Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

gida ina jin zuciya na ba dadin rabuwan da zan sake yi dasu sai kuma wani lokaci mai tsawo kila na sake ganin su.

****** ********* ******
Wanan ganin da mama tai min ya matukar tayar mata da hankali sosai gashi don samun guri wai harda kyauta kudi nai masu har dari biyar.
Wa ma yasan abinda nabawa uwata a daki don haka tun da safe tai sammakon barin gidan zuwa gidan aminiyar ta larai bamu da nisa sosai da ita.
Tana shiga suka gaisa larai tana ganin ta tasan akwai abinda ya faru don duk tai mata sakko haka agida da akwai matsala ke nan gare ta.
Tace may kuma ya faru mutumiyar tace bari kedai larai nai wa kaina abinda ya koma min ciki wallahi.
A zato na na hada auren yarinyat nan da garbati don na kawar da ita da uwar ta daga farin cikin da suke ciki .
Ashe ban sani ba na dauko wuka ne na dabawa kaina a ciki dana sani daya daga cikin wa yan nan shashashun yaran na cina mashi.
Kin koga yadda yarinyar nan Rahama ta koma Larai ?
Wai yau har Rahama ce da kanta tabani kyautan dari biyar cas kin gashi gashi nan .
Ta baje tayi kyau ta wani murje ta kara haske da ita kamar mai aure a birni yanzu fa uwarta ma bata cikin matsalan komai a gidan nan don sai bushashan ta takeyi.
Jin tai shiru larai tace da ita to ai baki san wani abuba ne Lauratu idan da yar taki kika bashi sabanin haka zaki gani fa.
Da sauri take kallon Lairai don jin abinda tace tace eh haka nane mana don kinga halin su ba daya ba da ita Rahaman.
Yadda nake jin labari fa ita yarinyar ce ta sai wa kanta zaman lafiya da kowa a gidan.
Don ko sabuwa dake hauka da farko yanzu ta aje shi gefe don mutuncin yarinyar a kan su ta dauke su tankar iyayyen ta ne bata je masu a tsaye ba.
Kin ga kuwa banga dan ki ko daya da zai shiga ya mayar da kanshi kamar bawa ba a gare su don a zauna lafiya.
Dama hakane dan hakin da ka raina sai yazo ya tsone ma ido shiya sa tun farko da kika zo min da maganan wanan hafin nace dake kinyi babban kuskure amma alokacin har haushina kikaji don may na fadi haka.
Kina ganin ke kin cuta masu ne baki san taimakawa rayuwan su kikayi ba ke .
Tace bari larai sabon atamfane ma fa ta daura a jikin ta kuma bana cikin lafen ta ba ne don nasan kayan lefen nata.
Gaskiya yaya sallah ya munafunce ni don da yasan akwai ci a wanan auren shine yaki jona daya daga cikin diyan shi.
Nan dai sukai ta kulle kullen su har take cewa duk yadda zatayi ta goga min bakin jini a gidan nan sai tayi don bazata bari tana kallo ina cikin daula ba dani da uwa ta.
Da tasan hakane da bala mai faci zata hada aurena dashi naje ko abincin ci ya gagare ni.
Kamar yadda ta kulla haka ta samu wata aminiyar sabuwa take fada mata wai suna may suka saka min ido ina yadda naga dama a gidan Alhaji gashi sai dinke dinke yake min kullun kuma yanawa uwata aike ba kakautawa.
Irin zancen da sabuwa ke so ke nan ranan da sakon ya samay ta nan ta haukacewa mutane a gida da masifa inda take shiga ba nan take fita ba ga miji kwance a daki ba lafiya amma ta tayarwa mutane da hankali.
Haka yasa shi daurewa yafito katakata dashi yana cewa ke Sabuwa kin ishe ni da masifa da tashin hankali a gida.
Ke lokacin da kika zo gidan nan haka wa yanda kika sama a gidan su kai maki ne shi ?
Don haka daga yau na sake jin hayaniyar ki a gidan nan kowa yaya ne nai alkawarin sai kin bargidan ko akan waye haba kin ishe ni Sabuwa kin kai min ko ina.
