fatima bakiyi min komai ba wallahi nima rashin ki yana damuna abubuwane sukai min yawa a nan gida shiya sa baki jini ba.
Tace karike min kanka kada kaci amanata don min ni taka ce, ka sani.
Yayi murmushi tare da,cewa ban maki alkawarin ni naki bane don haka ban dauka ba.
Dariya tayi daga bangaren ta tace kanace ina wasa ne ko gaskiya nake fada maka.
Yace ni ban yi alkawari ba don ki sani aure ma zanyi very soon don har an kammala komai ko.
Cikin wata irin murya mai karfi tace what are you joking?
Yace bana wanan da ke ai gaskiya na fada maki tun farko ina da mata a gida da zan aura.
Kalaman Sadauki sin tayarwa Fatima adamawa da hankali don haka sun gama waya bayan ta kashe ta kasa zaune ta kasa tsaye shawara daya ta yanke wa ranta shi kuma zatayi.
Washe gari haka na muka tashi ba dadi a gidan kowa zuciyar shi a cushe take mai.
Daga cikin matan gidan su mama ba wace ta damu da damuwan mu sai sha,anin su sukeyi da raha da yaran su.
Hjy kubura ce kawai ta shigo dakin namu zuwa rana don Saturday ne bata fita ko ina.
Ta samu na hada wa mama abin kari ina duke ina zuba mata sugar tai sallama falon.
Muka karba mata take cewa, daidai lokacin maji nace nabar mata sugar hakana.
A,a hjy maijidda ke ma bakin son sugar ashe da yawa ni gashi na rasa yadda zanyi na daina shan wanan sugar don ba lafiya yake ba mutane a jiki ba yanzu.
Murmushi Maji tayi mata tace ni sugar dama bai damay ni ba wanan yar tawa ce ma take yawan son samin sugar ko yaushe.
Ta zauna saman kujera a kusa da maji nan muka shiga gaishe ta mummy ina kwana tace lafiya yau ana gida ba,a fita ba ne.
Maji tace sun samu hutu ne shiyasa kika gan su a gida tace ayya har hutu yazo ashe?
Nan ta juya gurin Maji tace ashe kuma haka Alhaji sani yai muna akan zancen yaran nan ?
Maji tai dan murmushi tace kila shine yafi zama alheri a rayuwan su damu ma gaba daya.
Amma gaskiya Alhaji sani bai kyauta ba yaci kafa bai yada ganye ba yadda Alhaji ya rike shi har yakai haka kuma yanzu kan yar matsalan rayuwa zai kawo wanan dalili haka.
Ai yana da gaskiyan shi don ba mai son ya dauki dan shi ya bayar inda babu tarbiya.
Haba sadauki ne baida tarbiya hjy maijidda sai dai ace kawai wanan lalurar dake kan shi.
Kuma wanan aiba wai wani abin da za,a ki mutum bane kan shi shidai kawai yana da wata manufa ga hakan ne kawai ya sha zugi daga cikin gidan nan.
Tau koma dai maye sai ya,rike dan shi shima Allah ya bashi wata wace tafita ba shi ke nan ba.
Hjy kubura tai matukar mamaki a ranta yadda maji tai saurin basar da zancen a lokaci guda.
Don ita a zaton ta abin zai jawo mata matukar tashin hankali amma sai gashi tashi daya sunga ta basar da zancen ita ma.
Shiru sukayi a lokaci guda falon babu wanda,yai magana a cikin su sai hjy Kubura ta mike, tana cewa dama cewa nayi bari nazo na jajanta maki kan al,amarin.
Maji tace nagode Allah ya saka da alheri, ai zaki kai ga sarakuwa ba da dadewa ba insha Allahu.
Lokacin Bintu ta shigo dauke da ruwan da maganin maji a hannun ta .
Sai ta ce yar gidan maijidda ni dai da ma da Bintu kika hadasu da zaifi don kin san halinta tasan nashi.
Gaba daya muka kalli hjy kubura wace ni ban ma fahinci maganan ta ba,sai da naji mama tace ai da hakan zai faru sai nafi kowa farin ciki .
Da sauri hjy kubura tace mai zai hana hjy maijidda abu tuwona maina.
