Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

san haka ne.
Kada ki manta iskancin namiji ado ne a gare shi duk yadda ya iya lalacewa bai rasa macen aure a duniya itako diya mace fa ?
Ke tsohuwar kilakiya kada ki manta mun san komai wallahi, nan kikagama tambadewan ki ba mashinshine in bashi alhajin dayazo yatara ba ya dauko muna masifa a gida.
Kin ishe mu kin ishi diyan mu wai ke adole ga yar bariki to anriga ki indai barikine a gidan nan don gidan kikazo.
A haka cure ake barikin don shifa bariki iyawa ne dama don kinga ashe nafiki iyawa ke nan tunda kika fadi.
Dariya mummy tayi tace wai a haka ashe ke bariki kikeyi ke nan ba,a sani ba ko ?
Nafisa dake daki tayi tatil da ita ta leko tana fadin Umma rabu da wanan gajar matan mai muna mazuru muna shaho.
A,,,, mu,,mun,,san komai,,,wallahi, ikon Allah ai gara kija yar mayer yar ki daki kafin wani ya shigo yaga wanga tabaran nata a fita damu waje.
Haushi da takaici ya kama umma da Nafisa ta bude bbaki zatai magana ta wani daka mata tsawa tace don Allah rufa muna baki kinji kin jawa mutum gori a gida kawai.
Haka sukan ta faman jidalin su ita da mummy da bata iya hakkuri idan tana habaicin ta.
Maji dai bata kan tanka mata sai dai tai shiru kawai tace tabar ma Allah kuma Allah ya tsare mata zurian ta.
Irin wanan jidalin yakan tayar wa Baba da ciwon shi wani lokaci sai ya kwanta asibiti saboda bakin ciki dake damun shi gashi duk wanda ya sanshi sai yai mashi korafi akan Nafisa abinda takeyi baida kyau a gari.
Ranan dai ya tara iyalin shi yai masu fada sosai yace da mazan da suka isa aure da matan kowa ya fiddo da miji da mata aure duk aurar dasu zaiyi gaba daya kowa ya huta a gidan dasu.
Yace kai Imirah na fada maka ka kawo mace kafin na zaba ma da kaina wallahi kaji na fada maka.
Ya juya gurin mama Asiya yace danki yace min muje gidan yarinyar da yake so aiyi zancen auren su.
Mama tace ba dai wanan yar iskan ba da ta tsohe mashi ga shekaru da komai yace shi din maye inba halin su daya ba a ina suka hadu da ita?
Tunda yace ita yake so kuma shi zai zauna da abin shi ke ina ruwan ki da zancen su ne wai?
Zan tura iyayyen shi suje nema mashi auren ta nan dagobe insha Allahu.
Mama ta tubure tana fada tana zagin Ahmad tace badai ya auri wanan karuwan yarinyar ba agidan nan.
Baba yace ai sai mu zuba mu gani tunda kece zaki zauna mashi da ita ai kina bani mamaki wallahi.
Ki fara tambayan danki yaya ya hadu da ita kafin ki fara zagin yar mutane haka nan.
Ya juya gurin mamana yace idan danki ya dawo ina son ko fada mashi sakona yafito da mata na da karshen sabon wata duk aure zasuyi muddin ina raye a duniyan nan.
Mama tace shi sadauki yana da mata kuma na yaba da tarbiyan ta kwarai yace mashs Allahu haka nake son ji dama.
Duk gurin sun so sanin wacece matar don su sani ko yar gidan maikudine ko wani kusan gwaunati can.
Don kada yazo yafi diyan su zaben yar gidan mai kudi azo ana mazu feleke a gida.
Haka dai akabar falon kowa da abinda ke cikin ranshi manya da yaran su na gidan da aka kira.
Ina daki a zaune suka shigo kowa sai gunaguni takeyi maji dai ta shige tabar mu nan zaune muna hira.
Amirah ce takira yayan ta da waya take fada mashi hukuncin da Baba ya yanke akan su.
Yai dariya yace Amirah kice mun kusa shan buki ke nan yan kanne na sun kusa zama amare.
