Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

BA MUN BARKI GA ALLAH,,,,



Washegari aka hada lifaya, don taya murnan samun nasaran da sukayi akan wasan su da suka buga na kwallo.
Mun sha kwalliya sosai a lokacin in cikin wani dogon riga mai launin dark blue wanda yaji duwatsu a jikin shi sosai.
Nai rolling din kaina da dan kwalin shi wanda shima yana da duwatsu da aka jera mai a jikin bakin shi.
Ga zobunan gold sun cika min yatsu na dama duka hudu, daya sayo min wuyana saye da English gold.
Na saka wani takalma mai dan tudu akafana sai yar karamar jakar hannu dana rike.
Shigar tawa duk wanda ya ganni sai ya yaba da ita shi kan shi sadauki dana fito sai da ya kasa boyewa a ran shi ga kamshi dake tashi na jikina saboda mayukan danake amfani dasu a can yanzu.
Haka Amir shima yaji kwaliyan shi irin ta yara maza mai tsada sosai tare da saka mai hula irin ta yaran turawa.
Wayan shi ya dauko ya fara daukan mu hoto dashi, yana yaba kyawon mu ni da yaron.
A cikin wata irin dirkekiyar mota muke tafe dagani sai shi sai Amir wanda yake rike a hannun mahaifin shi yana waya.
Muna Isa gurin munga karamawan ban girma a gurin mutanen da muka samu suna jiran isowar mu gurin.
A gaskiya wanna mutane suna matukar girmama yan was an kwallon a rayuwan su.
Yana fitowa ya zagaya a bangaren da nake zaune ya bude min motar da kan shi yayin da idanuwan mutane yake a kan mu caaa.
Wasun su da yawa a gurin basu san cewa sadauki yana da aure ba don su ganin su a gurin su shekarun shi yai karami da aje iyali haka.
Hannun shi harde acikin nawa muka shiga babban holl din wanda yake makil da jinsin mutane kala kala.
Duk wanda yake da iyali acikin su tafe yake da iyalin shi a gurin.
Nan aka shiga gaisawa da mutane ana introducing din juna ga manyan masu kudin kasan turawa.
Inda matan dake gurin suka shiga kallon kalar shiga ta wanda ke baiyyana musulunci a fili.
Don haka aka shiga gimamani don suna matukar daraja matan musulmai sosai.
Ga wasu flowers da ake watsowa daga sama sai shagali suke suna shaye shayen su irin na al,adan su.
Nan sadauki suka hade da wani balarabe mai kudi dan kasan Dubai mutum ne mai tsananin arziki da tarin dukiya acikin nahiyar Arab side.
Gaba daya shine mutum na farko da yazo na daya a duk duniya arziki da tarin dukiya.
Gashi da ra,ayin son wasan kwallon kafa don matashi ne shima haka yasa ya kyasa taimakawa yan kwallo musanman matasa musulmai irin su sadauki.
Yana kuma da kamfani na kera gwala gwalai da diamond nashi na kanshi ga rijiyoyin mai da yake dasu kasa kasa na duniya.
Yana da kamfanin kera jiragen sama da na ruwa wanda yake mallakan shi na kansa.
Hannu Abu sufiyanu ya mika ya karbi Amir dake a hannu na ya dan yi mashi wasa tare da sumbatar yaron.
Cikin wasa yake cewa sadauki ya bashi Amir don yaron ya shiga ranshi.
Sadauki yake cewa ya bashi yace ya gode tare da kissing din yaron inda ya juya gurin na hannun daman shi yai mai magana.
Mutum ya amsa da insha Allah.
Nan yaja hannun sadauki wanda nake biye a bayan shi sun dan jima suna magana irin ta Siri a tsakanin su.
Wanda ashe alakace ta business suke kullawa a tsakanin su a lokacin, mutane da yawa sun San ba kebewar banza Abu sufiyanu yake da sadauki ba a lokacin.
Da hannu ya yafito na nufin na karaso inda suke a tsaye, yake ce min nai wa mutumin godiya.
