Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

mama din.
Akace wa babana to kai kaji abinda ya fadi sai da baba ya share zufan dake karyo mashi yake cewa baida wanan labarin .
Amma abari yaje gida ya tambayi mai dakin shi yadda akayi haka don shi dai bai san komai ba akai.
Sadaki kawai ta nuna mai kuma suna hannun ta tace zataiwa yarinya sayaya da su ne ya bar mata a gurin ta .
Nan yabar fada maimakon suji haushin shi sai tausaya mashi sukayi don sun san baida tacewa a gidan shi don mama tafi karfin shi.
In bashi sadaki da maza ke karba ina mace ina karba sadaki hannun mijin yarta.
Washe gari da aka sake tuntuban shi kan zancen Inna sai cewa yayi suje ya sauwaka mata .
Wanan labarin yai matukar tayar muna da hankali sosai dayazo muna kowa na ma baba kaico da rabuwa da Inna dayi.
Don yayi hasaran macen rufin asirin shi a duniya gashi tana haifa mai diya kyawawa masu tarbiya yace ta tafi da kanne na maza biyu duk ya yafe mata don mama tace bata rika su.
Sabon tashin hankali na shirya ni da mama sai gidan su Inna ta a yadda nai tsanmanin na samay ta cikin damuwa sai naga sabanin haka don dan kwana biyun da tayi har ta dan murmure sosai abinta.
Nan hankalina ya dan kwanta muka ba juna magana take ce min indai naga zaman bai min gurin mama na dawo nan na zauna tare da ita a gidan su.
Nace inna banda matsala gurin mama ko kadan tabkar a furin ki nake zaune a gidan ta don haka zan zauna gurin ta kusa da babana watakila idan yana gani na ya sauko ga fushin shi a samu ku shirya dashi.
Tace Allah sarki yarinya idan har kina hasashen komawa na wanan gidan to kina kaunan mutuwa na ke nan.
May zai mayar dani gidan Audi kuma indai ba wani ikon Allah ba kuma ai na bar gidan shi har abada insha Allahu.
Banji dadin hukuncin Inna ba nashiga damuwa take cewa dani na kwantar da hankalina gurin mama in Allah yakawo min manemin da hankalina ya kwanta dashi a daura min aure na nima na huta.
Cabdijam ni zawarci uwata zawarci dawani ido mutanen gari zasu kalle ni dashi ace auren uwata ya mutu akaina ko may.
Cikin tashin hankalin da na wuni ke nan a gidan su innata ina lalashinta ko zata sauko in baba ya huce ya aiko bikon ta ta koma dakin ta amma fir inna tace badai ita ba kan.
Haka na dawo gida da dare gidan mama ban gane komai ba a gurin Inna sai hakkuri da kwantar min da hankali da tayi.
Ina shigowa gida na samu mama tana waya ga alwal mai wayan sadawa tsaye kofan gida uana jiran tagama abashi kudin shi ya tafi.
Ko ban tambaya ba nasan da yarta take waya a lokacin don yadda naji suna magana na fahinci hakan.
Don naji tana cewa yanzu haka ma rikicin auren ta ake a gari don uban ta ya kara jajibo mata wani tsohon wai ta aura har kai tashin hankalin daya sauwaka wa uwarta tabar gidan nasu.
Banji may tace ba sai cewa tayi abani waya naji mama tana ce min karbi wayan anty ki ce daga birni ke magana dake.
Nakarba muka gaisa da inta take ce min ashe abinda ya faru ke nan Ramana ?
Sai na sa kuka take cewa nayi shiru na saurareta zata dawo wani sati in Allah ya yarda da tadawo zata turo a dauki mama sai mu taho tare da mama na huta da kauyen nan idan ba a ganni ba aibabu mai saka ido a kaina kuma.
Nan dai tai ta bani magana har na gamsu da maganan ta mukai sallama muka awal wayan shi da kudin shi yatafi yana godiya.
Mama tace min kin dawo a lalace na amsa mata tare da neman guri na zauna ina cewa ehmama.