Tace bamu ba ai harku yaya don yace wa su Maji wallahi duk fito da matan aure a aura maku dariya yai mata kawai.
Tace yaya kai kaga abin dariya ma ni wallahi duk na rude na rasa may nake ciki ma aallahi.
Yace ina samarinki ba sai ki fitar da daya ba kawai a zarga maki dashi, tace yaya ni duk fa basuyi min bane na ma rasa wa zan tsayar a cikin su ni wallahi komai ma ya jagule min yayana.
Yai dan murmushi yace kibari zandawo month end sai mu san abin yi tace ni dai da Baba zai min hakkuri ne har faba dayafi min.
Yace No Amirah ki godewa Allah fa gaki har kin gama karatunki ma may kuma kioe so yanzu inba aure ba kuma.
Tace yaya ke nan bazaka bashi hakkuri ba har zuwa gaba yace wa ni rufa min asiri please bari mu rabu lafiya da Baba don Alla dai.
Tace yaya naji maji tace wa Baba wai kai kana da mata shine mu bamu san wanan lucky girl din ba da tai wanan sa,an haka?
Yace No,No Amira maji ta dai fadawa Baba hakane kawai don ta kare ni gare shi ammani for nowa ban da kowa a kasa tukun na.
A kwai da wata wadda nake son fada masu akan ta don yar kasar ghana ce sai dai akwai matsala gaskiya.
Matsala kuma yaya ?
Yace eh don ba musulma bace Christian ce ita sunan ta Linda.
Yaya kafira kuma ?
Yace eh amma ai idan munyi aure zata musulun ta ne insha Allahu.
Tace ashe kuwa akwai case ke nan nasan maji da wuya ta yarda gaskiya don yadda bata kaunan kafirai ko kadan.
Ni dai daka jaye zancen ko zaka samu wata nan gaba ku shirya yar asali yar gari.
Yace ban ma san ni may yasa suke son mutum yai aure bane yanzu wallahi.
Amirah tace kasan maji kance ita dai muyi aure don yanzu Life is to short knowadays.
Hakane kuma fa Amirah gaskiyan maji ne rayuwan yanzu dan kalilan ne gaskiya.
Yace ni nasan zamu kwasa da parents din mu dama both don ko ita parents din ta takw ji yanzu.
Shiyasa tace zata zo Nigeria sai muyi auren mu kawai sai daga baya iyayyen ta su sani.
Amma ban yarda da wanan ba ni don ban son ni ai min haka gaskiya.
Tace yaya ai matsala shine yaran da zaku haifa zasu zama ruwa biyu ke nan fa?
Yace kai Amirah akwaiki da shirmay wallahi ni fa ban ko tunanen yin aure yanzu balle wasu iyali can .
Yaya kadai yi tunane kafin kazo da maganan nan gida don za,a samu matsala sosai wallahi.
Ki bari kawai idan nazo sai mu san yadda zamu bullo wa zancen cikin sauki haka zaifi ai.
Tace ni wallahi maji nakejiwa akan zancen nan don nasan halinta akan abinda bai mata ba.
Yace ke dai kawai kiyi shiru ban son kowa ya ji wanan zancen a bakin ki sai nazo tace shike nan .
Nan sukai sallama,dashi yace ta kwantar da hankalin ta yana nan zuwa month end insha Allahu.
Suna gama waya gulma yaci Amirah ta kasa barin zancen a ranta tace wata sabuwa wai yaya kafira zai aura fa ashe?
Muna hada baki da maryam gurin cewa kafirah fa kika ce antu ?
Tace wallahi yanzu yake fada min wallahi wai yar kasar ghana ce ita
Sunan wai ko Linda ?
Nace wayaga Leather ke nan kuma ?
Kai baima yuyuwa gaskiya kafira arniya mai fitsari a tsaye zai ce zai dauko muna.
Muji da wani irin gori da habaici gidan nan kuma ba,a gama wani ba har yau a fada wani ke nan kuma.
Ai da su Umma an samu abin dariya ke nan a gidan nan wallahi don shi za,a aza a faifai kuma ana talla lungu lungu inji maryam ke ta sababi haka.
