Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

gani kur,ani maigirma yazo muna da,warakan komai a cikin sa.
Malam zai sha yace to amma fa uwar ce zata sha tabasu da hannun ta,suma su sha hakan zai dan kawo muna saukin abin insha Allahu.
Zanbaki abu biyu zuwa uku kikai masu sufara yi insha Allahu idan sunyi badai samu ba in ma wani yakara kokarin yi masu sai dai ya koma ga maishi wallahi da izinin Allah bana mutum ba su dai kada suyi wa wani sheri a rayuwan su.
Nan ya mike yaje ya hadowa gwago mai masa abubuwan fa,zai bata yace takaiwa Maji da diyan ta Allah ya sauwaka.
Gwago bata tsaya ba ta juyo zuwa,sokoto a ranan sai dai cikin dare ta iso garin.
Don haka ta wuce zuwa gidan ta da abubuwan sai washegari take da niyar takawo wa Maji su.

******* ******** ******
Washegari ba a zuwa makaranta don haka yaran kowa yana zaune falo tare da iyalin shi.
Bintu tana daga ciki tana shiryawa don yanzu tagama gyaran guri don ita bata gajiya da aiki ko kadan,
Idan kaga yadda part din maji yanzu yake kalkalkal zakace ba mutane a cikin sa da yawa.
Wani lokaci har hajuya Kubura takanyiwa Maji ba,a tace hajjiya maijidda ki bani wanan yar taki mana.
Wallahi ni dai yarinyar taimin bata,da kiuya ko kada,akwaita da tsabta ga ta,da kwai wallahi.
Maji kanyi dariya,tace a,a kibar mi "ya ta,Allah ne yakawo min hutu ta hanyan ta .
Bintu tafito falon duk suka bita da ido har maji din, sai maji ke cewa kun gani tai aiki kuma harta gyara jikinta kuko kuna nan kuna bakin shiriritan ku da kuka saba ace gari ya,waye mace bazatai wanka ba ba kuma komai kukeyi ba. Mutane suyi ta shigowa suna,samun ku a haka.
Kai maji ko munyi kwalliya wa za muyi wa mutum ko saurayin kwarai baida.
Au sai da,saurayi ake kwalliya mace fa da kwalliya aka san ta ko yaushe don abinda kuke yi anan shi zaku je gidan mazajen ku kuna yi.
Bintu ta dan zauna daga kasa sai cewa maryam tayi kai Bintu ke kullun kamar bakuwa har yanzun baki saba ba ke.
Kila dai tsoro take ji a,a bata da tsoro wallahi, don ranan fa itace tafara zuwa gurin yaya sadauki ta kama shi.
Aini wallahi ranan Bintu ta bani mamaki sosai wallahi, don gaba daya na tsike ni a lokacin.
Maji wacce zuciyar ta ya sosu da zance amma sai take cewa ai Bintu tai kokari wallahi sosai.
Toke halan waya fada maki anabawa mutum manja da gishiri ya sha idan yana haka.
Tace nima labari naji wata yar ajin mu tanayi cewa wai duk yadda mutum yasha maye idan aga yai mashi yawa abashi manja da gishiri sai ya amaye su su rage mai aiki a jikin shi.
Ikon Allah inji maji tace Fatima shine kika gwada ke kuma gashi kuma na lura abin yai mashi amfani sosai don yasa yadan dawo cikin hayacin shi.
Amira tace wallahi aini duk mamakin Bintu ya kamani a lokacin don ni ba karamin tsorata nayi ba don na dauka ma mutuwa zaiyi ai.
Kai sadauki Allah dai ka,shirya kayan ka amma sadauki bai min da ba,wallahi.
Yaro kai kadai Allah yabani namiji amma kuma kai ke sani kuka.
Maji ki daina mashi kuka don Allah adaiyi ta addua inji Amira ta fadi cikin muryan tausayi.
Ai inayi Amira Alla dai ya,sauwaka kawai don na lura fa abin nashi yai girma sosai ko ba yanzu yafara sha ba.
