Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

dan samu saukin ciwon jikin da nake ji dana tashi.
Nai matukar mamaki kwarai da naga yaya yana sallah jam,i bai wuce shi duk asubahi sai naji fitan daga gidan zuwa masallacin uguwan sallah.
Ya dawo daga motsa jiki ya samay ni tsaye ina hada table din cin abinci a cikin kunyan abinda ya faru a tsakanin mu daren jiya yasani dukar da idanuwa nakd gaishe shi da kwana.
Ya kara so tare da dan rike ni daga bayan na yana cewa, ke baki gaji bane har kika tashi ki aiki haka mai yawa?
Kunyan shi nake ji ban yi magana ba sai dan murmusawan da nayi nace yanzu zakaci abinci ne?
Ba abinci nake son ci ba ke dai nake so yanzu ya bani amsa fuskan shi a daure tamau kamar ba wani magana yayi ba a lokacin.
Da sauri na kalli agogon ban gon dake falon sai na ji ya furzi iska yace zan makarar dake ke nan kike nufi ko?
Ya juya ya fara tafiya yana ffadin ok a dawo lafiya sai dai kafin ki dawo zan kai musa school din su sai kuyi sallama dashi.
Daga haka ya shige dakin shi ya barni gur8n tsaye koda na shirya nashiga yi mashi sallama na samu ya shiga wanka a lokacin.
Don haka na cire mai kaya daga cikin wardrobe din shi haka zai sa yagane na shigo dakin na juya nafita da sauri don na kusa makara ranan.
Bayan yafito kayan da ya samu na fitar ma saman gado don yasa yasa shi gane cewa na shigo dakin a lokacin sai daya gama shirin shi yafitone musa ke fada mashi nace na tafi don na makara yau.
Yana gamawa dama musa duk ya kagu su wuce don haka,basu bata lokaci ba suka fita zuwa school din da za,a kai shi na kwana.

****** ********* ******
Haka muka kasance da yaya kullun a tare muke kwana dashi yana yadda yaso dani tun ina jin nauyi da kunyan shi har na dan fara rage kunyashi da nakeyi sosai.
Yanzu yakai basai yace nazo dakin ba don kaina nake shiryawa naje don ma inhar banje ba shida kanshine zaizo ya dauke ni cak yatafi dani.
Ya gama binda yake ya koma gefe daya yana sauke numfashi a hankali tare da furzo iska daga bakin shi.
A raina nace wai dama maza basu da kunyane haka wai kamar ba shine mutumin da ke ta cika bakin shi ba abaya akan dole ne maji ta lakaka mashini.
Yanzun gashi shine harda wasu irin kalamai da ina ganin ba a hayacin shi yake fadar su ba idan mun kasance a dukule tare.
Idan kuma weekend ne zan iya cewa kusan a tare muke zama muyi shi agidan bai son fita nan da can yana nan ciki ya hanani shakat a gidan sai yayi yadda ranshi ke so zai sarara,min.
Watan shi daya cur a garin da dawowa bai fita zuwa koda Abuja bane yanan cikin gari.
Ranan ya shigo da yamma yake ce min na shirya zamu fita zuwa gida mu gaida su baba don baba bai jin dadi jikin shi ya tashi.
Na dan rude ina fadin subbahanallahi may kuma ya faru da,baba ni dai Allah yasa ba wani mugun abin aka aikata ba har ciwon shi ya tashi.
Tun karfe bakwai na fara shiryawa na saka wani atamfan super exclusive, mai ruwan yellow da zanen ganye kore zani da rigane sai gyalen da na yafa karo na farko a gidan aure na.
Takalma da handbag duk na fitar da zan saka sai wani irin mayen kamshi dake tashi ajikina na dade ina bata lokaci gurin gyara jikina kamar wacce zata gidan wani shugaban kasa.
Nasan idan na samu matsala ga shigana ba su Umma da mama ba har Amira sai na samu musguna daga gare ta.