Tace ni wallahi har girman shi ya zube min wallahi arniya fa Allah tsare mu da ita a gidan nan.
Diyan shi sai su girma suma su zama kafirai ke nan ko ?
Nace to shine daidai daahi don shima ai zuben yare ne gare shi baka taba ganin yaya kace mai dan hausawa ne kullun yana cikin kananan kaya irin nasu.
Ke Bintu inji Amirah yaya din ne mai zubin arna kuma?
Nace rufa min asiri anty kada yajini nawa ya samay ni a gidan nan kuma .
Maryann tace na rasa may yasa mafi yawan yan kwallo suke auren diyan kafirai wallahi.
A ji anty marayam fa ba,a cikin su suke ba suna ganin su kullun may zai hanasu fadawa tarkon su.
Shine ai tunda dasu suke mu,amula can suna ganin su fa ko yaushe inji Amirah.
Sai da muka watse ne zancen ya tsaya min a rai na nace cikin zuciya na ai dama muguntan mutum ke cin shi.
Yaya za,a kana dan musulmai kace arniya zaka aura a haka ma yaya aka iya dakai balai ka auro kafira mara sallah kuma.
Wanan kan sai yadda Allah yayi dashi kan don ba ranan shiryuwa gare shi ke nan kuma.
Ai su gasa junan su da mugun hali sune ma daidai da halin shi, ai tunda shi yace shi mugu ne su karata, can wallahi.
Maji suna waya take ce mai ka sayo kayan da aka taba a cikin kayan lefen ka don a cika.
Yace cikin murmushi maji ai yanzu angama yayin su kawai a rabawa yaran nan sai na hado wasu kawai amma kada a taba gold din don akwai wanda na sayo da tsada tun lokacin.
Mani tace zan dai zabi na kwarai na aje idan ka kawo sai akara ciki kawai yace duk yadda akayi maji shike nan insha Allahu idan zan dawo zanzo dasu din.
Sukai sallama tana mashi fatan alheri da saka mashi albarka tana rokon Allah ya tsare mata shi ya shirya su baki dayan su.

****** ********* ******
Kamar yadda yace karshen wata zai dawo hakan ne da yammacin asabar sai gashi a gida nan aka shiga murna ana zuwa gaidashi.
Nikan tunda muka gaisa na gudu falon na shige don ina tsoron wani disgi kuma ba wuya gareshi ysi min shi yanzu da dawowan shi.
Sai hira sukeyi maji da bata san bani falon ba tace don Allah Fatima dauko min jakata a daki na.
Maryam tace wata Fatima maji Bintu kan ai dodon ta ya dawo tashige ciki tun dazun.
Itace ta shiga ta dauko jakar ta leka ina kwance daki tana min sheri wai yaya yana kirana nace o,o, ni ya su may zan mashi kuma ne wai ?
Tace ke wasa nake maki dan Allah kwantar kada kiyi fitsari a wandon ki please ?
Ban sake ganin shi ba don bamu hadu ba dashi tun ranan da ya dawo daga tafiyan shi.
Kwanan shi biyu kawai ya juya ya koma Abuja sai da yai kwana goma sha uku ya dawo gida a jike da abin arziki.
Ko ni na lasa don ba cikin gidan ba har makwabta sun san sadauki ya dawo garin su Umma ya canza masu motar shiga don yace yana bakin cikin ya gan su a motan kasuwa suna shiga.
Ranan munyi kallon kayan lefe mun baza kauyanci bani ba har su Amira yan birni sai da sukayi kauyanci ga kayan .
Mummy tashigo ta gani sai faman mamaki takeyi da yaba kyan kayan tana cewa kai wace yar sa,an keda wanan kayan haka.
Ina son naga wanan mai kayan nasan ba karamin gida za,a kai suba haka kan.
Hjy Kubura ai shi kyawon aure albarkan shi kawai yar masu hali da yar tallaka duk dayane ga Allah Allah dai yasa andace kawai.