Tace ga abincin ki can dauko kici nace da ita mama na koshi kunu kawai nake son na dan sha na kwanta.
Ina cire kayan jikina ne naji mama nace kinji abinda yar uwar ki ta fada ko akan ki.
Nace naji mama amma ai al, amarin babane da wuya don nasan mama bazata bari ba idan taji tace nima hasashen da na keyi ke nan Allah dai ya haushe mu kan ta.
Mun bar zancen don ko inna ta ban fadawa maganan ba kada hankalin ta ya tashi sai in abin ya tabbata zataji.


****** ********* ******
Bai fadawa kowa dawowan su kasar ba bayan sun gama ganin likita haka ita ma yace bai son ta bugawa kowa waya zasu dawo.
Taja bakin ta tai shiru bata fada ga ranan da zasu dawo ba gidan har suka shigo b Nageria ba wanda yasan da zuwan su.
Karfe goma sha biyun rana suka sauka gida kano ya daukan masu shatan taxi din airport sai gida.
Alama ya nuna matan gidan basu gida a lokacin duk da weekend ne ranan hutu don motocin su baya gida.
A can kan hawa step din gidan ne ya hango Nasir a zaune yayi tagumi sai Amira dake tsaye bayan dan uwan nata tana wasa tsaletsalle akan steps.
Tun hango yaran ya sauke ajiyan zuciya yaran basu damu da tsayawan mota ba a haraban gidan nasu sai harkan gaban su sukeyi kawai.
Muryan mahaifiyar su ne sukaji tace Sweethearts da sauri yaran suka yo kan su cikin murna da jin dadi nan ta durkusa tare da rungumay su zuwa jikin ta sai kuma ta sake kuka.
Ya gama sallaman mai taxes yazo inda suke shima suka rungumay shi cikin murna yake tambayan su ina anty ta tafi yaran sukace tun safe bata tare da mu sunfita da yasmin a mota.
Ciki suka shige da kayan su wanka ta fara yiwa yaran tare da canza masu kayan jikin su tabasu abinci sukaci don sunce yunwa suke ji a lokacin.
Har tagama abinda takeyi bata ga shigowan shi ba gurin su haka yasa ta tsamani ko ya kwanta ne a lokacin don ya huta.
Dakin shi ta nufa don taga halin da yake ciki zaune ta samay shi a saman kujera yayi tagumi da hannayen shi biyu ta hayan rike haban shi dasu.
Sallaman ta yasa shi dago kai yana kallon ta yake cewa har kinyi wanka kin dai ci abinci ko ?
Tace munci nida yara kaine dai naga baka zo kaci ba shine na biyo ka nagani ko ka kwanta ne ?
Yace No banci ba kuma banjin ci din .
Haba dai saboda my kuma heartbeat kai dake da gajiya tare da kai ka tashi kai wanka kaci wani abin ko ?
Yace zan dai yi wankan amma bazan iya cin komai ba gaskiya yanzu sai zuwa anjima .
Wankan yayi duk tana zaune tana jiran shi har yafito ya shirya suna dan hira jefi jefi sai dai bai sako mata zancen matan gidan ba itama batai mashi ba tafice daga dakin nashi ta koma gurin yaran ta.
Har goma da rabi na dare sai lokacin ne Zulfa ta dawo gidan da yarta daka gansu kasan a gajiye suke tafe lokacin.
Wutan falon dake a kashe take kokarin kunnawa a lokacin don akwai dan duhu gurin haske wutan waje ne ke shigowa kawai.
Tana kunna wuta sai ganinin shi tayi zaune a falon ya harde kafafuwan shi yana kallon ta yace kashe min wuta ki wuce ciki bayan ya gama kallon wayan hannun shi don diba time.
Simi simi ta shige part din ta hankalin ta a tashe don tasan bata kyauta ba bata rike mai amanan da ya barmata ba na yaran shi.