Ba a kan ki aka fara kishiya ba ke ba wasu ne kika zo kika sama a gidan bane wai ko su ba mata bane da basu daga hankalin su ba ga shigowa cikin su.
Duk abinda ke fadan wai nayi wa yarinyar nan nayi mata sabuwa sai kizo ki kwata ke ma in na karfi ne ?
Ya juya zai koma daki ya yanke jiki ya fadi tun take mata da yaran gida aka saka kururuwa a gidan aka kwasa sai asibitin birni
Kwanan shi biyar a ka dawo dashi ba hannu ba kafa tare dashi abu kuma ya koma kasa sabo.
Wanan faduwar ya dawo da ciwo sabo gare shi hawan jini yazo ya shiga ciki kuma da sauran ciwar wukan zamani da ba, a rasawa.
Aiko yaran gida da matan su suka saka ta a gaba sai tabar gidan nan ko suyi mata dan karen dukan tsiya su kora ta.
Ganin zasu iya mata abinda suka furta a kan ta yasa ta sulale ta bar gidan baki alaikum tun basu illanta ta ba.
Haka ya sa suka dan sarara mata don ficewan ta gidan ya dan rage masu zafinta da suke ji a lokacin.
Kusan kwanan kin da tayi bata gidan duk fama da jikin Alhaji akeyi don jikin yaki mai dadi sosai a lokacin.
Haka nan ko yaushe cikin jike jike da dafe dafen magani ake mai wani ai mai tausa wani kuma dafa mai yasha.
Muna faman sintiri yi mai sannu a duk dakin da yake haka za, a kwashe shi tara tara zuwa dakin.
Ranan sai ga Sabuwa ta dawo wai iyayyenta ne suka zo suka bada hakkuri akai.
Washegarin da ta dawo ne ina dakina ina barcin safe misalin karfe sha dayan rana na gama dafawa mama hausatu shimkafa da wanken sana an ta.
Shine na dan kwata don na huta a raina can a cikin barci na nake jin ana sallama a daidai kofan dakina.
Firgigit na falka ina amsa sallaman tare da fadin shigo daga ciki ina kokarin saukowa a saman gado.
Lokacin suka shigo dakin Anty Sa,ade na ce daga birni tayi shigan ta na yan gayu ga kamshi na tashi daga jikin su.
Tana tare da wata yar matashiyar budurwa tare da ita sai diyan ta biyu da take tafe dasu.
Ban san lokacin da na yanka wani uban ihu ba na makale mata a jikin ta ina cewa wai ni Rahama yau ina zan saka kaina.
Sai kuma na fashe da kuka a lokaci daya na durkushe a kasa daidai kafan ta ina rusa kuka gwanin ban tausayi.
Naji tace yau ga tsiya taron da zakiyi min kuma ke nan Ramana daga gani na kuma sai ki saka kuka haka ?
Tace wa budurwan da suke tare maryam tashi mu tafi wanan bata son zamana a nan.
Da sauri cikin kuka nace anty don Allah kiyi hakkuri na daina ina kokarin share hawayen dake fuskana a lokacin.
Nashiga daukan yaran ina cewa kai Fatima kece kika girma haka na taba hannun babban dan ta sai ya jaye daga gare ni.
Nace baka san ni ba ko kokaga na zama wata bakauya dani ko ina fadi ina dariya tare da kallon fuskan yaron.
Nan muka shiga gaisawa dasu cikin murna da jin dadi ina tambayan ta yaushe tazo garin namu ?
Tace ikon Allah Ramana ke ce yau haka a dakin auren ki gaskiya naji mamaki da mama ke fada min wai aure zakiyi sai ko gashi na tabbatar da hakan yau da nazo dakin ki na gani.
Murmushi nayi tare da fita daga dakin da sauri na fita zuwa bakin randan ruwa na na kasa na debo masu run shi a cikin kofin silver mai marfi.
