Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Sai da suka natsune Bintu takw fada mata irin rayuwan kawai cin data samu a gurin Maji da kuma irin matsalar da take ciki akan dan ta da baijin magana da bukatar shi a gurin mahaifiyar shi na son tafiya wani gari buga kwallo da yake son zuwa yi.
Gwago tace kai amma ko hajiya da ta barshi don bata san ko shine mafitan ta ba arayuwa tunda har yai mata alkawarin canzawa idan ya dawo.
Gwago tana fada irin ta manya tana fadin ai gara ta barshi ya tafi don batasan abinda Allah ya shirya ba a kan yaron.
Suna ta zancen ita da gwagon ta har dai dare yayi don haka ranan a na gidan su Bintu ta kwana da,gwagon ta suna kewan junan su.
Sai washegari da yamma ta shigo gidan cikin jin kunyan Maji da yaran ta, sai faman yi matasheri sukeyi taga gwago ta gudu masu.
Maji tace yanzu Fatima haka zamuyi dake ni da nake fadin anan zaki zauna shine kina gani gwagon ki kika gudu gurin ta ko?
Ko dama bakijin dadin zama damune dai kika boye muna hakan ?
Da sauri Bintu takai kasa tana cewa ,a,a mama ba hakana bane kawai dai na tsaya ne na kara shirya mata kayan ta.
Jeki ga abinci can a kitchen ki diba kici inji Maji tana mata magana cikin kallon fuskan yarinyar.
Mama na koshi gwago tai muna gwaben ganye mun ci dazun mun koshi sosai ban jin yunwa yanzu. Sai dai anjima in Allah ya kaimu.
Daga nan ta samu guri ta zauna tana kallon maryan dake dakilar wayan ta tana dariya ita kadai.
Sun kai wani lokaci falon yana tsit kowa yana tsabgan gaban shi sai Bintu dake ta tunane kala kala cikin ranta yadda zata zauna a gidan nan dake cike da tarin matsaloli.
Fada sukaji tsakanin mama Asiya da uwargida ya kaure sai cacan baki suke a kan yaran su.
Maji bata fita ba tana zaune a falon ta har sukaci suka sude ko magana batayi ba, sai ma Amira da tace su daici kan su munafukan banza kawai kanku ake ji.
Sai lokacin Maji tai magana dacewa Amira ban son rashin kunya fa iyayyen naki kike zagi da munafukai kuma.
Kada na kara jin wanan kalamin a bakin ki ko kin manta cewa ke ma watarana uwace a wani gidan.
Shiru Amira tayi don tasan in ta kara furta,wani abu yanzu Maji zatai cikin ta da masifa sosai.
Har masu fadan suka kare cacan bakin su da tonon asiri ba,wanda yai magana a dakin daga dakin mummy Amarya ma ba tafito ba haka ma yaran ta.
Don ita dama,yar i don't care attitude ce a,gidan harkan kowa bata shiga sai in abu yakai mata karo.
Sai da yamma sosai gwago ta shigo gidan gurin Maji inda ta aika mata da abincin dare tace kada ta girka komai ta dinga bari akai mata daga nan gidan su.
Shine gwago tashigo yin godiya gurin Maji din da,wanan irin halarcin da take gwada masu haka.
Maji tace haba dai mai masa ai yiwa kaine ina laifi duk cikin shiyan nan baki aminta,da kibar yar ki a gurin kowa ba sai gurina, kika yaba da ni ai wanan ma wani mutuncine babba.
Murmushi gwago tayi tana cewa Allah dai yabar daukaka da girma Allah kuma ya kara shirya muna yaran mu.
Ameen inji Maji tare da sauke ajiyan zuciya a fili tace bari mai masa ba boyo a tsakanin nidake yanzu.
Jin haka yasa Bintu tai saurin mikewa,zuwa ciki tabar su gurin ganin ta,shige yasa maji hararan su Amira dake zaund suma din mikewa sukayi suka shige suna zunburo baki gaba.
Maji ta kara kwantar da muryan ta kasa, tana cewa hajiyan masa ina cikin matsala da,wanan yaron na,waje na.