Fatima tana da mijin ta da zata aura ai bada dadewa ba ma zasu kawo kayan auren ta.
Allah sarki ashe har wani ya riga mu niko tun jiya nake anyana hakan a raina, wallahi ni dai da haka zai yiyo da yafi komai sauki wallahi.
Gaskiya ba zai yuyo ba a haka ma ya suka kare kullun yana samin yarinyar gaba da hattara sai na jajirce mashi akanta.
Wanan ai ba matsala bace don bari zasuyi dasunyi aure amma wanan cin fuskan da Alhaji sani yaiwa mutane ban son a wuce lokacin auren nan Sadauki bai samu wata ya aura ba.
Komai na Allah ne inji maji tace an auri mahaukaci ma balle dan shaye shaye,
Hjy kubura tace ai shine lokaci ne dai bai yi ba amma sadauki yanzun ai abin so ne ga ko wace mace.
Zasu dawo suna da sun sani ai a baya don sun wa yarsu ai ba wani sukaiwa ba amma may ye abin kushe ga sadauki inba wanan harkan ba.
Tana fita dakin su maryam suka ce munafuncin banza kawai kamar da gaske.
Maji ta katse su tace ko na munafuncine tayi min don shine dama zaman kishin.
Tafi sauran dake ta nuna farin cikin su akan al,amarin amma ita dai ko tana da manufa ta dai nuna halarci ai.
Sai maryam ta,kwashe da,dariya tace kaji mummy da,wani zance wai Yaya Sadauki ya auri Bintu.
Kirmitsi ke nan inji Amirah, tace cikin kwashewa da,dariya, sai kuma tace wallahi fa da sun dace, don itace kawai ta karanci rayuwan shi.
Nace don Allah Anty bari zancen nan kina son ya kashe ni ke nan mama tazo ta kwashi gawata.
Maji tace da shima na kashe shi ranan yadda ya kashe min "ya.
Aka kwashe da dariya a falon nan sukai ta hira suna dariya wanda hiran tasu nake jin yana kona min zuciya daurewa kawai nayi ina dariyan yake.
Kada nai magana mama tace nima na kyamaci dan ta duk halarcin da zatai min amma saura kiris nace wa zai auri wanan kazami.
Don ni yanzu balain haushin da takaicin shi nake ji don wallahi duk yafita raina kwata kwata.
Sannu sannu aka fara rage zancen don sunga wa yanda su keyi a kan su basuma damu da zancen ba don ko a jikin su ma.
Min fita zuwa kasuwa don sayo yan abubuwan da ake bukata a gurin mu na girkin mu ni da Anty Amirah muka fita,mun bar maryam tana girki a gida.
Komai mun sayo harda ma abinda muka manta bamu saka a list ba duk mun sayo da sauran canjin hannun mu.
A gajiye muka dawo gida da kayan mu niki niki, nan muka zube a falo bamu dade da zama ba sai ga yaya yashigo wanda shigowan shi gidan ke nan tun safe da ya fita.
Tv yana kunne ya zauna suna kallo da maji suna gaisawa tambayan inda ya shiga take tunda safe haka.
Ya dan yamutsa fuskan shi yace wallahi ina cikin gari ina dan zagawa ne kawai.
Maganan da ake a tv shi ya daukewa kowa hankali a falon don photos wani yaro aka nuno bai wuce shekara sha, goma ba zuwa sha daya.
Wai wani yai mashi fyde ana neman gudun mawan gurin mutane don a,tallafawa iyayyen shi ai mashi aiki.
Salati falon ya dauka lokaci guda ga mahaifin yaron annuna yana kuka yana bayani acikin tv.
Hankalin kowan mu ya tashi nan maji tace oh wanan duniyar ina zaki damu haka yanzu wani daukan alhakine wanan karamin yaro haka ace wai kato yai mashi aika aika haka ba dadin gani.
Maji bari na,dawo abinda ya fadi ke nan ya,mike yabar falon da sauri.
Ashe yana fita asibiti ya nufa gurin da aka sanar akai taimakon kan yaron nan sadauki ya ba da kudin aikin dubu dari biyu dana sayen magani amma yace kada a fadawa mutane shine.
Amma duk da haka abin yanzu bai boyuwa don saboda al,amarin media da yai yawa.