Nakawo masu ba laifin sun karba sun dan kora ruwan suka aje kofin amma yaran su sunki shan ruwan sai turanci suke da uwar su da dayan budurwan da suka shigo da ita gidan.
Tambaya na take ina maigidan naki ne mama tace muna yana fama da jiki wai Allah ya sauwaka ya bashi lafiya.
Mun dan taba hira dasu wanda akan karatuna ne nake mata ina fada mata cewa nawa karatun ya rushe ke nan tunda zaman gidan nan da nakeyi ba fashi a cikin shi.
Tace komai ai na Allah ne baki san ko watarana zai yarda kije gaba ba ai nace cafdi anty bako a gidan nan ba.
Tace muje kikaini na gaidashi da sauran abokan zaman naki ko ?
Ban bata lokaci ba na mike muka nufi dakin mama hauwa inda yake kwance a ranan.
Kwance yake yana ganin mu yake kokarin mikewa zaune sai dai bai iyawa dole ya koma ya kwanta yana masu sannu da zuwa.
Kusa dashi naje ina cewa Alhaji anty na ce ta birni da nake baka labari tazo ganin mu yau.
Hannu yake daga mata alaman yana masu sannu da zuwa yai matukar bamu tausayi gaba dayan mu a dakin.
Gashi dai ya na son yin magana amma babu halin yin haka a gare shi sai in maganan ya zo mai yake samu yayi shi.
Muryan anty ce ke fadin an kaishi asibiti kuwa a hakan da yake kwance a daki ?
Mama tace an kai shi sai dai ba wani babban likita ne suka samu gani ba suka dawo wai akwai tsada ga ganin likitan.
Haba komai tsadan shi ai sai a kashi a ji halin da yake ciki yafi wanan kumshe shin da akayi haka a gida yana wanan wahalan haka.
Tace yana da yara manya ne maza suka ce mata eh tace idan suna kusa ina son magana dasu don Allah.
Daga haka muka fita na kaisu dakin mama hausatu tabata dubu biyar dakin sabuwa ma haka da mama hauwa.
Ai sai aka shiga saka mata albarka kwando kwando a ranan muka koma dakina kafin su yaya Hadi suzo gidan.
Tace gaskiya Ramana mijin ki ya bani tausayi mutum yana wahala haka an kunsheshi a gida ba wani maganin kwarai gare shi.
Kiyi hakkuri kinji duk wanan jerabawa ne daga Allah kici gaba da biyayyan dakike yi Allah ba zai bari ki tabe ga banza ba a rayuwan ki.
Muna cikin maganan ne sai ga yaya Hadi babban dan Alhaji yana sallama daga kofan shiya na.
Na fita naga shine nace mai ya iso itama na fada mata zuwan shi nan tafita daga waje gurin shi suka gaisa.
Take cewa dama tana so ne idan sun yarda sai akaishi asibitin can birni don zata koma ga jibi kunga sai ku isa ina can amma sai abinda kuka gani ga hakan.
Yai godiya yace sun gode zai yi shawara da sauran yan uwan shi takawo dubu hamsin taba shi tace ayi amfani dashi idan zasu zo din.
Da zata tafi tabani dubu ashirin wai na dinga amfani dashi tunda mijina da zai bani baida lafiya yanzu.
Sau mutanen gidan ta basu dubu goma wai su raba haba sai gida ya kaure da bakin albarka kowa na saka mata albarka agidan suka wuce muna kallon su.
Basu ki ba bayan shawaran da sukayi sun yake cewa tunda za, a taimaka masu gara su kaishi su gani kawai zaifi .
Haka su ka yanke shawara bayan kwana biyu da tafiyan ta suma suka take mata baya sai garin kano ganin likita.
Basu sha wahala ba don ta basu lanban wayan ta idan sunzo su kirata don ta sani.



ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, ,


IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH DON AMANA NE SHIGAN KI GROUP DIN MU, IDAN BAZAKI IYA BA KIYI MAGANA MU BAKI KUDIN KI YAR UWA, , ,


Taro na mutunci suka samu a gurinta ba bata lokaci ta wuce dasu asibiti inda saboda sanin ta gurin ba a dauki lokaci ba suka ga likita.