Yayan su Amira ke nan inji gwago maji tace shifa,wallahi sai tace cikin kariyan murya mai masa yaron nan yana son kashe ni wallahi.
Maganar safe daban ta rana,daban ya zama wa kowa kaya a gidan nan balle ko banza kin san irin zaman da muke a gidan nan.
Yanzu msi masa nifa har na fara,zargin ko yana shaye shaye ne don abinda yake abin ma bana kai sake bane.
Subbahanallahi i ji gwago Allah ya tsare ya kare hajiya amma kada ki mashi mumunan zargi haka don Allah.
Koma maye dai dole ke uwa hakkuri zakiyi kikara jan danki a jikin ki kina nusar dashi hanyan alheri har ya gane.
Mai masa ni yanzu har abin yana son yafi karfina wallahi don kinga sam yaki zancen shago kamar kowa shi kuma ba,wani sana,a yaje zuwa yi ba yadda kowa keyi.
Ina gani a gidan nan ko wani da yana kawo wa uwar n shi abin arziki daga shago amma ban dani sai ma shi Alhanin ne wani lokaci yakan ji tausayina ya dan taimaka min ko shi da kwankwami da komai yake min.
Tunda kinga ba karfine gareni ba don ni banyi karatu mai zurfi kamar sauran matan gidan ba.
Amma mai mas wanan yaron duk da haka bai zama min da ba wallahi takare da sake kuka wi, wi,wi a lokaci guda.
Ba kuka zakiyi ba hajiya kamata yayi ki kara jajirce kina mashi addua da fatan alheri, kin fasan bakin uwa taki ga "yayan ta.
Mai masa wallahi inayi sai dai kawai na kara akan wanda nakeyi don banda lokacin kai na ko yaushe sai na yarana tun bai zama haka ba ma, balle yanzu da al,amarin shi yai kamari sosai cikin gida.
Yanzu ke hajiya baki fahinci ko akwai wani buri wanda yafison yayi abin ba akan kasuwan ci din.
Saida Maji ta share hawayen da ke fuskanta take cewa, mai masa waifa shi ba komai bane gurin shi sai sha shanci wai kwallo.
Kwallo yake da ra,ayin yi maigidan mu yayi fada har yagaji yanzu ya saka mashi ido yabarshi da kwallon.
To hajiya wa ya,sani ko anan alherin shi yake ga wasan kwallon.
Wasan kwallo kuma mai masa za,a samu wa i alheri a cikin sa ?
To ba haka naji ana fadi ba wai suna samu ga harkan sosai kinga sai muyi mashi addua mugani ko anan arzikin nashi yake.
Hmmm mai masa ni wanan ai abin kunyane a gareni ace wai cikin gidan nan da na yafita zakka wai bai kasuwanci sai kwallon kafa kawai.
May zai samu a cikin wasan kwallon kafa kuma banda shashanci irin na sadauki kawai.
A,a hajiya ban son ki na fadi haka fa kin daiga ki godewa Allah idan har zaiyi wasan ya jawo mai alheri da kintsuwa ai gara a arshi ya,tafi yayi abinshi kinga,zaki rage taahin hankali don kin san inda yake.
Ni kuma nai maki alkawari insha Allahu zan taimaka maki akwai gurin malamin dazan tafi maki can kauyen mu sai yai muna istihara akan matsalarshi don muga may ke damun shi ne wai.
Don kingafa gidan ku babban gidane gaki da kishiyoyi marasa imani da tsoron Allah.
Don haka abu na farko shine mu fara,sani may ye nasabar wanan matsalar tashi ne wai ?
Shin daga Allah ne ko kuwa,saka mashi hannu akayi din a danbala makishi yakoma haka.
Hmmm mai masa ba,wanda ya saka mashi hannu shashancine kawai irin na yaran yanzu .
Ya hadu da miyagun abokai sun sauya mashi tarbiyan dana bashi tun farko don rashin tausayi irin na dan yau.
Kin taba zuwa akai maki istihara akanzancen ne ko kuwa dai haka kike gani ke ?