Sai gashi ya shigo dakin yana wani kamshi dashi yai mugun haduwa don shadda ce gezenah a jikin dark blue sai wani maiko da yauki takeyi har hulla sai da ya saka yau nace dankari a raina wani abu ko sai mahaifa.
Yadda yake kallon shigana nima haka nake satan kallin nashi shigan don duk wanda ta fan mu komai bakin cikin mutum dole ya kyasa muna.
Karasowa yayi har inda nake zaune a gaban mirror ya kura min ido can naji ya numfasa yace wai ke ashe haka kike dama kike ta faman boye kanki cikin mugun hujjib kullun kamar wata munafuka can.
Nace ai dama sunana ke na a bakin ka kuma boyewan danakeyi ai ba kaina naiwa hakan ba don da baka samay ni ba kai.
Namike ina cewa dama nasani na dinga kwalliya irin na anty Nafisa tunda shina ga yafi burge mutane yanzu.
Yace dako na halakaki tun lokacin don ba zaki jawa maji zagi ba, nace ai naga shine ra,ayin ku ku.
Murmushi yayi tare da kamoni yana mikar dani tsaye yace ki tabbatar da kin rufe min wanan jikin naki da kyau don kinsa akwai kardawa a gidan .
Yayyen nawa ne kuma gardawa ashe kardawan yawa gare su bamu sani ba masu kalle surar kannen su .
Yagane maganata sai yai murmushi kawai yace ai ban kalle ba sai dai ina shirin kallo don gada wani ya bani labarin abinda ban sani ba nida abina.
Da sauri na dago kaina nace may kake nufi da hakan ya wani lumshe idon tare da furzo iska yace ma,ana har yau ban san komai ba akan matata da rana ganin dare kawai nake mata koshi ma a,wahalce ga cizo ga yakusa da zagi.
Murmushi nayi na dukar da kaina kawai don natuna first night din mu dashi yadda naitakiran shi azzalumi macuci mazina ci kawai.
Isan kin shirya sai ki tashi mu tafi kada ki bata muna lokaci don ina da abinyi ni idan mun dawo don ba wani dadewa zamuyi ba can.
Kallon mararaicewa naimashi nace tare da turo baki, ni wallahi kullun abu kullun abu ba tausayawa mutum.
Yace wani abu kuma cikin kasheni da idanuwan shi don son jin amsa na.
Banyi magana ba sai gyalena da ke tashin kamshi kawai dana yafa akaina nan na kara fitowa wata shar dani nai marukar kyau har ya kasa dauke idon shi akaina.
Yarinya ke kikace kina so dabakice kina so ba da ba,abaki ni ba, yasani gaba muna tafiya yana min waka a baya na.
Wata landdrove jeep nagani a waje dark blue sai shaki takeyi van san da ita,ba a gidan sai wanan lokaci ko ba afada nasan ansha miliyoyi a waban gurin .
Ita muka shiga shike driving kamar bai son tukin motan nace amma ya kamata mu dan sayi wani abinda zamu shigawa baba da su Umma dashi kada mu je masu hannu a sake.
Kamar baiji mai nake cewa ba yai banza dani a raina nace bahagon mutum kawai wanda ba,a gane kallan shi kaman ba shine yanzu yake min waka ba gashi mintina kadan ya wani sha toka ya murde fusaka tamau dashi.
Gaban wani katon shago ya tsayar da motar shi sai da ya kashe motan ya juyo yana ce min fito mu tafi.
Har mun fara tafiya yace gyara rufe jikin ki dak yau don kinga an fara binki da kallo kiyi shiga kamar wata budurwa can.
Gyara tsayin gyalena nayi da kyau tare da bin bayan shi munyi sayayya sosai a shagon har sai da nai mamaki leda kusan bakwai akayo muna muka nufo gida dasu.
Ina ganin get din gidan nai wani lumshe idanuwana don jin dadin ganina a gidan da nai rabin rayuwana a cikin shi cikin jin dadi.
Muna fita gab da zamu shiga gidan sai naji ya riko min hannu na kallon hashi nayi ba tare da ya kalle ni ba yace eh haka nake son maman ki ta ganmu don tasan na rike mata amana.