Nan likita yai ta fada don may zasu aje shi a gida haka har tsawon wanan lokacin basu zo dashi asibiti ba.
Hakkuri suka shiga bashi ya duba shi aka bashi gado har na tsawon sati biyu .
Duk anty Sa, ade ce ke kokarin haka dasu gashi tana yawan zuwa duba su akai akai har zuwa lokacin da ya samu sallama daga asibitin.
Sunyi da likita nan da wata hudu zasu dawo dashi lokacin ya kara murmurewa za, a ai mashi aiki a gaban shi.
Itace taba da mota aka dawo dashi gida cikin iyalin shi da abinci masu gina jiki da zai dinga ci don lafiyan shi.
Muna nan muka ji dirin mota sai ganin su mukayi yana tafiya da kan shi ba kamar yadda aka tafi dashi ba da farko alaman sauki ya samu ke nan gare shi.
Mun ga yan zuwa gaida shi daga ko ina na muna barka da arziki suko su yaya hadi sai labarin irin karamcin anty sukeyi baki sake.
Suna fadin sunga inda daula ya yanke saka a gidan su sai kace ba a kasan nan ba mutum yake sun yaba da halarcin ta kwarai da gaske.
Sosai yake samun kulawa yadda ya dace abashi nan kuma aka koma yawon bin daki dashi duk wace keda girki za a kawo shi dakin ta yai kwana biyu kafin ta fita daga girki ya koma wani dakin kuma.
Ranan ina zaune ina kwalliya yana dakina nikan na mayar da hankalina ga shafan mai da nakeyi .
Ashe yana daga bayana ya falka ya kura min ido yana kallona a cikin tausayawa.
Shi kadai yasan abinda yake ji a ran shi a lokacin gamay dani yana ganin ya kuntatawa rayuwa na ya zama wajibi idan ya dan kara samun sauki ya sallamay ni naje na auri yaro wanda ya dace da ni.
Ban ankara ba sai jin sautin kukan shi nayi daga bayana yana tashi a hankali.
Ban lokacin da na shuri da kayan shafan nawa ba na isa gurin shi cikin tashin hankali nake tambayan shi ko jikin ne na kira mutanen gida suzo.
Yace dawo ki zauna Amarya lafiya na kalau wallahi tausayin ki ne kawai ya kamani ni san ban maki adalci ba a rayuwan ki.
Bazan iya biya maki bukatan ki ba amma na ajeki a hakana ina kallon ki gashi sai kara cikowa kikeyi shine nake ganin anya ban shiga hakkin ki da yawa ba kuwa nan da wani dan lokaci dole tun baki fahinta har kizo ki fahinci maynene sirin aure ke da kanki zaki fara son hakan a rayuwan ki.
Kinga duk halin da kika fada ciki nine da alhakin hakan a kaina ba wani ba don nine na ajeki batare da biya maki bukatunki ba.
Nace haba Alhaji bayan wanan kokarin da kake min may na rasa a gidan nan ni wallahi nagode kuma har gobe ina gode ma sai idan ban nufashi zan daina gode ma.
Na sa hannu na dan share mai hawaye nace kayi hakkuri Allah zai baka lafiya kamar kowa da yadda Allah.
Ajiyan zuciya naji ya sauke yake cewa ba komai zan dai san yadda za, a yi akan wanan ala, amarin naki nan gaba.
Haka yai min kwana biyu na ya koma wani dakin wasa wasa sai wanan halin ya zama mai jiki duk yake dakina da wuta bai zubar da kwalla ba a kaina wanda ni ban san ko na may ye ba.
Haka muka zauna dashi watan shi uku da dawo asibiti yaji sauki sosai ya murje har ya dan fara fita kofan gida yana shan iska waje tare da jama,a.
Ranan ya dawo dakina naga yana muku mukun ciro abu daga Aljihun shi na taimaka na ciro mai sai naga kudi ne masu yawa a ciki ya kira da yawa yace min yaki nan .