Gaskiya ban taba zuwa ba mai masa ina dai hasashen hakan ne kawai a raina.
Hajiya yanzu duniya tai nisa wallahi kibar mutum inda kika barshi kai kana kwana,wasu na maka hansari ne,
Balle yanzu ba,a zama kan yara ko nawane gareka dole katashi masu tsaye gurin nema masu tsari da kuma addua.
Gaskiya ni mai masa ban taba yin komai akan yaran nan ba gaskiya nidai nasan ina masu addua sosai wallahi.
Hajiya wanan zamani ai ya,wuce ko gurin mutane don zamani ya lalata mutane da son kai, don A LOKACIN MUKE,,,



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU, PLEASE,,,,


Bayan gausuwa a tsakanin su sai kuma dan shiru yafara biyowa baya hakan yasa Maji cewa yaran ku bamu guri mana ko.
A,a su zauna ai gara suji abinda zan fada da kunnuwan su don su fahinci maganan da zan fadi da kyau.
Tsit yaran har
Maji su ka yi a falon bawanda ya koda dan motsa sai gwago ce tafara magana kamar haka.
Na tafi kauye ne gurin wani malami amma dan uwana ne can gaba da kauyen mu.
Na samay shi akan zancen wanan yaron sadauki ne amma kuma sai wani magana ta daban tafito muna.
Kin san yanzu mutane ba imani da tsoran Allah a tare dasu.
Kin san yanzun muna a lokaci, ga imani a baki amma ba shi ko kadan a zuciyan bayin Allah.
Wai kuma a haka kowa ke son shiga aljannane , ga son duniya ya rufewa mutane ido da zukatan su.
Wanan duniyan da ba bakin komai take ba ga mai imani da tsoron Allah.
Wai may kuma ya farune hajiyar masa inji Amira da take jin digon bayanin da hajiyan masa keyi yai mata yawa.
Waiko kina da hankali Amira baki da kunya fa ke ko kadan ,ina ruwan ki da zancen mu ne wai.
Hajiyan masa tace barta ai zancen ne taji shi kamar da,tsawo a zuciyan ta.
Mai masa ina,sauraren ki kinji rabu da mara kunyar nan futsarara.
A,a hajiya barta don Allah duk ba yin kan su bane ai ,abinda ke tafe dani shine.
Yaran ki gaba daya wallahi an sa masu hannu, duk yadda kike fatan samun su gaskiya a yanzu abin zaiyi matukar wuya.
Don gaba daya an lalata masu rayuwan su ta inda ma baki zata ba wallahi.
Kai ni wallahi ban son irin wannan spercition believe din na,anyiwa wani wani abu wanan ai duk shirka ne.
Hmm kawai mai masa tace tare da fadin kaiyya bazaki gane ba ke yar nan sai an makara ko?
Tiryan tiryan yadda malam ya fada wa gwago haka ta fadawa Maji bata boye masu komai ba don taga basu da niyar yarda yaran.
Tabbas kuwa hajiyan masa na tuna anyi hakan don abin nima ya tsaya min arai sosai.
Don wata rana yaya babba ta ce wai kifine ta dafa wa yaran ta zaunar da sadauki wai ga nishi da ta aje mai saida ya cinye shi tas,
Ya kusa gama cine sai ga babangida dan ta ya,shigo yana cew sadauki ya,raga mashi amma,babu kunya a gaban mu yaya take cewa wai a,shi kadai tayi kada yaba yaron,
Amma dashi sadaukin ya mikawa dan uwan sauran da ya,raga sai tai wa yaron nata jan ido akan idan yaci sai ta bata mashi rai sosai wallahi.
Daga baya ne tunane yazo min cewa may zai sa yaya ta hana babangida cin kifin bayan tace a tare ta dafa masu shi.
Wallahi ko anyi haka don ba,a fi watanni ba yaron nan yafara birkice min na rasa gane rayuwan shi gaba daya a gidan nan.
Shagon da suke fita gaba daya ma ya daina fita duk fadan Alhaji dole yasa mai ido ya bar shi don ba yadda za,a yi dashi.