A haka muka shiga gidan mun fara cin karo da yaya Abdul yace tun daga nesa a,a,a Allah yayi hadi a gurin nan sai kace kuka hallici kan ku haka.
Murmushi ya sauke kawai tare da kara rike min hannu da kya yaya Abdul yace kaga zabe gaskiya kan nan ba irin wa yancan da suka zabo mata ba kamar suna barci.
Muna shiga cikin gida Rukaiyya diyar mama Asiya tana waje tsaye tana waya tana ganin mu ta wani watso muna idanuwan ta gaba daya a kan mu.
Dakin maji yace a fara shiga da kayan bayan ya cire wasu leda guda uku daga cikin ledojin da,muka shigo dasu yace min a hankali kiba wa su Umma kowa guda guda nace angode.
Dakin Umma muka faea zuwa tana zaune da yaran ta sai jin sallaman mu tayi har mun kawo kofan shiga ko duk sai ta daburce da ganin mu.
Zama yayi kan kushi na zauna kasan carpet daidai kafan shi muna gaida ita .
Cikin hali irin nata na shan kamshi take amsa muna kallo daya tai muna wani mugun hassada da bakin ciki ya darsu a zuciyar ta tace kina nan kina ta hakkuri da halin mijin naki ko don ba fasawa zaiyi ba na sani.
Murmushi kawai mukai mata don duk mun fahinci nufita amma muka kyale ta
Bamu dade ba muka mike na karasa gaban ta ina cewa mama ga wanan ba yawa dan tsara bane ta amsa a wullakance tana tabe baki tana fadin angode.
Na juya har na fara rafiya sai najuyo ina cewa yaya sagir fa idon ta nagani tana kallin kasan zanina da harara tabini ta tabe baki tace yafita dazun nan.
Dakin mama Asiya kuwa muna shiga dama Rukaiyya ta riga data fadawa mamata zuwan mu ko da ta gan mu.
Idon kyam a kaina yadda mukayi dakin mama haka mukayi a dakin ta bamu dade ba mukafito namika mata ledan tace to har da wani tsaraba can to angode.
A daiyi ta hakkuri don kin san abinda kika aura dama don haka sai a daure da hakan .
Muna barin gurin sai dakin mummy sai dai a rufe dakin yake yaran ta dai ne kawai a ciki alaman tana dakin baba a lokacin.
Yaran suka yo kanmu suna muna sannu da zuwa cikin rugumay mu Imirah yace yaya nace mummy takai mu gidan ka tace wai zamu damay ka kana hutawa .
Muma yaya kazo ka kaimu mu huta tare da kai kaji, ya shakan shi yace zanzo na dauke ku.
Yaran sukaji dadi suna ta murna yayan su yace zaizo ya dauke su zuwa gidan shi namika masu ledan tsaraban su wanda daban yake saboda akwai alawan yara acikin shi.
Sai dakin mama muka nufa kuma suna falo zaune da Amira muka shiga da sallama ina rike a hannun shi kamar wata yar yarinya can dani.
Sannu ku da zuwa mama tai muna Amira tana dago ido kallo daya tai muna naga tai sauri kawar da kan ta gefe daya tana cewa sannu da zuwa yaya.
Nace anty ina wuni ta ansa a wulakance da lafia kawai ta juya kan ta ya kalle ta yai murmushi yace sister ke nan yaya gidan gaban mama na tafi na durkusa a gaban ta nace mama ina wuni ?
Cikin jin dadi da ganin mu haka tace ashe kuna tafe ne yanzun tashi ki zauna Fatima kinji Allah yai maku albarka ai yanzu yaro yashigo da leda yake cewa kune kuka shigo.
Sadauki yace maji yaya na barku dazun haka yasa nagane cewa yashigo da rana ashe nice dai yakawo nagaida Baba da jiki ashe.
Mama tace mai lafiya muke yace to yaya jikin na baba tace a,a Alhamdullahi ai ya samu sauki sosai har ya tashi yayi sallah ko dazun.