Duk da ban San ko na may ye ba amma nai mashi godiya irin ta addinin musulunci wanda ya kara sawa mutumin jin dadi a ran shi.
Don shi mutum ne wanda yake son mutane masu yi mashi godiya da nuna farin cikin su gare shi.
Nan dai sukai ta gaisawa da mutanen arziki na duniya kala kala ina rike a hannun shi har taro ya fara watsewa.
Muka Fara ficewa daga sahun farko muka bar gurin don a lokacin a gajiye nake sosai ga Amir da nauyi ba kadan ba.
Muna a mota ya dan sasauta tie din wuyan shi yana juyowa inda nake zaune yana cewa my queen kin gaji ko don nasan baki saba irin wanna kwaram din namu ba ke.
Idanuwana na Dan lumshe nake cewa nauyin daukan wanan din dai ya isheni .
Yace Kai ni dake son na samu ma yafi haka girma idan son samu ne a gurina.
Nace kai Yaya idan Amir yafi haka kiba kuma ai sai dai na dinga barin shi a zaune guri daya don ina zan iya daukan wanda yafi wanna girma haka.
Yanzun ma a Yaya nake iya daukan shi balle ya kara yafi nan kuma ?
Ya dan juyo a mamaki yace Queen baban nawa zaki bari a zaune don tsaban mugunta kuma ?
Nace ai nima babana ne ko ko kamanta nima shi ya haife ni ne wai ?
Nace sune fa gata yanzu a duniya don sune sillar wanna rayuwan da nake a ciki yanzu.
Murmushi yayi don jin abinda na fada yasan ba karya na fadin ba haka zancen yake ko yaushe Ina matukar godewa mama da baba din.
Yace tare da kwantar da kanshi saman kafada ta nauyin ya karu min biyu wanda a lokacin ba nauyi naji ba sai wani sanyin dadi da naji a raina kawai.
Don farin cikina yanzu karuwa yake a kullun Ina mai godewa Allah na da biyayyan da yabani iko nai wa Maji ban butulce mata ba ga bukatan ta a gare ni na auren dan ta da duniya kewa kallon lalatace.
Matsalata daya yanzu shine ban gama tantace ko sadauki ya daina halin shi ba ko yanayi har yanzu.
Haka ne yakan rage min jin dadina a kullun na tuna da wanna rayuwan nashi na shaye shaye.
Ai fa tuni idanuwana ya ciko da hawaye yana magana jin nai shiru yasa shi dago kanshi daga kafadata ya kalleni.
Ganin da yai min a cikin rashin walwala komai ma na duniya yafita min arai a lokacin.
Da sauri ya Kara dagowa yana kallona acikin mamaki tare da kamo hannuna ya rike gam a cikin nashi yana tambayana may kuma ya faru haka queen ?
Na sauke ajiyan zuciya tare da zubo hawayen dake a cikin idanuwana kasan fuskana.
Yasake maimaita tambayan shi da wai may ya faru bana son ganin ki ko kadan a cikin damuwa queen.
Na sauke ajiyan zuciya tare da mayar da kaina ga nashi kafadan ina sauke ajiyan zuciya a hankali a karo na biyu.
Da sauri ya kara jawoni a jikin shi ya rugumay mu yana cewa kada kimin haka Fatima kinsan kwanciyan hankalinki shine nawa yanzu.
Na dauka yanzu zakifi kowa farin cikin gani da idon ki da kikayi na irin baiwan da Allah yai ma mijin ki.
May ye kuma ya samay ki a lokacin da nake tsanmanin farin ciki a gare ki Kuma ?
Na goge kwallan da suka fara zubo min a idona nace Yaya love tunanen bayane yazo min kawai.
Maganan tawa ta doke shi har ciki ranshi yace tare da riko min hannayena duka biyu.
Yace kiyi hakkuri Fatima nasan cewa na bata maku rayukan ku sosai a baya dake da iyayyena wanda nima a yanzu idan na tuna wanna rayuwan bana jin dadin shi a raina ko kadan.