Da dare muna zaune falo sai hira ake yana tare da uwarshi suna maganan da ta shafe su amma mu hankali mu baya a kan su.
Maganan da ake a TV ya mayar da hankalin kowan mu akan tv din labari ne akan yaron da aka nuna dazu da yamma.
Nan suke sanarwa cewa an samu wani matashi mai kishin kasa da addinin shi yazo yabiya kudin aikin yaron tare da daukan nauyin duk wani magani da za aiwa yaron har yaji sauki.
Wanan kuma ba kowa bane sai matashin dake tashe muke alfahari dashi acikin garin nan watau UF.
Shahararen dan wasan kwallon nan dake bugawa kasa kwallo yanzu ayaune kuma muka samu labarin yatafi wasu unguwanni na,tallakawa inda yaiwa mata da yara marayu kyautan kudi da kayan abinci da sutura.
Waya ya dauka ya kira wani nomba zai fara magana yaga wani irin kallo da uwarshi ke mashi na mamaki.
Yace yanzu danace kada a nuna wanan abin sai da kuka nuna amma sai mai labaran ke fadin duk da yace mu boye shi kada mu fadi wanan alheri nashi ga al,umma.
Munga ya dace ace mun fadawa duniya don matasa masu hannu da,shuni irin shi suyi kishi da halin shi suma.
For god sake banji dadin wanan nuna program din nan ba da kasa ayi cikin fushi ya kashe wayan nashi.
Sadauki muryan maji ce take cewa dashi wanan alheri keyi a gari haka bamu da labari.
Dukar da kanshi yayi kasa yana cewa maji Annabin rahama yace idan zakai alheri ko hannun hagun ka kada ya sani,
Amma kinga mutanen nan sai da suka baiyana ni a fili haka.
A dakin Umma kuma tana ganin abinda ake fadi ana yabon sadauki tace cikin wani tsawa don Allah ku kashe min wanan shegen karyan haka kafin na,bata maku rai.
Dole yaran suka kashe TV suka kunna kaset suna kallo ba don ran su yaso ba don sun fi son suga labarai akan dan uwan su saboda yanzu akan shi har wani jiji dakai suke a gari.
Baba kuma yana zaune a falon shi yaga wanan labarin sai cewa yayi Allah nagode maka da wanan baiwa da kaimin ta tsatsona.
Gidan hjy saude kuma tana kallo taja tsuki tana cewa aikin banza adai karata can, sai ga yarta tashigo dakin tana cewa yanzu ake min waya wai anga yaya sadauki yana raba alheri a tv.
Ke rufe min baki ki rabani da zancen wanan mashayi mai kyau dan maciji.
Nafada maki ki fita zancen wanan mara mutuncin, yaron da baida tarbiya ko kadan.
Rahama tace mama amma ni gaskiya na fada maki na ina son shi ko a hakan.
Bazaki so shi ba nace yaron da akace idan yasha har fitsari yake a wanda da amai kacakaca shine zaki wani ce nabarki ki aure shi bata karasa maganan taba Rahama tasa kai tabar dakin cikin turo baki gaba.

Washe gari mukayi bakuwa a gidan mu kowa bai santa ba sai dai tashigo gidan tana tako daidai da ita tana tambayan mahaifiyar U F.
Mama Asiya tai mata nuni da dakin maji cikin binta da kallon ke kuma daga ina.
Tana cewa o mun shiga uku U F kuma a gidan mu kamar gidan wasu arnaku can mukan wanan yaro yazama muna jaiba agidan nan wallahi.
Daga kofa ta tsaya tana sallamu alaikum daga ciki muka amsa mata.
Tashigo yar gaye ce ta karshe ga kyau ga ilimi yana nunackan shi a fili.
Sai data zauna take cewa maji tare da dan zaudowa saman kujeran ina wuni mama.
Lafiya kalau inji maji tace kunzo lafiya ta amsa da fara,anta lafiya kalau mama.
Sai sukai shiru maji ce tai karfin halin fadin ban fahince ki ba don ban sheda ki ba yar uwa.
Mama baki sanni ba,
well na dai zo ne nan don daki Umar U F ni yar adamawa ce ina son na auri yaron ki ne shikuma ban samu kan shi ba shiya sa nace bari na zo na nuna kaina a gare ku.