Bayan yai bugun gaban ita yar uwar shice tajini yabar mata yaran shi amana suka tafi ganin likita da matan shi a Uk.
Shadaya da dan kai sai ga hindu ta parker itama alokacin kamar yadda zulfa tayi hakane tana fada tana cewa don iskanci sai abi wutan ma akashe don sallon mutum ya fadi yaji ciwo ke nan.
Gashi a zaune fuska a daure yasa ta cewa dear saukan yaushe babu ko waya a shirya ma dawowan ka.
Ido kawai ya tsura mata tare da kallon agogon bangon dake manne a falon .
Itama agigon ta kalla cikin firgici yace miko min baby nan ki koma inda kika fito.
Tace kamar yaya nakoma inda nafito kuma gida fa na fito yace will you do as i said ?
Babu sauki a fuskan shi ta bude baki zata ce dear kayi hakk, , , , ya dakatar da ita cikin daga hannu yace please tun raina bai baci ba nai maki abinda baki zata ba ki aje min ya ta kibar gidan ?
Ganin ba wasa yasa tai mai yadda yace yarinyar dake barci a kafadan shi ta aje mai a saman kujera ta dan juta sai kuma taja ta tsaya ya nuna mata hanya da hannu dole tasa kai tafice gidan.
Gidan su ta nufa shi kuma yasa maigadin shi ya rufe mai get kada ya fara ya budewa koma waye yazo da daren nan.
Yace angama ranka ya dade kamar yadda kace haka za, ayi ban bude gidan nan sai gobe da safe.
Yana shiga dakin Hindatu ya nufa ya samu tana tsaye tagama saka rigan barcin ta a jiki tana shirin kwantawa.
Daga kofa ya tsaya tana ganin shi ta mayar da hankalinta gare shi yake cewa da ita abinda yasa ke bazance kibar gidan nan yanzu ba kamar yadda naiwa Hindu shine koda kin bar nan nasan gidan Daddy zaki nufa da nan da gidan daddy duk daya ne a gare ki don haka gobe karfe takwas na safe ki tabbatar da kin bar gidan nan baki alaikum.
Hankalin ta ya tashi tana shirin mashi magana ya fice dakin nata ran shi a bace ya koma part din shi ya kwanta.
Haka suka kwana rayukan su a bace ranan kowa da abinda yake ji a ranshi sai Sa, ade ne tai barci a tsakayin yaran ta hankali kwance cikin jin dadi.
Kafin ya kwanta sai da ya shigo dakin nasu ya samu sunyi barci ga wuta a kunne basu kashe ba ya kashe masu yafice daga dakin .
Washe gari haka ta tashi ta gyara yaran tare da abin karyan wasu duk lokacin bata san matan gidan basu gidan ba ma ita.
A zaton ta ko wace na dakin ta kwance ne don halin su ne hakan ta koma ta kwanta don agajiye take.
Hayaniyan da take ji yai yawa a falo yasa ta fitowa dakin ta sai gani sarakan ta tayi a zaune suna magana sai dai babu maigidan cikin su ga Hindu a gefe zaune cikin damuwa.
Hajiya ce ta kalle ta a lala ce tace a, a matar iko matar mulki matar so anga daman fitowa ke nan.
Hajiya ban ji shigowan ku bane gidan ina barci yanzu naji magana nafito nagani.
Bashi na tambaye ki ba ai duk abinda kukayi don kanku ke dashi in cin amana abin yine sai ku matsa kuyi tayi ni dai na fada maki in ma wani abin kukai mashi don ku rabani dashi Allah yafi ku ke da iyayyen ki.
Murmushi tayi tare da fadin ayi hakkuri hajiya kamar kullun maganan ta ke nan tsakanin ta da uwar mijin nata.
Shi mijin naki ance ya bar garin ko da yake yasan abinda ya shuka na rashin gaskiya.
Tace ya tafi nw ko ?
Hajiya tace rufe min baki mara gaskiya kawai ai bakin ku daya dashi.