Shin tsaya dai in tambaye ki Bintu wai dai ko ranan nan ma da kikace wai kin fada kwatane shine yai maki amai ga jikin ki wai.
Da sauri Bintu ta dago kai sai kuma ta dukar da kanta kasa don bata iya karya ba.
Da sauri maji ta dago kai tana kallon Bintu tace wai Fatima hakane ko kuwa?
Tace hakane Maji nan ta fada masu duk yadda abin yafaru da yadda ta samay shi a kwance har shigowan ta gidan.
Shiru sukayi dakin suna nazarin zancen Bintu kowansu yana yaba kaifin hankalinta.
Maryam tace shine da kika shigo baki fadi ba Bintu?
Haba Anty Maryam bayan nasan mama bata da lafiya shine zan fadi na kara mata ciwon kai.
Bazan fadi ba gaskiya don ban son hankalin mama ya tashi, don ba karamin tashin hankali zata shiga ba.
Baki gafa yadda yake bane nima da kyat na uya kai shi dakin shi kamar numfashina zai dauke nake ji a lokacin.
Ikon Allah wanan yarinyar akwai ki da mugun karfin hali wallahi danice ai ihu zan dinga kantarawa sai kowa yafito a gidan nan.
Da,sauri Bintu tace kai anty ai wanan rufin asiri ne ba abinda za,a bari wani yaji bane.
Kinji ke mai cewa zakiyi ihu maji ke fadawa maryam hakana tace ai Bintu yarinya ce mai hankali wallahi.
Ai kan inji Amira don akwai ta da dan banzan wayyo kun gan ta nan.
Sallaman mai masa ne ya dakatar su suka,shiga gayar da,ita suna mata ina kwana.
Maji tace a hajiyan masa ashe tafiyan naki ba mai dadewa bane har kin dawo ?
Nadawo hajiya dama tafiyan nawa ai donki nayi shi ba tafiyan kaina bane nayi.
Maji tagyara zama tana fadin ikon Allah ashe mu akaiwa tafiyan ke nan.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,


Ganin yanzu bata samun kasuwar sana,anta irin farko da Mud al,majiri ke mata talla yasa hankalinta ya tashi sosai.
Saboda a yanzu ta saba da rike yan canji a hannun ta tana kadawa a bankinta na gida.
Sai gashi yanzu da kyata zata hada naira dari daya ta kada a ciki ga wuni.
Hakan yasa duk hankalin maria ya yai matukar tashi ga fridge yai ta haukan kankara shi kadai amma babu kasuwan saye kamar farko.
Gurin mahaifiyarta taje da zanjen, budar bakin uwar tace shi,Aliyu ba zai iya dan fita maki dashi ba koda a cikin uguwar ku ne yana yawata maki dashi.
Da sauri tace ,a,a,a Umma wallahi mahaifin su bai yarda sam idan yaji nasan ba karamin tashi hankali zamuyi va dashi.
Ashe ke wawiya ce maria ke zaki bari yaji ne cewa yana talla.
Mutumin dan in ya sa kafa yafita tun safe dai yamma yake dawowa, lokacin ai har kunci kasuwan ku ko kungama.
Lalai Umma haka za,ayi nagode da wanan shawaran insha Allahu gobe zan fara aza mashi talla kuwa.
Kafinta shigo gida,saida ta tsaya ta sayo ma yaron farin roban ruwa dan madaidaici irin wanda zai iya dauka.
Washegari tun safe ta tsaya shininiki bata shirya yaran zuwa makaranta ba yadda ta saba tashi da wuri ta shirya su su karya su fita tare da mahaufin su, ya aje su islamiya sai ya,wuce gurin sana,ar shi.
Da maigidan nata yai magana sai cewa tayi yau bata jindadin jikin tane shiyasa.
Shi dai ya shirya yafita abin shi amma yana mata mitar tayi ta shirya yaran su tafi islamiya kafin su makara.
Daga wanan ranan ta fara,azawa yaron talla duk da Aliyu kara mine sai da yai kuka yana fadin mama makaranta fa kada a wuce ni gurin bita fa.