Don Allah ko daddy din shi yana gida shima mu gaisa dashi, don yasan ni na san shi.
Ikon Allah inji maji tace mahaifin nashi yanzu baya nan ya tafita yana kasuwa.
Tace ok ba matsala ai ina garin zamuga juna da dare idan ya dawo gida.
Sai ta wani harde kafan ta daya saman daya tana taunan cingan a bakin ta kas kas kas.
Mukan ido muka zuba mata wanan fitsara haka wai zamani ina zaki damu hakane?
Kai A LOKACIN DAI MU KE KAN,,,
Juyowa tayi inda muke a zaune tana cewa, sannun ku fa yan mata ya kuke cikin wani daga muna hannu?
Ni dai na mike zuwa ciki na hado mata kayan drinks na kawo mata ta karba tana cewa yauwa na gode fine girl.
Waya ta dauka ta kira layin shi mun dai ji tana ce mashi yazo gida gata nan dakin mama.
Nasan tambayan ta yayi wata mama, sai cewa tayi mummcy mana ta sokoto.
Dama na kusa karasa abinci na mike nafita, zuwa kitchen na duba girki na na samu ya dahu nan na tsaya na hado ma,bakuwar mu abinci mai kyau dashi .
Daga kitchen ina jin muryanta tana,waya sai kiran abokan ta take tana fada masu tazo sokoto yanzun haka tana dakin mumm din U F a zaune.
Sai gashi da saurin shi ya iso gidan tun a kofan gida ya sheda da gaske takeyi tazo garin don ganin motan ta da driver ta dayayi.
Tun da sadauki ya diso falon yaji wani irin bacin rai ya kama shi a ran shi yake fadin wai may mata suka mayar da kan sune yanzu?
Ya shigo da sallama a lokacin na fito daga kitchen dauke da abincin da zanbawa bakuwar mu.
Tana ganin shi ta saki wani shu,umin murmushi tare da cewa my man you think iam joking ko ?.
Ta wani shagwabe murya tana cewa I really miss you alot and i can't keep it,
Dole na biyo ka don nazo na ganka nakuma ga su mama da little sisters din mu.
Sadauki ya dan shafa sumar kan shi da hannun shi na hagu ya dan kalli inda Maji take zaune cikin kallon ikon Allah.
Don yasan yau sunga fitsara a gurin Fatima ba kadan ba don ita bata da kunya ko kadan.
Tace ya naga ka,wani bata rai ko you are not happy with me here ne?
Yace cikin yanayin su na yan duniya No ba haka na bane ban dai yi expecting din ki a nan bane.
Tace ai na fada maka zan baka surprise dama to gani yau a,sokoto kuma dakin mummcy.
Yace saukan yaushe ? tace wallahi dazun nan na iso dama nasan bazan sha wahala ba gurin gane gidan ku don sha haranka.
A kaduna na kwana shiya ka gan mu a wanan lokacin, amma fa gaskiya akwai nisa.
Yace to ya hanya?
Tai wani har da idanuwanta tare da langabe kan ta tace hanya lafiya kalai tunda na gan ka.
Sadauki ya juya inda maji take zaune ta hade rai ba yabo ba fallasa a fuskan ta a lokacin.
Ni dai na,aje abinci ina cewa, ga abinci nan tace yauwa sannu little sister wai ya sunanki ne tunda nazo kike wahala dani.
Sai da na dago daga duken da nake nace Bintu tace wawwwo, sunan mu daya dake ashe.
Amma ki daina cewa kanki Bintu kamar wata yar kauye akiraki da,Fatiman ki kawai ai nice, name ne sunan mu.
Sadauki dai yakai zaune daga dayan kujeran nan bakuwar ta mayar da hankalin ta a kan shi suna dan hira jefi jefi.
Wanka na,shiga na fito na saka wani dogon riga light gren mai kamar bubu daga sama kasa an mashi sharp yafito da sura na na,daura dan kwalin shi a kaina.
Sam na ma manta cewa da bakuwa a falon nan nafito ina cewa Anty Amirah wai yaushe ne zamu tafi gaida baban su Amata.