Ta juyo gareni tana cewa Fatima kuna lafiya ko cikin jin kunya nake cewa lafiya kalau muke mama.
Tace ashe musa an tafi makaran ta saiga babana yazo dashi ya sallamay ni ranan .
Cikin jin kuya nai murmushi tare dukar da kaina kawai nace wallahi mama yaya ne yai mashi wanan kokari kuma yasaya mai komai da zai bukata acan .
Sai a taya mu godiya gurin shi mama tace ince maki sun gode kwarai Allah ya saka da alheri.
Mama tace kai haba waban ai yiwa kaine kawai wa yasan abinda zai zama watarana kuma in Allah ya raya abinshi.
Kina dai waya da su ko don ki dinga jin lafiyan su akai,akai don haka na dakyau.
Gurin da Amira take zaune ya koma ya zauna saman hannun kujera yana cewa may kikeyi ne wai kin wani fuskewa mutane haka.
Tace cikin da yake yaya kawai dai hakanaji ashe zaka dawo yace eh waccan nakawo ta gaida baba da jikin shi don dazun ya tambaye ta.
Hummm wanan muba fukar matar taka ai ta iya sace zuciyar kowa da makircin ta harda ma wanda bamu zata ba duk ta sace munafuka kawai.
Kai Amira Fatima ce kuma muna fuka munafuncin may taimaki kuma haka ne wai .
Sai lokacin ta dago kai tace humm yayya ni wallahi mamaki ma kake bani yanzu dan ban yarda amma yau na shedawa idanuna gaskiyan zargina.
Yanzu kai yaya har ka iya fito da wanan a gari a matsayin wau matar ka har kana wani jerawa da ita, kamar wata mai mukami can.
Kasa kasa suke maganan su amma duk zancen su ni yana a kunne na don ina dan kusa dasu mama ce kawai bazata ji ba a lokacin don ita sai farin ciki da murna takeyi tagan mu a cikin farin ciki a tare.
Can ya mike don ba zai jure sauraren Amiraba don tana bakanta mashi rai da zancen ta gap yake da ya dauki matakin da bata zata ba a lokaci guda.
Idan nake a zaune ya kallo yana cewa taso muje gurin baba ki dauko wancan ledan muje mashi dashi.
Yana gaba ina bayan shi muka tsaya daga kofan falon baba muna mashi sallama.
Aka ansa muna muryan mamane take ce muna mu shigo ganin mu tare yasa baba dake a kishigide ya dan dago zaune cikin fara a yake cewa,aa Fatima tare kuke ashe?
Har gaban baba naje na duka ina gaida shi shima a kasa yaa zauna kamar yadda na zauna yana gaisawa da Baba din tare da tambayan shi karfin jikin shi.
Mun dan jima zaune suna hira da baba da mummy ni dai kaina a duke banyi magana ba.
Sai can baba yace sadauki gaskiya nayi farin ciki kwarai da ganin ka haka ji yadda ka kara murjewa nasan wanan duk aikin diyata Fatima ce don tasan abinda ya dace.
Ba kamar matar wanan mahaukacin ba da tazo gaidani dazun kaga nan yana taba kujeran gefen shi yace a nan ta zauna wallahi.
Baba yace wanan irin abubuwan dole su jefa mutum a cikin damuwa yau ace irin tarbiyan da na,baku a gidan nan amma a cikin zuria ta ake samun irin haka.
Sai yai shiru tare da girgiza kan shi can yace wallahi yaran nan suna kashe min zuciya.
Baba kayi hakkuri ka daina sa irin abubuwan nan a ranka kaga ba lafiyane a jikin naka bba yanzu.
Nan dai baba ya kara dan muna nasiha mukai masu sallama don dare ya somayi sosai.