Hjy kubura tace gaskiya kan shine magana ai shima mai kayan da dan tallakawane yanzu baga ikon Allah ba.
Maryam tace mumuy ai sai kinhaji daganin ta gidan nan ke da sarakuwan ki kune fa yan kai kayan in Allah ya yarda.
Tace hakane fa kedai mairamu sai fa na gaji abuna namu maganin akwabe mu.
Su Umma basu shigo ganin kayan ba wai su ba,a gaiyace su suzo su gani ba don haka basu zuwa.
Mummy tace kyale yan baki ciki duk hasadane da kyashi ke cin su kawai ba wani ba,a fada masu ba ko anfada masu ma basu zuwa aini na dawo raka wa yan nan mutane ko dan basu da imani.
Inkana binta nasu sai su kona mutum ga banza da wofi da jahilcin su wallahi.
Maji batai mai magana ba sai da yakai kaman kwana goma da dawowa tace tana magana dashi.
Ya shigo suka danyi magana da Amirah mutumiyar shi ya shiga gurin maji don dama idan zasuyi wani magana da yake serious daki suke shiga shi da ita.
Ya samay ta zaune a bakin gadon ta ya zauna asaman kujeran dake cikin dakin nata.
Yace maji yaya zancen su Amirah ne tace ai akan zancen ne nakira ka nan.
Tacs baka nan babanku ya tara mu kan zancen auren ku yace yana son gaba daya kuyi aure lokaci guda nan da karshen sabon wata.
Yace ni maji dama akwai yarinyar da muka shirya da ita akan zamuyi aure sai dai matsala daya shine ita ba musulma bace gaskiya.
Da sauri maji ta dago kai tace kafira ke nan ko may sadauki?
Yace eh maji Christian ce ita, yar kasar ghanace amma idan munyi aure nasan zata musulunta ai.
Kai dakata ba cikin kayana ba wallahi.
Kada kasoma ka kara min zancen nan wallahi don zan bata maka rai sosai fiye da tsanmanin ka.
Kai baka jin kunya ban gita cikin wani gorin ka ba zaka jefani wani idan su yaya suka samu labatin nan ina kake son na jefa kaina.
Ban taba sanin rashin hankalinka yakai haka ba sai ysu din nan da har ka dubi idona ba kunya kazo min wai da zancen auren kafira da bakin ka ko kunya bakaji ba.
Idan da kana da kani ko danka yace zaiyi wanan danyen aiki yaya zakaji a ranka.
Shiru yayi bai ce uffan ba sai ya dukar da kanshi kasa ya hada hannayen shi guri guda yana dan jijiga kafan shi a hankali.
Itama mama shiru tayi don bacin ran da ya ziyarci zuciyar ta a lokaci guda bai barin tayi magana.
Sai dai shi a zuciyar shi tunane yake ta hanya Baba zai gwada yagani ko da sa,a don yasan ance Baba ne yai tsayewa Ahmad har zai auri wacce zai aura din.
Amma nashi dai akwai banvanci saboda zaman kafira bare kuma ba kabilar hausawa ba.
Muryan maji yaji tajefo mashi tambayan da sai da ya girgiza mashi zuciyan shi tana cewa.
May ke tsakanin ka da fatima ne ?
Da sauri ya dago ya kalle ta yace wata Fatima kuma maji ?
Fatima nawa ke gidan nan da kasani?
Maji badai Fatiman nan taki ba ko ?
Tace inba ita ba wata Fatiman nake nufi ?
Yace kai tsaye ni babu komai a tsakani na da ita maji?
Ance maki wani abu a tsakani na da ita halan ?
Maji tace sai an fada min ko tunda ni yarinyan ce?
Wallahi maji ni ba komai a tsakani na da ita Fatima ai a matsayin kaunata nake daukan ta in ma,wanan ne shine kawai.
Shiru sukayi ba wanda ya kara magana daga cikin su ganin maji bata da niyan kara mai magana yasa shi mikewa yana fadin shike nan maji tace tafi shike nan.