Amma sai hawan shi tayi da fada cewa indan baije mata tallaba wa yake son ta azawa.
Ya dai ga duk almajirin da ta kira sai yace malam ya hana su yin talla yanzu.
Kuma gashi yasan da dan kudin take samu tayi masu dan lalurori a gidan wa yake son ta azawa talla.
Yaron haka ya dauka ranshi bai so ba ya tafi tallan ruwan yana turo baki harda kwalla a idon shi.
Da yake bai iya tallan ba shiga farko da kyat ya samu yayi dan ciniki yadawo da saura gida duk yayi zafi wasu ma duk sun yoye a roba.
Nan maria ta hau yaron da masifa da fitina har tana kirarin idan bai mayar da hankali ba yai mata, bazata sayi mashi komai ba da kudin ta.
Dole yaron ya dan kara dagewa ya mayar da hankali gurin tallan duk da ba,wani girma yayi sosai ba.
Ita uwar ganin yaron ya mayar da hankalin shi yanzu sai dadi take ji don har tana wa makwabciyar ta da ta rike almajirinta na farko habaici wai in an maka bakin ciki sai ka fashe haushi da naka tunda Allah bai hana maka,ba.
Hakana yaron tin bai saba ba yana fita da kuka har yazo ya sake jikin shi yana shiga mutane talla.
Ito ba abin da ya shille ta sai jin dadi take yi yana kawo mata kudi tana kadawa a bankin ta na gida kawai.

****** ********* ******
Raiha tun bata kula wayan Michael dake damun ta, da kiran akai akai har tazo tana daukan wayan shi.
Da farko tana ganin kamar hada kai sukayi da Nasir a kanta si da ga baya ta fahinci bada sanin Nasir din yake kiran ta ba.
Don yakan ce kada tai serving din nomban shi yadda Nasir zai fahinci cewa shine.
Don baya son Nasir yasan shine ya rusa mashi plain din shi a kanta.
Da lalashi da komai yasamu ta yarda ta tra mai da account number din da yasa ta ta,bude.
Tashin farko kudin da ya turo mata saida hankalin ta ya daga don dubu dari biyu ya turo mata ga account din ta.
Ta rasa yadda zata boye wanan kudin don haka ta fadawa mahaifiyan ta amma bata fada masu cewa ba musulmi bane shi,
Ta daice a waya suka hadu dashi yace a lagos yake aiki hankalin mahaifinta ya tashi amma da sukai waya da Michael yace ba komai yadai bata ne kyauta don ya fahinci ita diyar tallakawa ne.
Abinka ga kudi masu shiga rai sai mahaifin nata bai tsaya wani dogo n bincike ba kawai aka shiga harka dasu harda tayar da katangangidan shi daya zube badi guda.
Bai san cewa katanga mai muhinman ci agare shine ya mugun zubewa ba kan kudin.
Shiko Nasir ganin Raiha bazata samu ba yasa shi canza akalar sa zuwa gurin cigiyar wata sabuwar kamu da,zatayi daidai dashi.
Sai dai Raiha ta riga ta rusa mashi plain din shi na,wanan shekaran kamar yadda ya tsara al,amarin nashi.
Wata yammaci yafito ne daga ma,aikatar su sai ya hangi ra yarinya tsaye a,bakin titi daganin shigarta yar hannun ce don ta dan waye a fuska.
Daidai inda take tsaye yai farkin din motar shi inda ya bude yafito har inda take a tsaye.
Sun gaisa zakace ko yasan ta a bayane yake ce mata daga ina take haka ta tsaya rana yana bugun ta duk haduwan ta.
Amsan da ta bashi yass shi gane cewa tana da,wayo don sai yayi da gaske idan har tafiyan su zaiyi daidai.
Tun daga wanan ranan yafara dawai niya da yarinyar yana kashe mata masu gidan rana yadda ya kamata.
Yarinyar irin wanda idon su ya riga da ya bude da kudi da maza ne sosai ya sa shi fara ganin indan baiyi da gaske ba ba zai samu yadda yake so ba.