Wai wanan pretty din itace last born din mune gaskiya tana da kyau sosai wallahi.
Kamar bazai bata amsa ba sai can yace No diyar sister din maman mu ne ita ga dai sisters dina Amirah ga maryam itace yanzu a,matsayin last born din mu.
Yanzu ita wanan din ba blood sister dinka bace yace a dan hasale na fada maki yadda muke da ita ai ko.
Take ta hade fuskan ta, tace there's problem here yace akan may fa tace No barshi ina dai magana ne kawai.
Maji bata falon tashiga ciki don bata iya,karasa hadiyan takaicin da yazo mata har dakin ta yau.
Wanan abin haka ba kimtsi ke kiran kanta da,suna wai sarakuwarta ta ina ?
Kai duniya kowa da,tashi matsalar dai kenan yanzu ita haka duk rabin jiki kusan tsirara shine wai tazo nuna kanta a gurin sarakai a haka.
Kai wanan tanbadewar da fitsara da may yai kamane haka wai tundaga wata uwar duniya yarinya ki taso kice wai kinzo gurin na miji.
Ban kai ga zama ba naji muryan maji tana kirana daga ciki da sauri nake na nufi gurin ta.
Zaune take saman gadon ta hannunta yana rike da caunter na zikkiri take ce min har yanzu wanan fitsararar bakuwar taku tana nan ke nan bata tafi ba ko?
Nace ai zaci anan zata kwana ne don naga daga nesa ta fito.
Tsaki taja tare da kawar da kanta a gefe tace yaro zai jamin wani sabon abin fade a gida yaya zanyi na fada mashi yai gagawan fita da ita gidan nan kafin mutanen gidan nan su ankara da ita.
Nace mama bani wayan ki ta mike min gurin sunan shi nai mashi massage kamar haka.
Ka gagauta fita da ita kafin mahaifinka ya dawo yasamay ta nan.
Na tura mai ina turawa nafito daidai ya fara karantawa wani kallon ke ko yabini dashi.
Nace sannu da zama ko wani kallo ta watso min kamar tasan nice na turo mai da sako yanzu tace yauwa.
Amirah tace, yau zaki koma dai ko?
Murmushi tayi tare da,gyara zama tace a,a har kun gaji da nine ke nan ko Amirah tace a,a ha mutum ai bai gajiya da bakon shi.
Yana gama karata massage din ya dagi kan shi sai kai mukai tozali dashi ina kallon matar .
Harara ya,kara watsa min niko nai mashi dariyar mugunta a fakaice.
Muryan shi mukaji yana fadin Fatima muje na kaiki inda zaki sauka kafin dare yayi cikin diriricewa.
May kake nufi da hakan ba a nan zan sauka bane gurin mummcy ?
Yace baki da hankali ne a cikin gidan namu zaki sauka don baki da kunya to mu nan ba haka al,adan mu yake ba
Yace so ki tashi na kaiki kafin dare yayi ban son daddy na ya dawo ya samay ki a gidan nan haka.
Don mu ba haka al,adan mu yake ba ya mike don dale itama bashiri tamike tare da daukan hand bag din ta tana cewa ina mummcy muyi sallama yace ta shiga alwala ke nan.
Yana gaba tana bayan shi suka fice daga gidan aiko basu dade da fita ba sai ga Baba ya dawo daga kasuwa a lokacin.
Sai da suka bar uguwar ya sauke ajiyan zuciya tare da cewa look Fatima bai nai maki wullakanci bane da hakan amma idan har mahaifina yadawo ya samay ki a gidan akwai matsala babba wallahi.
Kakanki kin sani wanan tsarin da kikazo dashi ba tsarin mune na hausa fulani ba.
Tai wani wal da idanuwan ta tace nima nasan da hakan amma ban dauki wanan a wani abu can da zai iya kawo maka matsala kamar ka babban yoro haka.
Yace wai ma ba wanan ba may yakawo ki garin nan ne wai Fatima ?
Fatima tai wani marairaicewa tare da kallon shi cikin wani yanayi tace,
Matsala aka samu danaji kace an maka mata agida ana batun auren ka shiyasa na kasa zama naga gara nazo ayita a kare a gaban iyayyen ka.
Sadauki

Please Login or Register in order to submit comment