Ki daina damuwan kanki da yawa don sai ma ince ki godewa Allah saboda na San kece sillar daina duk wani mugun rayuwan da nayi a baya Fatima.
Ni kaina nasan har abinda ke kanki baki san kina yi ba akaina don wanna rayuwan da nayi a baya yana bata maki Rai sosai da sakaku kunya ga jama,a.
Fatima nasan kina son na fiye da son da Maji take min a baya wanda a baya nake ganin babu wani mai sona bayan maji da mahaifina da yan uwana biyu da Allah ya bani.
Amma sai haduwana dake Fatima na fahinci cewa Allah kan jefo wasu mutane a rayuwan bawan shi don kawai su taimakawa bawan shi a wani halin taimakon dayake bukata a rayuwan shi.
Hakane Fatima ke alheri ce a rayuwan mu gaba daya don a sanadin ki Abubuwa da dama nawa sun gyaru Fatima ta sanadin ki a rayuwana.
Most especially zan iya ce maki ibadana gaba daya a sanadinki Allah ya nufa na gyara shi.
Kin min Abubuwa da dama wanda ke baki San na San dasu ba a rayuwana Kuma bawai kina son na sani din bane kinyi ne kawai don ki taimaka min kawai.
Wanna maganan da yayi itace mafi girma da tsoro danaji don ban San may yasani wanda nai mashi a rayuwan shi ba.
Nace Yaya love idan abin da naima ya bata ma rai a lokacin ka yafe min don Allah don ba a cikin hankalina nai maka ba.
Ya langabe kan shi tare da girgizawa yace Fatima bata taba yi min abinda ba daidai da rayuwana ba dana sani.
A lokacin motar mu ta tsaya a kofan hotel din da muka sauka a ciki ya karbi Amir daga hannuna muka fito daga motan.
A gajiye muke don ba karamin gajiya muka kwaso ba daga inda muka fito nace ya kawo Amir din na kama mai don nasan shi ba gwanin rikon yara bane sosai.
Yace ki barshi don nima in son ya saba dani ko kin manta da sunan wanda yaci ne a gurina.
Ya ce don haka ke kuma sai ki dinga kokarin kina Sanya mu a cikin farin ciki da ni,imar ki.
Kina kashe Muna kishin ruwan sha,awan mu daga ni,imar da Allah ya tana dar muna a gareki.
Kunya ya kamani daga maganan da yayi haka yasani dan murmusawa kawai Ina biye a bayan shi.
Duk da gajiyan da muka debo Bai hana mu kasancewa a tare ba a daren wanda sai faman sanbatu yake akan irin ni,imar da Allah yai min a jikina.
Har muka bar kasar na yoghuslabea bai barni na huta daga jikin shi ba ga sabon kasalan da ke yawan taso min wanda nake gani sabon yanayin jin dadin da na samu ne hakan.

****** ********* ******
Watan mu cikin na uku ke nan yanzu rabon mu da gida ga wani irin mahaukacin soyayya da so da kaunan da yake gwada muna ni da Amir din.
Abin har yana bani tsoro irin yadda ya ke kashe muna kudi haka har sai da yakai nace mai yayana kayan nan fa sun Isa haka.
Sai dai ya girgizawa min Kai kawai yace Queen idan ban kashe maku ba na kashewa wasu wa kudi haka a rayuwana.
Nikan ban da tacewa dole na saka mai Ido na bishi da kallon mamaki don sai nake gani kamar ba Yaya sadauki dana sani a baya bane .
Wanda tsaraba ma idan ya sayo babu rabo na a cikin sa sai idan mamana tai min ci da karfi nake samu daga gare shi.
Allah mai iko sai gashi yau nice dungurungun a gurin sayan kayan baki daya.
Haka Amir yasha kayan wasan yara su kekuna da jirage teddy ga abin koyon haruffa na English da Arab kala kala ko wani da kalan sautin sa.
Bayan yasan cewa akwai su a gida wanda ya sayo tun yaron yana cikin ciki.