Bayan kun tafi shakatawan ku kun bar yarinya da dawainiyar yara kuma zaku dawo ku saka mata da sheri.
Ai duk inda yaje zai dawo ne ya samay ni gidan ba inda zai gudu min ko ?
Ke kuma koma ki zauna dakinki har ya dawo muji hujjan shi na maki wanan danyen hukuncin haka.
Don yana dan wullakanci yabi wayoyin shi ya kashe don kada a samay shi balle ai mashi magana ko ?
Hindatu tace yanzu maigadi da zamu shigo ya bani wanan takardan inji shi yace abani.
Hajiya da yar uwanta gurin hada baki suke cewa takardan may ?
Tace a, a cewa yayi kada na fara na zauna mai a gida har sai ya dawo in ba haka ba a bakin aure na.
Salati suka saka hajiya tace lalai yaron nan ya kai dan rainin wayo na gaske yar uwarta tace yaya tunda ya furta haka kada ta zauna tazo mu koma tun abu bai lalace ba.
Hajiya tace babu inda zata zama zatayi inda ya dawo in ya isa ya sake ta mu gani.
Hajiya ai wanan maganan dayayi a matsayin sakin yake in har ta zauna maigida aure ya kare a tsakanin su ke nan.
Inda Sa, ade take ta kalla tana cewa tsohuwar banza kawai kin samu yara kina masu wayo yadda kike so.
Shiyasa tun farko ban so wanan bakin auren naku ba don ke sam ba sa, an auren shi bane.
Fin karfi na kawai akayi amma wanan da nake gani da wuya in bata girmi dogon sarki ba
Hajiya mu tafi tunda baya gari har ya dawo sai asan abinyi don yanzu bata lokacin muke a hanka don ba komai zamu gane gurin wanan ba in ma mun tsaya.
Haka suka fita suka bar gidan suna sababi inda suke shiga ba nan suke fita ba akan zagin Saade.
Suna fita takai zaune tare da dafe cikin ta da taji yana mata motsi take cewa haba heartbeat yaya zakai min haka ashe yasan abinda ya shuka ke nan yace na shirya yaran su tafi makaranta idan sun dawo kuma anan zasu zauna tare dani.
kanta girgiza kanta cikin takaici may yasa ko yaushe yake abinda zai ja min zagi ga mahaifiyan shi ne bayan yasan irin zaman da nake gidan da hajiya.
Maigadi ne ya shigo ya katse mata tunanen ta lamban waya ya bata yace inji maigidan wai yabata idan ta tashi barci.
Gurin maigadi take ji wai iyayyen hindatu ma sunzo neman shi ya bata takardan da yace a bata kamar yadda yaba Zulfa na ta.
Layin shi ta kira ya dauka ba bata lokaci zai fara magana ta tare shi tana cewa heartbeat may yasa ko yaushe kake jawo min abin zagi ga yan uwanka da iyayyen matan ka ne ?
Yace ke ki saurare ni kada ki fara kiba kowa nomban wayan nan idan bani nace ba tace kai kana ina ne yanzu ?
Yace yanzu na sauka Abuja zan wuce office ke nan ki kula da shan maganin ki a kai kafin na dawo don da na dawo zamu tare sabon gidan mu da yardan Allah.
Allah ya kai mu tace yace kada ki manta da zancen zuwan mama na kauye da kikace zata zo ta zauna dake sai ki tura Hamza driver idan yakai yara gobe yaje yazo da ita.
Sukai sallama ya barta da mamaki don yaki bari ko suyi wani magana sa ya shafi zancen matan shi da ya tura gidajen su.
Suna gama wayan ta kira Awal mai waya ya sada ta da mama din lokacin ina zaune na saka lalle a kafana naji sallaman shi kofan mu.
Ya kawo wa mama waya sukai magana kan gobe driver zaizo ya dauke su don haka su shirya da wuri kafin yazo.
Mama tace tun ranan da mukai magana dake mu a shirye muke take cewa kiba mahaifin Rahama dubu ashirin hakama mahaifiyar ta dubu ashiri hamza driver zaizo dasu insha Allahu.