To kinji ke mai cewa wai duk sharce ne na malaman tsubo kawai ko ku din ai baku tsira ba nan ta fada masu abin da su ma suke ciki a rayuwan su.
Haba gaskiya abin kan da ban mamaki inji maryam don cewa fa su Lawisa basu kai mutu. Komai ba amma kullun gidan nan sune da sabbin samari kai gaka zaune ko tsoho bai zuwa yace yana son mutum.
Amma gaskiya duk wace tai muna wanan abin inji Amira sai Allah ya saka muna wallahi ko.
Ai ko baki ce Allah zai saka maku don zai koma kan mai shi da yardan Allah.
Yanzu dai ga,wanan yace na kawo maku ku fara sha nan da,sati biyu zan koma na karbo maku sauran hadin insha Allahu.tana kokarin sance ledan dake a hannun ta.
Kuma yace da hannunki zakiba ko wani yaro yasha wanan rubutun, shikuma sadauki idan da hali yace nazo mashi da kashin shi akwai abinda zai yi dashi wanda zai sa ko warin kwaya bazai so ya sake ji ba a,rayuwan shi.
Cabdi aikuma shine babban magana wallahi don nasan ba zai yarda ba ya bani saboda shegen tauri kai ne dashi inji Maji.
Lalai nima nayi tunanen hakan tun a can amma dai yanzu yi kokari ba,shi wanan.
Ta kara fito da wani kulli yace da nonon akuya zaki hada ki bashi ya,shanye yace idan har abin yai aiki zakiga kwana biyu yana yawan barci ki kyale shi maganin ne yake aiki a kan shi.
Nan dai taba da harda wanda su Amira zasuyi wanka da hayaki dashi don makarun asirin da ke kan su harda shi gaiyar aikin.
Mai masa nagode nagode kwarai wallahi, ban ma,san kalar godiyan da zanyi maki ba ni wallahi.
Wai yanzu don Allah shi mutumin bai fadi wanda yai muna wanan irin aikin ba ne don mu sani.
Yafadi bai fadi ba yadai ce min mata biyu ne sai namiji guda kuma ba,atare suke aikin ba kowa tashi tafishe shi ne.
Yace shi bsi son tonon asiri bukatar shi dai aiki yayi kyau asamu biyan bukata don fadin zai kawo hadin hasumi.
Ikon Allah yanzun ni mai na tarewa mutane har na samu makiya daga cikin su haka..
Mai masa may nakd dashi a gidan nan daya tsone wa mutane ido dashi har za aimin haka wai ?
Nuna yaran mai masa tayi tace gasu kuwa abinda kika raina,shine ya dami wasu ai.
Wallahi Maji nafi zargin su mama da Umma don sune basu kaunan mu a gidan nan.
Kada kuyi zaton haka ya kasance basu bane din don zato zunubi ne koda ya zama gaskiya.
Kada azo ana zaton wuta a masaka,asmay shi a makera.
Hakane fa to amma gaskiya su sunfi nuna basu kaunan mu sam wallahi tun muna yara mun san da hakan.
Yanzun dai abar wanan zancen don koma waye mu barshi ga Allah shi zai saka muna.
Yanzu mai masa nawa zanba wanan bawan Allah ke nan don ni har ma na rude wallahi.
Dole ki rude ai don wanan magan ba karamar magana bace saboda yanzu a lokacin muke kana barci ana maka nasari a kai.
Nan dai suka dan taba huran lokaci tsakanin su tai masu sallama tabar su nan suna jimamay.

****** ********* ******
Da farko maganan bai so damuwan Maji ba amma da,dare yayi kasa barci tayi tana nazari akan irin zaman da take da abokan zaman ta a gidan.
Wanda dai ita taga babu ruwanta da,hassadan ko dayan su balle zurian su , bata taba tunanen wai ta aikatawa wa dan ko dayan su wani mugin abu ba koda a,baki ne.
Amma yau gashi ita an sakata gaba har yan yaran da ta haifa a gida ba,a barsu ba don hassada kawai.
Ita dake da yara uku kawsi kacal amma wai sun tsone idon masu bakwai tara da hudu.