Kafin mu bar kasan ya turo da kayan gida ta hannun Yaya Bashar kayan zasu fada .
Wayanda na sani kenan wanda ban sani ba sai idan mun Isa zan gansu a can idan Allah ya Kai mu.
Daga can bamu nufi Dubai din ba wai suna da meeting a US da zasuyi acan na yan kwallo.
Sai da muka share wata daya a kasan inda ya kara hada business da wasu turawa na kasan don ya saka hannun jari atare da su.
Nan ma bai barmu hakana ba sai da yai min sayayya kamar wanda zai hada kayan lefe.
Suturu na alfarma da atamfofi masu tsadan gaske ya saya muna anan kasan.
Ni kaina a lokacin nasan na zama wata daga cikin matan manya a kasata ke nan.
Gashi nai wani irin kyau fatana yai wani irin lub lub dashi tankar dai irin matan, larabawan Pakistan din nan hakan ni da kaina nasan na samu canji a rayuwana.
Mun shiga kasar Dubai wanda a lokacin watan mu hudu rabon mu da gida kenan har na Fara kewan gida da yan uwana.
Duk da Ina waya da duk wanda nai kewan shi a raina amma duk da haka Ina son gani na a gida.
A kasan Dubai naga mata kasa she masu ji da kansu duk da na taba zuwa amma sai wanan zuwan ya zama min kamar na farko a rayuwana.
Ga matan Nigeria Nan zakace tankar a gida Nigeria kake Nan na Dan sake jiki naji Dan sauki shaukin gida da nakeyi a raina duk da irin kullan da muke samu a gurin shi.
Sam sadauki baya yarda nai hurda da matan hausawan da muke haduwa dasu a can acewan shi Bai yarda da hurda da irin wa ya Nan matan ba dake baro gida su zuwa wata uwar duniya da sunan neman kudi ba.
Gashi suna son yin hurda dani amma sai yace masu ni matata boye ta nakeyi don matar kulle ce ita.
Mutum zai yi mamaki yadda matan manyan kasar mu suke acan birjit dasu zakace a gida Nigeria ne mutum yake ganin su ba wani boyewa ba ne kamar nan da ba,a ganin su sai da ticket.
Gashi da farin jinin jama, a a tare dashi duk kowa na son shi wanda hakan ne muma iyalinshi ya shafe mu don mutane suna haba haba da mu a can.
A nan nuna min halarci so sai a kasan don sun it's taron bakin su dake zuwa masu ko yaushe. wani buki da aka shirya na yan kasan Nigeria inda akai ma Naira kaca kaca a gurin.
Don ko a can sai wanda ya Isa zai halarci wanna taron da aka shirya ida yan bussines din kasan mu suka baje nairan su a gurin.
Shiga sosai ta alfarma mukayi wanda nan ma wani dogon riga na saka mai balain kyau kamar alkyabba rigan take.
Bayan na saka wani English wear daga ciki na kawo rigan daga sama na dora akai.
Alkyaban irin mai tsananin tsadan nan ce ta matan manyan ko manyan ma sai wace ta isa take saka ta don yakai jarin wata a kudi.
Hular rigan yai min wani irin rufi yana rike da wani dan mayafi da yake like a jikin rigan Idan kinga dama zaki iya Dan zarga shi akai shi ma.
Sai ki koma kamar kin yafa idan kuma baki ra,ayin haka zaki sake shi ya biyo bayan alkyaban ne.
Haka na dan yafo shi yai min matukar kyau sosai ajikina kamar wata yar labawa masu fada aji.
Wuyana Kuma diamond necklace dan Kiran Dubai sai su awarwaro da zubbuna masu tsada na saka.
Yaya sadauki yake cewa gaskiya da nasan haka rigan nan yake da kyau da akwati daya zan saya maki nashi.
Nace Kai haba dai Yaya har guda biyar fa ka saya min su duk da tsadan dake gare su.