Nazo kamar yadda yace kusa dashi na durkusa yace ungo wanan kikai wa Innan ki asamu wani sana, a a dinga juya maki kudi suna dan shigo maki kina samun na kashi.
Don kinga yanzu ni ba fahita nake ba balle na dan dinga samo maki dan abin kwallam kina tabawa.
Gashi duk wani motsina idon mutane yana akaina ba halin nai maki wani alheri mai tsoka a gani.
Har lokacin da yake bayanin kudin suna a hannun shi ban karba ba sai da ya kara cewa cikin daure fuska karbi mana nace maki.
Nasa hannu na karba tare da godiya yace gobe sai ki shirya idan nabar dakin ki kije gida kikaiwa Inna ki ayi shawaran abinda za, ai maki dasu nace nagode.
Nan na duka gefen shi nai kuka mai isata tare da fatan Allah ya bashi lafiya.
Washe gari kamar yadda yace na shirya sai gidan mu na kebe da Inna ta nai mata bayanin komai kamar yadda yace min.
Tace to sai dai naga mamanki Altine don tafini dubura sai na barmata ta dinga juya maki su don nasan gurin ta sisin kwabo bai ciwon kai a cikin kudin nan.
Da haka na dawo gida na shige dakina ita kuma taga mama Altine tai mata bayanin komai suka yanke shawaran yadda za, a dinga juya min su
Mai hali baya barin halin shi ranan ya bamu dubu biyu biyu yace mu rike a hannun mu muyi amfani dashi.
Nan Sabuwa ta shiga fadawa wai ba, a adalci don may damay iyali da wanda baida za, a basu komai daidai.
Sau daya ya iya cewa ke Sabuwa daga haka kuma sai maganan ya tsaya mai ya dan dukar da kan shi.
Wasa wasa yana fadin yana jin kamar masasara ya kama shi nan suka kira wani nurse yazo yai mashi yan allurai a gida.
Sati biyu da yin wanan a tsakanin mu ina barci tsakar dare naji an fasa wani irin kuwa a gidan.
Duk wanda yaji wanan kuwan yasan muryan Sabuwa ce gaba daya mukayo waje sai ihu take tana fadin Alhaji Alhaji babu shi.
May kikace Sabuwa tace wallahi Alhaji ne daga yace na bashi ruwa yasha sai kawai naji ya sarke shike nan sai naji shiru.
Nan aka fada dakin amma ina yariga da ya tafi sai addua kuma din rai yayi halinsa ko a gare shi.
Hadi ya shiga yafito ya fasa wani irin kuka yace baba ya riga mu mama baya yarasu ko .
Daga inda nake tsaye nace da karfi Alhaji ya rasu yaya ?
Ban kara sanin inda nake ba sai dai na falka naga mama Altine da mama Asabe makwabciyar mu a kaina ina kwance saman gado dakina.
Ina iya jiyo hayaniyan mutane suna koke koke a tsakar gidan na tunkura zan tashi mama ta rike ni tace haba Rahama.
Kiyi hakkuri ki dangana Allah daya hada ki da Alhaji ya karbi abinshi sai hakkuri kawai.
Wani sabon kuka na fasa ina fadin mama da gaske Alhaji ya rasu shike nan bazan sake ganin shi ba.
Tace ya tafi Rahama adduan mu kawai yanzu yake bukata tashi takare shi yau ya koma ga mahaliccin mu sarki Allah.
Kuka sosai nakeyi haka gari ya waye muna cikin tashin hankali a gidan kafin wani lokaci har an hada shi za, a kaishi gidan shi na gaskiya.
Aka ce muzo muyi ban kwana dashi kafin afita dashi daga gidan mama tace min ki daure kada ki fara kiyi mashi kuka Rahama.
Ina rike ga hannunta muka shiga dakin da yake kwance an shirya shi cikin fararen kayan shi na tafiya kayan da kowa ke jiran ranan sawan shi tazo mai.
Nan mukai mai addua muna waje aka fito dashi aka fice dashi daga gidan nan gida ya barke da sabon kuka kuma.