Suna gama wayan awal ya karbi kudin shi ya tafi mama ke cewa dani kumshinki yazo a sa, a gobe ne tafiyan mu in Allah ya yarda.
Zanje na samu mahaifinki muyu magana dashi inji ta bakin shi akan tafiyan ki in ya yarda sai mu tafi idan kuma yaki yarda sai ki koma can wajen Innan ki har lokacin da na dawo.
Tunda ta kafe bazata dawo gidan ku ba har abada tabar gidan ke nan , Allah dai yai mata sauyi da mafi alherin sa.
A sanyaye na amsa da amin badon naso don dai kawai addua ce ta alheri tai mata.
Da yamma da baba ya dawo kafin ya shiga gida cikin hikima mama Altine ta samay shi a waje da zancen don zancen bai yuyuwa a cikin gida don mama lauratu.
Bayan sun gaisa sama sama dashi don haushi mama yake ji da ta barni gidan ta duk da gidan dan uwan shi ne amma yana jin takaicin haka don yaso tabarni na bi uwata can mukarata gidan su.
Mama acikin hikima takw mai magana tace to Audi dama zancen wanan yar ne Rahama dake gurina.
Don gobe zan tafi birni ganin diyata kuma zan kwana biyu shine nake son zuwa da ita don kaga babu kowa a gida idan ka yarda da hakan.
Yace Altine na fada maki ba yau ba ki rabani da zancen yarinyar nan a rayuwana na riga na gama magana akan Rahama.
Ba kano ba duk inda zata ita dade bata tafi ba babu ruwana a cikin harkan ta na fada maki ko.
To shike nan tunda haka kace mu Allah ya bamu ikon rike maka ita amana kamar yadda ka bar muna ita din.
Yace indai wanan irin tsiyane ai kice nace maki watarana akan ta mama tace ba amin ba tunda mun gama maganan ta ko dakai.
Ta banye kudi a haban zanin ta tana mika mai kallon kudin yake a cikin mamaki yake cewa na maye wanan din tace dama yar tawa ce tace a baka kayi hakkuri dashi ba yawa.
Sai da ya dan juya yana kallon kofan shiga gidan shi baiga kowa ba yai sauri ya karba yana fadin an gode ya shige gida har yai dan nisa mama ta juya zata shiga gida taji yace ki dai ja mata kunne ta kula da rayuwan ta a can Allah ya tsare tace amin nagode da karamancin da kai min.
Da tashigo ne take fada min yadda sukayi da baba nake cewa Allah sarki baba abin nashi akwai daure kai a ciki wallahi yana son iyalin shi amma tace ta raba shi dasu da karfi da yaji.
Mama tace ba abinda ya bani dariya sai waigen da yakeyi kada angan shi yana karban kudi yasan idan ta gani yau basu kwana aljihun shi.
Da dare muka tafi sallaman inna ta nan mama tai mata bayanin komai mama tace wa inna ta ina rokon ki Asiya ki bari yadda mahaifinta ya bari ta tafi ke ma kibarta Allah kuma yasa hakan shine Alheri ga rayuwan ta.
Don ni zaman ta gurin Saade zaifiye min zamata a kauyen nan ko bazan ta kara sanin duniya.
Inna tace ni na isa in hanaki yadda kike so da yarinya tsakanin mu dake sai fatan alheri da neman gamawa da duniya lafiya.
Allah yasa yarinyar nan gurin ta na karatun da take son yi ya cika ta wanan hanya.
Mama tace zata barni mu dan gana na kwana a gurin ta don sai zuwa gobe da rana zamu tafi in Allah ya yarda taima mama godiya takawo sakin Inna rabata tana godiya.
Bayan tafiyan mama inna sai faman nasiha take min na kama kaina na zama ya ta gari abin alfahari ga kowa nan gaba don wata rana sai labari.