Yace Queen ba tsada ba shagarki na fada maki shine mutunci na a idon jama,a da kuma matan abokaina.
Ina amfani mijin ki yana rike makudan dollars haka amma babu fitan kwarai ga iyalin shi ai sai duniya ta zage ni kamar ban godewa Allah ba ke nan.
Nafi son duniya su San cewa ke mai tsadace dariya ya bani nace to nagodewa Allah da irin baiwan mijin da ya bani yace to ke fa.
Isowan mu yaja hankalina mutanen dake gurin fitowan mu ya mayar da hankalin mutane sosai a kan mu don shigan mu ko makiyi dole ya kyasa muna ga Dan mu a hannun shi ya dauka a kafanshi Wanda barci yakeyi shi yaron duk da yasha kwaliyan shi sosai.
Matan da basu San mu ba sai tambayan sukeyi halan matar waye wai shin wanna guy din dan Nigeria ne wai ?
Aka fada masu Dan wasan kwallon duniya ne da ake Kira UF Dan jahar sokoto din nan da matar shi.
Lalai yayi abinshi don su keda lokaci gaskiya inji wasu Mata dake zaune saman wasu kujeru dayan tace matar shi yar wanene a Nigeria ita Kuma ?
Dayan tace ba yar kowa bace diyar tallkawa ne auren hadi ne ma akai masu shi ya mayar da ita haka da kike gani.
Kalleta cikin shigan matan manyan duniya kamar diyan wani hamshaki can da ita.
Matar dayan tace gaskiya ba laifi don first class ce gurin gwadawa tsara wanna don bata da makusa ta ko Ina gaskiya dubi dan data haifa mai mai dan karen kyau da shi don Allah.
Wata daga ciki taja tsuki tace kalli yadda yake wani tarairayan ta kamar diyan wani can.
Dayan matar tace ke ko aita isa yai Mata haka don gaskiya ba laifi akanta gara yai haba haba da abinshi don akwai muggan tsofi a gurin nan kema kin sani.
Gaskiyan shi kan gara ya kula da abinshi don tsofin nan da kike gani basu da dama gurin mace maikyau balle suna ganin ta haka yarinya danya da ita.
Dayan kuma tace ke ko ai mace rahamace fa ga mijinta gara yaji da abinshi kowa ya gani a fili.
A gaban matan dake gulman mu muka karaso suka shiga daga muna hannu muma hakan mukai masu muka wuce zuwa inda aka tanadar muna mazauni.
Sun bimu da kallon rigan dake jikina yasha jinin jikin su sosai wanda ko shagon sayar da irin su basu iya shiga don tsadan gurin.
Amma gashi a jikina Kuma mai high quality din na saka a jikina a lokacin.
Sai yatsune fuska suke su na rayawa a ransu dama sune a wanna matsayin haka ko diyan su a haka.
Don haka aka shi ga girmama ni a gurin don matsayin baiwan da Allah yaiwa mijina kawai don sun san ni din nashiga cikin sahun matan manyan yanzu.
Ganin saukin kan dake gare ni yasa wasu suka sauke girman kansu suna zuwa muna gaisawa dasu cikin mutunci.
Bamu wani jima agurin sosai ba don dare ya soma yi muka koma masaukin mu sai dai nayi kawaye da suka nuna ra,ayin su akan hurda dani duk da Yaya ya hade rai bai son hakan dani.
Washegari a masaukin mu sabbin kawayena suka kawo min ziyara nan muka sha hira dasu suna ta yaba irin kyawon da nayi a daren jiya gurin waliman da akayi.
Tare dasu da wasu abokan Yaya mutum uku muka Kai ziya gurin Abu sufiyanu daya gaiyace shi da kan shi.
Karban girma akai muna a gidan nashi inda muka samay shi don suna da appointment da Yaya da suka aje kan tana son ya dora shi jagorantan wani company da yake son yi a Nigeria na mai.
Da sunan zuwa yini muka shiga gidan sai gashi munyi kwana buy a tare dasu cikin kullawa da mutunci.