Mun koma dakin mama mukai mata sallama tana ta saka muna albarka muka fito daga gidan.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
[16/12, 00:22] Maryam Ummu Firdausi Group Ismail: IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,


IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH YAR UWA,,,,


A LOKACIN MUKE,,,,


Yau ya shirya unexpected ya samay ni daki bayan na dawo daga school yakw ce min zaiyi tafiya ne zuwa Mexico gurin wani taron yar kwallo da za,ayi kuma yana cikin wa yan da aka gaiytata su tafi taron.
Shiru nayi sai jin zuciyana kawai nayi ba dadi ban san har hakan ya fito a fuskana ba saida naji yana fadin baki son in tafi ke nan don engine din ko?
Ban fahinci may yake nufi ba da gakan cikin mamaki na dago kaina nake tambayan shi engine kuma ?
Yace eh mana ko karya nake yanzun ba kullun kike bukatan service ba na fahinci may yake nufi yanzu don haka najuya baya ina fadin wallahi, ni kan Allah ya kiyayye min abinda ake min a dole zaka wani ce can wai na saba ko nafiso indon tani ce wallahi mu zauna a hakana mana aga wanda zai sha wahala cikin mu.
Jinayi ya rugumoni ta baya yana fadin anki a zauna hakan sallon kijewa maman ki da kuka kice anki yi maki service kwana biyu kuma.
Allah dai ya kiyayye min wallahi kai wanan ya dama ni bai a gabana wallahi yace to tsaya mugani idan bai gaban ki da gaske din.
Gudu naje yi amma na makara nan ya samu sa,a na ya shiga aika min da sallon sakon shi.
A cikin mamakina sai gashi na zake nima yau ina mayar mashi da martani yadda yake bukata.
Mun dauki tsawon lokaci a dakin muna abu guda har sai da magariba ya kusanto sosai ya sarara min.
Rugomo ni yayi zuwa jikin shi tare da dan sinsinan wuya na yana fadin zan dauki tsawon lokaci a wanan tafiyan da zan yi don haka ki kula min da kan ki please .
Lumshe idanuwa na nayi ina sai dai a fili cewa nayi Allah ya kai lafiya ya bada sa,an tafiya.
Mun dauki lokaci ba wanda ya iya yi wa dan uwa magana a cikin mu sai can yadan min peck goshina naga ya mike ya fita daga dakin.
Maimakon na tashi daga kwancin ga lokacin sallah yayi amma sai kawai na lumshe idanuwa wani zurfafan tunane na shiga yi na yadda zan zauna kwana biyu bashi a gidan.
Irin yadda muka dan saba da juna a yanzu dashi.
Da kyat na iya mikewa na shiga bathroom don nai wanka nai sallah don har lokaci ya shige gashi takwasa zai tafi.
Ina idar da sallah namike da sauri na nufi dakin shi na samay shi tsaye yana gyara aninin gaban rigar shi.
Jin nashigo yasa shi dan juyowa gare ni cikin sakin fuska yau yake ce min ai na zata bazaki iya tasowo bane.
Karasowa nayi nake ce mashi mai za,a shirya mane wai?
Kinga ina tafiya da shirgine ni acan ina da kayan da nake amfani dasu ba sai na tafi da wani abuba daga nan.
Miko min yar hand bag dina na rataya kawai natafi don bashar yace min gashi ya taso zuwa kaini airport.
Na duka zan dauki jakar naji yana fadin wanan karon ma da Amira ke nan zaku zauna ko?
Murmushi yake nayi na karaso gaban shi nace duk yadda kace haka za,ayi yace ok zan fadawa maji ta turo ta idan nafita.
Ki dai dinga cin abinci ko zaki kara cikowa kafin na dawo nace idan haka bai maka ba sai ka karani mana.
Murde bakina yayi yana fadin wanan bakin wai yaushe ne zai mutu da bakar magana ne bari dai Allah ya dawo dani lafiya nasan maganin ki ai.
A tare muka fito falo dashi sai ga yaya Bashar ya shigo gidan nan muka gaisa dashi yana tambayana yaya kwana biyu.
Dago kai yaya sadauki yayi yace min tau ni zan tafi ke nan sai na dawo Allah yakai lafiya Allah ya sa ai nasara ga abinda akaje nema Allah ya tsare muna kai ya dawo muna da kai lafiya.