Haba jama,a kishi haukane wai da har zaka salwantar da dan kishiyan ka kan bakar kishin da iyakar shi nan duniya sai kuma lahira inda,za,ai hisabi.
Lalai yanzu lokaci yayi da kowa zai kama taka tsantsan da dan abinda Allah yaba,shi don gujewa sherin shedanu mutane.
Gaskiya sai yanzu tasan tayi mugin sakaci akan yaran ta don ita ko goro bata taba basu ba da,sunan wai tsarin jiki.
Musan ma ma,shi sadauki wanda ya tashi tun yana yaro da shiga idon jama,a.
Don haka yake kamar dan larabawa ga kyau ga ilimi ga kunya gashi da miskilanci.
Bai shiga harkan kowa ba,agida ba har gari baki daya, bazata iya cewa ga,ainihin abokin shi na kurciya ba balle ma yanzu da ya koma hakan.
Tayi tayi ta san ko da wa yake hurda da har ya fara wanan shaye shayen amma ta rasa aini hin abokin shi.
Dan dama dama,ma,yaron malamin da,sukai karatu a gurin shi na islamiya ana ce dashi Manir shi manir hae yanzu yana zama da mahaifin shi yana koyawa yara karatu a kofan gidan su.
Don haka bata zargin Manir da wani harkan sha,shanci ko kadan sai ma jin dadin shi na aminin shi da take yi.
Don tasan ko banza zai dan dinga mashi nasiha akan sabon halin da ya dauko ma rayuwan shi.

Sai da dare ya shigo gidan har zuwa yanzu inka gan shi kamar natsatse yake sai dai gaskiya bai bari ba don bai jin zai iya barin sha gaskiya da,wuya.
Amma dai yanzu shan da yakeyi na,tsanaki ne a ganin shi yana wayo ne don kada a gane shi.
Abinda bai sani ba shine karfin adduan mahaifane ke tasiri a kan shi lokacin.
Don Alhaji yaba bada kudi ana mashi addua yanzu sosai sabanin da can da yake daukan abin da,wasa.
Ya fadawa wani amin shi a kasuwa irin halin da yaron na shi sadauki yake ciki.
Mutumin yai murmushi yace Alhaji ke nan kai kama yi arziki yaro daya ke wanan halin.
Ni wallahi har da yarana mata suka fada cikin wanan mugun rayuwan nayi nayi abin yafi karfina dole nasa wa sarautar Allah ido.
Kasan sai mutum ya,daga hammatan shi ake jin wari amma yanzu duk wanda kagani yana da matsala akan iyalin shi sai dai mutum ya rufe kawai.
Don abubuwane gasu nan ba iyaka da lokaci ya kawo muna,sai dai Allah ya kyauta kawai.
Akwai wani malamina zan kaika gurin shi onda abinda abinda zai iya maka sai ya taimaka muna dashi.
Don kasan kowa da irin abinda ya karbe shi mai yuyuwa ni banci nasaraba kai kaci.
Abubuwa da dama Alhaji keyi akan Sadauki amma ba wanda yasani a gidan har ita mahaifiyar yaron ma kanta batasan yanayi ba.
Don ita gani take ita kadai ce keda damuwa akan yaron kawai shi ai yana da,wasu.
Bata san cewa shima abin kamar yafi damun shi ba, don shi ke fita yana ganin duk gari kowa yasan da dan shi mashayi ne.
Yazama mutumin banza ke nan a idon mutanin gari ai.
Suna hanyar su dawowa ne, wani abokin shi ya tare shi hanya yana ce mai bayan sun gaisa.
Alhaji yaya akayine yaronnka ya samu abin arziki, amma kuma kukai sakaci da hakan.
Ban fahince kaba ai wani dan nawa ke nan kake nufi daga cikin su.
Yace U, F mana dan kwallon nan dake gidan ka ance an zo sayen shi yafita zuwa ghana buga kwallo amma baku yarda ba.
Kana nufin Umar Faruq ke nan ko sadauki muke kiran shi ai shifa shi.