Tashin farko ya taya mata zuwa lagos kamar yadda yake a duk bayan wata uku don yin assignment din company su.
Ba wahala ta yarda zata bishi su tafi amma sai ya bata wasu kudin da zata sai wasu abubuwan bukatun ta da zata da su.
Kusan tare dashi suka tafi tasayo abubuwan da take so wa ranta a kasu da wani shago.
Daga baya suka shirya zuwa lagos kamar yadda ya bukaci suyi tare dashi.
Yaso yai mata irin yadda ya,saba yiwa mata don ya horar dasu amma sai ya fahinci kamar matafishi sanin bariki sosai.
Ya samu Michael yana fada mashi irin matsalar da ya samu akan sabuwar kamun da yayi yanzu.
Nan ya bashi shawara akan yabi yarinyar a sannu don mata yanzu suma sun yi wayo sosai.
Haka suka dawo bai samu yadda yake son bata training ba don in ya tura ta turai kada a samu matsala sosai da ita.
Bayan sun bar Michael ne ya bugo waya yana fadawa Raiha sabuwar yarinyar da abokin shi ya samu kuma yana son ya aiwatar da nufin shi a kan ta.
Raiha taji a ranta yarinyar ta bata tausayi don haka dole ne ta taimakawa ko wacece.
Sai bayan sun dawo ne ta samu wani abokin shaye shayen ta bashi kudi don yanzun bata da matsalar su ta ce yai mata bincike akan sabuwar yarinyar da Nasir yake target ga fitawar waje wurin safarar matan da yake a boye.

****** ********* ******
Tsaye ta hango wani guy a kofan gidan su kafar shi daya a cikin mota daya kuma ya daga waje ga waya a hannun shi.
Ganin Amira da,zata shigo gidan yasa shi saurin samun ta ya tsare ta yana fadin, barka dai.
Don Allah idan gidan nan zaki shiga ina son ki sallamo min Nafisat ne, wani kallo Amira tai mashi kamar zatai magana amma sai tace mashi kawai taji.
Tana shiga gida ta fara haduwa da Bintu wacce ta sheko ta rugumay ta cikin so da kauna zakace yar uwarta ce tajini tana cewa Anty Amira sannu da dawowa ya makarata ya hanya tare da karbar wa Amira school bag din da ke rataye a hannun ta zuwa cikin dakin su.
Mama Asiya suna waje da yaran ta sai tsaki suka ja suna fadin sai kace diyar wata,
Harda zuwa don kisisinar yarinyar nan yar kauye zuwa yi mata sanni da zuwa.
Wai ma mama may wanan yarinyar takeyi a gidan nan ne har yanzu, wallahi ban son ganin ta shegiya gata yar kauye amma ta iya ba mutun haushi da takaici gata aiki baya isan ta.
Uwarta ce ina ga kamar a nan take zaune yanzu tare da su kin san su da shegen kwashe, kwashen tsiya ai da son asani komai basu aje ba.
Dayar yar mama dake yankan akaifa tace may zasu bata banda wahala suma ta kan su sukeyi ai.
Ni Alhaji ma yafi bani mamaki don da watace cikin mu ta ajeta da yanzu ya fara fada za,a kawo mashi bakuwa a gida cikin yaran shi ta bata mashi tarbiyan ta.
Can kuma cikin daki da Bintu ta shiga da murnan ta tana fadin Mama Anty ta dawo.
To yar gidan Anty sai kace wace ta dawo daga wani guri haka kina ta wani farin ciki dake.
Mama ai duk wanda yafita ta dawo lafiya ai masa barka da arziki inji Bintu, kai Fatima ke kan halin ki sai ke wallahi.
Amma a ran Maji dadi taji irin yadda taga Bintu tana matukar son diyan ta wanda a da can baya ba ruwan su da juna a dakin kowa kan shi daban basu damu da junan su ba.
Amma zuwan Bintu cikin su yasa koda maryam bata kusa zata bita tana fara,a tana fafin Anty maryan antyn mu ta dawo.dole ta fito
Idan kuma maryam ce ta dawo sai ta nemo Amira tana fada mata cikin jin dadi har takai suna barin abinda sukeyi suzo su tari junan su cikin nuna jin dadin su.