Har yakai kofa tace dakata wallahi sadauki duk ka sake har zancen arniyan nan yafito a gidan nan sai na bata maka rai yadda ka bata min a gidan nan kagin kasa a zageni acikin gidan nan dagari sai na fara yima tukun mara hankali kawai.
Yana fitowa fuskan shi ta canza kala yayin shi gaba daya ya canza a lokaci guda kaman ba yanzu ya shigo da fara,an shi ba.
Amirah tana magana dashi amma ko kallon ta baiyi ba ya fice cikin bacin rai.
Duk muka bishi da kallon mamaki muna ko may yafaru dashi oho mashi.
Sai ga mama tafito dakin tana fada ita daya tana fadin ban taba sanin rashin hankalinka yakai haka ba sai yau din nan?
Maji may kuma yayana yai maki yau kuma?
Sai da ta harari Amirah kamar da ita take fada tace bar mahankali da rashin tunane kawai wai wata arniya yake fada min zai aura don ya gwada min shi dan duniyan gaske ne.
Ashe ko dagaske yaya keyi da zancen wanan arniyan ya fada maki maji ?
Au dama kukun sani ne ke nan ko ?
Shi yanzu aka rasa wanda zai fada min a cikin tun baizo ba na tare shi mara hankali kawai.
Maji ba yana son ta bane kuma shi zai zauna da ita abarshi mana yayi abinsh,,,
Bata karasa ba aiko maji tai cikin ta da fada sai da Amirah ta kwamce da bata tanka ba gaskiya.
Maji tace ai dama zubin ku daya dashi baku san mutuncin kan ku ba balle kiji zafin danaji.
Ranan kan naga fadan mama da bacin ran ta ance mai hakkuri bai iya fushi ba sai ranan na tabbatar da hakan.

****** ********* ******
Da yamma da baba ya dawo maji taje gaishe shi tayi sa,a babu kowa agurin nan take fada mashi Alhaji dama ina son in fada maka cewa.
Yaron nan fa yar gida yake son yi don da Fatima ce zasuyi aure ban dai fada maka bane sai komai ya daidaita a tsakanin su dama.
Yanzun ko yazo angama magana itace kawai naga ta dace ya aura don yarinyar nada natsuwa da hakkuri.
Cikin farin ciki Baba yace ikon Allah haka abin yake gaskiya nai farin ciki yau dajin wanan labari don ni kaina na dade ina wanan tunanen a raina.
Sai gashi Allah ya karba min addua na a cikin sauki da dadin rai maganan tazo min .
Zanga sadauki din in mashi murnan wanan babban albishir din da kikai min.
Tafita ta barshi da dadin rai sai murna yake har ya kasa boye farin cikin shi a fili.
Washe gari Baba ya aika akira mashi sadauki anyi sa,a ya dawo daga exercises din safe da yake fita da zaran sun fito daga sallah.
Rigan jikin shi ya sauya, ya nufi falon mahaifin shi don amsa kiran shi da saurin shi don yasan ba kasafai Baba ke aikowa kiran shi ba.
Da sallama ya shiga falon ya samu Baba ya daga kofi zai kurba tea da yake sha.
Yana ganin dan nashi ya sauke kofin ya fasa kurbawa yana cewa sanda sadauki sandagagare.
Zo nan zonan ka zauna yau in gwada maka farincikina dana kwana inayi jiya.
Mamakin may baba yaji akanshi yakeyi don rabon da yaji wanan kirarin da baba kan mashi inyai abin jin dadi tun yana karamin yaron shi kafin ya fara shaye shayen su bata.
Yace matso mana Babaatsonan kusa dani naji albishir din Alheri a gurin uwar ka jiya da dare .
Tazo tana fada min kun shirya tsakanin ka da yarinyar nan Fatima zan iya cewa nafi kowa farin cikin wanan hadin naku don na dade ina maka fatan haka a raina don Fatima yarinyar arzikice a gareka duk wani namiji da yasan kan shi zai so ace ya mallaki wanan yarinyar a matsayin uwar yayan shi nan gaba.
Duk bayanin da baba keyi sadauki ji yake kaman an watsa mashi ruwan zafi tun daga saman shi har kan shi .