Wallahi yaron ya iya kwallo sosai don hakane ma couch din su yai mashi hanyar fita amma wai baku yarda ba.
Sai abokin tafiyan Alhajin ke cewa kai amma kuwa Alhaji baku kyata ba da kuka hana shi zuwa ai wani hanyane na samu nan ma.
Abinda muke ganin yan kudu kawai keyin sa yau gashi ya kawo ga yaran mu.
Don Allah kubar yaron nan yaci gaba da,wasan shi kada ku lalata mashi hanyar samun shi.
Shiru Alhaji habu yayi don shi bai ma san da zancen ba a rayuwan shi don ba,wanda ya taba fada mai hakan.
Yace cikin mamaki gaskiya banda masaniya,akan wannan magan ni in ba yanzu ba din bai taba samuna da,wanan zancen ba gaskiya.
Amma zan bincika naji ko mahaifiyar shi ta san da zancen ita.
Gaskiya a bincika don kaga har team din farko sun shiga gasu sun dawo da abin arziki mai yawa wallahi.
Don Allah Alhaji kubar yaron nan ya tafi don akwai alheri so sai ga,wanan harkan don ba harkan banza bane gaskiya.
Ga yaron naka yana samun yabo sosai a gurin abokan shi dama mutanen gari don haka abarshi kawai yatafi ko zai zama alheri a nan.
Sunyi sallama da mutumin bayan sun kama hanya da abokin shine mutumin ke cewa kaga ikon Allah ko kai duk ka damu kanka gashi ashe mutane kallon mutumin kirki ma suke wa yaron.

****** ********* ******
Sadauki ya,gayar da Maji a cikin mutunci tare da tambayan ta lafiyan ta?
Maji tabashi amsa a takaice da da sauki, Alhamdullahi dama ai kaine kaso kashe ni da raina.
Murmushi kawai yayi irin nashi can saman fuska yace ayi hakkuri don Allah, insha Allahu na daina ai.
Suna nan suna dan hira shi dai yana zaune baice komai ba kuma bai ma sauraren su hankalin shi na daga maganan Maji.
Ke Amira dauko min ledan nan na,saman TV stand kikawo min ba mussu Amira ta mike ta dauko ledan take cewa kawo min ludayi a kitchen.
Bayan an kawo ludayin ta bude roban maganin ta,zuba tana mai addua a bakinta cewa Allah yasa wanan maganin yai muna aiki a jikin mu baki daya.
Babana zo nan tace tana zaune a saman salayan ta bai tsaya ba ya mike zuwa gurin uwar tashi.
Mika mashi ludayin da maganin ke a ciki tayi tana fadin duko kasha duk da bai so bai musa mata ba ya karba ya,sha ta shayar dashi da hannun ta kamar yadda aka umurce ta da tayi.
Haka taiwa Amira da maryam sai ga Bintu tafito daga cikin daki tace yaki ya ta zo ke maki karba kinji.
Bintu ta karaso kamar yadda suka sha haka itama tasha maganin daga hannun maji
Inda maji ta,shanye sauran maganin gabadayan shi da ludayin.
Sai kuma ta hada wani nasha tace a mikawa sadauki wanda ke zaune ya kurawa Tv ido kamar yana kallo.
Saida ta tabbatar yasha komai kamar yadda akace tace dauko mashi abincin shi kinji.
Ana kawowa bai tsaya ba ya karba tare da mikewa maji tana fadin ina kuma zaka tafine wai ?
ya ce dakin shi zai tafi yaci tace tau kadai ci abinci don naga kana,wani rama can.
Sai da safe ne taje gaida mijin su yake ce mata ta dagata yana da magana da ita, haka yasa Hajiya Kubura tafita daga dakin .
Yace dagata ai duk magan ta,shafe ku don ka sadauki ne zancen da zamuyi da ita.
May kuma dan nawa yayi inji hjy kubura take tambayan shi da sauri.
Baiyi komai ba wani magan ce dai aka tare ni da shi akan shi wai zancen kwallan ball din kafan da yakeyi.
Oho Allah yasa alheri ce ta samay mu akan maganan t
Tau

Please Login or Register in order to submit comment