Yau ma hakan ne don har baya taje tana fadawa maryam dawowan Amira inda maryam tazo da murna tana wa yar uwar ta sannu da zuwa Anty don ita bata fita ba.
Nan suka zauna a falo Amira bayan ta cire kayan jikin ta tafito Bintu ta aje mata abincin da ruwa tafara ci suna hira a tsakanin su.
Tana fadin kai yau wallahi akwai rana ga zafi duk dama na matsu na dawo na cire wanan kayan nasamu ruwan sanyi nasha.
Maji tace aiko mu dake gida wanan zafin ya ishe mutun Allah dai yai muna Rahama kawai.
Yaran suka amsa da Ameen ya Allah.
Amma kila an kusa fara ruwan sama ne don zafin yau yai yawa mama Bintu ke fadi.
Sai suka sa dariya gaba dayan su maryam tana kokarin cewa ke Bintu ai haka garin nan yake da shegen zafi walla,,,,
Sai gani sukayi an daga labulen dakin kawai ashe Nafisa ce gaba daya suka juya don ganin waye haka bako sallama zai fado masu kai tsaye.
Tau yar bakin ciki ashe anzo nemana shine don bakin ciki irin naku na gado kika ki fada min, to Allah bata ku ba.
Wai dawa kike yi ne inji Amira take tambayan ta a cikin daga murya.
Ke mana yar bakin ciki mai shegen kishin tsiya kamar na uwarta ni bani na hana azo a soki ba balle ki gwada bin bakin ciki karara a fili.
Nafisa niba sa,arki bace balle don kin kwaso dan rashin mutunci irin ki yace wai ni na kiri mashi ke don rainin wayo.
Ji yar rainin hankali oho sai yanzu ai na kara gane bakin cikin ki a fili wallahi don naga aikin hassada yau,
To wallahi a haka zaku kare tanbade lalace sai bakin kitifi ku da uwar ku a daki dangin yan caca da shaye shaye.
Kafin tace wani abu ba,wanda ya san Maryam har takai inda take tako shako wuyanta ji kake tas,tas, mari biyu masu lafiya ta kwashe ta dasu.
Umma fito wallahi gasu Amira can sun tarar wa Anty Nafisa da duka inji karamar kaunarta take fadawa uwarsu.
Haba gaba daya sukayo part din Maji hankali a tashe daidai duk su kuma sunyo waje inda Nafisa take tsaye da maryam.
Maji tana fadin ke Inna Isa kyale ta haka na barta taitayi ita kadai.
Daga nesa Umma ke fadin wallahi idan kuka kara dukan ta yau sai dai duk akai mu asibiti gidan nan .
Kaji man marasa mutunci haukan ashe ba,a kan sadauki kawai ya tsaya du, dukan ku kenan ya shafa.
Ke Nafisa may yakawo ki gurin wa yan nan matsiya ta ki jawa kanki tsiyan su irin ta gado ya shafe ki ke ma.
Nan take fadawa uwarta duk abinda yafaru uwar take cewa barsu tsiyane da talauci yai masu katutu a kai shine bakin cikin su gare ki.
Hassada ko sai dai su mutu dashi a gidan nan don babu mai kama kafar mu don mun riga mun masu nisa ko.
A haka zasu kare daki tsiya tsiya kamar madallacin malam ba komai sai tarin raggaduda kawai ciki.
Saurayi kuma sai sun ga har dan gidan gwauna a gidan nan gurin ku.
Sai lokacin sadauki dake tsaye daga kofa shigowa gidan tun farkon fitina yana tsaye yana sauraren su.
Ran shi yai matukar baci irin yadda yake jin ana zagin mahaifiyar shi da yan uwan shi a kan talauci.
Su madai su Amira duk da Maji tana masu fada bai sa sun fasa mayar masu da amsan zagin da suke masu ba don harda mama Asiya ta shige tsagal cikin fitinan tana cewa ai wanan mutanen kune baku san sherin su ba dama da kowa bakin ciki sukeyi a gidan nan.