Yaji dadi matuka da addu,ana yake ce amin nagode bashar yace bakani dadin auren ba riba biyu mama tai maka ga kuma Fatima na sharto maka addua haka.
Dan bugo yakai ma bashar daga haka suka fita daga gidan ina tsaye rakube daga kofan shigowa falon mu.
Sai da naga subar haraban gidan najuya na shigo gida zuciyana a cunkushe min, fadawa nayi a saman kujera na dade zaune a guri, ina ta faman tunane kala kala ni kadai can dai ganin dare ya soma namike tare da rufo kofan gidan don ban tsan mani anty Amira zata shigo ba har wanan lokacin.
Ina shiga daki naji wayan na yana ringin da sauri na isa gurin, da wayan take shi ya kirani na dauka a kasalance ina fadin Assalamu Alaikum.
Yace wa alaikis sallam baki barci bane Fatima nace yanzun dai nake shirin yi.
To may ya hanaki yin barcin har wanan lokaci sai nace a raina kaine mana ka hanani a fili kuma sai naji yace nine ko?
Nace ni karatu na tsaya yi kawai shine ba makara don ina test da zamuyi satin nan insha Allahu
Murmushi yayi yace to ki kwanta hakana ki huta don nasan kina da gajiya a tare dake.

****** ********* ******
Ya sauka lafiya don yana isa Abuja da safe suka daga sai Mexico gurin taron su.
Yakira wayana kafin su tafi tana kashe ina cikin class ban samu magana da shi ba.
Yinin daya da sadauki yayi batare da Fatima haka yayi shi a cikin tunanen ta.
Sai a lokacin yake sanin cewa akwai wani babbban alamari a zaman ta kusa dashi ji yake tankar itace jagoran duk wani farin cikin rayuwan shi a halin yanzu.
Bai samu lokacin kiran ta ba,sai da ya dawo masaukin shi a lokacin dare yayi a can.
Yana kwance dakin shi saman gado tunane Fatima kawai ke cikin zuciyar shi har zuwa wanan lokacin.
A nan ya fara tina abubuwan da sukai ta faruwa a tsakanin su abaya.
Irin yadda yake yawan mata tsanani da hattaran ta cikin gidan su yana daukan ta a matsayin itace mai mashi gulma a gurin maji.
Sai yanzun ne yake gane cewa bata fadawa maji komai a gamay dashi sai dai nata kokarin da takeyi gurin ganin cewa ta saka mai ido ya daina shaye shayen daya ke yi kawai.
Wani irin bacin rai ne yaji sai yanzu yake gane cewa ashe son shi takeyi da,alheri take hakan gare shi.
Yana jin ciwon irin abin da yai ta aikatawa yar mutane a baya a bisa gaskiyan ta.
Haka yasa yamike ya fara dan zagaye dakin a hankali yana zargin kanshi da aikata abinda ba daidai ba akan Fatima din.
Lalai dole ne ya gyara tsakanin shi da Fatima yadda zata fahince shi ta yadda zata daina mai kallon mugun da take mai koda yaushe.
Yace in har bai gyara tsajanin su ba baiyi wa kan su adalci ba don haka zasu dinga zama suna samun matsala a tsakanin su ko yaushe.
Gurin tagan dakin ya koma tare da budewa yana shakan fresh ai dake fitowa daga window.
Ya daga wayan shi da ke a hannun shi ya kira nomban Fatima bugon farko da,wayan yayi sai da yaji wani iri a zuciyan shi .
Ina hanya zan dawo gida naji wayana na ringing, hakali na dauka na duba yaya sadauki ne a layin.
A hankali cikin wani murya bayan nayi receive din call din nace hello yaya.
Ya dan rikice da jin muryana yana cewa Fatima kina inane haka naji dan hayaniya.
Nan dan ajiyan zuciya sai nace ina hanyane yaya nafito school zan

Please Login or Register in order to submit comment