Yadaga kai ya fadawa Baba ba gaskiya bane wannan zancen, amma sai yaga farin cikin da mahaifin shi ke ciki yafi karfin ya musulta shi a lokacin.
Ya san da zaran yace zai fada mashi gaskiyan zancen shi bai san komai ba akai farin cikin rayuwan shi zai iya sayawa zuwa bacin rai ta zama mashi sana din tashin ciwon shi.
Wanan dalilin yasa yaja bakin shi yai shiru, yana karba irin adduan fatan Alherin da mahaufin nashi ke mashi akan zacen.
Sukai sallama ya mike gwiwan shi duk ya mutu da kyat yake iya daga kafan shi da yake takawa a kasa dakin shi ya nufa cikin wani yanayi na susucewa a lokaci daya.
Yana shiga ya fada kan katifan gadon shi yayi yayi a lokacin ya samu ko dan kuka yayi ko zai samu relief, amma abin ya faskara mai.
Wayan shi dake gefe ke ringing har yagaji ya katse don kan shi bai daga ba sai kuma ga kiran ya kara shigo mashi lokaci guda ya daga daniyar zagin mai damun shi.
Bashar ne ya daga wayan yana tsaki yace yaya akayine wai Bashar din yace yana kofan gida.
Yace shigo ina dakina yana shigo yanayin da yasamay shi a ciiki yabashi tsoro sosai.
Lafiya may ya samay ka haka kuma ?
Ya watso maahi wani harara yace ban sani ba mugu ai kana daga cikin munafukan dake son wargaza min rayuwana nasani ba yau ba.
Bashar na zama yace may kuma mukayi mi muna fukan da bamu son ganin farin cikin ka?
Maimakon ya bashi amsa sai ya juyar da kan shi kawai gefe daya bai kalleshi ba.
Wai may ke faruwa ne wai ka koma haka lokaci guda kaman wani tababe yakara tambayan shi mikewa yayi zaune daga kwanciyan da yake yana cewa.
Kana nufin baka san sherin da maji ta kulla min bane agidan nan wai ?
Innalillahi kana da hankali kuwa yau man ?
Maji ce kuma zata kulla ma sheri a rayuwanka ?
Wani kallo ya watsa mashi yace ba sheri banr may nene?
Murmushi Bashar din yayi yace don Allah may akayi ne wai ?
Yace kaaai wai maji ta fadawa Baba wai mun shirya tsakanina da wanan yarinyae mun amince zamuyi aure.
Wata yarinya ke nan kake nufi wai?
Wata yarinya kake damuna akan ta gidan nan ?
Yace kana nufin wai Bintu?
Yace ita mana.
Alhamdullahi Alhamdullahi kai wani hikima sai manya wallahi tanan maji tafito muna Allah mun gode ma.
Ya dago jajayen idon shi yana kallon Bashar dake ta kwada hamdalla haka cikin mamaki.
Yace wanan abinda maji ta kulla min da may yakama Bassh?
Maji tarasa wace zata lakaka min auren ta sai wanan solaman yarinyar da kwatakwata bata cikin tsarina.
O Lindan ce tsarin ka ke nan ko yar arniyan ka mai dan buje ko ?
Wani wawan nashi yakai ma bashar din ya kauce ma nashi ta hanyan ja baya.
Sadauki ya mike tsaye yace haba man may zanyi da wanan yarinyar ko maryam dina fa batakai shekaru ba a duniya wai itace za,ace na aura ?.
Ita Fatima ba mace kake kallon ta ba ke nan ko ?
Wallahi zakasha mamaki kace na fada ma dan hakin daka rai shike tsone maka ido watarana.
Kai may ya kawo kane ?
Yace manta yau zamu zamfara ne dakai ko kuwa?
Yace bazan tafi ba.
Dariya ya kama mashi yace kafara angwancin ke nan ko?
Zanci ubanka fa Bash wallahi idan ka kara bata min rai yanzu zan rufe daki dakai nai maka tsinanen dukan

Please Login or Register in order to submit comment