Ke Amira shige daga ciki kada na kara jin muryan kowan ku yai tsaye yana nuna masu kofan dakin su da hannun shi.
Ranshi a bace idanuwan shi sun kada saura kiris ya fashe irin yadda ya hasala.
Yaran suka bi bayan uwar su da tafara shiga ciki ranta a bace yayin da ya juya inda taron mutanen gidan suke tsaye ya watsa masu jajayen idanuwan shi akan su.
Zo mutafi kinji don wanan mahaukacin yanzu yana iya muna haukan shi akai.
Gaba daya suka watse zuwa shiyan su a can suka yada zangon su yana jin sunci gaba da fitinar su ya shiga dakin mahaifiyar tasu.
Tsawa yadaka wa su Amira akan suyi shiru hakana bai son hayaniya ya isa.
To amma yaya don kawai an raina mu shine kowa ya kwaso sharan shi a kan mu zai yaba tsiyar shi.
Nace ya isa haka ya fadi cikin tsawa hakan yasa gaba daya sukai shiru da maganan.
Nan yakai zaune saman dayan kujeran da ya saba zama idan yashigo gidan, maimakon ya zauna yadda ya saba sai kawai yayi kwance tare da dora hannun shi daya saman kan shi daya na saman kijin shi.
Ya kai wasu mintina a hakan gaba daya dakin ba wanda yai magana daga cikin su.
Bintu ce ta mike don shigewa don dai ita gaskiya zaman ta a dakin duk a tsorace take dashi.
Don gani take cewa kiris ya rage ya kamasu da dukan tsiya a dakin.
Takai gaf da kofan zata shiga taji yana cewa "Ke kawo min abinci na na fita.
Da,sauri ta juya zuwa kitchen inda ta hado mashi abinci kamar yadda ya saba hada mashi wanan karon har da spoon din da yace dashi yake ci.
Bai masu magana ba ya mike zaune kamar zai dauki abinci sai kuma ya bude a,nan falon ya fara ci a hankali.
Maji ki yace daidai zaikai spoon din shi a baki batare da ya kalleta ba kiwa yaran nan magana su daina shiga harkan mutanen gidan nan ana zagin ki a banza.
Don bazan iya hakkurin wanan mugun zagin da ake maki ba a gidan nan haka.
Talauci dai ba mune muka azawa kan mu ba Allah ne yayi mu a haka ba yin kan mu bane ai.
Amma mutanen nan da,sun tashi da,wanan zasu zage ki ke da yaran ki, don tun ina karami nake jin wanan kalman daga bakin mama da Umma a gidan nan.
Sai kuma ni da na ja maki wanan gorin na dan shaye shaye da kuma cacan da suka ce ina yi wai.
To amma ba komai Allah na gani shida ya dora min wanan lalurar shine zai yaya min shi dakan shi aduk lokaci da yaso.
Ke kuma Amira na roke ki da kuyi hakkuri da kowa a gidan nan don rayuwan mahaifiyar mu kin dai san ita ba mai son fitina bace a ranta.
Haka ke maryan wanan zuciyar taki matsayinki na mace ki rage shi don gidan wani zaki tafi.
Inda Bintu take zaune ya kalla tare da,watsa mata harara yace ke kuma da sauri Bintu ta dukar da kanta a kasa tare da mannewa jikin kujeran da Maji take zaune a kai.
Yace kada ki yarda naji ance kinjawa uwar mu bacin rai a kanki a gidan nan zaki hadu dani.
Sai lokacin Maji da takaici ya isa tai magana tace kai ku tsaya wasu,wasun ku amma kada ka hada da yar mutane da bataji batagani ba da kowa a gidan nan iyakarta imu a shiyan nan ba ruwan ta da kowa a gidan nan.
Inda na tsayar da ita anan take bata taba saka kanta ga harkan kowa ba cikin gidan nan.
Don haka tafita a ido ka kada kasa min "ya a cikin zancen ku wallahi kaji na fada maka gaskiya.


Please Login or Register in order to submit comment