Naji matukar dadin nasihan Innata ga albarkan da take ta saka min yafi a kirga
Kwana nayi ina tunanen yaya rayuwana zai kasance a gurin anty Saade ko baba zai yarda ya barni nakai ga samun cikan burina a rayuwa.
Da safe na shirya zan tafi gida gurin mama inna takawo adduoi tabani tace na fake na kula da yin su ko yaushe don suna da falala da faida nai godiya naiwa kakannina sallama nafice gidan tare da jaddawa Innata zancen karatun kanne na kada a bari ya dakata masu.
Shiko baba sai da zai bar gida ne washe gari yake fadawa mama cewa kinji wai Altine zata birni da yarinyar nan.
Wani uban ashar ta lailayo ta watsa ma mama Altine tana cewa munafuka makira dama ta fahinci duk itace mai hura muna kunne akan halin da muka tsira yanzu ni da uwata .
Da sauri tace kai may kace mata kan magan tafiyan da ita ?
Yace may zance da ita banda Allah yakai lafiya idan na barta nan din wani abu zatai min ban da karin bakin cikin da zata jefani ciki kawai.
Jin haka tace malam kakoyi tunane kafin ka bada bakin tafiya da ita birni tana nan ma bamu inmata ba balle rashiga birni idon ta ya bude ai watarana ma sai tace bakaine ubanta ba don raini.
Don haka wanan magana ajeye shi babu zancen tafiya gare ta ba inda zata tafi tana nan cikin mu dadi da wuya haka zata zauna garin nan.
Yace yanzu kan sai anjima in na dawo nai mata bayani don na makara kada mota ya wuce ni na rasa.
Abinda ita dashi basu sani ba yaune tafiyan mu zuwa burni sai dai baba ya dawo ya samu labarin tafiyan mu kawai gurin jama, an unguwa.
Komai na amfani mama ta dauka takai makwabtan ta boyo kayana dake gidan ta tasa an kwashe ankaiwa inna ta gurin su.
Haka yasa na fahinci tafiyan namu mai dadewa ne don ban taba ganin haka ba wani bako ta dauko da matarshi da suke yawon neman gida tace ya zauna a dayan dakin dake gidan da iyalin shi.
Sha biyu da rabi na Rana hamza driver na kofan gidan mama ba bata lokaci muka kama hanya.
Da zamu shiga mota yara sun fadawa mama lauratu sunga motan birni kofan gidan mama Altine sai gata tafito daidai mun fito zamu shiga mota.
Nan ta buga kasa tana fafin ba inda mama zata dani don ubana ya hana tafiya dani mama tace da ita kin makara don ni ubanta ya riga ya sallama min ita kamar yadda kika bukaci yai masu ita da uwarta to tun jiya mun gama magana dashi ko.
Nan taje har da tare gaban mota ta baje hannayen ta wai sai taga yadda za, a tafi dani birni.
Tana jin hamza driver yasa giyan mota tsoro ya kamata ta ruga da gudu gefe tana Allah ya isa tsakanina dake mai kuli kuli.

****** ********* ******
Mota na tashi nabi kauyen mu da kallo hawaye na zubo min a idona una tuna rabuwana da mahaifiyata da yan uwan haihuwana.
Biyu da rabi shaf muna cikin garin Kano ta Dabo jalla babban hausa yaro koda may kazo anfi ka .
Sai bin garin nake da kallon mamakin ikon Allah gine gine kamar ba mutane ne sukayi shi ba da hannuwan su.
Abin hawa tun ina girgawa har bakina da zuciyana suka daina aiki sai binsu da kallo kawai nakeyi.
Mutacan mu wuce nan driver na ta aikin tukin shi sai ga mu wani katon unguwa mai gine ginen zamani kala kala.
Muryan mama ce ke cewa dani ikon Allah Rahama yau gaki birni a kanon dabo tunbin giwa yaro ko da may kazo anfika.
Nace mama harda maita da sata sunfi kowa tace yarinyar sawasa kin ganki mayan ka.
Nace aiko har

Please Login or Register in order to submit comment