Daga ranan muka shiga takaba sai tambayana ake zuwa yi wai banda komai tare dani ko ?
Sai dai nai masu murmushi kawai ba amsa don ban san may zan ce dasu ba ni don mama tai min dalla dalla akan tambayan da ake min.
Sai da aka watse an tafi sallah nake cewa da ita mama nifa ba wa abin da ya taba shiga tsakanina dashi irin haka.
Tace ke don Allah rufe muna baki da wautan ki keda kwanaki akewa radw radin ciki sabuwa har da yaji tayi kan haka zakice wai ke ba abinda ya taba shiga tsakanin ki dashi.
Kada na kara jin wanan zancen ko ga wani balle ai maki daukan mahaukaciya.
Haka dole naja bakina muka shiga takaba ni da sauran matan shi a gidan inda nake zama da mama Altine da wata tsohuwa cikin yan uwan Inna ta.

****** ********* ******
Tunanen makoma na yadda zan koma gidan mu cikin ukubar mama ya fara damun zuciya na.
Har nakaiga furtawa ga mama tace to yaya za, ayi ya zama dole yanzu kan ki koma gidan ku gaban iyayyen ki tunda nan baki da kwai baki da dunge a gidan to zaman may zakiyi masu a gida kuma ?
Hakana muke wankan a dadafe ranan da ya cika sati biyu ne yar gurin sabuwa ta zo ta kwashe min ruwan randana nai mata magana cewa bata ganin yanzu sai na sayi ruwan tunda banda mai debo min.
Daga can kofan uwarta ke cewa ke ma dai baki jin magana wallahi may yakai ki gurin wanan mai farar kafan ki debo min tsiya.
Ga uban ku nan tun ranan da ya tsiri auren wanan matsiyaciyar yarinyar bai kara lafiya ba sai da ya kwanta daman shi.
Shine ni zakije ki debo min tsiya kikawo min har ana maki kwakwazo akai kan ruwa.
Mama Altine ce tafi ban ko sani ba tace boyar Allah maida yukan ki kube yau ina wanda kuke fadan a kan shi ya kwanta daman shi.
Ke har wani dadi kikaji kina cikin wanka kike sababi haka kamar wacce abin bai dama ba.
Aiko ta juya kan mama da masifa wai mama ta kama girman ta kada yanzu ajisu da ita.
Karya ta fadi banice na jawo masu masifan rayuwa ba kala kala don iyayyena suna makwadaita aka cinna mai karfen kafa.
Allah yasa yaya Hadi yana shigiwa lokacin ya taka mata waigi da cewa ke sabuwa kin fa ishe mu a gidan nan dama don baba nake daga maki kafa.
Yanzu ke ba, ace kin kashe muna mahaifi ba sai wanan yarinyar da kullun baba cikin saka mata albarka yake har ta bar duniya keko fa daidai da rana daya banji makamancin wanan kalman ba daga gareshi a kanki.
Don mu har wasiya ya bar muna akan yarinyar nan kan ko bayan ranshi mu kula mashi da rayuwan ta kada mu bari ta shiga wani hali na wahala.
In ma kashe baba ne badon kada mu bata mai gawan shi ba ai sai muce kece kika kashe muna uba.
Don matsalanki ya kara jefashi ga ciwon da yayi na ajali karshe ma bamu san may kikai mai ba sai gawan shi muka gani a dakin ki.
Cikin wani irin tashin hankali take cewa yanzu Hadi ashe sherin da kuke kulla min agidan nan ke nan ku da muna fukan uwayen ku ban sani ba.
Tsofin dake gidan suka fito sukai mata caaa akai suka ce fitinan ta ya ishe su idan kin matsa zamu mayar dake gidan ku ne.
Tace wani gida ga gidan mijina da dakina da ya mutu ya barni a cikin sa ai yanzu kuma sai ido don jini ya riga ya gauraya da ruwa ko.
Fitinan sabuwa ne yasa diyan shi

Please Login or Register in order to submit comment