Ya dankawa Yaya duk wani abinda ya dace na mallakan company da yake son yi a Nigeria din.
Don ya zamo masu babban wakili a can idan min koma gida Nigeria don samun nasaran shi.
Taron nasu ya samu halartan wasu manyan engineers yan Nigeria wanda wanda shi halinshi ne ya daukaka matasa na kasashen duniya don ci gaban su da kasan su.
Mutane sunyi murna da wanna anin alherin da sadauki ya jawo wakasan mu Nigeria.
Gashi matashi mai tashen zamani sun San matasa zasu samu aiki da dama a wanna harkan insha Allahu.
Ga kyauta na alfarma da sukai muna nagani a fada bamu ba harda su Salma kawayena dasu ka raka mu sun samu alheri sosai a gurin su.
Haka yasa na tuna da masoyiyata yar uwata Maryam wace nai alkawari a raina duk abinda na samu nima tare da ita zan raba shi.
Don Maryam ta nuna min so da kaina da bazan iya mantawa dashi ba a rayuwana don itace silar komai da nake ciki a yanzu.
Ba don ta gwada min so da kaunan ba da ban Kai haka a gidan su ba da tuni na gudu na koma kauyen mu duk da halarcin da mama itama take nuna min.
Idan da ban jin dadin zama da Maryam indon ta Amirace kawai ba zan iya zama na tsawon lokaci ba a gidan.
Na samu kyautar mota daga matar maigidan irin da matan su ke yayi a lokacin.
Tare da wani dan karamin kit wanda ke dauke da gwalagwalai a cikin sa Kiran kamfanin su ta alfarma wanda sai wanda ya Isa ne zai saye su a nan Dubai din ma.
Ranan da zamu bar gidan matar tana rike da hannu na tana yabawa da halaiyar mu na kirki don har su Salma da muke tare da su sai da ta yaba da halinsu.
Kwanan mu biyu a masaukin mu na Dubai din muka dunguma zuwa airport inda zamu biya kasar saudiya muyi umurah a can kafin mu dawo gida Nigeria.
Mun Isa kasan muyi ziyaran fiyayyen halitta manzon rahama, a Madina muka dan fi dadewa acan din.
Ranan jumma,a muka shiga garin makka muka fara umarah tare da sallah jumma a.
Adduoin danayi a can sun fi yawa akan samun shiryuwa da kariya na zuria da neman zaman lafiya a gidan aure na tare da mijina da sauran yan uwan shi.
Muna Shirin dawowa ne zazzabi da nake fama dashi ya tsanata a kaina wanda dole muka tafi asibiti ganin likita a can din.
Bamu sha wahalan ganin likita ba sosai kasancewa da wani abokin wasan su sadauki dan kasan muke tare.
Nan a ka shiga min duk wani test da binciken da ya dace ai min a lokacin inda a take results yafito cikine a jikina Dan wata uku Kuma again.
Ya kara auna ni tare da min wasu binke komai nawa normal yabamu shawara Alan Amir da zaran ya dan Kara shan nono na wata daya mu cire shi daga nono.
Yabamu magani na yara da zamu dinga bashi Yana sha kafin a yaye shi daga nonon.
Muna barin asibiti masaukin mu muka koma inda sadauki ya rugumoni zuwa jikin shi yana murna tare da fadin my queen ban San irin godiyan da zan maki ba a rayuwana ba.
Don kin min komai a rayuwana gashi a Dan kankanin lokaci zaki wadatani da zuria a gidana kyawawa abin son kowa.
Nan ya nemo bakina muka mannewa junan mu sai kalman godiya yake sako mun tare da kara manne ni a jikin shi.
Bamu dauki lokaci ba dana ji sauki sosai muka dawo gida Nigeria cikin yan uwan mu tare da tarin arzikina alheri mai yawa da muka dawo dashi a gidan.
Mun kwana bit a garin Abuja kafin mu Kama hanya zuwa sokoto birnin shehu inda yan uwa da abokan arziki

Please Login or Register in order to submit comment